NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 14 of 37

shi ne tunda ka fahinceta a hakan, to sai ka koma can Bakorinku ka nemi daurin bakin su Inna Tambai da aminan Babanta domin sanin kan ka ne, a duniya Hadiza bata da uwa kuma aminiyar shawara bayan Inna Tambai, sannan kuma tafi son Babanta fiye da komi na duniya, idan ka sami amincewarsu ina gánin za su shawo maka kan Hadiza." Yanzu a duniya Yusuf ji yake bai da masoya irin Saminu da Hadizan Jos da Mama Binta. A ran nan ya koma Kaduna kashegari ya yi ayyukan kanfaninsu da dama ya yi sa` a daya daga cikin wa`anda ke da alhakin mallakar kanfanin ya na nan ya je Kaduna, ya yaba da aikin da Yusuf ya gudanar har ya nemi Yusuf da ya zo gidansa da yamma, gaban Yusuf ya fadi ras domin a niyyar Yusuf so ya ke da yamma ya nufi Bakori ya kashe su Inna Tambai da Baba lliya da dadin bakinsa, amma sai ya tuna aikinsa na gaba da komi, idan babu aikin nan matar ma tsanarka ta ke. Ya cimma uban gidansa da karfe tara daidai na dare sun yi rubúce-rubuce har zuwa karfe biyun dare akan kanfaninsu. To a lokacin ne Yallabai ya lura ba haka Yusuf ya ke ba akwai dai wani abu a kalkashin ransa, yana tambayar Yusuf bai tsaya wani kawaici ba ya warware mai irin damuwar da ke cin sa a rai, nan da nan Yusuf ya fara kawo kwalla ya ce, "Yallabai ni na san na yi kuskurena amma yarinyar nan ta ki hakura, ga shi abin haushi wai abokina na kut da kut zata aura." Yallabai ya yi shiru tausayin Yusuf ya kama shi balle ma da yaron ya nuna mai shi maraya ne, duk zuri`arsu a kan shi aka rataya, sai ya ce ma Yusuf "To kai ba ka dan sakarma iyayenta 31 kudi ne ko kamar abokin na ka?" Yusuf yace, "Inal Yallabai ai wa'annan sun fi karfin a rude su da ku". Yallabai ya yi dariya yace "kai wawa ne ba ka san halin kanawa ba kenan. Bari na baka wani guntun labari: akwai wani bakano za shi England neman auren baturiya fara kal, sai abokansa suka ce masa 'wai wai Alhaji ka rufa mana asiri, kai da ba ka jin turanci ita kuma bata jin hausa? Ka dai ci gaba da auro filanin mata kyawawa', sai Alhaji ya yi dariya ya sa hannu aljihu ya fid do takardar 'yar wazobia wata naira hamsin ya daga masu ita yace, 'kun ga wannan, to babu yaren da ba ta ji a duniya, sai dai idan baka da ita'. Yusuf da Alhaji suka bushe da dariya. Yallabai yace, "Gobe zani gida Katsina sai ka shiriya zan tsaya Bakori na ga iyayen ita yarinyar wa anda su ke da karfi akan maganar, sai ka shirya da wuri karfe takwas na safe." Yusuf ji yake kamar an ce an bashi Hadiza dan murnar Yallabai zai sa baki a al'amarin. Karfe goma sha daya na safe suka isa gidan Inna Tambai. Yusuf ne ya fara shiga ya firgita Inna da cewa ta yi manya-manyan shinfidu ga shugabansu nan gaba daya ya zo ganinta, ai ko Inna ta rude har wata darduma ta shinfida bisa tabarma. Sun jima ana gaisawa yawancin gaisuwar a bisa matuwar Baba Kado. Sannan Yallabai ya gangaro bisa zancen Hadiza shi dai Yusuf na gefe ya takure, (manya na magana). Yace, "To Inna Tambai ai ina ganin da kai da kaya duk mallakar wuya ne, ki tuna fa ke mai nemarwa Yusuf aure ce, bayan kuskuren da yayi domin ko ita takun Ubangiji na iya jarabar ta da irin hakan, shin ashe idan da ta yi wani aure sannan ta fito ta zo tace a duniya kuma babu wanada take so sai Yusuf ashe mahaifiyarsa bata isa ta tursasa Yusuf ba akan ya yi hakuri ya auro Hadiza, domin kamar kanwa ce a gare shi? Dole ne kuma ya aureta ba zai ki ba domin kuskuren aure ba inda ba a yin sa. Amma yanzu inna kuna kallon Hadiza kun kyale ta zata bar dan uwanta akan wani kuskure kalilan na kuriciya?" Inna Tambai nan da nan ta ga gaskiyarsu anan, domin ta sha ganin yarinya ta 32 ki mijin sai daga baya, a dawo a neme shl bayan ta yi aure ta hayayyafa, kuma a rnatsawa namijin dole ya aura hakanan bayan a da can babu irin wulakancin da bata yi mai ba. Yallabai ya katse tunaninta yace "Wannan Amiru ba fa halin sa kuka sani ba, bayan Yusuf tun yana cikin ciki kun san halinsa. Don Allah ki natsu ki sami lokaci ki yi ma Hadiza nasiha irin taku ta manya". Inna Tambai tace, "Ranka shi dade wannan zance na ka fa abun dubawa ne, na yi ma alkawari zan yi iyakar kokarina, sai dai kuma idan haka Allah Ya kaddaro, to sai Yusuf yasa hakuri" Yallabai ya ji vwani irin sanyi domin babu wanda bai son ya nemi alfarma a ki yi masa, to anyi mai alkawari yace Yusuf ya dauko mai jaka cikin mota. Yusuf ya fita da sauri ya kawo jaka ya tsugunn yaba shi, ya bude ya fiddo bandir din 'yan wazobia sabbi fil na dubu as hirin ya baiwa Yusuf yace ya mikawa Inna Tambai. Inna ta bude hannaye tace, "kai Yusuf ina zan kai wa annan kudi ku bar su kawai". Ya yi dariya yace, "Haba Inna ku amsa, karamin aikin Yallabai kenan idan ki ka ji babban sai ki rike baki." Sun isa gidan Malan Iliya motar Yusuf ce gaba ta Yallabai na biye, sun kuma ci sa'a Malam din na gida. Bayan an gama gaisawa Yusuf ya gabatar da Yallabai kamar yadda ya gabatar da shi wajen Inna Tambai, shi kuma Yallabai ya shiga kurunta matsayin Malam Iliya a wajen Baba Kado, ya nuna masa shi kadai zai iya lankwasa Hadiza
🏠