ana ci gaba da kokarin shigar da kansa amma abisa dukkan alamu bai samu
fuskarta ba, ya kawo kudi dubu ashirin ya bata, da farko 39
an ta ki amsa amma sai ta yi tunanin don ta raba shi da
wa'annan kudi har wani abu ne a wajensa? Sai ta amsa ta
yi godiya.
Ko sisi bata taba ba ta adana a banki ma`ajiyar
kudinta. A wannan dare kwana sukai zance daya na Mamud
Hadiza da Hadiza.
Bayan sati daya Mamud ya sake dawo wa Kadina
wajen Hadiza har ya shaida mata idan zai koma Katsina zai
biya ta Bakori ya gaida Malan Kado Sannan ya shiga
Malunfashi ya gaisa da su yaya Amina. Hadiza dai bata ce
masa komi ba domin a ganinta ta kai matsayin a bar ta ta
zabin mijin aurenta da kan ta, saboda ta wuce zamanin
auren dole.
A ranar da yaje Bakori tamkar an yi ma Malan Kado
gafara kowa ya gan shi ya san yana cikin murna, domin
Allah ya kawo masa mijin Dije miji kuma na fada aji ako ina
cikin fadin kasar nan, lalle Allah na amsar addu`o` in bayinsa
in dai sun roke shi, wai yau kamar Dijen da ake muzantawa
gidan sa itace babban mutun irin Yallabai Mamud ke
tsananin so da aure? Baba Kado ya je masallaci ya yi nafila
raka'a biyu yana ma Ubangiji godiya.
a
A Malunfashi ma gidan Yaya Amina bayan tafiyar su
yallabai Mamud, maigidanta Malan Isa ya shigo suka zauna
a daki suka zubawa kudin da ya ba su ido, Amina tace,
"Yanzu Malan duk fadin jihar nan ta mu wanene bai da
labarin wannan mutumi da kyawawan halayensa?" Malan
Isa yace "Ke maganar jaharmu kadai ki ke yi, gaba daya
kasar za ki ce, a gaskiya wannan yarinya ba karamar sa`a
gare ta ba a rayuwa sai kawai ki shirya ki je can Jos din ki
ji yadda aka tsayar da ranar bikin waccan Hadizan sai a zo
aje Bakori a samu a daidaita ayi masu biki rana daya kamar
yadda shi Alhaji Mamud din ya bukata".
Amina ta sadda kai tace, "Ai ni Malan tsakanina da
zuri arku bani da kalmar godiya sai addu`ar fatan alhairi
kawai, duk abinda za ai ma yaro sanadiyar arziki sun yi ma
wannan yarinya ko `ya`yan da muka haifa da kai iyakar
dai zumunci kenan." Ya ce, "Wannan duk ba wanı abu bane
40
mu dai fatanmu Allah ya daidaita Dije da wannan bawan
Allah yasa itace sanadiyar zaman lafiyar gidansa domin na
san aminin Rilwan ne ba tun yau ba."
Amina bata tsaida ranar tafiya Jos ba tana ta yan
kintse-kin tsenta a tsanake, yayin da hankalin yallabai Mamud
ya jirkita ya dimauce bai ganin kyan wata diya mace face
Hadiza a kullun yana bisa hanyar Kaduna yana kuma dankara
mata iyayen kudi ita kam Hadiza tana adanawa a banki.
Suna kammala hidimar kasa shugabansu na wajen
aiki yayi mata alkawarin sun dauke ta aiki, saboda haka
wannan ya fi komi farinciki wajen Hadiza domin tana tunanin
yadda zarmanta zai kasance a Malunfashi kafin ta sami aiki
domin tana ganin bata iya zama Jos babu Hadizan Jos
kuma Mama Binta na so ta auri Mamud.
Suna isa Jos komi ya kacame na shirye-shiryen bikin
Hadizan Jos da Dr. Sani inda zai aje ta Abuja wato inda ya
ke zaune kenan da kanfaninsa.
Kusan a wannan lokacin kowa ya azazzalawa `yar
Bakori ganin ta sami miji mai son ta.
Yaya Amina ta iso, sai da ta turke Hadiza a gaban
Mama Binta sannan ta ji wannan danyen labari wai bata
son Mamud, kafin Hadiza ta ankara har idanun Amina sun
juye tamkar an watsa mata barkono tace, "Tafdijam! Ai ba
ki isa ba dan ubanki, tun yaushe na ke jin labari kina samun
samari kina basarwa, to wannan kam tunda ya nuna kauna
babu abinda zai sa a fasa."
Hadiza ta bata rai ta dan muskuta tace, "Ni wallahi
Yaya bana aurensa, tunda na ce bana iya rayuwar iyalan
sa, ban ga dalilin da zai sa ku tada hankalinku ba."
Amina ta harzuka zuciya ta zo mata wuya, ta ce, "To
sai ki fada mana wanda kike so tunda mu ba mu isa ba."
Tace, "Ni a yanzu ba ni da kowa a dai kara min lokaci."
Hadizan Jos na zaune can gefe daya ta yi tagumi
tana jin badakalar da ke faruwa akan Hadizan Bakori, ita
kanta ta dan tsani Hadizan Bakori anan domin bata son
taurin kai iri wannan, tunda tace babu tsana tsakaninta da
Mamud me zai hana ta hakura da yadda iyayen ta ke so?
41
ita kuma wadda ake abun don kanta ta kakure ta na,
ts shakar kuka. Mama Binta tace, `A gaskiya Hadiza ki baiwa kan ki shawara wannan ba zancen bata rai ba ne har
ayi kuka, zancen gaskiya ne randa ka rasa mai fada maka
gaskiya ka shiga uku, ki jure kawai ayi maku bikinku
hankulanmu su kwanta, ba kya tausayin tsohonki? Wallahi
Mamud yace da suka je gaishe shi kamar ya hade su don
murna, amma kuma ace duk ke kadai ki watsa farin cikin
kowa?'
Wasu hawayen suka taho a guje da ta ji an anbato
Malan Kado, tasa hannu ta goge ta murje hancinta ta ce,
*Insha Allah zan yi masa bayani zai fahinceni." Amina ta ja
tsaki tace, "Zancen banza me ke gareki wanda za ki fadi
mashi, to ko wannan dan iskan yaro Yusufa ki ke zaman
jira?" Hadiza ta yi war da idanu bakinta a bude, itama `yar
Jos ta bude bakin suna mamakin maganar Yaya Amina.
Yaya Amina ta cigaba da cewa, "Idan shi kike kunata kina
da wahala, domin uwar da ta haifeshi ma ance yanzu kuka
take da shi, sa