Reading So Makamin Cuta Complete By Surayyams Chapter 7 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bedsheets a hannun ta
' kallo daya jasmine ta mata ta cigaba da cin abincin
"Da yaushe kika cire min bedsheet din nan

,kallon rashin fahimta talatu ta maido mata
Tare da cewa wallhy ban cire miki ba
Ni ma cewa kawai yayi na goge miki in ya hushe sai na kawo

Wa kenan? Ta ajiye spoon ta mida kallo kan talatu
Wacce ba musu tace "Ogah,

Shi ogan ne ya wanke kenan kome?

Uhm,ai lokacin bakki lpy ne'naga shine tuntuni dakin nan na kula dake
Ya jikin? tafada tana dan sosa kai

Dakata anan' Ni bance ki min bayani ba jeki...jasmine tafada tana rau rau da ido

Sum sum ta fice
Oh my god tace tana maida kanta kan sofa hade da lumshe ido cikin jin dadi
He's done so much ko wa ya sashi oho
Shyasa mana naga dakin yamin daban
haba
Nasan dai wannan ba gyran talatu bane

Haka ranar ta wuni jiran ko zai dawo ko ma ta kalle shi ta ji sanyi a ranta amma shiru
Har karfe 10 saura na dare bai shigo ba
"Hala ma yanzu yana chan tare da yan matan sa ni ena nan ena whalar da kai na
Zuciyar ta ya raya mata a yayin da take jingina bayan ta da window
' lumshe idon ta tayi cikin tunani
take wasu zafafan hawaye suka biyo baya
Haka kawai takejin mummunan kishin sa da haushin sa lokaci guda a ranta...
Takai minti 10 a hakan
Sannan ta laluba ta koma kan gado ta yi kwnciyar ta


Gefen tania kuwa bakar riga tasa doguwa mai diso dison ja wanda ya mata kyuw sosai
Suman kanta ta watso su gefe kamar yadda indiya keyi sannan ta zuba make up din ta irin na kece raini
' waya takeyi kusan minti 50 amma sam ba ajin meta ke cewa
Tana kammalawa ta kulle ko ena tsaf, du wani abun amfani kamr su document da sauran su ta killace sa ta kama hanyar zuwa gidan gonar zahida

Wuri ne mai dumbin tarihi a rayuwar su rodriquez family don anan sama da kashi 80 na arzikin su ya fara tashi ...

Fadin kywun tsari da haduwar wajen bata lokaci ne
Don haka makil yake da yan uwa da abokan harkan ta anata shagali
' wata figiggiyar mata ce kusan age mate din zahidan take cewa
Beauty queen banga bakuwar na mu ba fa har yanzu
Kinsa na taho da zuga na
Sunata jira
Ajiye wine glass wata ma agefe tayi
Tare da cewa nifa ayita ta wargaje kawai yau din nan da bala'i na zo nan wajen
In fa tsoro take a aika aje a dunkulo mana ita koya kuka ce?
Shewa ne ya karaade wajen
Ana ta kace kace

Ku tsaya ku tsaya zahida ta fada cikin dariya

'ku kwantar da hankalin ku mahaukaciya ce zata zo
Nan ma aka sake fashewa da dariya alaman yawancin su a buge suke
Jabir ne ya shigo
Ba jira ta karaso wajen nasa
How far ? Tace tana duban sa alaman tana sauraro

Kalau "ya dada matsowa gefen kunnen ta "
Na bincike sa da kywu ki kwantar da hankalin ki baisan da patyn nan ba fa"
Yanzu haka ma suna tare da kamal suna meeting kinsan kwanan nan zaa fara world olympics

Ohhhhhh perfect ta fada cikin wani nishadi tana sake murmushi
ya dube ta yace
' ke
Wai me zaki ma yar mutane haka ne
Naga kin wani dage sai hade hade kike yi ba sauki

Oh jabir ,forget it
Kawae zan dan koya mata manners ne
Ai ta tsokano tsuliyan dodo tunda tasa shi ya ci min mutunci gaban workers ena
Hmmm toh kiyi dai a hankali
If not zata sake fada masa ya miki wanda yafi wancan

Shhhhh no way, tafada tana dariya mai ban haushi
Ai zan dealing da ita ne in such a way dat sai na mata izini tayi magana nan gaba

Zahi....

