Inna tace, "Wani iko sai
Allah! Yau ke ce ki ka canza kamanni haka? cikin dan
kankanin lokaci. Kai Allah dai ya saka mana tsakaninmu da
su Ankudi, duk sune suka tsangwameki suka hana ki yin
abin kirki. Yaya su Amina da kannanki?" Dije ta ce "Lafiya
lau. Ta ce, dan Aliah na ce tana gaisheki kuma wai kun
kyauta tunda kika kai ni baki sake zuwa ta." Inna ta yi
dariya ta ce, "Wallahi ba haka ba ne, kullun kina raina Dije,
idan na yunkura zani sai ki ga wata hidimar ta danne ni;
kuma, Malan ya sami kimanin wata uku yana fama da
zazzabi akai-akai." Dije ta ce, "Allah sarki, ba mu sani ba,
amma dai ya warware ko Gwoggo? ta ce "E ya wartsake
sarai Dije."
Sun sami fiye da awa daya suna hirar yaushe gama
amma zuciyar Dije batai mata dadi ba, dòmin bata yi mata
zancen da take son ji ba, wato ita dai ranta na ga Yusuf,
abinda take so ta ji daga bakin Inna labarin Yusuf ko ya
dawo akan batun aurenta domin ita abinda ta dasawa
zuciyarta shi ne Yusuf yana son ta, illa wasu kyale-kyale na
matan jami'a da suka debe masa hankali wanda ta san ita
da an jure an yi bikinsu, zata jure da duk wani abu da zai
rinka yi mata na wulakanci, har Ubangiji ya dawo mata da
hankalin sa, to bata samu goyon baya ba.
Ta dubi wata 'yar karamar agogo da ke bisa tebir ta
ce, "Lah Gwoggo tara ta yi, bari na je mu yi hira da Baba,
akwai wasu adduo'e da na ke son dauka a hannun sa."
Inna Tambai ta ce, "To Dije in ce dai gobe anan zamu sha
yinin mu? ta ce "E, isha Allah zan zo."
Ta shiga shagon da ke kusa da anguwarsu ta sayi
dan littafi da biro saboda daukar addu'a wajen Baba Kado.
Ta yi sa'a Baba Kadon na tsaye suna sallama da amininsa
malan lliya. Ta durkusa ta gayas da Malan lliyasu, ya сe,
"Wato Dije idan da ban zo ba sai ki koma ba za ki je gidana
mu gaisa ba ko?" ta ce, "Haba Baba wace ni? Aniyata saі
gobe zan zo, ai ko ban yi niyyar zuwa ba na san babu
yadda za'ai Baba ya amince min har na koma ban je na
gaisheku ba. Malan Illiyasu ya yi dariya ya ca "To ne yadda
22
Ta yi mashi sai da safe ta shige cikin gida. Su Ankudi
da yaransu ana zaune a falo suna hira ta yi sallama ta shiga
ta nemi waje ta zauna. Bayan kamar minti goma Malan
Kado ya shiga gidan ya wuce kai tsaye dakinsa yasa baki
ya kwallawa Dije kira, ta isa dakinsa ya mika mata wata
kullin leda baka mai kulle da nama balangu ya ce, ta je ta
ci. To amma ita Dije sai ta hada kan kannanta suka zauna
suka ci gaba daya. To ire-iren wannan zumudin na Malan
Kado suke haddasa tsana tsakanin Dije da su Ankudi.
Bata gama cin naman ba Malan Kado ya sake kwalla
mata kira, ta kakkabe hannunta, ta dauki litafi ta nufi inda
Malan ya ke zaune wato a bakin kofar dakinsa, ta nemi
kujera yar tsugunne ta zauna ta gefensa, suka shiga hirar
makaranta, tana bayyana masa irin matsalolin da ta fuskanta
amma yanzu ta shawo kan komi.
Tace "Baba akwai wasu addu'oe da ka sha fada min
cewa idan mutun ya shiga cikin rudani ko damuwa ya rinka
karanta su insha Allah zai shawo kan abinda ya dame shi"
ya ce "E kwarai kuwa akwai su, kala-kala, sai ki shirya na
rinka fada maki kina rubutawa."
A kalla ya tsara mata addu'oe kamar kala biyar sannan
ta tambaye shi na tsari da na aljanu suma duk ya gaya
mata.
A zuciyar Dije bata cika amincewa da kowa ba baya
ga mahaifinta domin a ganinta shi kadai zai iya rufa mata
asiri idan ta yi abin neman rufin sirri, tana son ta ji labarin Yusuf don haka take ganin wajen Babanta ya dace ta ji wannan labarin ba tare da an yi tseguminta ba.
Ta cije ta daure ta sadda kai kasa nuna alamun jin kunya ta ce, "Baba" ya amsa amma kuma sai ta yi shiru ta
kasa magana, ya dago kai ya dube ta ya ce, "Menene Dije?"
ta ce "Wai Baba kuna samun labarin Yusuf?" Malan Kado
ya yi shiru a bisa dukkan alamu Dije ta lura bai ji dadin tambayar da ta yi ba don haka sai ta yi dana sanin yin tambayar, Sun dauki lokaci babu wanda ya yi ko wani motsi
mai karfi, ko wanne da abinda ya ke raya ma ransa zuwa
can Malan Kado ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Wallahi yadda
23
na ga kin murje na dauka kin manta da żan cen Yusufa,
ban yi zaton har yanzu kina tuna shi ba Dije. Ki vi hakuri ki
manta da zancen Yusufa in Allah ya yaırda, za ki sami miiin
da ki ke so tankar yadda ki ke son Yusufa, domin a yadda
na sami labari, yanzu ko mahaifiyairsa kuka take akan
yarinyar da ya ke nema da aure, gaba daya an ce ya canza
rayuwarsa.
Ki yi hakuri Dije da Yusufa kamar yadda na yi hakuri
akan shi domin nayi iya kar kokar na yaron nan yaki dawo
wa gare ki, har kudi na rabawa malamai ayi mana rokon
Allah akan Yusufa amma kin ji shiru, saboda haka na
dangana na bar wa Allah zabi yasa hakan tafi alhairi."
Kan Dije na sunkuye a kasa, kunya da bakin ciki suka
baibayeta, tabbas Yusuf dan sha'awa ne, hankalinta ya yi
matukar tashi, shin me ma ya kai ta ta yi zancen Yusuf
hakan ta kara tsananta tausayinmahhaifinta a ranta, wai
har rokon Allah ys bayes da kudı ayi akan Yusuf bayan ta
san yana yi da kan shi, mya ko alhakin mahaifinta ba zai
kama Yusuf ba? N