enene na zaro idon aiki kala nawa ne
ya halatta ga diya mace?" Yusuf ya aje hularsa a jikin gado ya je
ya zauna kusa da ita ya ce "Don Allah Kubra idan har da gaske ki
ke to ki fasa ki rufa min asiri da bacin ran Yaya Amina don ba za
ta so aje aikin ki ba." Hadiza tace "Bacin ran ta za mu duba koko
haduwa ta da Ubangiji? Ka ma daina wannan maganar, ilmi dai
na yi don tspron lalura amma aiki na hakura da dai na zabi fannin
da ya dace ne to." Yusuf yasa hannú ya dafe kai ya dago ya dube
ta yace, "Kubra ban amince ba, ki tuna fa duk wahalad ilmin ki
babu wanda ya sani sai Yaya Amina da `yan uwan mijinta, dama
- dama idan da Baba Kado da ni mu ka sha dawainiyar ilminki sai
na amince, amma yanzu kullun ina kokarin na ga mun shirya da
Yaya Amina sai kuma ta ji ance kin aje aiki dole zata kara tsanata."
Hadiza ta sha mur tace "Kana nufin ta nemar min ilmi ne don na
nemar mata kudi koko?" Ya dube ta nan da nan ya razana don ya
ga irin kallon da baya so idan ranta ya baci ya gyara zama yace
"Look Kubra ki fahince ni mana wane irin zance kuma ki ke......
74
" Tace, "To na fahinta kai ma ka fahince ni. Zan bar aiki don
tsakanina da Mahaliccinmu ka gane?" Ya dan dube ta har yanzu
bata daina irin kallon da bai so ba sai ya ce "To na ji amma don
Allah ki ban lokací zan yi tunani ko mi kenan zan sanar da ke." Ya
yi haka ne domin baí son abinda zai kawo rudani tsakaninsa da
Kubra saboda ya lura ta fusata, shi kuma ba wai yana son aikin
nata bane dole sai dai yana tsoron Yaya Amina.
Bayan sallar isha'e da Yusuf ya dawo masallaci ya tsaya
jikin wata itaciya a harabar gídansa yana tunanin matakin dauka
yadda ba zai batawa Yaya Amina ba kuma ba zai cutar da Hadiza
ba. A karshe ya yanke shawarar da ya ke ganin ta dace. Ya iske
Kubra kwance bisa gado ya isa gare ta ya zauna a bakin godo,
ya yi tagumi da hannaye bibbiyu ya kira sunanta 'Kubra' ta amsa
'Na'am' yace "Zai yi kyau ki shirya ki je gida can Malunfashi
wajen Yaya Amina ki nemi shawararta kaman yadda ki ka nemi
tawa ko?" Ta dan runtse ido tabbas itama tana shakkan tunkarar
Yaya da wannan magana, sai tace, "Amma tare za mu ko?" Shi
ma gabansa ya fadi ras domin irin yadda Yayar ke nuna masa
abun ya fara baci, a kwanan baya za su Katsina daurin aure sun
biya gayas da ita shi da abokinsa da kyar ta amsa, da zai tashi ya
aje mata dubu biyar, amma abin mamaki yana shiga mota ta
aiko karamin danta ya aje mai kudin a cikin motarsa, wannan
abu ya yi ma Yusuf ciwo domin ko darajar abokinsa bai sa Yaya
ta raga mai ba.
Ya ja dogon ajiyar zuciya yace, "To Kubra idan dai kina na
raka ki zan raka ki, amma zan ba ku hili ku yi shawara wallahi
tsoron Yaya nake." Tace, "menene abun tsoro game da maganar
lahira, ni dai idan ba ka zuwa ni ma ba za ni ba." Ya jingina jikinsa
zuwa jikin Hadiza ya lumshe ido ya shiga tunanin yadda za su
wanye da Yaya Amina.
Ranar asabat da azuhur suka isa gidan Yaya Amina, sun yi
sa'a Yayan na daki tare da wata tsohuwa Gwoggon Yayarce,
don haka sun sami kyakkyawar marba wajen Gwoggon da ta
zan kaka ce ga Hadiza, ta rinka yi ma Yusuf wasa na maigida.
75
a
Bayan sun jima cikin barkwanci Yusuf ya dubi Hadiza yacе,
"Zan koma dakin Saminu na jira ki." Sai Yaya Amina tace "Tafiyar
me za ka yi, itama ta tashi ku tafi mana." Gwoggo ta juya
fusace tace. "ke Amina ya kamata ki sakar ma yaran nan mara,
ina dalilin irun wannan riko? Ko wannan rabon ai ya dace ace kin
janye hushin ki." Amina ta kawad da fuska gefe daya cikin nuna
jin zafi tace "Ni ban ce ina hushi da su ba Gwaggo, harkarsu се
dai babu ruwa na." Yusuf dai ya mike ya yi waje.
Hadiza ta karkace kai ta ce, "Yanzu ma matsawa ya yi
wai sai na kawo ma Yayan shawara don na ce masa ni, fa zan aje
aiki." Yaya Amina ta galla mata harara tace, "zancen wofi ina
kuma ruwa na da aje aikinki? Ke daman yanzu kina da wani aiki
ko sha'awa wanda ya zarce nashi? Ai bukatarki ta biya kin fake
da karatu sannan aiki kina zaman jiransa to kin same shi me
kuma zaki ci da aiki?" Nan da nan hawaye tar daga idanun Hadiza
tace, "Wallahi Yaya ba haka ba ne, matsalar aikin namu ne, ba ta
matar aure ba ne---". Gwoggo tace, "Ke Dije kuna dai zaman
lafiya da mijinki ko?" Hadiza tana share hawaye tace, "E
gwoggo. Tace "To ki aje aikinki ki bi mijinki sau da kafa, Amina
ko ki bar ni da ita kada ki kara kawo mata irin wannan shawarar."
Da suka tashi tafiya Yusuf'ya kawo kudi kamar yadda ya
saba ya baiwa Yaya Amina itama Gwoggo aka bata na ta rabon
mai tsoka.
Kamar Gwoggo Halima ta san da zuwansu dan lokaci
kankani ta shirya masu abinci iri iri, Hadiza ta yi rashe-rashe a
dakin Gwoggon tana ta zuba shagwaba, kai ka ce Gwoggo tà
kawo ta duniya, ita ko Gwoggo Halima sai kara rawan jiki take
yı ganin ciki dai ya bayyana fili jikin Hadiza.
Yusuf vace, "Gwoggo ina son ku je Abuja ku zauna ke da
Inna Tambai nan da sati biyu saboda zan yi tafiya London." Gwoggo
tace, "To Allah Ya nuna mana; a dai dai nan Malan Tukur ya
shigo, bayan an jima da gaisawa Halima t