Ehhhhh ,ta dakatar da shi da cewa

Just enjoy ta ce sannan ta wuce tayi gaba abunta
tsaban wani farin ciki dake bin zuciyar ta a lokacin
Oder wine tasa aka sake karowa aka baza ma mashaya sai shewa mata keyi ana rawa jifa jifa
Karfe 11 da minti 58 wacce ake kira da preetyhot ta yi ihu tana cewa i wish
yarinyar nan yanzu zata diro da sai na yayyan ka ta tanayi tana gwadawa da hannun ta .
Wani shewa aka sake bugawa
Ana mata tafi

12.00pm aka bude kofar wajen
Duk da basu sani ba mafi akasarin su saida sukace wow
Ganin yadda tania ta hadu
Dadin abunda ya sa kowa ya maida hankalin sa kanta saboda
Excatly irin shigar da zahida tayi shima ita tayi harta dan kunne da takalmi

Chak wajen ya dauke akayi shiru kowa da abunda ke sakawa a ransa
Wasu sunyi tunanin special quest ce kawai
Wasu suna kawo ko kanwar zahida ce
Amma ba wanda yayi tunani itace namar da suke jira tuntuni
Taku cikin jan aji da kasaita take har ta iso gaban zahida wacce numfashin ta ya kafe yana neman daukewa tsaban bacin rai
' ido da ido suke kallon juna fuskr tania dauke da wani shu'umin murmushi
'chan ta fashe da wani busashen dariya mai kularwa ganin yadda zahida ke bari har lashess dinta na rawa

' how dare yhu " zahida tace a hatsale

Shhhhhhh karki sake ki min tsawa
Zuyi tayi tana ma sauran yan matan wulakntaccen kallo sannan ta juya tamaida kallon tattare da sake dan karamin dariya tace ""hmm waht a kingdom party
Wayannan bayin ki ne ko kuwa yan cirani ne?

What? Preetyhot tace rai a bace

Nan fa mata suka soma mikewa tsaye alaman sun soma fahimtar wasan
Wacece wanannan zahida ?

Rai a bace tace ai ba sai na gaya miki ba "don itace mahaukaciyar da takeji zata hada shoulders dani
Just lokat at her
Tuni figagiyr cikin su ta karaso tana kare ma tania kallo
Don rainin hankali ma irin kayan ki ta sa? Ke wacece ?waye uban ki

Itama tania watsa mata harara tayi ' sunana tania ubana kuma sherrif
Wai tambayar kayan dana sa kike? nop, kiduba da kyau ai bansa kaya ba
Dan dafe kai tayi kamr da gaske
Ta cigaba " tunda na shigo nan na lura kuchakai ne ku baku da wardrobe choices,besides nazo hidimar mahaukata ai saida shigar hauka

Don shi mahaukaci zaki iya fahimtar da shi wani abun ne kawai inka maida kanka siffar sa,

Hannu ta mika zata zuba mata mari
Dam ta rike ta suna watsa ma juna kallon banza

Sosai wajen ya kaure da surutai wasu matan ana taro su zasu shiga fili


Ya isah haka ku kyale ta,rainin yayi yawa
Ku gwada mata ku ba mahaukata bane ita din ce ita kadai

Hmmm na nawa kuma? tania
Ta fada hankali kwance

Meke faruwa anan jabir ya fada yayinda yake kara sowa tare da zugar sa shima
Ganin yadda kowa ke tura wa tania bomoboman mugayyen kallo ya sa ya fahimci komai
Duk da ba wanda ya amsa shi

Ke ,,yace da niyyar juyo tania nan take ta buge hannun sa da karfi

A fusace zahida ta chakomau gwalbar giya zata rafka ma tania
ta tayi sauri ta kare kanta suna kallon kallo"
Buuuura uba ,,to hannun ki ya sake taba wanann anan sai na kashe ki ..

