Reading UWA UWACE COMPLETE BY FATTY NOOR Chapter 50 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

amsar da ba za ta fallasa abin da suke kokarin boyewa ba. Abbatin ne ya amsa masa da cewa zai taho da Asabe dasu Ummakati tunda basu sami zuwa asibitin yau ba. Cike da farincikin hangen nesan amininsa Munzali ya yarda da amsar har ma ya murmusa.

Da isarsu gidan bayan maigadi ya bude gate suka ga mota a ajiye a kusa da bangaren Munzali. Su Innayo basu shiga cikin gidan ba amma Abbati ya bi bayan Munzali har cikin falo. Zaune a ciki kuwa ba kowa bane illa Daddy da Zakiyya suna gaisawa da Kande mai kula da Qibdiyya. An janyo centre table gabansu inda Kuku ya ajiye musu kayan motsa baki.

Daddy yana shan juice sai wani gadara da fizgar kai yake irin na matasa masu zafin kai ko gaishe da maigidan bai yi ba. Abbati kuwa gabansa ne ya buga sosai har sai da ya dafa kujera yana mai fargabar ko Shazali ya nemi Zakiyya ne.

Munzali bai bi ta kan Daddy ba don sam baya son girman kan yaron. Amsa gaisuwar Zakiyya ya yi tayi masa sannu da jiki tunda taji labarin rashin lafiyarsa a wurin masu aikin gidan.

"Amma dai bana jin dubani kika zo yi ko?" Ya tambayeta bayan ya zauna.

Abbati ya cigaba da tsayuwa a bayan kujera yana jiran jin amsarta. Maganar da Zakiyyan tayi masa maimakon amsa tambayar Munzali kusan kara tsorata shi tayi.

"Abbati ina kwana? Ya wajen Hanne?"

Bakinsa yana sarkewa ya ce "lafiya kalau"

Dan dukar da kai tayi saboda jin kunyar rashin hakurinta da zargin wani abu ta ce "dama naga har an koma makaranta ne baka dawo da Qibdiyya ba"

Nasa gaban ne ya fadi yanzu. Ya kalli Abbati a fakaice ya daure ya daidaita fuskarsa don kada ta gane da matsala. (Fyaden da yake tunanin Lilu ya yi mata)

"Saboda yanayin jikina Asabe ta dauketa..."

Daddy ya katse masa magana da sigar izgilanci yana tabe baki.
"Asaben ce za ta wani iya kula da ita?"

Duk wanda yake falon harda Zakiyya yaji rashin dacewar furucinsa da sigar da aka furta shi. Munzali yaji bacin rai sosai akan hakan. Ko hauka take baya jin ya dace dan kanwarta ya yi magana irin haka a kanta. Cikin fushi ya nunawa Daddy kofa yana fada.

"Malam get out! Idan bata ci darajar komai ba a wurinka ai taci ta zama silar mallakar motar da kake karade garin nan da ita. Bayan kuma ka san na saya ne don ka dinga kai min 'ya makaranta. Ko an fada maka ban san irin yawo da gangancin da kake da ita wanda ni ke biyan kudin gyara ba? Duk kuma a cikin alfarmar Asabe da tasa ni auren yayarka?"

Kafadarsa Abbati ya dafo "ya isa haka ba lafiya gareka ba"

"Don Allah kayi hakuri" cewar Zakiyya a tsorace da fadan nasa.

"Ya fita kawai za a kawota da weekend. Sai ki fadawa makarantar zata yi fashin sati daya."

Rashin kunya Daddy yaso yi musu sai dai dukkaninsu sun yi masa kwarjini. Yanayin jikinsu ma ba daya ba. Ya san uwa da ubansa zai ci la'ada waje idan ya kara magana. A hanyarsa ta fita ne dai ya yi magana da kunkuni ya ce,

"A jikin 'yarka zan fashe"

Kalaman sun sami nasarar shiga kunnuwan Abbati. Matsalolin gabansa basu hana shi juyayin maganar a zuciyarsa ba a hanyarsa ta kai su Innayo gida. Dukanta zai yi?

