ika masu
kicin da na'urori na girke girke, ya rinka mamakin a ina Hadiza ta
sawo wa` annan na` urori masu tsadar tsiya? Ya yi murmushi ya
61
ce lalle Hadiza na shirin sangartashi, ya dauko faranti ya koma
dakin Hadiza, ya zauna a gabanta dirshan ya fid do zabuwa ta yi
narai-narai da maiko, an kuma shafe ta da magi mai tauraro da
atarugu da albasa. Yusuf ya yago cinya ya ce, `Kubra'. Ta dago
kai a hankali ta yi mai wani irin kallo wanda ya zarce wanda ta
taba yi masa a wancan zamanin da suka yi irin wannan magana,
tsigar jikinsa ta tashi yar, ya lumshe ido sannan ya dan bude ya
ce "Kubra, Allah! Allah!! Yasa ki haifa min`yan mata shidda
masu irin idonki su rika kallona kamar yadda kike kallo na." Ta
tumshe ido.
Ya mika mata cinya ta kai bakinta tana ci, ya ce, "Amma
kin ba ni mamaki yanzu nan kin nuna min bacin ranki tamkar
nayi laihi yanzu kuma na ga kin huce." Ta ce, "Haba Yaya ai dole
ne na yi ma haka, a zatona ka manta da wannan alkawarin wanda
yana daya daga cikin abinda ya gina kaunata da kai haka nan
yana daya daga cikin abinda ya sa na tsane ka, domin ina
mamakin wanda zai fada wa diya mace wa`annan kalamai
sannan ya dawo ya ce bai son ta."
Ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Har yanzu inan nan a yaya? Ni
ma ai an yi min alkawarin raba ni da suna Yaya ko?"
Ta dan rusunar da kwayan idanunta ta ce, "Idan na kira
ka da D ya isa?" Ya ji wani irin dadi ya rastsa shi ya ce, "Me ke
nan kike nufi?" Ta ce, "Ina nufin Darlin ko?" Ya sake tsinkewa
don dadi yace, "Me zai hana ki ce Darling din gaba daya?" Tace,
"Yanzu a gabansu Gwoggo da su Basiru da irin su Sha'aibu ba
zan ji nauyi ba? Amma ko idan na ce D kamar su Gwoggo ba za
su gane ko me nake nufi ba." Yace, "Na gamsu, na gode, ni ba za
ki samman zabuwar taki ba?" Sai ta dan zolaye shi tace "Ta
Kubra ce fa mara fasali". Haba nan da nan ta jagula masa lissafi,
amma sai ya dake ya maida shegantaka yace, "Haba ba dai Kubra
dina ba, kine zancen wata yarinya ce Dije" Sai ta dan yi murmushi
tace "Oho dai ai yan karin magana sunce kowa ya raina tsayiwar
wata ya hau ya gyara idan zai iya." Yace, "Haka ne, ko da can
rashin wayau ne ya hanani gyarawa, amma yanzu zan kara mikar
62
da komi ba ki ji abinda Inna Tambai tace ba ne? Cewa ta yi namiji
shi ke mikar da mace......."
Yusuf ya kammala shirnsa tsab Hadiza na tsaye rike da
agogansa, fuskarsa a murtuke tana nuna alamun bacin rai da
damuwa Hadiza ta ce, "D kawo hannunka na daura maka
agogonka, wai me kuma aka yi ma ne sai huci kake? Ya mika
mata hannu yayin da ya zuba ma fuskarta ido, yace "Na yi maki
tambaya, saboda Allah Kubra yau kwana nawa da bikinmu?" Ta
ce, "Yau kwana shidda wani abu?" Ya ce "Abunda ke bata min
rai shi ne wa'annan matan masu isar mu da zuwa wai ganin
daki, sun hana mu sakat mu kwanta mu huta wannan wacce irin
aladace! Da sassafe karfe takwas zasu tayas da mu har mu
kwanta bacci gidan nan ba a kara barin mu sakat haba ina dalili,
mutun ba za a bar shi ya huta ba?" Hadiza ta yi dariya tace "Ga
wasu mattan ma can falo suna zaman jiranka tun kana wanka
suka zo, ina zaton a bayaninsu daga kauyensu Gwoggo su ke."
Yusuf ya girgiza kai yace, "Bana iya zama har hutun wata daya
a garinnan ki shirya abinda kike so wa'anda za ki yi anfani da su gobe insha Allah za mu koma Abuja."
Da yamma Yusuf na gaba Hadiza na bayansa suka shiga gidan Gwoggo Halima, kai ka ce Gwogo Halima bata taba ganin
danta Yusuf ba da Hadiza sai a wannan rana, sun birgeta sun bata sha'awa haka nan sun tsuma mata zuciya domin sun yi
matukar dacewa da junansa ko wanne sai kwarjini da kuriciya
ke bayyana daga gare shi. Murna da jin dadi suka hana Gwoggo Halima kulle bakinta.
Bayan an kammala gaishe gaishe da ban gajiyar biki Yusuf
yace, "Gwoggo gobe da sassafe Falanke zai tafi Abuja da motar
kayanmu, yayin da ni da Kubra za mu tafi da azuhur." Gwoggo
Halima ta sha bula tace, "Ni fa ba na son sokonci ca na ke hutun
naku wata daya ne shi ne za ku gudu tun jama'a ba su gama
ganin daki ba." Yusuf yace "Ai kin ji matsalata wa'annan mutanen
da ke hana mu kwanciya mu huta, su za su kore mu."
Gwoggo Halima ta dubi Hadiza tace, "Ke Hajiya Hadiza
60
kin amince da hakan?" Hadiza ta yi dariya tace, "To Gwoggo
yadda yace yana so ai haka za'a yi ko?" Gwoggo Halima ta dan
harare su tace, "A to ke ke daure masa gindi Hadiza." Hadiza ta
kyalkyale da dariva ta ce, "Allah Gwoggo babu ruwana." Gwoggo
ta ce "idan haka ne, shi ya tafi ke ya bar ki anan jama'a su gama
ganin dakin amarya." Yusuf ya yi zanbur yace, "Haba Gwoggo
ai itace shugaban tafiyar". Gwoggo ta dalla mai harara ta ce
"To shugaban yan rashin kunya ban yi da kai ba."
Da suka gama hira sun tashi tafiya Gwoggo Halima tace
"Babu abinda za'ai maku wanda za ku tafi da shi?" Hadiza tace,
"A yi mana hura Gwoggo." Sai Gwoggo tace, "Insha Allah za'ayi
idan kun je wajen Tambaya ku ce ina gaishe ta ina sauraronta
jibin don mu je Malunfashin."
Yusuf da Hadiza sun sami yadda su ke mafarkin son rayuwar
ta kasance komi ya yi masu a