kwana sun yini ana zirga-zirga a Kaduna kafin su gama
abubuwan da suka kai su, don haka sai cikin dare suka isa Bakori.
KASHI NA GOMA SHA BIYAR
Da karfe biyu na rana Baba lliyasu ya daura auren Yusuf
da Hadiza, an gabatar da addu'a ta musamman ga marigayi Alhaji
Kado daurin aure da 'yar kwarya-kwaryar walima ta kayatar,
duk dawainiyan abinci na gidansu da na gidan Inna Tambai Yusuf
ya yi komi domin ya san dai karshe Hadizan ce za ta yi.
Baba Rilwan, Baba Garba da Baba Malan Isa zuwa kannen
Hadiza su Saminu sun halarci daurin auren, haka nan matar Baba
Garba da Mama Binta da Hadizan Jos su kadai za mu iya cewa
sun halarci bikin a bangaren dangin yaya Amina mata.
A ranar da biki zai tashi tun da safe Yusuf ya sa Falanke
ya sawo mai zabbi guda biyu yace ya a adana su can a gidansa
wato Falanken.
A can ma Kano an daura auren Amiru da Salma a daidai
lokacin da ake daura na su Yusuf. Karfe goma sha daya na dare
Yusuf ya dubi Falanke kowannensu a gajiye likis, yace "Falanke
na gode, Allah va bar mu tare, amma kafin ka tafi gida ka kwanta,
nima ba zan shiga wajen amarya ba sai ka yi min wani aiki daya."
Falanke da kyar yake daga ido don tsabar gajiya yace,
59
"Me ya kuma rage Yallabai?" Yusuf yace, "Ina son ka je ka dauki
zabuwa daya ka kai ma Talle mai tsire ya gashe min ita yanzu ka
kawo min, ita kuma daya zabuwar ka mikawa Gwoggo kace ta
soyo ta gobe da safe ta aiko min."
Falanke yace "Tirkasahi! Wannan aikin amarya ne ko? To
amma ka san kila su Gwoggo yanzu gajiyar biki tasa sun kwanta
ba ka bari da safe na kai mata?"
Yusuf yace, "To yi sauri ka cimma Talle mai tsire ya gaso
dayar."
Falanke ya dawo karfe daya saura 'yan mintoci na dare
yana magana a gajiye yace, "Yallabai ga zabuwa an yi sa'a yarinya
ce zabuwar mai maiko, a sha amarci lafiya. Ubangiji ya bada
raboa daren yau, amma fa a sa mai suna Shu'aibu." Yusuf ya yi
dariya yace, "Kai ka yarda a fara sa sunanka, bayan ga sunan
Baba Kado." Falanke yace, "Tuba na ke Yallabai kai na bisa wuya,
Allah ya kawo mana takwaran Baba Abdulkadir, mu kwana
lafiya."
Yusuf ya shigar da mota garejin gidansa, sannan ya yi
wata addu'a wadda Mallan Tukur ya ba shi. Ya shiga falonsa
kamar ya doshi dakin Hadiza amma ya kanne ya nufi na shi dakin,
ya sunce kaya ya fada kewaya ya yi wanka tare da alwala sannan
ya fito ya dauko maganinsa na ciwon jiki ya kora ya saka kayan
baci ya dauki turaren da Hadiza tace, tana so ya nufi dakinta.
Abin mamaki karfe biyu ta yi amma sai ya rinka jin karatun
Alqurani na fitowa daga rediyon dakin Hadiza yace a ransa kada
dai ace Hadiza ba ai bacci ba?
Ya murda kofar a hankali ya shiga, ta yi dai dai bisa gado
a bisa dukkan alamu bacci mai nauyi ya dauke ta, ya nufi inda
rediyonta yake ya kashe ta yi firgigi ta tashi nan sai ta tsuke mai
fuska tace, "Don me zaka kashe min? Ni na riga na saba, kwana
na ke da karatun Ahmad Sulaiman domin rediyon mai juya kanta
ce." Yusuf ya dan firgita da yanayin fuskar ta yace, "Na yi zaton
ba ki sani bane." Ya tsaya shi bai zauna ba haka nan shi bai
kunna rediyon ba, amma Hadiza ta kara tsuke fuska fiye da
60
shigowarsa, ya cije yace, "Hadiza akwai bukatar mu gabatar da
nafila tashi ki yo alwala?" Sai da ta bata lokaci sannan ta je ta
yo alwalar, bayan sun idas da nafilar ya dade yana masu addu'a
a fili tana amsawa da "Amin".
Sai ya juyo da sauri ya kamo hannuwanta ya rike zai kai bisa kirginsa ta fisge ta mike ta koma can gefen gado ta tsaya
yace, "Me kuma ya faru?" Ta juyo ta dan harare shi ta kawad da
kai ya dauki turaren da ya shigo da shi ya je zai fesa mata tace "ba na so" cikin tsiwa.
Baya son rigimar ta yi tsami sai ya fita da niyyar ya je falo
ya yi tunani ko zai iya tunano abinda zai shawo kanta, amma sai
ya ci karo da gasassar zabuwar sa ya dauka ya juya ya koma dakin Hadiza don ya cika alkawarin da ya daukar mata. Yanzu tana zaunè bakin gado ta yi tagumi, ya tsaya a
gabanta ya langabe kai ya ce, "Ki dubi girman Allah ki saurareni
na gabatar da nauyin alkawari daga bisani kina iya ci gaba da
musguna mani, zan iya jurewa har Allah yasa ki daina." Ta daga kai tace, `Wai menene?' Ya tsugunna a gabanta da `yar leda à
hannu yace, "Akwai wani zamani idan ba za ki manta ba na yi alkawarin cewa ran da duk na gan ki a dakina, a rannan zan
kawo maki zabuwa wadda zan yi maki lakabin sunan da nake so
wato KUBRA, to Allah Ya yarda yau ga ki a gidana kuma kin ci
ma'anar sunan wato BABBA da larabci shine Kubra, a yau kin
zama babba a gidana, a zuciya ta, a cikin gidanmu ma keсе babba tunda kece matar babban yaya.
Hadiza ta yi wata irin`yar siririyar dariya `yan kananan
hakoranta masu daukar hankali suka bayyana a idon ango Yusuf
tace, "Allah da gaske ka ke, idan da gaske ne bude ledar na gani
idan zabuwar ce!" Yusuf bai san yadda zai bayyana farincikinsa
ba a wannan lokacin, sai ya dube ta ya ce, "Ina zuwa ki jira ni."
Ya mike ya nufi kicin don ya kawo faranti ya dora zabuwar a kai,
amma sai ya tsaya cak yana alajabin yadda Hadiza ta c