*

Bakin Uwani bushewa yayi har ta rasa yawun hadiya da Salihi ya ajiye motarsa a jikin katangar police station ya ce ta fito. Hannunta yana rawa ta murda hannun kofar ta fita ta fara bin bayansa. A daidai gate din da zasu shiga kafafunta suka yi mata nauyi saboda tsabar tsoro. Jiki a mace ta coje a wurin don ji take kamar ta kwasa da gudu. Muryarta ta fito kamar mai shirin kuka ta nuna kirjinta da rawar jiki.

"Karata kayi? To me nayi maka? In kana so na dawo gidanka ai ka san umarni kadai zaka bani ba sai ka hadani da hukuma ba."

Kiris ya rage ya kwashe da dariyar kalamai da yanayin fuskarta. Kuma don karfin hali so take ta nuna masa cewa bata ji komai ba.

"DPO ne yake son ganinki"

Habar mayafinta kamar yaji me aka ce ta sabule ta rasa yadda zata gyara shi tsabar firgici. Da kansa ya saita mata mayafin a kafada yadda zai zauna ya ce "muje"

Suna tafiya mayafin ya kara cirewa ta dube shi idanunta suna shirin zubar da kwalla.
"Da ka fada min inda zamu zo ai da na saka hijabi. Ko babu komai zan shiga da mutumcina" a fusace ta wurga gefen mayafin kafadarta tare da cewa "in zaka zauna ka zauna ko in cireka kowa ya huta"

"Ina ruwan mayafi za a huce a kansa"

Allah ne Ya taimake shi yana gaba da ita da tuni ta ga dariyar da yake dannewa. Maganar da ya yi ce ma ta kara kular da ita.

Yawancin 'yan sandan da suka tarar a wurin counter sun gaishe shi da girmamawa saboda DPO Yahaya ya fada musu cewa surikinsa ne tun zuwansa na farko. Uwani bata sami sukuni ba sai da suka shiga cikin ofishin DPO din taji yana gaisheta tare da kiran Salihi da yaya.

"Bari nasa a kawo shi" cewar DPO bayan sun gama gaisawar.

Ba a jima ba kuwa sai ga wani dan sanda ya taso keyar Habibu wanda alamu sun nuna anyi lugude da jikinsa. Yana ganinta ya sunkuyar da kai don ya sha gargadi akan ko hada ido ya sake yi da ita sai an masa fin dukan yanzu. Ita kuwa mamaki ne sosai ya kama ta.

DPO Yahaya ne ya yi magana domin warware mata me yake faruwa.

"Kin san wannan mutumin?"

"Eh" ta amsa da baki tare da gyada kai.

"Good. Kamar nawa ne kudinki da yake hannunsa?"

Tunda ta fahimci ba tuhumarta aka zo yi ba sai ta hau lissafi. Akwai kudin kujerar Hajji, kudin sallamar agent, kudin hotel din da za a kama mata a Makka da Madina (bata san cewa duk a cikin kudin da ta bayar ake cire na kujera dana masauki ba), kudin fili, kudin masu gini ma ta hannunsa suke bi, kudin sallamar dillalai....

Lissafi ya dinga tafiya a yayinda ta cigaba da fadin nawa ta bawa Habibu. Da aka tambaye shi bai musa ba.

"Sai kayi musu bayani game da komai kamar yadda kayi mana."

Kai ya dukar ba don kunya ba sai tsoron hukuma. Da farko babu batun dukansa a lissafinsu. Sai da ya yi kokarin sayesu da kudi domin a kashe maganar. Sannan ne suka nuna masa cewa akwai bambanci tsakanin 'yan sanda da muna 'ya'yan sanda.

"Kudin Hajji babu su gabadaya nayi amfani dasu, filin da kika yi gini kuma ku biyar na sayarwa wurin. Ban san waye ainihin mai wurin ba ma. Sannan..."

Gajiya tayi da jin bayanin nasa mai neman sanya mata hawan jini ta ce "ya isa! Ya isheni haka. Allah zai saka min."

Ta dubi DPO Yahaya ta dan rissina kai tayi masa godiya sannan ta tashi ko bangaren Salihi bata kalla ba. Da sauro ya tashi ya bi bayanta.

