NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 2 of 26

allah suka kebe da Amiru yana tambayansa, labarin Fa`iza. Yusuf ya yi murmushi yace, "Wallahi yanzu ma hidiman ta na zo yi anan Kano." Amiru ya yi shiru yace, "Baka dai dauki shawarar da na ba ka ba kenan a wasika ta?" Yusuf yayi murmushi. Amiru yace, "Ni dai murna ta daya da baka batawa yarinyar nan `yar kauyenku rayiwa ba". Yusuf yace, "Wai Hadiza? Na ji ance ma sun mayas da ta hannun kakanninta can wani kauye kusa da Dabai ina jin sun samar mata wani mijin ne a can. Ni abinda ke damuna yanzu shi ne Fa`iza ta shirya kasaitaccen bikin zagayowar ranar haihuwarta to shi ne nake son na dan nuna tawa murnar." Amiru yayi murmushi ya ce, "me ka ke so ka bata? Allah yasa bukatar bata fi karfi na ba. Yusuf yace, "kada ka damu da karfi na zo domin akwai wasu. kudi da a kai man biyan bashi tun zamanin mahaifinmu na da rai ranci kudin to shi ne zan yi anfani da nawa, ga su nan a jaka dubu talatin ne." Amiru ya zaro ido yace, `Yusuf yaushe ka canza halinka ban sani ba? To wallahi bari na baka labari idan kana zaton wa`annan 'yan kudin zai shawo maka kan Fa`iza kana shirmene, domin ina da kanne mata a gidan nan ina kuma kallon hidimar da samari ke masu amma wannan ko kallo bai ishe su ba, saboda duk abinda kake takamar za ka bata akwai dubun su a gidansu. Ban hana ka neman Fa'iza ba illa ina baka shawara idan zata so ka ta so Yusuf amma bana tsammanin kamar 'yar gidan Alhaji Abba na Zariya har kudi za su iya rudar ta.' Wannan maganganu na Amiru kamar ba da Yusur ya ke ba, shi fa ya riga ya yi niyya babu mai hana shi, dole Amiru ya raka shi kasuwa, ya yi sayayya, ya sai ma kansa wasu tsadaddun boyel kala da fari sol da mai ruwan bula yadi biyar biyar zai yi doguwar riga da wando sannan wan takalmi sawu ciki suma masu kyan gaske farare. Gimbiya kuwa ya sai mata leshi mai tsada mai ruwan bula da wata agogo Civic da zoben zinari ya nade su a iril takardar nan ta nade sakon girmamawa. A Kano ya kwana biyu aka kammala masa dınkunan sa. Amiru yace, `Baba zai aike ni Legos wallahi da na halatcı wannan biki na Faiza, ko don in ga wannan Faizar'. Yusuf yayi dariya yace "Na gode Amiru Insha Allah kaine na farko da zan fara aiko ma da hotunan mu na wajen bikin." Yusuf ya yi kokari su je tare da Awal amma Awal din ya ki, yace "Wannan sai manya, ba irin bikinmu ba ne. da dai Wasila 'yar nan Zariya ce dole na je rakiyarta ba yadda zan yi." Yusuf ya cake cikin farin boyel ga takalma wa anda 2 suka dace da su yan zamani ya zuba, ya zuba kyautar da zai ba Fa`iza a wata farar leda ita kanta ledar naira dari ya saye ta, ya hau mashin ya nufi wani studion daukar hoto ya dauki daya daga cikin yaran mai hoto aka tsadance akan dubu daya da dari takwas yace duk motsin da Fa iza ta yi ya dauke ta amma kada ya dauketa da wani namiji idan ba shi ba. A masaukin baki na Alhaji Abba Zariya anan akai wannan biki. Guri kam ya cika ya batse da samari da 'yan mata, na haraban gidan domin a haraban aka yi. Fa'iza da babbar kawarta Shatu suna falo sun gama shiryawa, sai Fa'iza ta je bakin taga ta tsaya ta yane labule ta dubi dan adam din da suka taru albarkacinta ko wanne yaci kwalliya kamar ran sallah. Ta ce `zo nan Shatu ki yi kallo'. Shatu ta isa inda Fa'iza take ta dafa kafadar ta tana kallon jama'a. Shatu tace, Wai ke fa'iza yanzu yaya zaki yi da duk samarinki ne da ki ka hada su anan?' Fa'iza ta yi dariya tace, `Na yi haka ne don kowa ya san matsayinsa, zan nuna masu Isma'il kadai na ke so wanda ya ga zai iya ci gaba da wahala ruwansa'. Shatu ta yi ajiyar zuciya tace Kina hangen Bello ga shi can kamar zai tashi sama don shan kamshi?' Fa'iza ta ce, bar ni da shi yau zai zan matsayinsa.' Yusuf ya harde hannayensa a kirji yana ta dan shawaginsa can Shatu ta hango shi tace, `Fa'iza wancan fa mai farin boyel?' Tace `shi ne Yusuf wanda na ke ba ki labari ina dariya, ni wallahi yaron dariya ya ke ba ni an yi masa baiko saboda ni yasa aka warware.' Shatu ta yi shiru ta tsurawa Yusuf ido, sannan ta nisa, ba tare da ta dauke idonta daga kan Yusuf ba ta ce, "Kin san wani abu kuwa?" Fa'iza tace "kaman me fa?" Shatu tace, "Yusuf din can ba fa karamin namiji ba ne, ina tabbatas maki duk mazan da ke gurin nan babu mai kwarjininsa da zatinsa, ke ki dube shi a hankali in da duk ya gitta sai kin ga kamar yafi kowa girma da kyau, ina so ki lura nan gaba idan yaron nan ya kammala jami'a ya sami aikin da zai huta ina tsoronsa da 'yan mata domin sai yayi 3 da gaske. Allah ya dawo min da Tijjani na lafiya daga Canada sai kin ga kamar su shi 'da Yusufe vet5 Fa'iza ta jima tana kallon Yusuf ko daya bai cikin 'yankayanta, bai bata sha'awa amma maganar Shatu kuab aA san gaskiya ne. rom dub aory wA hab ab syeb uduq Tace, Don Allah Shatu ki dan taimake ni kivinganta sb sY masa jin dadin bikin nan domin na san saboda ni, ya ciwosd irie bashin boyel din can ko kuma ya aro?" Suka kyalkyale da dariya. Fa'iza da Shatu suka keta fili suka fito sai walkiyaw gimbiyar take yi, tafe take tana gaisaw
🏠