NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 19 of 26

a, sannan ta subuls jakarte daga kafada tare da takardun da ke hannunta ta shige daki ta aje ta fada kewaye ta yi alwala ta fito ta vi sallar mangariba sannan ta koma falo ta nemi gefen kalet ta zauna tare da hade kafafunta. Amina ta juya a fusace ta dubetta ta ce "Munafukar banza munafukar wofi, kin je kin shiryawa ubanki karyar da ki ka saba, shi kuma don rashin tunani ya hau kai, to Allah ya ba ku sa`a tunda ba mu da mutunci ba mu da daraja a idónku ai ban ga anfanin zamanki ba anan, domin Rilwan da Isa da Garba duk daya ne sai ki koma can gidan ubanki ki karaci sakarcin ki." Nan da nan Garba ya dakatar da ita yace, "Haba! Haba!! Yaya Amina menene na gorin gida? Mu mun fid da tsammanin Hadiza ta rike `ya yanmu, idan ta rike kanınanta ai mu ta yi mawa, ban ji dadin wannan magana taki bia, don Allah idan rai ya baci a san abinda ya dace a fadi." Duk wannan bai sa Amina ta saurara da bala'i ba haka nan sam bata amince da zamanta ba, sai dai ta koma can Bakori har sai da Garba ya yi ma Rilwan waya yayi ma Amina fada sannan ta dan sausauta amma da sharadin kada Hadiza ta sake zuwa wajenta a Malunfashi. Hadiza ta yi kuka ta yi kuka kamar ranta zai fita ta kwana tana rokon Amina amma kemerme Amina ta ki janye hushin ta. A kodayaushe tana kokarin rubuta mata wasiku na neman gafara amma dai babu amsa. A wata jumma'a ta shirya taje ta yi kwana biyu a Malunfashi, babu dai maganar arziki a tsakaninsu sai dai akwai banbanci tunda ta gaisheta ta amsa. Lokacin da zata koma Kaduna ta shirya tsab, kkarsierita maza suka daukar mata kavanta ta durkusa gaban Amina tace, "Don Allah don annabi Yaya ki yi hakuri, kin ga abin rai, ina iya yin hatsari a yau na mutu ga shi ki na hushi da ni, me zan ce ma Ubangijina?" Amina ta yi jigum zuciyarta s natsu tace, "Tashi ki tafi Allah ya tsare, na hakura." 45 KASHI NA GOMA Tana zaune bisa tebir din ta aiki ya cukume mata wayar da ke gefenta na dama tayi kara ta dauka, sai ta ji ashe shugabansu ne gaba daya nan da nan ta kara kwantar da murya alamar biyayya ya ce, yana son ganinta yanzu yanzu. Ta shiga ofis din Yallabai ta tsaya cikin girmamawa sai da ya umurce ta da ta zauna sannan ta zauna, yace, "А sashen ofishin da ki ke wato (Banking Office) a koyaushe daga ofishin gwamnati akan baiwa wannan ofis alfarmar kujerar Makka to a cikin sa'a wannan shekarar kujerar а hannunki ta fada." Hadiza Abdulkadir yarinya mai cike da sa'a ta yi luu da idanu kamar zata some don murna sai dariya kawai, ta rasa bakin magana, duk irin kalmar da ta furta sai ta ga kamar bata yi daidai ba. A wannan dare ta rasa yadda za ta yi ta runtse ido, ga murna ga tunanin Mahaifinta Baba Kado saboda tun tana yarinya babu bukatar Malan Kado irin yaje dakin Allah, domin bata mantawa ko labari ya ji ance ga wani za shi aikin hajji sai ya yi kokari ya je gidansa ya roki alfarma cewa don Allah in ya je ya roka masu suma Allah ya kirasu su je wannan waje to ita yanzu yaya za ta yi ta tafi ta bar mahaifinta? A gaskiya bata iyawa duk inda zata ci rance insha Allah ita ko za ta cu su tafi tare. Kashegari tana isa ofis abinda ta fara yi shi ne cekin din kudinta na ajiya tabbas tana da kudi da za su kai shi amma babu guzurin kirki ita kuma bata son ta kai shi ya shiga matsala, ga shi yana da lalurar rashin lafiya a tare da shi. Sai ta yi ma Hadizan Jos waya ta gaya mata zancen tafiyarta, ta yi mata murna tace ita ba don ciki ba da sun je, sai Hadizan Bakori tace, "Matar Dakta taimako na ke so." Tace, "tunda ki ka hadani da rabin raina za ki samu fadı na ji." Tace, "wallahi tafiyar nan ce bana son yi ba tare da Babana ba, to amma kudina basu kai ba shi ne na ke neman rance, in Allah ya dawo da mu lafiya na amshi ariyas dina zan maido ma ki." Ta ce, "Gaskiya kin kyauta fadi min ko 46 abinda ki ke so da nambar akwatun ki na banki insha Allah gobe suna iske ki." Hadiza ta fadi mata. Ta shirya ta je Bakori tace, "Baba ka shirya za aima hoto zan tafi da shi domin na biya maka kudin kujerar Makka ni kuma gwamnati ta ba ni a wajen aikina." Malan Kado ya saki casbahar da ke hannunsa yа се "Ke Dije! Kin san abinda kike fadi kuwa?" Tace, "Baba amma ai kun fi karfin na ja ku da wasa." Malan ya sadda kai kasa kwalla ta fara taruwa masá. Hadiza tace, "Haba Baba ai tsakanina da kai sai addu`a, babu zancen kuka anan." Yace, "Bań ni Dije wai yau ke ce kika biya min zuwE Makka? Ni ko idan ban yi kukan dadi ba me zan yi?" Bayan ta kammala da Bakori sai ta zárce Malunfashi ta sanarwa da Yaya Amina. Amina ta yi murmushi ta ce, "To yanzu ke da kina da aure ai da tafiyar ta ku tafi armashi." Hadiza ta dubi uwar a kunyace tace, "kai Yaya in Allah ya yarda zan yi auren ne." Tace, "Ke dai ki ka sani." Duk shirye-shirye sai da Hadiza ta kammala masu, da lokacin tashinsu ya yi ta je Bakori da miotar ofis din su ta dauko Babanta, su Malan Iliyasu da Inna Tambai kamar za su lashe Dije har Kaduna sukai masu rakiya sai da suka ga tashin su sannan suka koma B
🏠