Daga kafa kawai take tana saukewa ba tare da sanin ina ta nufa ba. A zuci take kukan bakinciki. Tanadin da ta soma tun ranar da ta fara daukar albashi ya rugurguje. Darasin da ta kasa tsayuwa ta koya yau duniya ta fahimtar da ita a cikin 'yan tsirarun dakiku. 'Duk gudun mutum ba zai wuce kafafunsa ba'. Babu wani bawa da ya isa ya tsallake kaddararsa. Talauci da babu take gudu kuma gashi sun zo sun risketa. Kai ta girgiza ta gyarawa kanta da cewa taje ta riskesu dai. Aikin da take takama dashi bata san makomarta ba akan shi. Kudi kuwa yanzu da matukar wahala ta fito da dubu hamsin indai ba motarta za ta sayar ba. A karshe dai mutum biyun da take ta kokarin ta wuce a rayuwa su ne dai suka rage wadanda zata koma garesu. Uwa da Miji.

"Shigo mota mu tafi."

Gefenta ta kalla inda Salihi yake binta da mota ta kawar da kai. Ransa ya baci ya daga mata murya.

"Meye haka kike yi ne kamar wata mara tawakkali? Ki zo mu tafi nace."

Ba musu ta zagaya ta shiga. Suna tafiya tana goge hawayen da yake ta yi mata zarya a kumatu. Sai da ya saita motar yadda za ta iya shiga gida sannan ya yi mata magana. Muryarsa ba da karfi ta fito ba kamar dazu amma tana iya gane zancen nasa ba da wasa yake so ta dauke shi ba.

"Ke ba Innayo bace. Bana jin har abada za ki taba zama ita. Mutane masu irin zuciyar mahaifiyarki kalilan ne"

Daga kai tayi ta dube shi sai taji a karon farko bayan wasu shekaru wai tana jin nauyinsa. Salihi ya yi mata kwarjinin da ko zamanin samartaka bata jin ta taba jin haka a kansa. A dole ta mayar da kanta kasa ta cigaba da sauraron shi.

"Ni ba mahaifinki bane. Ban taba aibata miki uba a gabanki ko bayan ido ba amma na san halinsa gaba da baya. Ta yiwu bisa kuskure na taba yin wani abu da yasa kika ji kamar tarihin iyayenki zai maimaita kansa a naki gidan auren..."

"A'a" ita ce amsarta da sauri.

Dan murmushi ya yi ya nuna mata kofar gidansu.

"Ki je ki roki gafarar Innayo gwargwadon girman laifukanki. Idan kin tabbata ta yafe miki ki kirani zan zo na daukeki mu koma gida"

Kama kofar tayi za ta fita ta dawo ta kuma zama cikin rashin kuzari.

"Za ta yafe min kuwa?"

Dariya ta bashi ya ce "zan iya rantsewa ko yanzu ma ta yafe tun kafin ki roka. Ai ba ita bace abin ji ba, ni ne."

"Au, baka yafe min ba?"

"Kin rokeni ne?"

Fuskarsa a sake take. Hakan ne ya bata damar yin murmushi ita ma. Jikinta a sake kamar burodin da ya tsumu cikin ruwan shayi ta bude motar ta shiga gida.

***

Tunanin Abbati akan manufar kalaman Daddy ya katse a lokacin da Innayo ta soma labarta masa abin da ya sami Ayaah da suka isa gida. Rokonsa tayi da su sake yiwa Suhaib da iyayensa godiya. Ta sanar dashi cewa Munzali bai sani ba. Kuma taki fada masa ne saboda halin da suka riske shi a ciki a asibiti. Amma don Allah tana so kada Abbati ya manta wurin yi musu godiya. Hakan zai sa suji cewa lallai sun ji dadin abin da dansu ya yi musu. Ya soma mamakin inda suka san juna sai ta fada masa zuwansu duba Qibdiyya harda babarsu. Murmushi mai ciwo ya sami kansa da yi. Halin Mami da 'ya'yanta na karrama mutane abin yabawa ne. Zai so ace ya hada zuri'a da wadannan kamilallun mutane. Ina ma kaddara bata riga fata ba? Da ace shi ma mai tsafta ne kamarsu da zai yi duk abin da ya dace domin samun amincewarsu wurin bashi 'ya.

