NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 21 of 37

u ya kai ta gidan Malan a Danja a motar Yusuf. Mallan yace, "Madallah ku kwantar da hankalinku in dai matarsa ce to babu fashi zasu aiko maku har gida." Kwana daya da yini daya Inna Tambai ta shiga yi ma Hadiza nasiha akan ta janye akidarta na kin auren Yusuf ta hakura su yi aurensu domin wannan sako ne daga Allah. Hadiza tace, "Inna ki yi hakuri idan de ina da rabon aure a duniya zan sami wani mijin ne amma duk wulakancin da Yusuf ya yi min sannan kuma ace daga bisani na zo na aure shi a bisa tsinuwar mahaifiyata?" Inna Tambai ta hasala zuciyarta, ta kara turnuka tace, "sai ki ta zama har duniya ta nade, tunda ke da uwarki Amina kun fi kowa zuciya a duniya ba a yi maku laifi ku yafe, daga yau insha Allah babu ruwana bisa zancen aurenki ran da duk akace an daura maki aure da wanda kike so, idan ina duniyar ban mutu ba kamar ubanki na zo na shiga cikin 'yan rakiya". Hadiza ta yi raurau da idanu tace, "Don Allah Inna me yayi zafi haka?" Tace "Don ba ni na haife ki ba haka nan kin nuna min Allah bai ba ni haihuwa ba." Nan da nan Inna tasa kuka ita ma Hadizan kukan ne dai wiwi. Sun wuni zungur cikin mummunan yanayi babu mai cewa wani abu, ko wanne zuciya kamar ta fashe don daci. Bayan sallar issha'e Hadiza ta yanke shawarar zuwa ta ga Mallan lliyasu sun jima da Mallan din a dakinsa suna hira. Zuwa can Hadiza tace "Don Allah Baba na zo da wata muhimmiyar matsala ina so kada ka rufe mın komi ka sanarshe ni komi dacin amsar babu komi ka gaya min." Ya dube ta da kyau 49 ya tausaya mata yace, "ina jin ki Dije, ki sawa ranki tamkar kina magana da mahaifinki ne." Tace, "Wai Baba bayan rigimar aurenmu da Yusuf sau nawa Yusuf ya kara zuwa wajen Babana?" Malan Ilyasu ya dan daga kai sama nuna alamun tunani yace, "A gaskiya Dije babu adadi ba zai kirgu ba." Tace, "Zaka iya tuna kalaman da mahaifina ya rinka yi akan Yusuf bayan rabuwarmu kafin ya rasu?" Mallan lliya ya girgiza kai ya ce "Ai daidai da rana daya ban taba jin marigayi Alhaji Kado ya yi mummunan lafazi ba akan Yusufa bayan na yabonsa da yi mai kyakkyawar addu`a kamar yadda na san yana yi maki a kodayaushe domin lokacin da muka sami labarin an fasa aurensa da Faiza babu abinda ya fito bakin bawan Allah nan mahaifinki sai cewa ya yi`kila dai rabon yaron nan sai ya auri Dije ne ka ji wai an fasa aurensa, itama kuma Dijen ka ga bata sami miji ba a can Malunfashin',sai na ce don Allah Mallan Kado kada na sake jin zancen yaron nan Yusuf daga bakin ka,y a yi murmushi ya ce Mallan Iliya ba dama." Hadiza ta yi jigum a ranta ta rinka tunanin wai wannan wane irin so ne Baba ke yi ma Yusuf? Tayi ajiyar zuciya tace "To Baba tunda ake zuwa neman aurena tun daga kan Yallabai Mamud har zuwa Amiru ya taba nuna maka gara su da Yusuf?" Malan lliya ya yi shiru sannan yasa habar riga ya goge kwalla ya ce, "Ai akwai wata maganar da marigayi ya taba yi mani a lokacin yana kwance asibiti ba lafiya farkon tafiyarki Malunfashi kenan, ya nace da zancen Yusuf sai na rika yi mai fada nace ka san wanda Allah zai ba Hadiza kila ma yafi Yusuf? Wallahi Allah ya jikan bawan Allah nan yana kuka ya rinka ce mani shi kowa za ki aura bai kai Yusuf ba, ko da kuwa shugaban kasa ne domin shi yana ganin Yusuf tamkar yayanki Tasi'u inda kuma na ji dadín Yusuf shi ne, har Alhaji Kado ya bar gidan duniya bai yada shi ba ya nuna masa gatanci kamar Tasi`u ne domin lokutta da yawa zai zo nan gidana ya ba ni kudi sabbi masu yawa yace ga wannan ni ma na taba idan nace ina ka sami kudi har ka ke rabo ya kan yi dariya yace, "Dana Yusufa ya zo ko yayi min aike." 50 Hadiza na share hawaye tace "Baba!" Ya amsa, "Na'am Hajiya Dije?" Tace, "Wannan rana da aka sa za`a yi arenmu da Amiru kada a canza a daura da su Yusuf din amma fa Baba Yaya Amina sau takwas tana tsine min jiya akan Yusuf." Yace, "Wannan duk ba komi ba ne idan kin bi Allah kin kuma yi biyayyar aure babu abinda zaki gani sai albarka, ki ci gaba da kyautatawa mahaifiyarki tare da neman gafararta." Wanshekare lokacin da Mallan Iliyasu ya je wajen Inna Tambai suna daidaita yadda zasu sawa su Yusuf kudin sadaki sai ga Hadiza ta kawo mai wasika tace ya kai ma Yaya Amina ta neman gafara. Malan Iliyasu ya isa gidan su Yaya Amina ya yi sa'a ya cimma mijinta Malan Isa, bayan sun gaisa da Isa, ya shigar da shi zaure ya kawo mai tabarma sannan suka fito shi da Amina. Duk hanyar da Malan lliyasu ya bullo mata sai ta bulke haka dai suka hadu shi da mijinta ana lallasinta ana bata hakuri, daga karshe tace aje ayi aure ba za ace ta hana 'yar ta aure ba, domin ta san in ba Yusuf ba Dije ba za ta yi aure ba amma fa babu sauran wata hulda tsakaninsu. Mallan Isa yace, "Zancen wofi kenan idan kince babu hulda babu ruwanki da ita kenan" Ta ce, "Shikenan Mallan tunda dai kun tilasta min na yafe a yi aure amma kowacce irin matsala ta sami kanta kar ta neme ni haka nan dukkan walakacin da zata sami kanta gidan Yusuf babu ni babu zuri`ata." Mallan Iliyasu ya mike ya shuri takalmansa yace, "Aure ka
🏠