an sakon domin ita dai
ba yarinya ba ce irin kallon da Amiru ya rinka satan yi mata
ta san kallon so ne, ire-iren kallon da maza kan yi mata ne,
amma yau na Amiru ya sha bamban da na kowa.
Asabe tu dauike jakar Hadiza ta balle ta zari naira dari
cif ta ce "wannan shi ne lada na, domin samun miji kamar
Amiru sai yar gata wajen Allah. Gaskiya kina da daurin
gindi ga wanda ya yi ki Allah!" Hadiza ta yi dan murmushi
tace, "kai Asabe wai ke ki ka daura mana auren ne da shi
sai cewa kike mijina". Asabe tace, "Amiru dai ya amshi
kwatancen gidanku da lamban wayarki ta nan ofis don Allah Hadiza kada ki watsa mana kasa a ido in dai kina so ki
ji dadin rayiwar aure to ki mika wuyanki ga Amiru."
Mahaifin Asabe ya zo Kano fatauci, to a gidan kakansu
Amiru ya zauna a karshe suka rinka hulda da mahaifinsu
Amiru to wannan itace dangantakar da ta kulla zumunci
mai karfi a tsakanin zuri`a biyu, duk su Asabe a Kano aka
haifesu, gidansu Amiru tamkar gidan mahaifinsu ne, yanzu
tana zaune ne gidan babban yayanta da ke aiki a wani
kanfanin kusa na Alhaji, Baban Amiru anan Kaduna itama.
Asabe ta kammla jami` arta.
A daren jiya ne Amiru ya je gidansu wajen yay..ta
akan huldansu ta kanfanin Alhaji to anan ne ya ke cewa,
"Asabe gobe zan zo bankinku don wasu kudi da na ke so a
tura su zuwa Japan."
Amiru na shiga matarsa wajen cin abinci ya nufa,
yana tafe a motarsa yana tunani me ya hana wannan
kyakyawar yarinya aure? Kuma da alama babu alamar sakarci
a fuskarta domin mace mazinaciya kallo daya namiji zai yi
mata ya gane, ya fada a fili, "kodayake komi fa mukaddari
ne, kila lokacin auren na ta ne bai zo ba."
Yana isa Arewa Chinese Restaurant bai shiga ba sai
ya kashe motar ya fito ya tsaya ya jingina jikin motarsa ya
50
jawo wayarsa ceilular y narsa lambobin Hadiza na ofis, ta
dauka yana jin muryara sai ya ji kamar ya saki wayar duk
ya bi ya rude, hai dauka haka zai tsinci kan sa ba, amma
kuma vana tsoron kada ya zama ragon maza. Sai ya daure
yace, "Hello Hadiza, Amirun ki ne, kin ga ne ni?" Nan da
nan itama Hadiza ta ji wata irin kasala da gajiya sun dirar
mata kai wannan wane irin mutun ne ko halinsa bata sani
ba, amma har taji ta bada ran ta gare shi, ta jure ta yi
murmushi tace, "har ka zama nawa, ashe abin ba bu wuya?"
Ya kyalkyale da dariya yace, "To me ya yi saura idan ka ga
abinda zuciyarka ta amince mawa ai sai ka mika ma abin
nan sauran gangar jikin ka, ita kurna ta shiga kasaftawa
amma don Allah Hadiza idan an tashi kasafta ni a bi ni a
hankali domin na dade ina neman wadda zan mallakawa
kai na na rasa sai yau ke Allah ya baiwa."
Hadiza ta lumshe ido ta yi ajiyar zuciya tace, "Don
Allah ka bar ni na yi aiki, ka ko ga tulin aikin da ke bisa
tebiri na?" Ya ce, "zan iya barinki amma saii kin ba ni
wayarki ta gida". Ta sanar da shi, yace, "sai kin ji waya ta
anjima".
Tana isa gida aka sanar da ita wayar Amiru uku, а
ranta tace, lalle mijina dai ya zo; kafin ta yi komi wanka ta
fara yi wai ko taji karfin jikinta, akwai aiki kam a ofis amma
tunanin Amiru ya fi saukar mata da gajiya.
Ta gama cin abin ci ta hau gado don ta dan huta ta
san kila yanzu Amiru zai sake yo waya amma sai maigadi
ya sanar da matar gidan wai ana magana da Hadiza in ji Amiru.
Yana zaune cikin motarsa amma kofar motar a bude
take don haka ya dan zararo kafafunsa waje, ya saka kaset
na wakar Sirajo mai Asharalle a cikin wata waka da ya yi
masu a birnin Kano a lokacin bikin wani abokinsu. Hadizan
ta iso vana rangwada kai da gani ka san saurayi ne ya yi
kiran, ta yi mai sallama, ya juyo ya amsa salamarta sannan
ya fito sun gama gaisawa ya leka cikin mota yana kashe
kaset din Sirajo taca, "Haba don mi za ka kashe? Ai ko
wakan da dadi." Yayi dariya yace, "Idan kina so bari na ba
51
S
S 1823
ki aron kaset din, tunda kina son wakan Sirajo ashe ran
bikin mu zai cashe kenan" ta yi murmushi tace, "kai ne dai
yau Allah ya hada ni da mutun mai yanke komi da kan shi".
Yace, "Haba Hadiza duban ni fa na zama tuzuru saboda
zaman jiranki? Ya dace ace yanzu ina da 'ya'ya biyu amma
rashin samunki kinga ko daya ba ni da shi". A zuciya Hadiza
ta rinka raya mata kai lalle Amiru ya yi gaskiya babu wanda
rya dace da ita face shi, ita kam ko wane irin hali gare shi
ya yi mata ta na son shi yanzu ta ga mijin aure. Ta daga kai
ssuka hada ido sai kowanne ya yi ajiyar zuciya.e
Yace, "Hadiza abinda zai tabbatas min da cewa kina
SASO na shi neina son ki ban tarhinki kaf amma don Allah har
sida labarin samarinki domin na san dai kamar ki ba kya rasa
ewexsmai so. bbaw nemen eni abeb sn nimob iletnsd
zid
Ta murde hannayenta bisa kirjinta tana kallon kasa ta
warware ma Aminu labarunta kaf illa dai kawai wajen labarin
wahalas su Ankudi bata fadi mashi ba haka han wajen
sdaurenta da Yusuf sai tace za a yi mata auren zumúnci da
yrdan uwanta a zamanin tana firamare sal shi dan üwan ya
ki yace ta yi masa kankanta. amiins
a Amiru ya yi shiru yace, "lo yanzu fa da ki ka girma ai
6anya dace ya dawo me ya h