NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 7 of 26

lumshe ido kamar bai ji abinda ta ce ba, zuwa can yace "Wallahi kuwa". Ya mike ya nufi dakinsa yace ma gwoggo a cikin ledojin nan a duba akwai busasshen kifi a dauke a gyara kada ya lalace. Kwana biyu da dawowar Yusuf duk ya fita kamannunsa domin mugun zazzabi da damuwa ta sakar masa, tun Gwoggo Halima nayi masa dariya ta dawo abu ya dame ta. Aka diba aka ce kila maleria din sa ce ta dawo likita yace, sam ya auna jinin babu maleria, to ai fa sai gwoggo da malan Tukur suka shiga neman masa maganin gargajiya, kamar na shawara da basir saboda irin sambatun da aka ji yana yi a hankali Malan Tukur ya lura duk ciwon da ake tunanin yana damun Yusufa ba su ne ba, sai kawai ya koma rokon Allah wanda a kullun yana rubutawa Yusufa Bissimillah kafa dari babu daya sannan addu'ar (Ya Hayyu Ya Kayyum bi Rahamatika Astagfirillah) ta zamanto abin ambaton Yusuf a kodayaushe, cikin ikon Allah wannan su ne sanadiyar warkewar Yusuf tas, ya murje ya roki gafarar mahaifiyarsa. Yusuf ya fid do takardunsa ya shiga neman alkı lunyulungu kamar karamar hukuma da ma'aikatar karamar hukuma da maʼaikatar ilmi ko za'a dauke shi malamin makaranta, har dai gidan redio Katsina ya leka amma shiru ka ke ji. Babu dare babu rana ya rungume Malan Tukur tamkar yadda zai rungume mahaifinsa a kullun yana ta dibar karatu da nasihohi da dabarun zaman duniya, idan har baya tare da Malan to yana shagon Falanke tela yana hira. 14 Falanke tela kamar yadda su Yusuta kan krasa sunansa na gaskiya Sha'aibu, aminin Yusuf ne tun suna yara, illa dai kawai Falanke bai yi ilmin zamani ba kamar su Yusufa. Falanke mutun ne mai ban dariya ga barkwanci don haka tunda ya fara sana'ar dinkin keke a kullun shagonsa cike ya ke da samari ana hira ana ban dariya yanzu haka Yusuf sai ya kai karfe dayan dare a shagon Falanke suna hirarsu, wani zubin har Yusuf ya amshi maballi ya rinka taimaka masu. Kamar kullun yau jumma'a da la'asar sakaliya Yusuf ya shiga shagon Falanke sai yace, "Falanke za ni gidan Malan Tukur akwai wata addu'a da na ke koyo ina son na gama daukar ta a yau ko za mu tare ne, daga can sai na raka ka Funtua sayen zaren dinki?", Falanke yace "Wannan zance na ka Yusuf shine abin yi, daman yau kuiyar dinkin nan na ke yi". Suna zaune gaban Malan Tukur yana baiwa Yusuf karatu, duk sha'awa ta kama Falanke, ya rinka raya ma zucıyarsa lalle shi ma zai dawo daukar karatu wannan dunıyar shirme ce kawai. Mota irin ta daga wane sai su wane ke iya shigar ta a kasar nan ta danno kai ta shigo zuwa kofar gidan Malan Tukur, gaba daya su Yusuf suka raja'a wajen kallon wannan galleliyar motar tamkar gajimari. Direban ya fito da sauri ya bude mai motar mota. mota. Alhaji Yahaya ya fito cikin kyakyawar shiga kai kace domin shi aka kera wannan mota. Yusuf da Falanke suka rusuna suka gayas da Alhaji Yahaya yayin da Malan Tukur ya mike suka shiga dakin zaure shi da Alhaji Yahaya domin su gana, kimanin shekara goma sha takwas kenan Alhaji Yahaya na zuwa wajan Malan akan wasu bukatansa na duniya. Alhaji Yahaya babban ma'aikaci a Abuja, haifaffan garin Katsina ne, kusan Alhaji Yahaya na daya daga cikin manyan ma'aikatan da Katsina ke takama da su a matsayin`ya yanta. Sun jima suna zantawa da Malan aka bukatar da ta 15 kawo shi. Malan yace, "Kamar kullunı hana son ka ji komi Insha Allah za mu kai kukanmu wajjen Ubangiji, abinda kuma duk ya zartas mu dauka shi ne mafi alhairi a pare mu". Alhaji Yahaya ya yi murmushi zuciyarsa ta yi mai dadi don haka ya ke zuwa wajen Malan domin malan mutun ne mai dayanta Allah. Malan Tukur yace "Alhaji akwai wani taimako da na ke nema a wejenka ina fatan za'a taimaka min idan har an ga abin bai fi karfinku ba". Alhaji yace "Haba Malan kа fada mana". Malan yace "yaro gare ni ga shi nan waje ya kammalo karatunsa na jami'a amma mun nemi aiki mun rasa, shi ne zaka taimaka ka samar masa aiki". Alhaji yace "A kira shi Malan"; Malan ya kwallawa Yusuf kira. Alhaji yace, "Ina takardan imakarantar taka?" Yusuf gabansa ya fara bal bal, duk farin ciki ya mamaye shi tabbas ya san batun aikin sa ne kuma babu abinda zai hana irin su Alhaji samar masa. Yace "Ranka shi dade su na nan". Ya dubi Malan ya ce "Baba suna cikin takardun ka na zaure bari na je na kawo" nan da nan Yusuf ya milka takardu hannunsa na rawa. Alhaji Yahaya ya duba takardun Yusuf da kyau ya kada kai yace, "Bapu komi Malan ai yaron ya yi abinda ko wacce ma'ikata ke so, zan iya samar masa aiki a ko ina, amma ba dole ne sai aikin gwamnati ba ko na kamfani ne masu zaman kan su zan samar masa". Yusuf ya karkatar da kai cikin murmushi yace, "Godiya nake ranka shi dade". Alhaji ya fid do katinsa mai adireshinsa na gida da na ofis ya baiwa Yusuf yace ka same ni Abuja ran talata mai zuwa. Yusuf ya fito shi da Falanke suna ta murna da zumudi, Falanke yace, "Don Allah Yusuf idan Abuja aka aje ka nima ka yi min hanya na koma can da zama an ce sana'ar dinki tafi ci a can". Yusuf yace, "Insha Allah na yi maka alka
🏠