Yana ajiye su ya kira Shazali ya nemi ya bashi adireshin inda zasu hadu.

"Da azahar nace maka zamu hadu ba yanzu ba" yace da shi a gadarance.

"Allah Ya kaimu azahar din."

Danne zuciyarsa ya yi wurin bayar da waccan amsa. Baya son ya nuna tsantsar damuwa da tashin hankalinsa a zahiri. Abu ne mai sauki Shazali ya yi amfani da wannan damar ya wulakanta shi. Gashi bashi da juriyar wulakanci. Karshe idan abin ya kare da rikici sune zasu kwana a ciki tunda Qibdiyya tana hannunsa.

Maganganunsu da Innayo ya tuno yaji ya kamata ya kira kamar yadda ta bukata. Akalla ko godiya ne ya yi.

***
Cije lebe Mami Khadija tayi a yayinda ta gama sauraron bayanin Suhaib game da Danliti. Wayarsa da ya karbo ya mika mata bayan ya budo mata chats dinsa da Jiddo.

"Mami" ya ambaci sunanta a tausashe saboda yadda ya fuskanci abin data gani ya tabata.

Sakin fuska tayi ta kai hannu kan bandejin da aka nade masa kafa.
"Allah Ya baka lafiya Suhaib. I am proud of you. Ka tseratar da mutumcin wata kaima in sha Allahu babu mai taba mutumcinka dana 'yan uwanka ."

Kawar da zancen take son yi sai dai ko kadan bai yi niyyar barin maganar haka ba.

"Mami jiya kusan kwana nayi ina neman fatawar da ta tilasta miki zama da ...."

Bata bari ya gama magana ba ta dakatar dashi da hannu a lokaci guda tana mikewa.

"Zanyi abin da ya dace Suhaib. Abin da ya kamata nayi tun da dadewa." Ta karashe maganar a hankali tana fita daga dakin.

Da taimakon Allah ta isa dakin da aka saukesu ita da Farha.




I just published "41" of my story "UWA UWACE...". https://www.wattpad.com/1221353664?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=BatulMamman17&wp_originator=dmTI6%2Bd4xW4ySQC9IZSN5Ctp1ECDjPlql7uEEwxNyy6mwmTs5Ncm6yv57bRsBRlDWFHVlr6suRV3pFd4sJuu9eSkRnJfcM3791OugVz9A24ZB4FNIQX9hKS8ACJWWt%2FZ



UWA UWACE...41



Batul Mammanđź’–






***

Suhaib ya kamata ya kira amma gangar jiki da ruhi suka ki bawa Abbati hadin kai. Haka yatsansa ya dinga jujjuyawa akan sunan Farha yana tuhumar zuciyarsa da rashin jin magana har ya kai ga kira bai ankara ba. Cikin sauri ya kai hannu zai katse kiran sai dannawar tasa tayi daidai da sallamar muradin rayuwarsa. Zuciyarsa wani irin dokawa tayi sai da ya dafe kirjinsa. Ba yadda ya iya dole yayi saurin bin kiran da wani.

Sake dauka Farha tayi cikin macewar jiki da faduwar gaba. Sallamar da ta kuma yi ta riski kunnen Abbati da sautin karaya da tsoro. A take yaji tausayi da soyayyarta sun taso masa. Baya bukatar tuni yana sane da cewa shi mai laifi ne. Cikin kankanin lokaci ya sanya mata rai da soyayya harma da tunanin rayuwa a karkashin inuwa guda. Sai kuma ya soke mafarkin da ta fara ba tare da ya bata gamsashen bayani ba. Barinta cikin rashin sanin tudun dafawa ba karamin cutarwa bane. Bai tashi sanin hakan ba sai yanzu.

Ajiyar zuciya suka sauke a tare wanda sautin ya shiga kunnuwan junansu. Hakan ya sanyasu yin murmushi a lokaci guda.

