NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 24 of 26

ar gona yaddiisl je sai dai aka maido shi gida barin jikinsa ya shanye." ed em irla Karfe shidda na yamma Hadiza da Saminu sun iso gud asibitin Funtua, hankalinta ya kara tashi yadda ta ga bakin Alhaji Kado ya jirkice tayi kuka ta yi kuka har sai da ta san vavix kuka ba zai mata maganin komi ba sannan ta hakura. Tana erda nan zauna tare da su Malan Iliyasu can wajen karfe tara nalauek dare sai ga suInna Tambai, anan suka dawo da wani sabon kukan.stnores s вnenлu ly usb st awuat ly et aslulleo isa Inna Tambai ta lallashi Dije suka tafi Bakori ta kwanaA a can amma asuba na yi ta dawo Funtua gani take ta yisogal kamar zarta iske ya mutus sy syhams haао ву вyhsb ly вy ise Misalin karfe daya da rabi na rana Armiru ya iso yace mata ya yi waya ne Kaduna matar Baba Garba ta ke sanar 00 61 masa garabinda ya faru shi ma daga Abuja ya ke. Tace, "Wallahi ciwon Baba kuma ya tashi". Amiru ya ce, "Dama yayi masa kárfi haka?" Tace, E' yace, "Amma Hadiza ya dace mu kai shi wata asibitin da tafi.wannan". Tace, "in dai law sbud cayill 57 82 on samu ne na fi son A.B.U. Zariya". Yace, "A to barı mu ja mu ga likitan wannan asibitin ko?" Suka jora zuwa ofishin likita suka yi masa bayanin bukatarsu ya dauko katin Alhaji Kado ya duba sannan ya rubuta takarda wadda za'a kai can A.B.U. Zariya. Ya debe su a motorsa sai Zariya sai da ya tabbatas an duba Alhaji an bashi gado sun shiga yi masa abinda ya dace, sannan yace Hadiza ta zo ya kai ta G.R.A gidan abokinsa da safe sun kawo ta shi kuma ya wuce Kaduna. Kimanin kwana biyar haka Amiru ya rinka jele hanyar Zariya har sai da ya ga sirikinsa ya fara gane mutane, sanna kuma kullun zai ga Hadiza ta rungume shi tana ba shi abinci. Sai hankalin Amiru ya kwanta ya ci gaba da harkan kasunwancinsa. Da zai tafi Lagos sai ya bar wa Hadiza cellular din sa ya ce "idan akwai wata damuwa ki yi min waya, da zarar na sauka Lagos zan sanar da ke lambar wayan daki na, haka nan ga ta ofis din mu na Kano da Abuja ga kuma na abokina Yusuf shi ma yana aiki ne a Abuja sannan ga ta mahaifina!" Hadiza ta bude ido ta се, "lah ba na iya yi ma Baba waya," ya ce, "haba Hadiza ashe, shi ma ba Babanki ba ne, in dai ki na cikin damuwa, ki buga mashi." Ta raka shi har gindin mota, tana yi masa Allah ya kiyaye, hanya, ya ce, "kin tabbata dai wa'annan kudin sun ishe ku?" ta ce, "Haba Amiru sai kace wadda zata sai rai, yaushe zamu kashe wa'annan kudade." Tana zaune kusa da Babanta tana bashi ruwan lemo sai cellular ta yi tsuwa, ta dauka ta yi kunnenta a zatonta ko Amiru ne, sai ta je an ce, "Ina Amiru" ta ce, "ya je Legos?" aka ce, "wa ke magana?" ta ce "matarsa ce Hadiza" sai ya yi dariya ya ce, "Ran amariya ya dade, idan ya bugo ace ina san magana da shi abokinsa ne Yusuf daga Abuja;" ta ce "zan sanar da shi, sai anjima." Alhaji Kado ya rinka badardarawa maganarsa guragura wai menene kuma wannan? Hadiza ta yi mai bayani. Ya bude baki numa alamun yana mamaki. ita da su Malam Iliyasu suka rinka yi mai dariya.. 58 Ana ta murna sauki na ta samuwa, daga Legos Amiru ya yi mata waya ya ce, "yau dai sauran kwana ashinrin da biyar bikinmu. Ubangiji Allah ya ba Baba lafiya don mi ji dadin shagali." Hadiza ta ce, "amin" ya ce, "ki gaida min Baba, sai na zo gobe." Da azuhur bayan su Malam lliya sun yi mai alwala sun kawo dutse ya yi sallah. Kafin ya kwanta, sai shakuwa har idonsa na kafewa. Nan da nan Hadiza ta ruga kiran likita, suna isowa tana rike da hannun likita. Likita na duba Alhaji Kado, amma i.na, babu Abdulkadir, ya amsa kiran sarki Allah. Hadiza ta yi waya dakin Amiru amma shiru ba'a dauka ba, ta yi ofis din su nan ma ana ta surutu bisa layin, kwatsam idonta ya fada bisa lambar Yusuf. Ta na yi bugu daya, Yusuf din ne ya dauka, ta ce, "don Allah ka nemi Amiru ka sanar da shi sirikinşa ya rasu yanzu a nan Zariya." Kafin Yusuf ya yi wata tambaya, ta kife layi. Tana sharan hawaye a fice zuwa bakin titi, ta nęmo masu motar haya wadda zata dauki gawar Alhaji Kado. Kafin mangarib har an kai shi makwancinsa, ya bar su Hadiza da juyayin rashinsa da sauran rigingimun duniya wa'anda ba su karewa sai in irin wannan ta afku. Ana sallar mangarib, yaya Amina da mijinta suka iso amma ita anan zata zauna har sai an yi sadakar uku. Kashegari Hadiza da Inna Tambai suka gyara dakin marigayi Kado suka shinfida dardumarsa inda za su rinka zama kenan. Ita da yaya Amina da Inna Tambai da mutanen da suka zo masu ta'aziyá, koda yake inna Tambai bata ga ta zama ba domin Hadiza ta bayas da kudi an yanka rago sannan an sawa buhun shinkafa ta ce a dafa saboda zuwan baki na nesa. Aiko misalin sha biyun rana sai ga motoci biyu ta maza da mata daga Kano iyayen Amiru. Inna Tambai ta yi murna da shawarar Hadiza da suka gyara dakin marigayi da ina za su saka wa'annan kosasun mutane? domin dakin su Ankudi, zaman shi sai ka daure. lyayen Amiru har da daron sinasir da daron waina 59 da na shinkafa suka zo suka ce a baiwa jama'a sadaka, sannan kuma
🏠