NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 13 of 37

ya ke mata, ya ce, "ina son na ga Mama ta nan gidan". Hadiza ta mike da sauri ta fita, daman zaman ya gallabe ta, yaya zai tasa ta ya rinka yi mata kuka ita lokacin da ta yi nata kukan rashinsa yana ina? Ba yana can ya sami Fa`iza ba, to itama yanzu ta sami Amiru don haka kada ya matsa mata. Ta sanarwa da Mama sakon Yusuf sannan ta cimma Hadiza a daki ta kwantar da Fatima ta koma inda Hadiza ke kwance ta zauna, ta dubi`yar Jos tace, "A gaskiya kin ba ni kunya wai duk bakinki da irin tsiwarki amma wai ki ka kasa ce wa Yusuf komi sai ma wani gatanci da ya samu wanda ban ga Amiru na ya samu ba". Hadiza ta tashi zaune 'ki vi hakuri, ni kai na nayi mamakin yadda na yi ma Yusuf, saboda na tsane shi a bisa 28 labarin da ki ka bani, to amma ina shiga falo yadda na gan shi sai na ji duk na sare domin kwarjininsa da barkwancinsa ya fi karfin a yi mai wulakanci. Na san a da Yusuf ya yi laifi to amma yanzu Hadiza ki tausaya masa, ki duba fa har tsugunnawa ya yi bisa gwiwowinsa yana kuka? Haba! Hadiza ai namiii irin su Yusuf komi su kai idan har $un gane kurensu sai a yafe masu haka nan, wallahi yadda ya tsugunna a gabanki ba don kuka ya ke yi ba ni kam yau da na dauke ku hoto da sauran fim din Fatima, kin ga irin kyan da ku ka yi kuwa? Kai Hadiza ke da Yusuf Allah ya yi ajiyarsa!" Hadizan Bakori ta daga kai ta dube ta ta ce, "kina da hankali kuwa? Kin manta an tsaida min miji Amiru?" Hadiza ta ce, "Na fi kowa sani, amma in gaskiya ta zo a fade ta, haka nan kuma sau nawa ake sa rana a warware wani lokacin ma ana gobe za'a kai amarya gidan miji ake canza mijin" Hadiza ta cе, "Tunda ba'a yi akan ki ba, insha Allah ba za`a yi akai na ba, su Fatima ga su can gidan Amiru". Suka dade suna kallon juna sannan suka kyalkyale da dariya. Hadizan Jos ta ce, "Tafdijam! Ina ganin Bakatsine ba na auren Bakano, sadda duk miji zai saka hulà sai dai kiga (birki kunne) haka nan za su ranbadawa idanunsu kwalli bajau wa ya aike ni!" Hadizan Bakori ta dingi dariya har tana kwantawa ta ce, "Wai ya ake sa hula birki kunne kuma Hadiza?" Ta ce, "Idan Amiru ya zo ki dube shi tsab za ki gani, amma kin hada da su Yusuf gogaggun Katsina idan an saka hular nan a murza ta sai ta kusa danganewa da gira, ke komi na Bakatsine fa daban ya ke, idan har an sami tsantsar Bakatsine za ki same shi da daddadan lafazi mai tsima jiki da kashe kwanya sannan ga kyan iya shirya lafazi yadda zai shigi bil adam, sai kuma wata baiwa da Allah ya yi ma su na kamun kai, wanda shi ne ya haifar da wata ilhama ta kwarjini na musamman a gare su, to kin ji dalilin da yasa Katsinawa su ka yi zarra, amma fa ba su danne `yan Bauchi ba domin suma sun hada yawancin abinda Katsinawa suka tara, ko kin san duk Nigeria ba wanda ya kai jama'ar Bauchi da Katsina mulki irin na 29 Kuma sun iya domin irirn jininsu kenan. Hadizan Bakori ta ce, "kai Hadiza da dai Dr Sani ba dan Katsina ba ne, sai na ce ya ba ni da bakin ki, to Allah ya taimakeshi ya fito daga jiharku ta Katsinan. Ni kam ina kin Yusuf ne a dalilin ina ganinsa a namiiin zara irin su ne a kullun suka hango abun sha'awa jikin wata za su bar ka zuwa gare ta".. Ina son kuma ki fahinci abu daya a wajen Kanawa kamar yadda ki ka fahinci Katsinawa wato a duk kabilar arewa babu masu ladabi da biyayya da sanin ilmin Islama kamar 'ya'yan Kano daga nan sai`ya`yan Maiduguri, in da duk Bakano ya ke yana girmama na gabansa, haka nan bai iya saba maganar iyayensa ko yaya take, sannan za ki same su cikakkun mutane masu sana`ar gado tun suna `yan kanana, amma kin hada da yaranmu na jihar Katsina yawancinsu sun faye girman kai da nuna isar ba a isa ba, da sauransu, to kin ji abinda ke ba ni sha' awa da halayyar kanawa. A can falo kuma Yusuf ya yi zaman dirshan bisa kafet gaban Mama Binta ya fi awa daya yana kashe ta da lafazinsa masu dadin sauraro, ya ce, "Wallahi Mama ina tausayin kaina ina tausayin Hadiza domin yadda na ke sonta itama ni kadai take so, to kin ga na kyale ta ta cutu akan wani jin kai da kunya?" Mama ta ce, "E to sai na yadda da kai anan domin zurfin cikin Hadiza yawa ne da shi, duk yadda ka ke da ita da wuya ka san abinda take so ko wanda bata so, haka nan mu dai tunda muke da ita a gidan nan ba mu san ko me ke bata ran Hadiza ba." Yusuf ya gyara zama ya ce, “To kin san Allah daya ne Mama, duk duniya daga ni sai Baba Kado wato mahaifinta muka san cikin Hadiza da bai dinta, yanzu idan da yana da rai tabbas ya san tafi so na fiye da Amiru babu tantama ba zai tsaya sauraronta ba zai umurtai ni na ci gaba da shirye-shiryen biki, yanzu haka idan zan aika na kira ta zata zo, illa dai zata rinka fada min maganganun wulakanci amma idan na dubi kwayar idonta wani zubin zan ga ba har cikin zuciyarta take min ba, sai dai saboda jin dacin abinda na yi mata, na kuma tabbatas idan da 30 ni ne aka sa mana rana babu yadda za ai ta fito wajen wani idan ya kira ta." Mama ta ce, "Lalle Yusuf dole ne ka nace domin ba a san rabo ba, ni dai shawarar da zan baka
🏠