NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 10 of 37

za ta je Jos. Ya yi mashi kwatancen gidansu na Kaduna. Suna aje waya ya latsa wayar gidan Yaya Garba, wani yaro ya dauka yana jin an ce Hadiza a ke son magana da ita sai ya ce mata, "Anti Hadiza ga Baba Amiru". Ta je da saurí ta dauki waya ta ce, "Na yi hushi angona, haka mu ka yi da kai saboda Allah Amiru?" Yadda Hadiza ta rausayar da murya ta tsumar da Yusuf amma a lokaci guda kishi ya dirar masa wai Haidizansa ke ma Amiru magana mai dadi irin wannan? Kamar ya aje amma kuma bai iyawa, ya ce, "Ba Amiru ba ne, Yusuf ne. Kina lafiya?" Ta ja tsaki ta aje wayar. Hadiza na sauraron aiken Amiru ne domin ya yi mata alkawarin turo direba zai kai ta wajen taron sunan Hadizan Jos, to amma shiru a zaton ta shi ne ya yo waya ta dauka da niyyar ta yi masa tsiya sai ta ji Yusuf, to bayan ta dawo ta zauna sai kuma Amirun ya yo wayar ya na bata hakuri akan ta yi hakuri tafiya sai gobe, domin ya samu ya kammala `yan hidimomin gabansa ne don haka shi ne zai kai ta ba direba ba. Yusuf ya je ofis a washegari, ya rinka duba fayal-fayal don ganin irin ayyukan da ke gabansu, a kalla akwai zuwa Legos don shigar da wasu takardun kwangila da aka ba kanfaninsu na sa wutar lantarki a garin Zariya, haka nan akwai zirga-zirgar zuwa Kaduna kamar sau biyu a satin nan shi ma ana bukatar kula da kwangilar hanyoyin da kanfanin su ke yi, akwai son akai ma gwamnan jihar Kaduna wasu takardu don sa hannu suma na sabon shigar aiki ne. Yusuf ya ja birki daga nan ya ce, "Yauwa". Maganar zuwа Kadunan nan ita tafi damunsa domin wata dama ce da zai samu ta kusantar Hadiza ba tare da aikinsa ya raunana ba, ya mike ya nufi ofis din Shugaban kanfanin, ya gayas da shi bayan ya yi sallama. Yusuf ya shiga nuna mai mahimmancin kasancewarsa a Kaduna na tsawon lokaci don ya samu ya gudanar da wa`annan ayyukan da suka taso. Shugaba ya duba a tsanake sannan ya ce, "A lalle kam, bayan wannan ma akwai wata takarda da ta iso a 21 daga Kaduna za` a zauna mitin da gidan gwamnatin da kamfaninmu a sati mai zuwa don haka ina ganin kai ya dace ka wakilci kamfaninmu, saboda haka duk sauran maganar shiryeshiryen maganar kudaden tafiya sai ka sami Yakubu akawuntanmu sai in ce sai mun ji waya ko kuma ince sai Allah ya dawo da kai lafiya". Yusuf ya ce, "zan yo wayar domin ta yiwu wani abun ya taso daga baya." Ya isa gida ya yi sallama da su Falanke ya kara jaddada ma Falanke cewa kada a kara barin wata 'yar iska ta shigo mai gida. Falanke ya ce, "Haba Yallabai tun yaushe wannan ta kwaranye mu dai addu'ar mu Allah Ya bamu Hadiza a matsayin matar sunna". Yusuf aka yi murrmushi aka сe "To Amin, mun tafi farautar aure sai mun dawo." A gidan Baba Garba babu kowa daga Hadiza sai mai aiki sai ko mai gadi yana can bakin get. Hadiza ta ci kwalliya amma a saukake kwalliyar matafiyi yadda ba zata wahala ba, jefi-jefi ta kan dan dubi agogon hannunta ta na zargin Amiru da son ya ja masu tafiyar dare. Yusuf ya isa gidan Baba Garba ya rubuta ma Hadiza wasu "yan maganganu na rokon arzikin son ya ganta, maigadi ya kai mata wasika har gabanta ya fadi a zaton ta ko Amiru ne ya kara aikowa yana bada hakuri, to sai tagaYusuf ya rubuto ta ja tsaki ta tsaida maigadi ta rubuta masa amsa kamar haka Yusuf Ni Hadiza yanzu na manyanta a halin yanzu a gani na kuma wannan zamani na da zan sarrafa al'amurana na zabin aurena saboda haka ya dace na auri mutumin da bana so? Maigadi ya mika ma Yusuf takarda wani daci ya daki zuciyar sa, wai shi ko maye ne bai kyale yarinyar nan ne? Tabbbas ya san ya yi nacin son Fa'iza to amma itå Fa'iza bata nuna masa masifar kiyayya irin haka; nan da nan idanunsa suka yi jajur ya rinka ganin duhu har shi maigadin, yayin da ita kuma Hadiza tana can tsaye gindin taga tana kallon irin halin da Yusuf ya shiga da ta ga ya shiga motarsa ta saki labulen ta dan rintse 22 idonta ta ja tsaki ta ce,`shit kawai'. Ta kwanta bisa gado ta rinka tuno irin son da ta nuna masa a da anan ma ta kara tsanarsa. Yusuf na kokarin fidda motarsa daga gidan Baba Garba yayin da Amiru ke kokarin cinna tasa motar ciki, suka rinka huci na jirı zafin dayansu yayin da shi Amiru na jin zafin me ke kawo shi wajen Hadiza idan ba yana samun fuskar Hadizan ba ne? Yayin da shi Yusuf yana jin zafin wai kan wannan Hadiza ke muzanta shi? Tunda Hadiza ta shiga motar Amiru taga canjecanje da dama, ranta ya bata ganin da yai ma Yusuf ne, don haka itama sai ta share shi ta daure ta ta fuskar. Sun sami kimanin tafiyar awa daya da rabi, kafin Amiru ya dan juyo ya dubi Hadiza ya ce, "yaya kina son wani abu mu tsaya nan garin?" Hadiza kanta a sunkuye ta yi tagumi bata tsinka masa ba sai akwai ta girgiza kanta nuna alamuna'a, ta kara takurewa jikin taga, to anan ne kuma abinda rai ke so sai Amiru ya dan rikice ya yi yakace dama bai bullo ma Hadiza da hushi ba, ai fa sai ya shiga rarrashi, na tsawon lokaci amma bai shawo kan Hadiza ba. Amiru ya ce, "Amma a gaskiya Hadiza kin bani mamaki ca nike idan duniya da gaskiya nine da hushi, ki d
🏠