NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 6 of 26

an itace rana ta farko da ya fara jin kunya da cewa wai yana son Fa'iza da aure. Ya yi karfin hali ya daga kai yana kallon mutanen da ke kai da komowa a kofar gidan su Fa'iza, babu wanda ya damu da shi tamkar dama bakon Malan Inusa ne ba wai na diyar gidan ba. Mota da mutun biyu a gidan baya direba na janye 'da su, suka iso gidansu Fa'iza, nan da nan kowa da kowa ya maida hankalinsa a kan wa`annan baki hatta Malan Inusa ya mike ya nufi wajen su, yayin da ya ke tafiya ne ya ke cema Yusuf "Ina jin ma yallabai ne Shehu angon Fa'iza". * Yusuf ya mike a hankali ya tari yana tanagal - tangal, a haka ya rinka tafiya a kalla ya yi tafiyar awa biyu cif a kasa, can hanyar Hanwa low coast ya mike ya sami wani tsaunin dutse ya haye ya yi zaune. Ga abinda ya rinka fadi: "Fa'iza ba ki cuce ni ba, babu wanda ya ingiza ni cikin wannan wahalar sai ni kai na Yusuf sai ko kaddara" Ya yi shiru sannan ya ci gaba, "To wai minene laifin Fa'iza anan? Idan ma Allah ya isa na yi mata lalle zata dawo kai na in ga bala'i, na rasa Fa'iza na rasa rayiwata, ina son Fa'iza a yau na yadda Fa iza bata so na. Why?" Abinda Yusuf dai bai da labari shi ne, a lokacin da mahaifin Fa`iza ya ce lokaci yayi su ba shi mijin da suka zaba, babu tantama Ismail Fa'iza ta fiddo, anan take mahaifinta yace, "Fa'iza idan dai ni zan ba ki shawara ki dauka Isma'il ba mijin aure ba ne, domon na yi iya bincike na banji gaskiyar sana'arsa ba, saboda haka idan aure za ki yi na tsoron Allah, ki kiyayi Isma'il". Ana cikin haka ne, a wata rana sun je filin jirgi rakiyar Baban su Allah ya dora idon Shehu dan gwamna na wannan zamanin akan Fa'iza. Alhaji Abba yayi binciken da musulunci ya kayyade aure ya fada akan Shehu. Yusuf ya yi kuka daga karshe yace, "A yau babu Fa'iza, babu Dije tana can gidan wani mijin". Amma rashin Dije alhairi ne domin ita ma ya san ba wani son shi take yi ba, auren kawai take so ayi mata. Ya duba agogon hannunsa karfe goma da rabi na dare, ya mike ya nufi gidan su Awal, a kalla hankalinsa ya dawo jikinsa ya fada a fili "THE GAME IS OVER!" Tafiya yake har ya ga ji likis, gajiyar ta fara tambayarsa, ya rinka jin kamar ya watsar da kayan da ke hannunsa wato dai tsarabar Fa'iza amma kuma ya bai wa kan sa shawara gara ya jure ya rike ya kai ma su Sarai kada asarar ta yi mai yawa. Ya isa gidansu Awal karfe daya saura na dare, abin mamaki Awal na zaune a zaure yace "Awal lafiya baka kwanta ba?" Ya ce "Ina zan kwanta na yi bako ya bace a gari, don Allah ina ka je Yusuf?" yace "Bar ni kawa Awal ba ni ruwan sanyl na sha." Ya kawo masa ruwa har da damammar hura a kwano, 12 Yusuf ya sha nan da nan idanunsa suka kara kadawa su kai jawur. Yace, "Yanzu nan saboda Allah Awal ka san an daura auren Fa'iza?" Awal yace, "kai yanzu din nan a yadda ka zo kana ta faman rawar jiki ko na shekara ina fada ma an daura wa Fa'iza aure yaushe za ka yadda da ni? To ai garama dai da hakan ta faru, wallahi Yusuf baka jin magana haka kawai da rana tsaka ka canza halayyarka, ni wallahi cikin sha'anin nan mahaifiyarka kadai na fi jin tausayi, bayan irin kuncin da ka saka ta na jama'ar gari sai kuma yadda ka rinka mai da kan ka dan karya saboda Fa'iza. Shi ne, ka yi ma Allah Subahanahu godiya da bai makareka da auren Fa'iza ba, sannan ka roki mahaifiyar gafara a bisa karyace - karyacen da ka rinka yi mata". Yusuf ya dafe kan shi "Don Allah Awal zan sami panadol na sha kai na tamkar ana fasa kwakwa". Awal ya mike ya bude wata jaka ya mika masa panadol. Yusuf yana jin Awal na ta sharara bacci yayin da shi komi ya yi mai zafi daga zuciyarsa har kwakwalwar kan sa, ya rinka jin shin a duniya akwai wanda ya taba shiga kunci irin na shi? domin shi dai yanzu bai ga kamar Fa'iza ba a duniya son ta ya ke, son da bai iya misiltawa dan adam yayin da ya san shi da Fa'iza har abada, to wannan kalmar ce ke wahalad da shi. Da safe ya dibarwa Awal tsarabar da ya yi ma mutanen gidansu. Awal yayi godiya ya dubi Yusuf yace, "Ka tabbata za ka iya tafiya Bakorin nan ko dai mu je na raka ka asibiti, ka ko ga yadda yanayin jikinka ya canza?" Yusuf yace, "Babu komi zan lallaba, ai gida za ni" Awal ya ce, "Shi kenan mu je na raka ka tasha." Ya isa gida, Salmanu na zaune cikin shagonsu, wasu yara na sayen Omo da magi mai tauraro, ya hango Yusuf na sauka bisa dan acaba da wani dan acaban ya labto kayan Yusuf nan da nan Salmanu ya sallami yara ya nufi wajen Yusuf, yana yi masa barka da`zuwa tare da amsan kaya yana shiga da su cikin gida. Rabon da Yusuf ya ga fara'ar Gwoggo Halima tun zamanin yana neman Dije sai 13 ko yau tamkar zata kama shi ta rungume. Ya sami tabarma ya kishingida da ganinsa ba sai ka tambaya ba ka san yana tattare da matsaloli Gwoggo ta kama aje masa abinci a gabansa amma ban da ruwa babu abinda ya taba. Ya fara tambayar jama'ar gida kamar kannansa da su Malan aka tabbatas masa kowa lafiya. Gwoggo tana murmushi tace, "Sai kuma mu ka ga Fa'iza da wani ana hidimar daurin aure ba da kai ba?" Yusuf ya
🏠