Farha ce ta fara yin magana da cewa "nayi sallama baka amsa ba"

Tunanin Qibdiyya ne kadai ya hana shi nuna mata zahirin halin da zuciyarsa ta shiga sakamakon jin muryarta kadai.

"Kiyi hakuri. Wa alaikum salam. Kina lafiya?"

"Alhamdulillah. Kai fa?"

"Nima Alhamdulillah"

Shiru suka dan sake yi sannan ya yi ta maza ya ce "Ya Farha muna cikin wani yanayi ne yanzu dake tsananin bukatar addu'a. Don Allah ina neman alfarma ko sau daya ne ki roka mana sauki a wurin Allah."

Tausayi taji ya bata. Ta matsu taji mene ne ya yiwa kyakkyawar alakar da suka fara ginawa shamaki har tazara irin wannan ta wanzu a tsakaninsu.

"In sha Allahu zan yi"

"Baki tambayeni ko meye ba?" Ya ce da dan murmushin karfin hali.

"Na san idan ya kamata naji ba za ka boye ba"

Allah Sarki zuciya. Kalaman Farha kara nutsar da ita suka yi cikin zuciyar Abbati. A kullum yana kara yabawa da irin tarbiya da tsaftar tsatson da ta fito. Kafin ya manta ainihin dalilin kiran nasa ya ce ta yiwa Mami godiya akan taimakon da Suhaib ya yiwa Ayaah kafin su zo Kaduna suyi da kansu. Tunanin sake ganinsa nan kusa yasa ta fada masa cewa suna Kano ga kuma halin da Suhaib din yake ciki.

"Kuna gidan da muka zo biki?"

"Eh"

"Zan zo koda ni kadai ne saboda Munzali ma yau ya fito daga asibiti idan baku koma ba zuwa gobe ko jibi. Don Allah kada ki manta da adduar."

Zai katse wayar kenan yaji ta ce "baka bani abin sadaka ba. Naji ance ku Kanawa ko me zaku yi sai an biyaku"

Dariya ce ta kama shi ya ce "dadin abin kauyenmu a Jigawa yake nima bakon Kano ne"

Da murmushi Farha ta ce "Ai shikenan tunda ka fara rowa"

Da kyar ya iya sallama da ita suka ajiye wayar kowannensu yana jin matsananciyar kewar dan uwansa.

Daga nan zagaye ya dinga yi a titi domin zaman wuri daya ninka masa damuwa yake yi. Wani masallaci ya tsaya a gefen titi da aka kira azahar ya yi sallarsa tare da fatan samun nasara daga wurin Maikowa da komai. Akwai mutane da dama da zai iya kira su wulakanta masa rayuwar Shazali ba tare da ya daga hannu ba. Ya san manyan da zasu yi komai domin farincikinsa. Amma ko kusa ba zai nemi kowa ba. Domin kofar da yake son rufewa ce zata sake budewa. Shi yasa ya zabi kai kukansa inda ba a barin mutum ya dawo empty handed. Kamar jiransa Shazali yake yi kuwa sai ga waya. Sanar dashi adireshin inda zai je yayi da dariyar mugunta. Wannan yasa ya figi motar a guje da fargabar me ya sami 'yarsu.

***

Minti arba'in kafin Shazali ya kira Abbati ya amsa wayar wani kusan gwamnati wanda yake yiwa kawalcin 'yan mata. Da yake zancen nasu ya hada da yadda zasu koma biyan malaman makarantun kwana kamar yadda suke yi a ta maza ana basu dalibai sai ya fita daga gidan. Hirar sirri ce baya so ko Abdul ya san me yake ciki. Mukullan mota ya dauka ya ce masa zai je siyo wani abu ya dawo. Minti goma da fitarsa kuwa Abdul ya kamo hannun Qibdiyya yace ta zo ya kaita wurin mamanta.

Bata yi musun binsa ba don ta soma galabaita. Sam taki cin abinci sannan ga rashin iyaye ko wani idon sani. Abdul gani ya yi tana jan kafafu ya sunkuceta ya goya. Durowar da ya taba gani Shazali ya ajiye mukulli ya duba yaci sa'ar ganin mukullai daban daban a ciki. Lokutan baya bai taba tunanin dauka ba duk da idan Shazali zai fita yana rufe shi a ciki.

