fadi jarabawar nan!" Hadiza tacе,
"Haba don Allah ki rika addu`a Insha Allah za ki ci ne".
Hadizan Jos tace "Masifar Baba kadai ma ta ishe ni". Ta ce
"Babu komi za'ai nasara."
Suka saki juna, Hadizan Jos ta murda kofa zata shiga
ta juyo suka kara dubar juna ita da 'yar Bakori sukai
murmushi tare da dagawa juna hannu, Hadizan Bakori ta
ce, "Ina nan ina maki addu`a."
Minti uku, minti biyar, har zuwa minti ashirin Hadizan
29
Jos bata fito ba, sai 'yar Bakori ta fara tsorata, tayi uagumi
har tana hardewa wajen adclu'a, zuwa can ta fito ta fada
kan Hadizan Bakori tana fadin taya ni murna Hadizaı, tare
da mika mata takardar.
Hadiza tana dubawa tare da cewa "Eye! Hadizan ba
7 Credit. Credit a lissafi, Credit a turan,ci ai kuma jarabawa
ta hadu Allah ya maida mu clanshinki."
Baba Rilwan ya yaba yace, "To abinda za`a yi gobe
sai ku je Malunfashi ku amso ta Hadiza idan ta ci ku zo na
shirya maku gagarimin bikin taya murna." Hadizan Bakori
gabanta ya fadi ras wato tana cikin hatsari kenan tace,
"Baba idan ban ci ba fa?" Yace, "sai ki sake daukar wata
jarabawar har sai kin ci."
Ai ko rannan 'yan Bakori ba ai bacci ba kwana ta yi
cikin zullumi.
Sun zuba ado na atanpa iri daya wadda Mama Binta
ta dinka masu. Suna isa Malunfashi Hadizan Bakori tace a
wuce zuwa makaranta kafin aje gida, Hadizan Jos tace,
"Haba ba kya bari mu je gida ko ruwa mu sha?" `Yar Bakori
ta galla mata harara tace, "Tafdjam! Ko kin san jiya kvvanan
zullumi na yi, shi ne ba kya tausaya min? Ai duk na kosa na
ga abinda na shuka ko hankalina ya natsu."
Suna isa suka ci karo da malaminsu yace, "Ina taya
ki murna Dije domin gaba daya jihar Katsina ke ce ki ka zo
na daya a kyaun sakamakon jarabawa".
Hadiza ta dubi Hadizarı Jos ta kwantar da kanta bisa
kafadar `yar Jos tace "Na gode Allah da ya fid da ni wannan
shedarar siradin."
Lokacin da suke bude mota suna fita a kofar gidan
Malan Isa, kowanne Hadiza ta koma mashi kamar bakuwa
don tsarin kyau a cikin gida ma Yaya Amina na ta wangale
baki ganin yadda diyarta ta canza wata uku kacal. Abinci
kawai suka ci sukace zasu wuce Baba Rilwan yace kada su
kwana kuma suna son tsayawa Bakori su gaisa da Baba
Kado.
Cikin kwana bakwai aka gama shirye-shiryen karatun
su Hadiza suka kama karatu a jami'ar Jos; Hadizan Jos na
30
karanta fannim Public Admin,yayin da Hadizan Bakori ke
karanta fannin Account.
A farkon shekarar karatunsu direba ke kai su daga
bisani Mama Binta da kanta ta rinka koya masu motar har
suka kware suka rinka kai kan su makaranta, idan an tashi
su dawo gida.
Yadda duk ake son diya mace ta kile to Hadizan Bakori
ta kai karshen kilewa, an goge an cakare har an koma bayan
cakarewar an cake, abin nufi anan Hadiza ta zama macen
shiga gaban kowacce irin kasaitattar mota ko kuma muce
ta shiga dan tsuntsun nasara mai shawagi.
Hadiza Abdulkadir sanbaleliyar mace, doguwa mai
kyan tsayi, akwai ta da shafaffar mara, cikin ta ya dame
daf don haka ya fid do da tudun mazaunanta a sarari
damewar cikinta ya kara sawa kirar nononta su fito das.
Abinda ke jan'ra'ayin jama'a da nacin kallon fuskar hadiza
Bakori shi ne, `yan kananan hakora masu kyalli da daukar
hankali yayin da suka yi daidai da `yan kananan labbanta,
labban da akodayaushe suke walkiya. Hancin Hadiza dan
guntu ne ya yi tsari da`yan kumatunta, 'yan gwibi-gwibi idanuwan Hadiza ko sune abin sha'awa a irin kallon Hadiza
tamkar an watsa taurari don walkiya, mawuyaci ne Hadiza
ta dubi mutun da kwayar idonta bata saukar maka da sha'awa ba, domin akwai baiwar kwarjini na musamman da Allah ya yi ma Hadiza cikin taurarin lelonta wannan kenan, akwai ta, da sambala-sambalan yatsu don haka ne
ma a kullun idan tana latsa lambonin konfuta Hadizan Jos
ta kan ce mata "kai Hadiza Allah ya yi maki baiwar yatsu
na gari tamkar an halitta maki su ne don ki rinka watsa su
a bisa konfuta."
A cikin makarantarsu, Hadizan Bakori bata da kawa ko saurayi baya ga Hadizan Jos sai ko Abba Abba. Shi ko Abba Abba irin karatu daya suke yi da Hadizan Bakori sai dai ya na gabanta da shekara daya, saboda haka, a kullun
suna tare suna bitar karatunsu.
Ita kam Hadiza a yadda ta dauki Abba Abba abokinta,
wani mutun mai natsuwa wanda ya san abinda ya kawo
31
shi amma shi abinda ke zuciyar Abba Abba son Hadizan
Bakori yakes, so kuma wanda ya ke kyautata zaton zai kai
su ga aure, domin shi a duniya bai ga abinda Hadiza zata yi
ba bai birge shi ba, komi na jikinta sha'awa ya ke ba shi, ya
yi kokarin ya furta ma Hadizan amma ta ki bashi fuskar
hakan, har lokacin fitar shi ta zo.
A wata rana yaje ajin su Hadizan Jos ya nemı ganinta,
tace, "Yaya dai lafiya ko Abba?" Yace, "Babu wani abu
Hadiza ina son mu yi wata 'yar magana ne da ke". Tace "To
mu je mu zauna". Suka jera suna tafiya har zuwa wajen da
aka tanada don dalibai idan suna son zama su huta, ya dan
jima yana mata `yan kame-kame daga karshe dai ya yane
rigar kunya yace, "`Yar Jos tsakanina da ku yanzu mun
zama tamkar `yan uwa domin haka ma wasu ke d