ta yi mai murmushi tace, "Na fi son
miyan shuwaka."
Yusuf bai yi odar na shi abincin ba sai da ya ga
majinyaciyarsa ta dan ci abin kirki sannan ya yi odar dankali da
koda da kwai da shayi ya dan kakkafe ido yana zolayar Kubra
yace "Kubra a zo a taya ni mana kada ki manta ni ma fa na sa
ma naki abincin albarka." Hadiza ta rausaya kai tace, "Haba D,
so kake na yi amai ko?" Yace "Sai na tara maki hula ta ki yi a
ciki." Tace "Baka jiye min wahala kenan?" Yace, To me kike so
na sai maki yanzu?" Ta dube shi ido cikin ido tace "lemo tanjirin
da goro." Ya yi dariya yace, "Oh ni dan Yusufulle Allah Yasa dai
cin goron ba mai dorewa ba ne domin bana son wa'annan
kyawawan hakoran su yi ja."
Ciki dai sai da ya shiga wata hudu sannan Hadiza ta koma
hayyacinta har ta fara jin dadin amarci. Sau biyu Inna Tambai da
Gwoggo Halima Basiru na kawo su har Abuja suna gayas da
Hadiza. Ba wai gidan Yusuf ba kadai hatta 'yan aikin gidan
Gwoggo Halima kamar ta hade su don so da kauna. Albarkacin
Yusuf, babu jin dadinta irin yau ga ta a gidan Yusuf na Abuja tare
da matar da suke so kuma har da juna biyu; ko tari Hadiza ta yi
sai Gwoggo Halima ta ji har cikin ranta, wannan irin son ya rinka
dawo ma da Hadiza tunanin mahaifinta, ina ma yana da rai ta
auri Yusuf? Amma anya ko Yaya Amina na son ta domin ko da ta
ji labarin rashin lafiyar Hadiza na juna biyu ne babu abinda ta yi
illa tsaki da kin yadda ayi maganar.
To wajen aikin Hadiza ma dai har yanzu tana bisa aikinta
tun tarewanta Abuja takardan taransufa dinta ta iso a daidai
lokacin da ta sami wata biyu gidan Yusuf haka dai ta rinka zuwa
aikin cikin ciwo ga wani masifan kyau da tayi saboda haka sai ta
rinka ganin kamar duk mazan da ke shiga bankinsu ita kadai
suke kallo, wannan abu ya dami Hadiza don haka sai ta yanko
yadi kala-kala ta baiwa Falanke ya dinka mata manya-manya
72
hijabai ta rinka zubawa idan zata aiki amma duk wannan bai
janye wasu kwazababbun mazan ba da yawaita kallonsu a
fuskarta ko kuma kyawawan yatsunta.
Yauı wata bakwai kenan da auırensu kuma watannin cikinta.
da yamma tana kwance bisa cinyar Yusuf hannun Yusuf na bisa
kan Hadiza yana warware mata kitso, yayin da idanun Hadizan
ke lumshe tunani ya rinka karakain a a zuciyarta, ita dai kawai ta
san ta yi sa'ar miji domin irin dawainiyar da yake yi akan ta itta ta
san bata tba shi wadatattar kulawa saboda yanayin aikinta, sau
tari bata dawowa daga aiki saigab da mangariba kullun shi Yusuf
aka fi samu a gida yana aiwatar da abinda ita ya dace ace tana
yi sannan kuma bai nuna damuwarsa haka nan ita gaba da ya a
tsarin rayıuwarta sai take ganin aikin banki bai dace da ita ba in
dai tana son gyara lahirarta. Waya ta yi kara ta katse tunanin
Hadiza, Yusuf ne ya mikar da hannunsa ya dauki wayar, Hadizan
Jos ce bisa layi tace, "kwana hudu Yusuf ba zuwa babu waya,
ka san dai don ta Hadiza ba za a yi zumunci ba daman kai ne mai
kwaranniyar gidan na ku." Yusuf ya yi dariya yace "Gaskiya ne
Hadiza kwarai ko na kwna biyu ban kira ki ba abubuwan ne sun
mani yawa, ga kula da Kubra sannan ga lura da shi ainihin bebin
domin yana matsawa Kubra da rigima sai idan ina kusa ina taya
ta hidima da shi." Hadizan Jos ta kyalkyale da dariya tace "Da
alama za' a haifo mai rigima inn ka."
Hadiza ta mike zaune ta ams he wayar daga hannun Yusuf
tace "To ina jin irin sharrin da ake man har jaririn da ke ciki ba ku
raga masa ba ko?"
Sun jima ana wasanni irin na aminan junan daga bisani
Yusuf ya roki arziki da cewa 'yar JJos ta shirya ta raka su sayesayen jariri gobe. Aka aje wayar da wannan alkawarin.
A vvata alhamis rannan Hadiza ta yi sa'a ta dawo aiki da
wuri kamar kowanne ma'aikaci, bayan ta idas da sallar la'asar
sai ta fiddo akwatuna har uku na kayan jariri tana gyarawa tare
da kiyasta kudinsu a zuci yanzu dai cikinta wata takwas hatta
kayan da zata saka ran suna D din ta ya kammala ko hankicin da
73
zata yi anfani da shi ba wai bebin ba sai da ya tabbata ya saya.
Hadiza ta yi jigun tana tunani to wai ita ina anfanin aikin
da take yi? Na farko dai bata baiwa Yusuf kyakkyawar kulawa
sannan ga shiga fitinar maza kullun, kuma ko sisi baya bari ta
kashe cikin albashinta ya dauke mata nauyin komi, shin wai me
zai sa baza ta hakura da wannan aikin bankin ba ta rungume
Yusuf da kyautar da Allah ke shirin ba su?
'Salamu Alaikum' Yusuf ne ya turo kofar dakin Kubra ya
shiga ya cimmata zaune dirshan bisa kafet ta yi daidai da kayan
jaririnsu ta waiwaya ta amsa masa yace, "Na kwalla kira Kubra
kamar sau uku amma na ji ki shiru, duk shirye - shiryen haihuwar
ne, ai ni ba ki sani ba Shugabana zai takura min kwarai ainin, wai
London za mu ni da shi nan da sati biyu." Ta dube shi tace, "Shi
ne me D, kai za kai min haihuwar? Don Allah kada ka damu kuyi
tafiyarku, inda duk ka ke addu` a ce taka, ni ba ka san ma abinda
ke damuna ba wallahi ni fa so na ke na aje aikin nan." Yusuf ya
fiddə ido yace "Me ke damun ki ne Kubra? Ki aje aiki fa ki ka
ce!" Ta yi dariya tace, "To m