a lokaci guda ya je ya yi maki
irin wannan cin mutuncin a gaban Inna Tambai mata mai
mutunci da ita? Wai ko dai tabin hankali ya same shi iyayen
ba su gane ba? Amma ni yanzu ina ganin mai kyau kamar
ki a fadin jami`armu? Kin san Allah wani lokaci har tunani
na ke yi na ce ko mutumin kauye zan aura domin ni sai na
ga mutanen kauye kun fi mu kyau". Hadizan Bakori ta cе,
341
"Ina son ki ko don seli ki mai suman."
Hadizan Jos tace Ya Ubangiji Allah ka hada ni da
wannan Yusuf sai na rama maki wulakancin da ya yi maki,
shi din me? Don Allah ba ki ji labarin inda ya ke yanzu ni ko
ne mabuta masa na zage shi tas, wai ke don Allah wace irin
zuciya gareki da har kika kyale shi, ai idan nice har gaban
Gwoggo Halima zan same shi na wanke shi tas."
Hadizan Bakori ta ce, "Wallahi ban kara jin labarinsa
ba. Tun tamba yar da na yi ma Babana a hutuna na farko da
na ba ki labari amma ran da mu ka je Bakori na hada ki da
inna Tambai ki sha labarin inda ya ke clomin ta sani sai dai
ina tabbatar maki idan don ni za ki yi nnasa tsiya don Allah
ki bari domin idan na yi haka ban gode wa Allah kenan ba
a bisa baiwar da ya yi min, lalle na san na shiga fitinu a
dalilin shakuwa da kaunar da na ke ma Yusuf, amma kuma
canjin rayiwar da na rinka samu a dalilin rashin aurensa sai
ta zamar min kwanciyar hankali da daukakar rayuwa."
"A gaskiya na san na so Yusuf amma na san ina kara
son shi ne saboda zan bar azabar gidanmu na sami yancin kaina to irin rayuwar da na samu a gidan mahaifiyata da ci gaban makaranta ta sai suka gusar min da Yusuf a raina, sai kuma Allah ya kara yi min wata daukaka ta basirata wadda a dalilin ta na zo wannan gida, kin ga na sami ci gaban rayiwa, domin rayuwa ma a wannan gida makaranta ce, yanzu dubi ko na'urorin da ke kicin idan ba dalilinBaba Isa ba yaushe zan zo nan har na san su? Ki tuna fa ki ga yadda gidan mahaifina yake to yau y shi na zo gidan da zan kwaba kek ko burodi cikin minti goma a injin sannan na gasa cikin yan mintoci, da sauran girke-girke, haka nan yau ni Hadiza Dije na iya tuka mota bayan mahaifina keke gare shi? Kin san Allah ba na jin haushin Yusuf da rashin aurena domin ko da zan sami irin wannan rayuwar a gidan
sa karshenta zan sha wuya can gaba, domin na lura namijin zara ne. Kin ga ran da ya sami dadin raina min wayau zai yi yace zai auro `yar duniya kamar shi su ci duniya yace ni yar kauye ce, domin sai yanzu na ke tsanar tsarin rayuwarsa cika son komi na `yan duniya ni kuma a lokacin rashin ye
35
wayau sai na rinka biye masa wai don kada ya kira ni
bakauya.
Suka yi shiru na dan lokaci can Hadizan Jos tace,
"Kai! Ni kam Allah ya hada ni da Yusuf na fada masa
magana domin wanda Allah ya ba mata mai hali irin na ki
ya gama mallakar komi a rayuwa amma don tsageranci irin
nasa zai ma Baba Kado haka, a gaskiya Hadiza akwai
yarinyar da Babanta ke son ta kamar ki?"
Hadizan Bakori ta kyalkyale da dariya tace,`Kin ji
sokoncin naki ba, ba ga ki ba da Baba Rilwan ba?" "Yar Jos
tace, "Wai ba kya jin yadda ake kwafdata da zagi wani
lokacin?" Hadiza tace, "Ai ba kya ji ne kamar wata yar
bebi, kyan ki Dr. Sani ya nemi bulala, idan mun kai mashi
ke". Ta kyaikyale da dariya tace "Sai ya nemi bulala biyu
kenan."
*
Abba Abba ya hakura ya sakawa Hadiza Abdulkadir
ko a ranar da suke sallamar ban kwana, wato a rannan zai
koma Bauchi mahaifarsa ya kammala jami'ar Jos. Suna
tsaye ya dafe hannunsa jikin dalbejiya yayin da ita kuma
Hadizan ta mikar da dogon hannunta tana tsinko ganyen
dalbejiya, ya yi gyaran murya, yace, "Hadiza na ji sakonki
wajen Hadizan Jos amma ni ban dangana ba ina tabbatas
maki wata ran sai kin yi da nasanin kin amincewa da ni,
amma dai ga adireshina nan da nambar talfon din gidanmu
ina saurarenki ako dayaushe, zan yi zaman jiranki ko nan da
shekara nawa ne, har zuwa ranar da ki ka janye sarautar
haranta ta soyayya a tsakaninmu". Ta yi murmushi tace,
"Ni kam na fi daukar kauna ta yanuwantaka da
mahimmanci fiye da kaunar soyayya wadda ke karewa balle
a zamanin nan namu mai cike da rudin kwadayi."
Abba yace, "Kwadayi kamar yaya?" Tace "E mana
yanzu za ka kulla soyayya da mutun dan lokaci kadan zaı
iya barinka a dalilin ya ga wadda ta fi ka, kyau, ko ta fi ka
kudi da dai sauransu duk me ke kawo haka in ba kwadai
ba?
Abba yace, "Haka ne amma ni ina daukar wannen
36
dama can ba soyayya bace ta gaskiya ta riya ce, amma
kuma wani lokacin skwai fa kaddara".
KASHI NA TARA
A kullun dai su Hadiza suka ziyarci mahaifinta a Bakori
ba shi da wata magana irin ta, "Wai Dije yaushe za ai aure
ner" Ta kance, "Wallahi Baba da zarar na sami mijin zan
kawo maka shi da kai na ni kai na ina son na yi auren
saboda danmiwar da na lura kana nunawa haka nan kuma
ganin yanzu ni ce babba a gidan nan". To irin wa'annan
kalaman na Dije ta samu ta danne zuciyar Malan Kado daga
zancen aurenta sai ya rinka tausaya mata yana ganin kamar
da gaske bata sami mijin ba ne, ya yi alkawari a ransa zai
daina damunta da magana ya shiga yawaita yi mata a