Wurin kala shida ya soka a jikin kofar saboda kusan duka girmansu daya kafin ya yi sa'ar jin ta bude. Ajiyar zuciya ya saki gami da sake ruko kafafun Qibdiyya a cikin hannuwansa. Yana sako kafa a waje yaji kamar an dauke masa kansa sakamakon hada kan da bango da Shazali ya yi. A kofar gida ya zauna yana wayarsa. Duk gwajin mukullan da Abdul yake yana ji. Haka ya shigo gidan a harzuke ya banka kofar ta rufe da karfi kafin ya hankada shi. Da kyar Abdul ya iya tsayuwa akan kafarsa don gudun kada ya kifa da baya ya danne Qibdiyya. Bayan ya sauketa kafafunsa ta rike ta buya a bayansa tana kuka. Shi kuwa kunnen bangaren da ya hadu da bangon yaji ya dauke dif sai wata kararrawa ce take bugawa kamar an kada tara a firamare.

"Har kayi tsaurin idon shiga lamarina Abdul? Waye ubanka a garin nan da kake jin ko kasheka nayi za a tada magana ma?"

Abdul babu amsa sai kunnensa da yake ta bubbugawa ko jinsa zai dawo daidai.

Kafadunsa Shazali ya rirrike ya shiga jijjiga shi yana masifa. Abu biyu ke damunsa. Na farko ya san duk kaunar da yake yiwa Abdul ya rasa shi kenan domin ba zai kuma kawo shi gidan nan ba. Na biyu kuwa wani mutum ya wuce ta kofar gidan a daidai lokacin da Abdul din ya tura kofar gidan. Babu tantama ya san cewa an ganshi. Bayan kuma ba a taba jin duriyar kowa a gidan ba.

Da kansa da ya gaji ya sake shi ya nuna shi da yatsa. Har lokacin dai bai dawo daidai ba. Kana ganin kwayar idanunsa zaka gane a cikin dimuwa yake.

"Ka jawowa kanka bala'i don na fuskanci akwai ganganci idan na mayar da kai makarantarku. Ka jirani in kai yarinyar nan wurin ubanta na dawo."

Cikin gidan ya wuce ya tafi dakinsa ya barsu a dan sararin tsakar gidan. Kukan Qibdiyya tuni ya dauke sai ajiyar zuciya saboda tsorata da tayi. A gabanta Abdul ya durkushe ya fiddo wata 'yar karamar waya kirar samsung mai torchlight. A makaranta ma ba a san yana da ita ba. Bai taba kiran kowa ba sai Shazali da suke musayar text messsage. Shi ma kuma bai san yazo gidan da ita ba. Gefen siket din Qibdiyya ya samu ya saka ta ya yi mata nadi biyu. Siket din sai ya dage sama amma ba za a gane da wayar ba saboda dan fadin rigarta.

"Ki boye wayar nan in kin hadu da babanki ki ce ya kira babana."

Da ka ta amsa tana rike dashi har Shazali ya dawo. Hannunta ya fincika ya fita da ita a ransa yana tunanin ko wa zai hadu dashi cikin makota ba zai damu ba domin yana dawowa zai fita da Abdul ya bar gidan gabadaya.

Fitarsu ke da wuya Abdul ya fadi a tsakar gidan. Jini kuma ya dinga silalowa daga cikin kunnen da ya bugi bango ta bangarensa.

***

Duk wata addua da Abbati ya sani ya karanta ta a hanyarsa ta zuwa gidan shakatawar Comared. Manyan motoci ya gani har biyar a harabar gidan. Da yake gidan gona ne mai dan karen girma. A kusa da ta Shazali ya ajiye tasa ya fito ya kira shi a waya. Maimakon ya dauka sai ya fito ya yi masa jagora zuwa ciki. Karfin zuciya ne ya hana shi far masa da duka tun a lokacin saboda bai san me zai sami Qibdiyya ba idan haka ta faru.

A cikin gidan kuwa Alh. Tahir ne zaune a wani daki wanda kofarsa take cikin falon suna magana da Comared.

