abu gajiya."
Sun yi shiru kowanne na sake-sake cikin ransa, har yanzu
dai Hadiza bata iya dubar Yusuf ba, shi din ma a kasa-kasa ya ke
kallonta duk maganar da zai furta mata yana zullumi don yana
tsoron kar ta birkice masa, don haka a dosáne yake, haka nan
itama Hadizan ta lura da cewa a firgicen ya ke, amma babu
abinda zata iya ce masa, illa dai kawai ta yi alkawari ba za ta
sake yi mai tsiya ba a dalilin maganganun da su ka yi da Mallan
56
Iliyasu ta tabbatas wa ranta duk duniya babu mai son mahaifinta
Baba Kado sai ita da Yusuf haka nan ta na alfaharin har ya mutu
yana kaunar Yusuf, don haka ya dace ta auri Yusuf a ko wane
mataki na fannin farantawa mahaifinta rai, kamar yadda Inna
Tambai kejaddada mata cewa 'Dije kin gamawa marigayi komi
tunda ki ka auri Yusuf a dalilin son da ke tsakanin mahaifinki da
shi Yusuf.'
Hadiza na son Amiru tana kaunar halayansa, taso kuma
kwarai ya zama mijin aurenta amma kuma soyayyarta da Yusuf
wata irin kaunace wadda ke cikin jininsu illa kawai bacin rai ya
haddasa tsana da kiyayya mai tsanani a tsakaninsu, wadda kuma
yanzu gatancin da Yusuf ya nuna wa marigayi Alhaji Kado
yasa Dije na jin nauyi da tausayin Yusuf, don haka ta yi alkawarin
shanye duk wani batanci da yayi mata, ko a da bai son ta tunda
yana son mahaifinta ya gama mata komi.
a
Yusuf ya katse zaman shiru yace, "Bari na tashi na tafi
kila na takura ki, kin sadda kai kin kasa sakewa." Sai Hadiza ta
daure ta dago kai a hankali ta dan dube shi kadan tace, "Na ce
ba, ko zai yiwu gobe ka ba Basiru mota ya kai ni Kaduna akwai
wasu kaya da nake son daukowa, kuma akwai zancen bayas da
katunan da ka aiko min."
Yusuf har ya so ya karyata kunnuwansa, shin da gaske ne
Hadiza ke mai wannan lafazin a hankali mai ratsa jiki, ko dai zolayarsa take? Yusuf cikin murmushi na rudani yace "Me zai
hana ya yiwu sai dai zan fi so ni na kai ki domin akwai bukatar
zuwanmu Kaduna ni da ke a dalilin taransufa na aikinki komawa
Abuja, haka nan akwai wani dinki da nake so mu je wajen telolinki
na Kaduna za mu kai na wani boyel les wanda za mu sa a daren
dina." Ta dube shi tace "Me zai sa ba za ka ba Shuaibu ba?" Yace
"Ai na bashi aikin hannu na wani farin boyel na ga ma har yanzu
bai gama mana ba." Hadiza tace, "Amma ina ganin zai fi kyau
mu tafi da zinaran nan Kaduna mu aje a banki ko?"
Yusuf ya kara matsawa kusa da Hadiza ya tabbatas Hadiza
ra'ayinsu daya sha'awarsu daya tunaninsu daya yace, "Wallahi
57
abinda nace ma Gwoggo kenan a ranar da za'a kawo kayan
amma ta hau ni da fada kin dai san halin Gwoggo komi tace an yi
rashin kunya."
Hadiza ta mike ta dauko kit suna kara dubawa, yana gaya
mata wanda ya saya a London tun wani zuwansu da Shugaba,
da wanda ya taba sawowa a umarar shekara biyu da ta wuce da
wa'anda ya saya farkon zuwansa aikin hajji, da wa'anda ya saya
a Indiya. Hadiza tace, lo Gwoggo kake ba ajiya?" Yace, "Wallahi
banki na ke aje abuna kin san mutanenmu ba su faye sanin daraiar
wa annan abubuwan ba".
Tun Inna Tambai na jin maganar Hadiza da Yusuf samasama har bacci ya kwasheta, yayin da Yusuf sai da yasa Dije ta
gwada duk sarkokin nan da zabba da abun hannu an yi sa'a abun
hannun mai sukuro ne, ana iya ragewa ko kara girmansu, a Madina
wata balarabiya 'yar kasai Jordan ta sa Yusuf ya saye su domin
yace bai san size din matar da zai aura ba.
Bai bar dakin Inna Tambai ba sai misalin karfe goma sha
biyu na dare. Falanke ya dade da bacci a mota ba don tausayin
Inna Tambai na kwance a waje ba kila Yusuf da sai an kira asuba
zai bar gidan, duk ilahirin kayan lehen nan kuwa babu wanda
basu yi daidai da shi ba. Shi da Hadiza suna dubawa, yana fada
mata yadda ya sayi kowanne. Ta dube shi tace, "Akwai irin
wannan turaren da ka shafa cikin kayan nan?" Ya dan lunshe ido
ya ce, "Kina son shi ne?" Tai mai murmushin da ya shekara bakwai
bai gani ba, ta ce, "Irin turaren da na fi so kenan domin bai
yamutsa hankali." Suka dubi juna suka yi dariya, yace, "Ba irin
sa anan amma na yi alkawarin aje maki nawa". Ta ce, "Lah ka
bar shi ka rinka shafa abinka". Ya ce "A'a idan kin zo mun rinka
shafawa tare."
Wanshekare karfe goma da rabi na safe ya iso shi da
Falanke don daukar Hadiza tafiya Kaduna. Ta fito ta cimma masa
yana tsaye gindin motarsa rike da wata 'yar karamar rediyo mai
kama tashoshin kasashen waje. Kwalliyarta irin ta kamamnun
musulmai ta kayatar da Yusut ainin ya kuma yi alfahari da ita
58
har zuci, ta dafa gefen mota ta dan rusuna ta gayas da shi.
Ya bude mata kofar gaba ta dube shi tace, "Ba da Sha aibu
za'a ba?" Yace, "Da shi za mu mana." Tace, "To ai shi ya fi dacewa
ya zauna a gaba ni na zauna a gidan baya." Suka dubi juna su kai
dariya shi da Falanke."
Ta koma gidan baya ta zauna Yusuf ya shiga, amma kafin
ya tayas da motar sai da ya dauki lokaci yana yin saitin madubin
gaba a daidai fuskar Hadiza, ta dago ta duba suka yi ido hudu ita
da Yusuf ta madubi, nan da nan su kai ma juna murmushi, Yusuf
ya saukar da wata sansanyar ajiyar zuciya.
Sun