aman ya tsaya na ruwa, domin ruwa da shayi ne kawai a cikinta. Nan da nan kwalla ta kawo ma idon Yusuf a
yanayin da ya riske Kubra, ya zauna a firgice cikę da zullumi ko zai rasa Kubra ne? Ya ciccibo kirjinta gaba daya va rungumeta bisa cinyoyinsa muryarsa ta kasa tsayawa daidai, ya daure cikin rudanin murya yace "Kubra me ke faruwa da ke?" Tayi layau da hannunta ya yin da ya cafe hannun ya dora kan kirjinsa sai ya ji hannuwan sanyi karara, cikin murya ta rashin lafiya tace "Wayyo Allah D kai na, tun bayan tafiyarka na fara ciwon kai sai zazzabi,
to shine nace ma Basiru ya samo min fanadol mai kyau amma sai
ya zo da abokinsa su kai mani allura. Da farko na ji dadin allurar
domin na sami bacci amman tunda na farka ban yi zaton zan vi kwanan duniya ba."
Yusuf ya kara shiga wanin rudanin har bai san kome kuma
69
zai yi ba yace "Kubra shirya mu je asibitin Funtua." Tace "D bana
iya zama ka jure ka hakura har zuwa gobe mu koma Abuja a
duba ni a can."
Ya kwantar da ita yace "Ina zuwa". Ya cimma Falanke
yace, "ya ba ku tayas da injin ba?" Falanke ya ce, "Mun duba
ashe babu mai ne a ciki, ya jikin Hadiza?" Yusuf yace "To ni kam
sai kuma abinda Allah ya yi domin idan ma da ciwon da jahilcin
wannan bakauyen yaron Basiru, wai dubi sokonci daga ta nemi
fanadol ya debo wani wawan abokinsa ya zuba mata allura, babu
nazari balle bincike." Falanke ya bude baki yace "Me ya sami
Basiru da inin wannan kankanbar?" Yusuf ya ce "Oho! Raini mana,
don Allah ga kudi aje a sawo man injin. Falanke daga nan ka biya
ka zo min da Basiru." Ko da falanke ya dawo sai da su ka yi
kiciniyar tayas da injin haske ya sawwaka a gidan sannan Yusuf
ya zarewa Basiru jan ido yace, "Basiru a bisa wacce hujja za ka
debo wani wawan abokinka ayi ma Kubra allura?" Basiru ya shiga
yarfar da hannuwa yana yan kame kame ya ce, "Haba yaya ka
ko ga yanayin jikin Hajiya Hadiza a lokacin, ya zame min dole na
nemo taimakon gaggawa ganin ba ka nan." Yusúf ya galla mai
harara ya ja tsaki yace "To ga ta can kwance rai hannun Allah
idan har ta mutu kai ne sanadi kuma kada ka yi zaton zan taba
yafe ma, tabbas ka ja an yi mata alluran da suka gama aiki."
Basiru ya yi rau-rau alamun kuka, ya yi kokari ya baiwa
Yusuf hakuri amma kalaman su ka ki fita hankalinsa gaba daya
ya jagule. Sai su Falanke da Yusuf ke kai da kamowa akan Hadiza.
Hadiza ta sami bacci amma Yusuf zaune ya kwana yana
rungume da Hadiza, in ta motsa ya juya ta yana yi mata 'sannu
har karfe shidda na safe ya sa ruwa da tawul ya goge mata jiki
tsab kamar ta yi wanka. Yusuf da kan shi ya fiddo kwalayen da
suka yo ma kannan Hadiza saye-sayen komawa makaranta ya
mika masu tare da makuden kudade yace su biya kudin
makaranta. Sannan yace idan gari ya yi haske su koma gida
amma su shaidawa Inna Tambai Kubra ce babu lafiya shiyasa ba
za su tsaya ba sun koma Abuja don ta ga likita.
70
Karfe shidda da minti goma sha shidda na safen ya tsaya
da mota kofar gidan Gwoggo Halima ya yi mata sallama yace
sun shige Abuja domin kwana ya yi akanı Kubra jiki dai ya ki dadi.
Ta yi masu kyakkyawar addua.
Suna isowa Zariaya sai idon Yusuf ya kyallo wani
shahararran asibiti mai suna Mayfair Cliniic. Ya juya ya ce "Falanke
yi ribas mu shiga asibitin nan, a zamanin da na ke karatu anan na
san labarin asibitin akwai wata mata jair fata mai suna Dr Banu
kamar aljana tai ke don sani, bari mu shiga ta duba min Kubra."
Bayan nas ta amshe su an bude masu kati an auna nauyin
Kubra an auna yadda B.P din ta yake sannan ta rubuta dukkan
rufotonta a katin. Nas ta shaida masu ga likitan da za su gani.
Yusuf yace, shi Dr Banu ya ke son gani, tace yau lahadi tana
gida. Yusuf ya nemi kwatancen gida akia yi masu.
Cikin sa' a Dr Banu ta duba Hadiza a gidanta, a kalla sai da
su Yusuf suka kwashe awa biyu a gidan [Dr Banu tana diba Hadiza
da yi mata abunda ya dace, cikin ikon Allah ciwon kai ya sauka,
sai rashin jin dadin jikinta da kwabewar ibaki, bakinta ya yi takab
kamar wadda ta yi watanni tana ciwo. Daga karshe Dr Banu ta
shaidawa Yusuf kada a kara yi ma Hadiza allura ko shan magani
sai da izinin likita domin tana da shigar ciki na sati uku.
Yusuf yayi jagwale ya rinka jin kamar ya koma Bakori ya
shake Basiru, wai cikin da ya ke addu'a tun kafin ya mallaki
Kubra shi ne a lokaci guda Basiru ya nemi halakawa don tsabar
kauyanci da sokonci. Amma dai abu daya ya karfafawa Yusuf
zuciya har ya manta da tsanar Basiru shi ne bayan sun fito daga
gidan likita Falanke ya mike hanya santal sai Hadiza ta rausayar
da sanbala sanbalan hannayenta a bisa Yusuf yayin da shi kuma
duk ya tattaro hankalinsa ya dora akanta yana hanzarin son ya ji
abin da zata fada. Tace a hankali "D bakina babu dadi amma da
zan samu sakwara miyan ganye da na ci." Nan da nan murna da
zumudi suka kama Yusuf tabbas sauki ya samu, ya umurci Falanke
da su biya Shagalinku. Anan ma an yi sa'a domin sai da gidan cin
abinci na Shagalinku suka lissafa masu suna da miyar ganye kala
71
uku, Yusuf ya dubi Hadiza sai