akori.
Hadiza ta cika `ya hazika, jarima kamar namiji domin
sai kace ta taba zuwa aikin Hajji komi ita jke ma ubanta,
idan masallaci za su tana nan rike da shi, idan wajen cin
abin ci ne mai kyau ta ke zuwa tana sai mashi. Hadiza bata
mantawa suna dawafi tana makale da kafadar mahaifinta
sun isa dai dai indararan rahama ta ji Baba Kado na sheka
mata albarka tare da rokon Allah ya baiwa Dije mijin kwarai,
itama a lokacin tana rokon Allah ya gajarce mata wannan
zama ya kawo mata mijinta, jin abinda mahaifinta ke fada
sai ta ji idonta ya cika da kwalla taf domin tausayinsa.
To haka dai aikin hajjin su Baba Kado da Hadiza ya
kasance, bayan an sauka arfat an kammala da jifar shedan
da dawafil ifada sai Hadiza ta dauki Baba Kado suka shiga
tsarabe-tsarabe, ita kam ta sawo akwatuna uku da kaya a
47
a ciki sai abin hannun zinari guda hudu da sarkan zinari
cikakken saiti, to sauran sayayyar fa duk na'urorin kicin ne,
idan ta yi aure ta zuba a kicin dinta.
Baba Kado yace, "Wai Dije wa'annan injinan na mene
ne? tace, "Baba akwai na hada biredi a kuma gasa cikin
`yan mintoci haka nan akwai na daka nama ayi danquu
nama akwai na daka sakwara akwai ma wanda zai fere
maka dankali duk cikin dan kankanin lokaci, wannan
tukunyan kuwa zata iya dafa kafar sa ko kan rago cikin
'yan mintoci." Malam ya dafe baki yace, "ke Dije ba ko
karya suke ma ku ba dan dai ku yi masu ciniki ne?" Tace,
"Haba Baba duk muna anfani da irin su gidan Baba Rilwan."
Tafiya ta yi kyau domin su Alhaji Kado an dawo gida
lafiya, a kullun zauren nan na shi shake ya ke da dattawa
kaman su Malam lliyasu, Alhaji Kado ne zaune bisa wata
sabuwan darduma ya zuba jallabiya fara sol mai dogon
hannu ya dora rawani da kanbun wuya, da gani dai ka ga
sabon Alhaji, ba su komi sai sauraren Alhaji Kado yana
bada labarin kasa mai alfarma. Malan lliyasu ya ce, "to
Alhaji yaya ciwon ka fa, ina ta yi maka zullumi kada ciwon
nan ya hana ka sukuni?" Alhaji Kado ya ce, "abin mamaki,
sam bai taso min ba, in ban da sau daya a Madina muna
shirin barin ta, ai ko sai ciwon kai ya taso min nan da nan
Hajiya Dije ta kai ni asibitin larabawa kada ka so kaga irin
magungunan da suka hada min yanzu haka ina nan da su
cikin jaka, cikin ikon Allah dan lokaci kadan na nemi ciwo
na rasa, na tambayi Hajiya Dije ko nawa ta biya? tace min
ai su can kasan magani kyauta ne, ko aikin tiyata za a yi ma
mutun duk a kyauta ne."
To haka dai Alhaji Kado ya kasance, yayin da Hadiza
ta adana saye-sayen aurenta a karkashin gadon Inna Tambai
ta sallami kowa da tsarabarsa sannan ta zarce Malunfashi
ta ba su tasu, ta kwana bakwai a can tana baccin gajiya
kafin ta koma Kaduna.
Abuja ma kwananta daya wajen Hadizan Jos, a Jos
ne bata samu kwana ba domin tana son ta dawo Kaduna
da wuri ta gama shiriya-shiriyan ta kaman su gyaran gashi
AR
a salun zuwa kai sabbin dinkunanta domin washekare zata
koma aiki saboda aikin na su ne babu isasshen hutu.
KASHI NA GOMA SHA DAYA
Yau kimanin wata daya kenan da `yan kwanaki da
dawo war su Hadiza daga kasa mai tsarki, karfe goma sha
daya na safe tana zaure bakin aikinta, Asabe wata `yar
kabilar ibira ta zo wajen Hadiza ta zauna tace, "kai Hajiya
Hadizz kowa idan ya je aikin Hajji yana yin baki amma ke
sai kyau naga kin kara." Hadiza ta yi murmushi tace, "ke ko
ga ni fa ga Babana me zai dame ni?" Suka bushe da dariya Hadiza tace, "Hala baki da aiki ne ko ki ka bar mazauninki?"
Asabe tace, "Wannan ofis din za'a rasa aiki na dai zo ne na shaida maki muna da walimar suna ran asabat din nan a
gidanmu." Hadiza tace, "Idan har ba zani Malunfashi ba insha Allah za ki ganni."
Daga bayansu aka rinka yi masu sallama Asabe ta juya ta dubi mai magana suka amsa masa. "AMIRU NE” ya ce, "Asabe na je mazauniki ban iske ki ba aka ce min
kina nan." Asabe ta mike da sauri tace, "lah har ka įso, yaya kaga manaja?" Yace, "har akawuntan ma na gani
mun gama da su, komi ya kammala", tace, "yayi kyau" Duk maganar da su ke da Asabe yana satan kallon Hadiza, daga karshe ya kara gayas da ita itama ta gáyas da shi
cikin nuna damuwa, sannan ya yi mata sallama suka fita
tare da Asabe zuwa gindin motarsa, tace, "yaushene tafiya Japan din?" yace, "Ban fidda rana ba amma dai ban wuce sati daya yace, wai Asabe na tambayeki mana", ta kara
matsawa kusa da shi tace, "me ya faru?" Yace, "Don Allah
wannan yarinyar matar aure ce?" Tace "lah Hadiza bata taba aure ba." Ya ce, "kina ganin idan na ce ina son ta zata yadda ta aure ni?" Asabe tace, "E to babu ruwan ta dai da kowa, amma kila mijin ne bai zo ba." Amiru ya ce, "yanzu ga ni na zo" Suka kyalkyale da dariya, yace, "kina da
wayanta ta gida?" Tace, "E amma ban rike da ka ba sai dai
ga ta ofis." Ta fada masa yace yi mani kwatancen gidansu
49
anan ma Asabe ta yi masa yace, "ki taya ni addu'a Allah ya
ba ni sa'ar Hadiza" Ta yi danya ta ce, 'To amin'.
Ta koma wajen Hadiza a guje tana murna, tace
"Albishir Hadiza sai kin ba ni goro." Hadiza dai sai dariya
ko da Asabe bata gaya mata ba ta s