m za'a daura domin wannan shine burin mahaifinta a zahiri
insha Allah kuma kowa sai yace gwamma da aka yi kuma albarka
na tare da Hajiya Dije duniya da lahira saboda tabi iyaye yadda duk Ubangiji ke son dan kwarai ya bi. # * *
Bayan Mallan Tukur ya dawo sallar azuhur ya shiga dakin gwoggo
Halima fuskar nan cike da annuri, bayan ya zauna ne, Halima
ke cewa, "Kai Mallan wannan irin fara'a haka kamar an
aiko mana an mana gafara?" Yayi murmushi ya ce, "Halima
kail Ai dole ne na yi murna da na ya sami aure?" Halima ta
51
danne murnarta ta nuna kamar bata gane ba tace, "Wane
dan kuma?" Mallan ya dube ta da kyau ya yi dariya yace,
Mata sarakan gulma kamar wadda ke iya bacci, wadda
bata da wani sukuni duk kin fita kamanninki a dalilin wannan
auren shi ne yanzu na zo da albishir har za` a a rinka nokewa
a nuna min ba'a san abinda na ke nufi ba, to da na Yusuf da
Dije alkawarin Allah ya cika, Mallan Iliyasu ya zo min da
zancen sadaki da komi da komi na aure yau sauran kwana
goma sha daya a daura aure ayi biki, na aiki yaro a kira min
Basiru ya zo ya je ya yi ma Yusuf din waya a Funtua.
Halima ta kasa danne murnarta, ta ce "Allah Yasa alhairi".
Anan ne Basiru ya yi sallama ya shigo ya durkusa yace "Ga ni
Baba an ce kana nemana?" Malan yace, "E ka je ka yi ma Yusuf
waya ka sanar da shi an bashi Dije." Sai Basiru ya rike baki yace,
"Ikon Allah! Baba wannan albishir din ai gara na je Abujan ta fi
karfin waya." Gwoggo Halima ta yi dariya tace "Don ka tatse
shi ko, ya fiddo kudin sabon mashin din da ka ke nacin ya sai
maka", aka kyalkyale da dariya. Malan yace, "Amma ina ji maka
tafiyar dare". Yace "Babu komi Baba, ku yi min dai addu`a Allah
Ya kiyaye hanya."
Basiru bai isa gidan Yusuf ba na Abuja sai misalin karfe
goma saura na dare, ya iske su Falanke amma Yusuf na tare da
shugabansa suna gudanar da wasu ayyukansu don haka bai zo
ye işke bakonsa ba sai karfe goma sha biyu da minti arbain da
tara ya shiga gida, ya sami Basiru ya langabe a falo yana
avengyadi.
Abinda Yusuf ya fara kawo ma zuciyarsa shine cikin daya
biyu ko zancensa da Hadiza ko kuma wani babu lafiya a gida
"Kai me ya faru Basiru, waye babu lafiya, don me baka yo min
waya?" Basiru ya yi dariya yace, "Babu komi sai alhairi yaya,
kwantar da hankalinka zancen aurenku ne ya tashi kai da Hajiya
Hadiza, har sun sa sadaki Baba Tukur ma ya biya,"
Yusuf a tsaye yake sai ya nemi kujera ya zube yana
washe baki yana shafar kai yace, "Godiya ta tabbata ga Sarki
Allah, Ubangiji Allah Ka ba ni ikon rike amana, wai ka fadawa
Falanke kuwa, ya ban iske shi nan ba?" Basiru ya ce, "Gaskiya
kin gaya mai na yi domin ina ganin wannan albishir din kai ya fi
cancanta na fara sanar mawa."
Yusuf ya kwallawa yaronsa Jerry kira yace, "Kira Falanke
a baskwata." Falanke ya iso ido cike da bacci, Yusuf yace "To.
shugaban mayaka, aure fa ya tabbata akan mu, ni da Hadita
Faianke yace, "Ranka shi dade idan na yi guda ban yì laifi ba?
Yusuf yace, "Don Allah kada kayi domin ko wajen matan ma
ance babu kyau balle kuma namiji." Ai sai Falanke ya shiga rawa.
yana juyawa dama abu ga mai kiba Yusuf da Basiru dariya suke
suna tintsirawa har dai Yusuf ya mike ya fiddo kudi a aljihunsa
ya rinka likawa Falanke suna ta tintsirar dariya Yusuf yace, "To
ya isa Falanke sai kuma ran biki rannan za kayi rawa da `yan
koroso." Falanke yace, "Ana magana ran ka shi dade? Amma
don Allah ina rokon shaddar nan wadda ka zuba a ranar da muka
je gaisuwar Baba Kado, ita zan zuba ran daurin aure." Yusuf
yace "baka son a dunka maka sabbi?" Yace, "Wa`ancan nake so
ranka shi dade." Basiru yace, "Ni ma yaya ina tunin mashin dina."
Yusuf ya ce, “Kai sakarai ne wata mota nake son saya maka ko
don saboda kai su Gwoggo anguwa, kila ma gobe za` ai cinikin motar.". Basiru ya rasa kalmar da zai yi godiya anan ya kara amincewa lalle ba karamin so yaya ke ma Hadiza ba.
Yusuf kwana yayi bai runtsa ba, bayan ya gabatar da nafila
ya yi ma Baba Kado addu'a domin ya san darajarsa ya sami
Hadiza sannan ya yi ma Jallah godiya sai ya zauna ya fiddo biro
da takarda ya shiga rubuta abubuwan da zai shirya a lehen Hadiza.
Da safe bai nufi ofis ba sai gidan shugabansa ya yi masa albishir. Anan ne Shugaba yace "zancen tafiyar mu Legos aiki
babu kenan. Sai ka fara hutu daga gobe don ka ji dadin gudanar
da hidimar bikin tunda lokaci ya kure." Yusuf yace, "A'a ranka shi dade za mu iya zuwa aikin Legos domin zan yi anfani da
wannan damar na hado lehe daga can."
Yusuf ya sallami Falanke da Basiru yace su tafi da motarsa
53
su jirasa a Kaduna za su aiki Legos na kwana biyu.
A Legos Yusuf ya dauki yarinyar kanfaninsu Bimbo suka
shiga kasuwa ya zabo lesisika na shiga tsara da atanpopi na fita
kunya, da duk wani abu da ya dace da rayiwar diya mace 'yar
bimi. Bimbo ta sa Yusuf ya sayi akwati hudu da kit na biyar. A
gaskiya ya ci mutuncin naira, naira kuma ta mutunta kaunarsa
ga masoyiyarsa Hadiza.
Da suka yi sallama da Shugaba ya kawo cek na dubu dari
biyu da hamsin ya ba