shi yace, "Ga wannan a sai ma amarya dan
kunne sai mun zo daurin aure." Yusuf ya ce, "Ranka shi dade
wannan ai kace a sai ma `yan Bakori dan kunne ba amarya
kadai ba, Allah ya saka da alhairi." Jirgi ya sauke Yusuf a Kaduna
su Felanke na jiransa ya zuba akwatunan lehe sai gida Bakori.
Wanshekare dangin Gwoggo Halima suka shirya zuwa kai
lehe. Yusuf ya kashe ya tsare yana fadin don Allah Gwoggo idan
an je ace ma Inna Tambai ta ba Hadiza wannan dan karamin
akwatin ta adana domin duk zinari ne a ciki, idan ba zata iya
adanawa ba a dawo min da shi zan kai banki saboda taron
jama'a." Gwoggo Halima ta danna mai harara tace, "Wai kai
mevasa ba ka da kunya ne, lehen ma sai ka fadi yadda za`a yi?"
Bayan masu kai lehe sun nufi gidan Inna Tambai su Ankudi
da Sabura sune 'yan taryar baki. Duk da su Ankudi suke kauyawa
amma sun san darajar zinari don haka suka fara rade-radin ko ba
komi lehen Yusuf ya fi na Amiru tsada idan akai la'akari da
tsadaddun zinaran da ya zuba.
A daidai lokacin da ake shagalin amsar lehe, shi kuma
Yusuf da Falanke na can takure zauren Mallan lliya suna godiya
waien Mallan din, anan ne Mallan lliya yace, "To Yusufa aure
abu ne mai wuya ga wanda bai fahinci dokokin Allah ba amma
kuma abu ne mai sauki idan aka bi tsarin Sarki Allah, haka nan
wanda duk ya rungume sunnar Manzo bil hakki da gaskıya yana
tare da dukkan nasara duniya zuwa lahira. Ina so na gargade ka
anen Yusuf wato a yadda al amuran aurenku suka kasance kai
da Dije vanzu dole ne kai ka zama mata: ita zata zama mijin,
54
abun nufi anan a dalilinka ta shiga hali iri-iri wanda ya ja batawarta da mahaifiyarta bayan tsegunguman jama'a, to kaga anan yanzu
tana cikin radadin kunar zuci, dole ta tsinci kanta cikin tsanar ka
wanda zai jawo ta kasa kyautata maka, amma idan duk akai hakuri za ka amshi mulkinka a hankali."
Maganar Mallan Iliya ta shigi Yusuf sosai ya kuma
amincema ransa zai bi shawarar Mallan din. Bayan sun baro gidan
Mallan lliya Falanke yace, "Ya dace anjima mu je ka gayas da
Inna Tambai Malunfashi dai mallan lliya ya gargade mu kada mu
je yanzu sai can gaba in kura ta lafa." Yusuf ya shafa kansa
yace, "Wallahi Falanke ban ki ba na koma da zama gidan Inna Tambai amma ni tsoron idon Hadiza nake don baka san yadda
muka yi da ita ba ne a karshe." Falanke yace, "Ka san Allah
lafiya lau domin jiya da naje mun sha hira nace ango na gaisuwa
ta ce, nima ina gaida shi dazun kuma da safe kafin ka tashi mun
je ni da Basiru, wallahi abun da ta fara ce min `yaya Sha`aibu
ya aiko ka ne?' Na ce "E cewa yayi in zo in ga tashin lafiyarki."
Yusuf ya yi murmushi yace, "Ku take nuna ma fara'a amma yanzu
da żata ganni sai tsana zan je dai amma ba yau ba ina tsoron
bacin ran Hadiza."
Sai da Yusuf ya sami kwana hudu a Bakori amma bai leka
Hadiza ba sai dai dan kwarako Falanke na nan bisa hanya kullun.
Inna Tambai na dai lura da Hadiza irin nasihohin da take mata
suna shigarta don haka da alama tana kaunar ganin mijin nata.
Shi kan shi Yusuf duk ya kagara a kawo masa Hadiza kila a
gidansa ba za ta rinka yi mai kallon nan da bai so ba wanda ya ke
firgita shi amma kuma yadda Falanke ke cewa ta canza yana
kwadayin ganin nata, don haka sai ya shirya shawara ya baiwa
kaninsa Basiru kudin cefane ya ce ya je ya sawo kayan ciki da
wake ya kai ma Hadiza yace, tayi mai farfesun kayan ciki da
alale. Hadiza ta amshi kayan girki tace ma Basiru 'ka je ka
tambayo shi kamar na mutun nawa za'a girka kuma da karfe
nawa ya ke so?'
Haba murna da dadi suka lullube Yusuf da ya ji aiken Hadiza
55
ya ce "Kа ce mata kamar na mutun hudu da karfe biyu da rabi
na rana za'a zo a karba." Abinda ya kara birge Yusuf shine a irin
kwanonin da Hadiza ta zubo abincin sannan kuma irin alalan da
ta taba yi masa tun zamanin suna samartaka a wani zaman
jinyarasa da ta yi.
Karfe takwas na dare Yusuf ya fesa wanka ya zuba wanda
da riga na shakwara da janfa na kirim din boyel ya mulke jikinsa
da wani turare mai dadin kanshi da ake kira (hold the heart of
your love). Ya fito yana tayas da mota Falanke ya iso da sauri
yace, "Yallabai ba zan yi rakiya ba?" Yusuf yace, "Bisimillah, za
ni ban gajiyar aikin abinci ne." Falanke yace, "Ai yau kam amarya
ta biya mu."
Inna Tambai na zaune tsakar gida tana shan iska ita ko
gimbiyar na cikin daki tana sauraron wa'azin Mallan, hasken
musulunci. Su Yusuf su kai sallama suka shiga, bayan sun jima
suna hira da Inna, sai Innar ta ce "Ku shiga daki mana ai Dijen na
ciki."
Suka shiga tana zaune ta mike kafafuwa, sanye da jallabiya
mai ruwan zuma, ta amsa sallamarsu kan ta na sunkuye, Falanke
ya gaisheta sannan ya dubi Yusuf ya ce "Ranka shi dade zan je
cikin mota na jira fitowarka." Yusuf yace, "Babu laifi ga makullan,
sai na fito."
Yusuf ya zauna bisa tabarma shi ma ya mike na shi kafafun
ya dubi Hadiza a sunkuye ya ce, "Amarya wa`azi ake saurare
ne?" Bata iya dago kai ba ta amsa`E' yace "Allah yasa wanda
zai anfanemu ne." Tace "Amin" Ya sake cewa "Ya gajiyar aiki?"
Tace, "B