Heyy calm down sis ya fada yana zare hannun zahida daga jikin tania

Riko hannun ta yayi cikin sigar rarrashi' ki kyaleta
Muga gudun ruwan ta
Kiyi aiki da basira mana zahida

Gyada kai kawai tayi
Nan ta ja gefe
Hayakin taba wani ke busawa
Sosai ba ruwan sa sai kallon tania yake
Yanayin yadda tania ke kauce wa hayakin tabar ya burge zahida
Don Har wani yamutse fuska take tana korewa alaman bata so
A dabaran ce ta masa signal kan ya kara matsawa daf
Ba musu ya biye mata
Daga gefe kuwa sai kus kus ake
Jabir ma na tsaye duk dai maganar bai wuce kan tania da tayi tsayuwar ta a tsakiyan su hankali kwance

Busa Hayakin daya sake na karshe sai ta soma tari
Tun tanayi tana kakkaucewa har ta soma yi sosai ba tsayawa
Dariya ciki ciki suke mata
Ba mai ce mata sannu
Wasu burin su kawai akashe su mata lilis su huce haushin kiran su bayi da mahaukata data yi
' rike kirjin ta ta yi sai tari take
Cikin wajen jabir ne ya fara nuna damuwar sa da shike yana da mugun son mata
ganin abun yaki tsayawa
Har ta kama kan desk alamn tana bukatar ruwa

Cikin wani shu'umin dariyar mugunta zahida ta karaso gaban ta
Duk da wajen ya kaure sai dariyar suke mata ana jefar ta da maganganun banza
Bai dame ta ba sai tarin ta take yi abunta
A idon kowa zahida ta dauko wata sabuwar kwalbar giya ta bude fushhhh..ta tsiyayya a cup
Tayo kanta da shi tace gashi
'kadan ma kika gani
Da kyar tania ta dago jajyen idanun ta sakamakon tarin ,ta mata alaman bata shan giya
amma sai ta basar
Ta dunkufu kan taniar da karfi ta dura mata abaki tas ta shanye

Ihu aka kaure da shi ana dariya wasu har suna daukawa a waya
Dum tania ta tsaya a filin bata motsa ba sai rike kai datayi
Jiri ne ke debar ta
Nan zahida ta karoso daf cikin dariya tace meet in hell baby girl

Bata gama rufe baki ba tania tayi luuiiiii ta zube kasa
Da dai ihu aka sake yi ana shewa ana daukar ta awaya
Daga baya
Duk akayo kanta a duba ko suma tayi a sake dagota

Nan fa labari ta soma canzawa bayan kaiwa minti 3o ana daga tania amma shiru ta kafe bata ko motsi
Ruwa da duk abunda suk san zasu sa ta shi sunyi amma shiru
To meya same ta kowa ke fada a ransa anyi jungun jungum

Daga karshe Sannu a hankali aka soma zamewa ana barin wajen
Domin jabir ya tabbatar musu da cewa *mutuwa* tania tayi..

Mutuwa fa kace jabir? Cewar Zahida a tsorace
Na shiga uku
Ni ba kashe ta nayi niyyar yi ba

Wht me kika mata zahida?
Ya fada yana kallon ta
Batace komai ba aai ido take fitarwa

Hannu ya mika ya dauko wine din data bata ya kalla
Yace kar ki ce min kinyi poisining din yar mutane zahida

Noooooo muryn ta na rawa tafada
Believe me jabir ba abunda na bata wallhy

To me kike nufi da ba kashe ta kikayi niyya ba afterol ke kika dura mata wannan abun kowa na gani

I know tafada tana yarfe hannun ta hankali tashe
Amma ai bansa komai a ciki ba

Lier,yace a fusace
Damn it ...

