ya cewa ga iyakar zuwansu Bakori, domin wani lokacin tsakar dare suke shirya tafiyar sai dai jama'ar Bakori su wayi gari su gan su. Ba tare da sanin Yusuf ba Falanke ya shirya ya je Tsiga wajen wani tsohon Malami aminin kakansa, ya fede masa bire har bindi na halin da Yusuf yake ciki. Tsoho ya yi shiru sannan ya ce, "Ina son ka yi kokari ka kawo min abu daya daga cikin wa'annan ko dai ka yanko min gefen kallabinta ko kuma sawun kafarta insha Allah idan na hada wani abu in dai har nan da
kwana biyar babu magana mai karfi to ya hakura ba matarsa ba ce
Falanke ya koma ya yi sa'a Hadiza na gidan Inna Tambai
ya tsaya a kofargida gindin wata itaciya ya aika a kira mai Hadiza
aka ce ya shiga, ya kafe ba zai shiga ba, ya matsa mata da aike
sai da ta fito, ya shiga kuranta ta yana wasa Yusuf, zúwa can ta
ce, "Abinda ya kawo ka kenan Falanke?" Yace, "Don Allah ki
auri dan'uwanki Hadiza mai kaunarki". Tace, "Falanke kuna son
ku zama sanadiyar batawa ta da mahaifiyata ne?" Yace, "Me zai
sa ki zarge mu da wannan? Ai shi aure tunda aka halicci duniya
aka san shi da rikici insha Allah mahaifiyarki sai ta yi alfahari da
aurenmu". Ta yi dariya tace, "a cikin satin nan zan fara raba kati
insha Allah ba zan manta da na ku ba Falanke, ni ka ga tafiyata,
sai anjima".
Ta juya ta rinka tafiya a tsanake, shi ko Falanke tafin
kafarta kawai yake kallo, yana kallon in da take takawa sawunta
36
na bayas da shaida.
Ya duba ko ina bai hangi kowa ba, ya fiddo wata leda ya
durkusa ya debi sawun kafar Hadiza na hagu da dama, ya kulle a
leda sai Tsiga wajen Baba Tsoho.
Baba tsoho ya dan danki kadan ya ce ta isa. Falanke ya
mayas da sauran cikin aljihu, Baba tsoho yace, "In dai na yi
wannan aikin nan da kwana biyar babu bayani to ya kyale ta".
Falanke ya fiddo kudi dubu biyu ya bashi, Baba ya girgiza kai ya
ce, "Na gode mai da kudinka ai wannan kulla sunnan Manzo ne
Allah ya ba mu lada, ya fi min wa'annan kudin."
Wannan kenan a gidar Gwoggo Halima kuma, kullun a
rikice take, gani take yi tamkar zata rasa dan da ta ke ji da shi a
dalilin Hadiza, ya bi ya sukurkuce ya rame ya tsangwame kan sa
kamar ba wata mace a duniya sai Hadiza, to har sai ta rinka
raina taimakon da Malan Tukur ke masu. A wani marece ta shiriya
ta je kauyensu Danja wajen wani tsohon Malami aminin
mahaifinta, rabonta da shi tun zamanin tana goyon Yusuf da
suka rinka samun matsala da Babansu Yusuf shi ne ta kai kukan
ta wajensa, ya yi mata istihara yace, ta yi hakuri domin shi ne
uban 'ya'yanta, haka nan akwai daukaka a cikin 'ya'yan da
zasu haifa, ya kawo taimako ya bata suka zauna lafiya lau da
Babansu Yusuf har sai da mutuwa ta raba su.
Ta isa Danja ta je wajen Malam ya rinka yi mata fada
domin bata kula shi, "Ya dace ace ko su Yusufa kina turowa
suna gaishe ni". Ta ba shi hakuri tace, "ko yanzu ma zancen shi
wannan din na zo maka da ita". Yace, "Lafiya ko?" Ta kwashe
tun farkon lamarin Dije da Yusuf ta gaya ma Malam. Malam ya
yi shiru yace, "Aure kenan! Yau sauran sati biyu da` yan kwani
bikinsu da shi wancan abokin nasa?" Tace, "E Baba, ni kam idan
wannan aure ba mai yiwuwa ba ne, na fi son ka yi mai asirin da
zai ji ta fita ransa kwata-kwata, wallahi ba ka ga yadda yaron
nan ya lalace ba". Mallam yace, "Ba komi, zan yi istahara kwana
uku ki dawo. Idan fa matarsa ce ai ba mu da yadda za mu yi, in
kuma ba matar ba ce dole ne ya hakura".
37
Gwoggo Halima duk ta kosa taji abinda kwana ukun za ta
haifar domin cudewar lamuran ta isa.
A can kuma Abuja bom din su Yusuf ya fara tashi domin
Amiru ya isa Abuja ya je ofis din wani abokinsu Ashiru bayan
sun gaisa, Ashiru ke cewa "To kai Amiru mu fa ba mu gane ba
wai daurin auren wa za mu cikinku kai koYusuf?" Amiru yacе,
"Wanda kuka zaba". Ashiru ya yi murmushi yace, "ni fa ina
tsoron yarinyar nan Hadiza a cikinku na rasa wanda take yaudara,
yanzu ran nan suna waya da Yusuf lokacin ta je Jos har ya ba ni
mu ka gaisa kai ka ce sun riga ma sun yi auren, yanzu haka cikin
satin nan Yusuf ya zo da hotunan ta, to amma duk ace wai kai
zata aura ni fa ina tsoron yanmatan zamanin nan wa'anda
idonsu ya bude, kada kana takamar ka yi aure ashe Yufuf ka
auro mawa, abinda fa mutun ke yi shi ke samunsa Amiru". Anan
zufa ta rinka karyo ma Amiru, duk wani son Hadiza sai ya ji ta
fita ransa fit, amma ya cije bai nunawa Ashiru ba, ya mike yace,
"Kai ni wannan bata damuna an ce matar mutun kabarinsa sai
kun zo daurin aure".
A mota ya rinka sake-saken ba zai yadda Hadiza ta yi aiki
ba, ko alama, domin a ganinsa itace barakar da zai bar wa Yusuf
da Hadiza har su rinka saduwa.
Ya isa wajen buga katuna anan ma ya cimma sakon Yusuf
kamar yadda ya umurci ma aiki ya aiwatar, ganin wani matsiyacin
hotan Hadiza da na Yusuf, sai kawai Amiru ya amincewa ransa,
wannan aure ko ya auri Hadiza shi da Yusuf ke da ita domin idan
ya hana ta zuwa aiki zai hana ta ziyarar 'yan'uwanta ne a Bakori?
Komi zai iya faruwa idan taje ganin gida wannan tunanin ya rikitar
da komi na Amiru.
Da ya bar w