"Har yanzu babu wani canji dole sai da namijin?" Ya sake maimaita tambayar da bai san sau nawa ya yiwa Comared ba.

Fuska ya kyabe kamar mai jin tausayinsa har zuci ya ce "ko dazu sai da na sake kiransa har nace ko ni zan iya yi maka aikin yace a'a"

"Allah Sarki mutumina. A hakan ma nagode sosai. Na san kai mai taimaka min ne har inda karfinka ya kare."

Comared ya tashi daga bakin gado ya ce "so nake ka kwantar da hankalinka. Yaron kwararre ne ya san me yake yi. Kafin ka farga anyi an gama"

Suna ciki suka jiyo sallamar Abbati domin dai shi Shazali bata gabansa. Hasali ma hankalinsa yana wurin Abdul. So yake ya koma gida ya yiwa yaron rashin mutumci kafin ya watsar dashi a titi.

Falon wayam babu kowa sai kayan ciye ciye da karar tv data AC. Qibdiyya Abbati ya nema da ido babu ita babu dalilinta. Cikin zafin nama da gajiya da danne bacin ransa ya riko Shazali ya tsayar dashi a gabansa. Da kakkausar muryar da shi kansa bai san bacin rai zai taba bashi irinta ba ya ce,

"Shazali ina Qibdiyya?"

To shi ma Shazalin bai san dakin da Comared da Alh. Tahir suke yana kusa dasu ba, shi yasa ya bashi amsa babu kwana-kwana. Dariyar mugunta ya fara da ita kafin ya ce,

"Tana nan kalau ko farcenta ban taba ba. Nan da awa guda idan kaso zaka tafi da 'yarka gida. Bukatarmu kawai kabi umarnin da aka baka"

Murya kasa-kasa Alh. Tahir ya tambayi Comared me yake faruwa. Ganin babu wata mafita sannan ya san a cikin matsi abokin nasa yake shi ne ya yi masa takaitaccen bayani. Bai kai ga yin magana ba suka ji Abbati ya daka wata irin tsawa. Su biyun duka jikinsu ya amsa duk da ba dasu yake ba. Barin ma Comared wanda tun isowarsu gidan yasa aka bata maganin bacci. Tana dakinsa na sama yana jiran Abbati da Alh. Tahir su shiga daki shi ma yaje ya afka mata.

"Shazali! Ka fito min da Qibdiyya idan ba haka...."

Cike da dakiyar 'yan barikin da suka yi nisa Shazali ya katse shi da cewa "in ba haka ba sai me Abbati? Kana da abin da zaka iya ne? Duk wani k'usan gwamnati ko maikudin da kake takama dashi ta dalilin wa ka sanshi?"

"Ana takama da Allah waye yake ta mutane? Wawa irinka ne zai dogara da halitta mai kayyadajjen wa'adi bayan akwai Maihalittar da bashi da karshe. Da nace maka ni da Munzali mun tuba ba da wasa nake ba."

"Aikin banza. Wane d'an son zuciyar ne ya ce muku Allah zai karbi irin wannan tuban naku? Shekararku nawa a wannan rayuwar? Kudi da duk wani connection dinku a kasar nan ba jikinku bane sanadinsa? Sai yanzu kuna tunanin kun gama tara abin da kuke so zaku wani ce kun tuba? Malam in zaka sha giya kasha ta duba. Allah Gafurur Rahim ne kowa ya san wannan. Kawai ku cigaba da gashi suya sai ranar sallah. Idan mutuwa tazo ka gaggauta istinginfari me yiwuwa a dace."

Karkada kai Abbati ya yi da murmushin takaici. A matsayinsa na bawa mai tarin zunubi kuma mai neman rahama ya yi imanin cewa shi din ba kowa bane. Amma duk da haka bakinciki mara misaltuwa ya danne zuciyarsa saboda maganar Shazali. Tsanarsa ta kara ruruwa a zuciyarsa saboda kalaman izgilancin da yaji daga bakinsa. Nasa imanin da tawakkalin kuma suka karu domin ya yarda cewa lallai shiriya ta Allah ce. Su da suka tuba ba

Please Login or Register in order to submit comment