Dai dai kun mutanen dake wajen ne ke maida martani ciki ciki kowa na analysing case din

Kuka zahida tafashe da shi na tashin hankali
Ga shi duk kawayen nata sun gudu abun su
Sai yan gulma da ganin kwakwaf
Ganin yadda ta daga hanali tana kuka gavan gawar tania ya sa jabir tausaya mata
" rarrashin ta ya shigayi ya dago ta sukayi gefe
Kukan me haka zahida sai kace yau irin haka tafara faruwa da mu? C'mon All is well.
meye amfanin kudi da power mu?kinsan wannnan ba komai bane
Why wasting ur tears

Yarfe hannun ta shigayi cikin jimami
Tana dada kararo hawaye
Jabir ni yanzu shikenan dreams dina ya ruguje akan ashween?
I can't lose him..
Tafada tana girgiza kai

Ohh ba ma kisan da kikayo ya dame ki ba?Hmm na lura tunda kika fara wannan soyayyar taki kika canza wallhy
For god sake Ki kwntr da hankalin ki zahida
Maza nawa kikayi da su shima bazai gagara ba

Zaro udo waje tayi tace..no
Mutuwa fa tayi
I know yanzu ni za'a ce na kashe ta 'don kawai a raba ni da shi

Wani kallo ya bita da shi
To da ma wa ya kashe ta ?

Ko bude baki batayi ba suka ga shigowr jami'an tsaro sai dai ba wanda suka saba gani ba ..

Kuuuuu cikin ta yayai kara don tagama yanke hukunci aranta zasu binne case din su rufe maganan su ya su,

Cikin bunkasa jamian suka karaso gaban ta
Rike hannun jabir tayi ko zata samu gwarin gwuiwa
Saida saura biyu masu uniform suka kammala dube dube kan gawar tania sannan suka dada tabbatar da cewa ta mutu nan babban su ya dubi su zahida yace
" sunana inspector sadik ya fada yana nuna id card
Zamu tafi dake cid ana tuhumar ki da laifin kisan kai

Cikin'karfin hali jabir yace
Kai asuwa?
No way,
Idan kana da cikaken proof zamu zo da lawyer
Ya ja hannun zahidan zasu tafi

Dakata malam
Police din yace
Yana shan gaban sa

Nan cece kuce ya kaure tsakanin har ya kaiga an kira jamal a waya da madam hidayat

Fir police yaki amincewa haka suma suka ki bada zahida a tafi da ita station
Police kuwa Sai dada tono magana yake
Har da cewa" kin sha cewa zaki kashe ta ,sannan mun sami labari wannan hidimar musamman dan ita kikayi

So what?
Jabir yace a fusace
Dama ba abunda kuka sani sai sharri wa mutane
Tabe baki yayi cikin zuciyar sa ya dubi zahida da gaba daya bata cikin hankalin ta

Riko ta yayi gefe
Zahida meye haka ?kin jawo mana masifa kuma kina dada tabbatar musu ke kika aikata
Why are yhu lookiNg restless
Nasan mummy da jamal na kanyi daga sama ki nitsu mana

Nan tace Ba damuwa ta bake nan jabir
Damuwa yadda news din zaije wajen ashweeen
Jabir ya zanyi ta karashe kamar zata yi kuka

Shhhhhhh kar ki damu ,komai zai zo cikin sauki
Bari mugama da wannan nikam ma bantaba ganin sa sai shegen naci

Dan karamin tsuka taja tace barni da su ta wuce ta koma suka cigaba da yi

Shiru yayi kamar mai nazari
Cahn sai ya daga wayar ta da niyyar kira
Sai ya ci karo da shigowar kiran ashween din
Shikan sa sai da yaji yarrrrrrr a jikin sa
Sannan yayi excusing din ta
Waye ne?
Ta tambaya ,
shiru yayi baice komai ba
Nan ta karbe wayar lokacin wayr amma ta kasa amsawa har saida wayar ta katse
' haka ashween ya cigaba da kira sai da yakai 10 misdcols bata daga ba

Tuni jabir ya mata alamn kar ta dauka kar allura ta tonu garma gaban su Cid police din

Daga gefe kuma suma suna lura da duk wani motsin ta
Har yakai ga babban su ya sa baki akan cewa sai ta dauki call din ashween tunda akan bincike take

A fusace ta juya hannun ta rike da wayr tace
Wai ba ance ko jira lawyer na bane
Me ye na samin ido?

