gogaggen katako sai walkiya da sheki
su ke, Inna Tambai, ta rinka yabawa tace, "Kai Hadiza amma fa
kin yi kaya da kyau sai dai tsada". Hadiza ta yi murmushi tace,
"Amma Inna rai da rai ne fa! Idan ka gaji da wannan fantin za ka
iya canzawa, kuma katakon bai komi."
Yakunbon Amiru ta yi sallama ta shigo, nan da nan Hadiza
ta fara sunkuye- sunkuye nuna alamun jin kunya, Inna Tambai ta
kai ta daki ta debo mata ruwa suka shiga gaisawa sannan Hadiza
ta leko daga can bakin kofa a tsugunne ta gaida Yakunbo, sai
Yakunbon tace, "Ke Hadiza tare muke fa da Amiru yana can
kofargida."
Hadiza ta mike a cikin jin kunya ta surutuka, ta ce, "To".
Ta nemi tabarma ta nufi zaure, yana tsaye a zaure rike da wata
yar karamar casbaha, ya daga kai ya dubi Hadiza ya amsa mata
sallama yana mai 'yar siririyar dariya yace, Hajiya Hadiza!' Tayi
murmushi tace, "Yallabai barka da zuwa, zauna mana". Ya cе,
"Na gode". Ta zauna itama a gefe guda na tabarma tace "Menene
na godiya kuma?" Ya ce "Ai dole ne wanda aka karrama da
41
gurin zama?"
Sun jima yana yi mata dan barkwanci, sai ya rasa ta fuskar
da zai iya bullowa Hadiza da cewa ya fasa aurensa da ita, domin
mutuncinta da kamun kan ta zuwa kwarjinin da Allah ya yi mata
sun cika masa fuska, zuwa can Hadiza ta ce, "Ina fatan ka zo
mana da katin gayya domin ina son aikawa da na jama`ar nesa".
Amiru ya tsurawa Hadiza ido sannan ya sunkaya yace, "Anya ko
Hadiza zan kawo katunan nan kenan?" Gaban Hadiza ya fadi ras
"Me kuma ya faru, Amiru?" Wannan itace tambayar da ta fito
daga bakin Dije cikin murya mai fargaba.
Amiru yace "E to ya zama dole na yi nazari a bisa al'amuran
aurenmu da ke daga bisani na nemi shawarar magabata na, to
sun nuna min yin hakuri zai fi alhairi a gare mu"
Hawaye wasu na bin wasu daga idanun Hadiza har ta kai
Amiru bai iya hada fuska da fuska da ita don tsabar tausayi
saboda ya tsani mace na kuka balle macen da ya ke da tabbacin
ransa na so ya dai hakura da ita ne akan tilas.
Cikin murya mai sheshekar kuka ta ce, "Amma Amiru
idan ka bar ni ka ci amana ta, me aka fasa cikin shirye-shiryen
aurenmu?" Ya kara kawad da kan shi gefe daya yace, "Hadiza
ban ci amanarki ba domin na dawo maki da wanda ki ke so ya ke
son ki, kuma dan uwanki kamar yadda ki ka gaya min tun farko".
Ta kara share hawayenta da gyalenta yayin da wasu suka tararo
tace, "Wannan zance kana yi ne a bisa son zuciyarka babu wani
son da ke tsakanina da Yusuf wanda har zai sa kace ka fasa
aurena."
Ya dan yi shiru yana tunani shin ko dai kishi ya ja masa ya
yi wawanci! Lalle Hadiza na son shi, to yanzu ya zai yi, ya ce ma
Yakunbo ta bar kaya kar ta amsa a ci gaba da aurensu shi da
Hadiza har da ita Salmar, nan ne ma zai gane wadda tafi son shi
idan suna rayiwar aure?
Yace "To Hadiza yanzu kam zancena ya koma hannun
manya!" Tace "me ka ke nufi?" Yace, "Baba Kabir ya ba ni mata
42
Gaba daya tun daga zuciyar Hadiza har cikin idonta sai ta
rinka ganin duhu lunfashi ya rinka kokarin dauke mata, ta sa
hannu ta danne kirjinta, ta rinka kuka a bayyane, Amiru ya juyo
a firgice yace, "Shi kenan Hadiza zan iya hada ku ku biyu idan su
Alhaji a can Kano sun amince min."
Hadiza ta girgiza kai tace, "Babu komi Amiru ban ce ka
roki kowa ba wai don ka aure ni insha Allahu Allah zai ba ni miji
lokacin da ya dace na yi aure". Ta rinka addu` a a ranta wadda
zata sami natsuwar ranta don hakalinta ya dawo jikinta, yayin
da shi kuma Amiru ya rinka lallashinta yana yi mata nasiha, ta yi
shiru sai dai goge hawaye akai akai.
Amiru yace, "To Hadiza na gode kwarai da irin kaunar da
ki ka nuna min Ubangiji Allah Ya sa yadda mu kai din nan ta
zamar mana alhairi baki daya".
Hadiza ta yi juriya tace "Amin Amiru, ni ma ina godiya ga
niyyarka ta aurena da ka yi, wanda yasa mahaifina ya rasu cikin
kwanciyar hankalin ya bar ni da miji na gari na gode da wannan
taimako a kodayaushe ba zan manta ba."
Yace, "Babu komi Hadiza aure nufin Allah ne, insha Allah
ba za ki yi dana sani ba da auren Yusuf". Ta daga mai hannu ta
ce, "Zancen Yusuf ba ya tare da ni don haka ka bar zancen kawai."
Yace, "To na bari, ina da hoton Salma a mota ko kina da bukatar
gani na kawo maki?"
Wannan shi ne lokaci na farko da ta taba tsanar Amiru
tace, "A'a bani da bukata". Ya dan cije lebe yace, "Ba dai kishina
ki ke ba ko Hadiza?" Ta dube shi da kyau ta ce, "idan ma har na
yi kishi a wannan lokacin ai daidai ne". Ya duba agogon hannunsa
yace, "Ai gara ki yi ma Yakumbo magana mu tafi kada dare ya yi
mana."
A cikin gida babu abinda ke fitowa daga bakinsu Inna da
Yakumbo sai ban hakuri ga junansu, bayan Inna Tambai ta fiddo
mata kaya akwati shidda ta dubi kaya babu ko kallabi da ya
salwanta, aka kira yara suka rinka fidda kaya zuwa motar Amiru.
Bayan sun tafi Hadiza ta shiga dakin Inna Tambai tana
43
wanisaboon kukan tana fadin "Ni dlai Inna na shiga uku anya ko
zan yi aune a duniya?"
Inna Tambai cikin nata bacin ran, ta danne ta ce, "Dori me
za kima kanki mummunan lafazi, lɔabu komi gara d