NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 2 of 37

a zarar Amiru ya nuna sha'awarsa shi kenan Yusuf ya haranta ta. To amma rudin da ya ga Yusuf ya shiga a tun daren jiya da ya ga Hadiza abin na tada hankalin Amiru. A cikin gida kuma suma su Inna Tambai abinda suke ta kiyastawa rayuwankansu kenan, da wacce riga Yusuf ke wannan irin wannan hidima ?Yayin da bai iya minti ashirin a waje sai ya shigo cikin gida ya leka dakin da Hadiza ta ke ya gaishe su. A tun daren jiya da akai rasuwar Gwaggo Halima ta ke zuwa amsar gaisuwa haka nan da zarar ta gama abinci ta kan shiryo ta taho.Duk da dai yanzu zumuntar ta su ta yi sanyi tun batawar Yusuf da Dije sai su kashe shekara ma ba su nemi juna ba hatta lokacin bikin su Hassi da Sarai ko da Halima ta kai ma Tambai goro bata je ba sai dai ta kai mata abin hasafi. A yarda aka shirya ran lahadi da la'asar su Yusuf da Falanke za su koma Abuja yayin da Amiru zai zauna anan gidan Yusuf har sai an yi sadakar bakwai to amma zumudin Yusuf da irin yadda ya ke nuna maitarsa a fili sai duk Amiru ya rinka zarginsa. yi A daren asabat din bayan Amiru ya kira Hadiza don su sallama, sun gama sallamarsu a natse har sun shiga mota sai Yusuf ya tsayar da su ya ce "don Allah su jira shi yana zuwa minti biyar"ya koma cikin gidan su Hadiza ya leka har dakin da suke zaune ita da Inna Tambai da Yaya Amina da bakin mata guda biyu da suka shiga a lokacin gaisuwa, ya ce, "don Allah Hadiza zo nan minti biyar". Ta mike ta fito ba tare da sa ma ranta komi ba. Suna tsaye a filin daga shi sai zaure, ya kara kallonta sannan ya sunkuyad da kai, ga dai Hadiza da ya kwana ya wuni tunani a gabansa,duk wata kalma da ya ke tunanin fadi mata ya san ba za ta yi tasiri ba, domin wannan ba Dijen da ba ce, in ma da hali zai iya cewa wannan babu wani wayon da zai iya nuna mata a halin yanzu. Ya cije ya daure ya ce, "wallahi ban san wai Baba ne ke kwance a asibiti ba, me zai hana ni zuwa gaishe shi?" Ta daga ido ta dube shi kawai, sai Yusuf ya ji gabansa ya fadi domin 2 idanun Hadiza sun canza mai, ba kowacce mace ke da irin wannan idanun ba, a karo na biyu yá sake wata rashin kunyar ya се, "Amma ke ma Hadiza ba ki san ni ne Yusuf din da ki kai ma waya ba?" To anan sai Hadiza ta sha mur ta ce, `wai me wannan mutumin ke nufi, yana tsammanin ta na da lokacin shi ne har yanzu duk da dai bata san shi din ba ne amma bari ta gwasale shi taga sai me?' Sai tace, "ina ruwa na da sanin kai ko wanene, ni kam na yi maka waya ne a bisa bin umarnin mijina Amiru!" Nan da nan wani gululu ya iso wuyan Yusuf amma sai ya tokare shi ya tuna wannan ba irin`yan matan da su ke zagi ba ne, ya gyara kurensa ya ce, "To Hadiza ni kam gobe zan koma Abuja Ubangiji Allah ya gafartawa Baba halayyarsa na kirki Allah yasa sun bi shi, Allah ya kara hakuri". Anan sai ta dan saki ranta tace, "Mungode, mungode Allah ya saka da alhairi a bisa dukkan abinda akai mana." Kafin ya ce wani abu ta juya zuwa cikin gida. To wannan shi ya kara sukurkutar da Amiru da suka isa gida sun jima ana hira da su Falanke amma sai Yusuf ya nufi can gidansu wajen Gwoggo Halima yana ta raragefen hirar Hadiza amma dai kunya da jin nauyi sun hana ya tambayi Halima ainihin labarin Hadiza abinda ya ke son ji. Ita kanta Gwoggo Halima ta zargi Yusuf na Cıkin yanayin damuwa amma sai ta dogara damuwarsa akan rasuwar Alhaji Kado domin'sanin shakuwar da ke tsakaninsu. Abu daya mutuwar Alhaji Kado ta kawo mata, wato ta janyo mata Yusuf domin ta fuskanci hankalinsa ya dawo gida tamkar da, saboda yaushe rabon da ya zo ya zauna su yi hira irin ta wannan zuwan? Har ta manta, a koyaushe ya zo yana can sabon gidansa duk lokacin da zai zo gare ta cikin sauri don kawai kada ta yi mai fadan aure. Gwoggo Halima ta dago kai ta dubi Yusuf yayi wani zama rashasha kamar wanda aka zare ma lakka duk yadda Allah ya halicce shi ya saki sharaf. Ta ce, "idan ка кoma Abujan kuma sai vaushe?" Yusuf ya sa hannu ya shafi hancinsa ya ce, "Ina tsammanin ha zan dade ba zan dawo, kiia ma nan da sati biyu." Gwoggo Halima ta ce. "ai gara ku je ku kwanta dare ya yi ga tafiya a gabanku gobe." 3 Ya mike yana rangaji ya nufi motarsa ya ja va nufi gidansa ,anan ya cimma su Amiru da su Falanke ana ta hira ya jima cikinsu amma bai iya cewa komai babu abinda ke azazzalal zuciyarsa sai yadda zai amshe Hadiza hannun Amiru tabtas mutuwar Baba Kado tamkar shi kadai akai mawa, domin idan da ya na da rai a yau yaje ya same shi ya ce, atabau shi Dijen shi ya ke so, to lallai ya yi imani Baba Kado zai rushe maganar Amiru ya ba shi. Wannan tunanin ya kara tsinkar masa da jijiyoyi, dole ne ya nemi hanyar da zai san inda Hadiza ta ke zaune a Kaduna haka nan ya nemi lambar wayarta, idan ya sami wannan zai yı abubuwansa cikin sirri kenan. Wanshekare ran lahadi kenan bayan sun je anyi addu'a da su, Yusuf ya riga Amiru dawowa ya bar shi a can saboda haka yana isowa bai tsaya ko ina ba sai dakin da ya sauke Amiru ya fara kwance masa jaka zuwa akwatinsa neman cikakken bayanin Hadiza, me zai faru
🏠