NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 12 of 26

Allah, ina laihin wanda ta yi? Allah ya anfana ya isa haka, ki dubi Dije yadda ta koma kusan kansu daya fa da Amina! Sannan ace wai taje jama'a kamar da namiji." Amina tace, "Malan ba ni aron hankalinka nan, ka taba jin inda aka ce aure ya hana neman ilmi ko ilmi ya hana aure? Wallahi tana cikin makarantar idan Allah ya kawo mijin na kirki sai ayi auren, amma yanzu na hanga ban ga wani tsayayye ba, Allah kadai ya san lokacin auren mutun, saboda haka tunda Ubangiji ya baiwa wannan diya taka basirą ka barta ta nemi ilminta ba' a san iyakar al'umar da za su anfana də ita ba, wallahi da yau bata san komi ba su Rilwanu ba za su matsa maka ba akan son ta ci gaba da karatu, mun yi maka alkawari a yau ta sami miji za'a daura mata aure. Ka yi tunani ana son taimaka mata ne a bisa baiwar da Allah ya yi mata". Malan yayí jigum, can yace, "Haka ne Amina, yadda na ke jin zafin Dije kema na san haka kike jin zafin ta, na tabbata ba za ki so ta da halaka ba, tunda kin ga akwai alhari idan mun bar ta ta je neman ilmin shikenan a dai shaidawa Rilwan din wannan yarinya amana ce fa a hannunsu". Amina ta yi dariya tace, "Dan wannan Malan kada ka ji komi ka rinka sawa ranka tamkara gaban ka take ko a gabana, kar kaji komi wallahi." Dije da mahaifiyarta Amina suka koma Malunfashi cike da murna da zakwadin an amince masu zuwa jami'a don haka ko da Dije ta kare hutunta ta koma makaranta bata tsaya bata lokacin ta ba ta kama karatu fiye da yadda ta saba. A ranar da suka aje biro wato sun gama jarabawar karshe a makarantan 'yan mata ta garin Malunfashi a rannan Dije bata kara kwana ba sai dakin Yaya Amina. Wanshekare Amina ta ce ta shirya ta je ta yo sallama da mahaifinta Malan Kado domin a yadda Rilwan ya ce ran asabat zai zo ya tafi da ita za su fara kwas din konfuta na 07 wata uku kafin jarabawarsu ta fito. Dadi ya kara lullube Dije. Kwananta daya a Bakori ta dawo Malunfashi ta shiga shirin tafiya Jos. Mahaifiyarta Amina ta ce, "Ina so ki kara natsuwa bisa wadda ke gare ki, wannan gida da za ki wata rayiwa ce ba irin ta mu ba, rayuwa ce irin wadda sun mallaki komi na rayuwa, ta fannin abin duniya to kada ki ga an sakar maki komi, ki nemi wuce gona da iri. Ki iya da talaucinki haka nan ki tuna karatu za ki yi ki dawo wajenmu masu talauci, ki kama kan ki ban da kananan maganganu, sánnah ki yarda da Allah a komi na al'amarinki, yarda da Allah zai kai ki matsayin da ba ki zata ba, ki mallaki abinda ba ki taba mafarkin mallaka ba. KASHI NA TAKWAS Hadiza Abdulkadir ta bude sabon babin rayuwa mai cike da al'ajabi a birnin Jos. Gidan Rilwan gida ne irin na`yan bokon zamani duk abin jin dadin dan adam ya tanadar masu shi a gidan. Lokacin da Dije ta isa gidan tun a harabar gidan gaban ta ya rinka faduwa bal-bal, suna shiga falon hatta kafarta rawa take, ta nemi kasa bisa kafet ta yi zaune. Rilwan yace, "ki zauna bisa kujera mana". Amma ina! tamkar Dije bata ji shi ba ita dai gabanta kawai ke faduwa, bata taba ganin gida irin wannan ba. Dakunan bacci a bisa bene, don haka Rilwan ya haye zuwa dakin baccinsa yayin da iyalin gidan su ka san dawo war sa nan da nan suka zo falo gaida Dije. Babbar 'yar itace Hadiza ta mikawa Dije hannu tace, "Sannu da zuwa ni sunana Hadiza Rilwan". Dije ta ce "nima suna na Dije Kado". Hadiza ta yi dariya tace "sunan mu daya kenan" Mama Binta itama ta iso cike da fara'a tacе, "A'a sunanki Hadiza kinji daga yau kada ki sake kiran kan ki Dije Kado sai dai Hadiza Abdulkadir shi ne ainihin sunanki." 28 Hadiza Abdulkadir dai har yanzu tsokar cinyoyinta rawa suke yi a firgice ta ke, har Hadiza ta dauko jakarta ta ce ta zo su je dakinta inda zai zama dakinsu su biyu. Ganin yadda aka kayatar masu da dakin ya kara bugun kirjin Hadiza, komi ya kara rikice mata a zamanin da Hadiza ta shigar da Dije kewaye don ta yi wanka ta rasa yadda zata bullowa wajen wanka balle inda zata tsugunna don fitsari dole ta nemi alfarmar Hadiza don ta koyar da ita. To haka Hadiza ta rinka fuskantar irin wa'annan bokin al'ammura amma cikin kwana bakwai ta fahinci komi. Suka fara zuwa kos din konfuta na wata uku, inda anan kuma kullun suka dawo gida Hadizan Bakori ke kara yi ma Hadizan Jos bayani (yadda mama Binta ke kiransu kenan har sauran jama'ar gida suka dauka yadda za'a rinka banbanta su). Daga Hadizan Bakorin har Hadizan Jos babu wadda ta fito da sakamako mara kyau a lokacin da wata ukun su ya cika a makarantar koyon konfuta, saboda haka ne ma Baba Rilwan ya yi sha'awa ya sawo masu konfuta ya aje cikin gidansa har suka rika koyar da kananan kannensu. A daidai wannan lokacin ne kuma WAEC ta sakar masu sakamakon jarabawarsu. To Hadizan Jos mákarantar gwamnatin tarayya ta Bauchi ta yi don haka Baba Rilwan ya bada mota suka tafi Bauchi amso sakamakon jarabawa. Lokacin da za su shiga ofishin malamin da sakamakon ke hannunsa Hadizan Jos ta rike Hadizan Bakori gam-gam tace, "Wallahi Hadiza gabana tamkar ana luguden uku, uku, na tsorata kada fa na
🏠