Ke suspect ce Madaam" don bincike ya tabbata akanki' dole kuma na yi aikina akan tsari'
So pick ur call

Bude bakin jabir zaiyi magana
Da mamakin su police din ya daka musu tsawa
Pick dis call ko ya kara zama hujja akanki
Mamaki ne ya rufe su duka " amma dai wannan baisan da wa yake ba ko?zahida tace da fuskar mamaki
I told u ..bako ne sai an farsa masa baki jabir ya amsa rai a bace
Ko ya kula su kiran ya sake shigowa still yana ringin bata daga ba

Tsaki police din ya ja ya karaso bazata wajen zahida ya cafke hannun ta mai dauke da wyar zaiyi dialling
Ihu ta zuba tana kokarin kwace hannun ta
Take jabir ya zaburo zai kai mata dauki
police ya juya ya daka masa tsawa
Taku daya ka kara sai nasa an harbe ka
Ba yadda ya iya ya koma gefe ya tsaya sai huci yake

Ganin haka ya sa ta fashe da Kuka tana damke da wayar shima yaki sakewa

Nan aka bude kofa
Daga ido da zatayi sukayi ido hudu da ashween

Wani kuuuuuuuu cikin ta yayi lokaci guda ta sake wayr a kasa fas..jikin ta ya shiga kar kar wa




🙆🏽‍♀




*surriem*
[23/08, 03:02] ‪+234 806 071 2446‬: *⚜BRILLIANT WRITERS ASSO🖊*



💔

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_


_Story and written by_
*SURAYYAHMS*🔥



*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.



*Page▶10*



Meye haka? sake ta da Allah
Ashween yace yana karasowa wajen su

Ba musu police din ya sake ta nan take tayi kasa ta fashe da kuka sosai
" a nitse ya yo gefen ta ya tsunguna ya dago ta yace
Zahida me kika aikata?me nake gani" da gaske kin kashe min tania? murya ciki ciki yake maganan alamn baya so kowa yaji

'da kyr ta dago kai ta kallesa itama murya ciki ciki ta ce im sorry ,ashween pls understand me" dan Allah kar ka rabu dani ,
Na amince kamin komai duk da nasan ban kashe ta ba,
But Pls dont leave me ta karashe cikin wani sabon kukan
Baice komai ba
Ya juya ya nufi kan gawar tania da aka rufe da investigation cloth irin farar yadin binciken nan
Fuskar sa dauke da alaman tsananin damuwa ya tallafo gawar yana bata hakuri ,,sai hawaye tsilli biyu da suka biyo baya a idanun sa

Gefe da shi ta zo ta rakube da niyyar rarrashin sa amma ko ya kula ta
Kamar wanda aka zaburo sa haka ya mike zumBut zai yo kan polisawa nan...
Dai dai lokacin jamal ya shigo
Itama zAhida Da sauri ta mike suka isa wajen sa da jabir
Ni ne lawyer zahida rodriquez Yace cikin kwarewa

Nan aka soma bayanai enda jamal ya kafe sai dai a bar zahida taje gida daga baya a cigaba da bincike

Da mamakin ta police din yace ai hakan bazai yiwu ba sai idan an sami lawyer mai kare gawar ko wani dangin ta gudun kar ayi zalunci

' bata da lawyer yanzu ,kuma ni kadai ne dangin ta ""ashween ya fada a raunane alaman mutuwar ya taba sa

Ka tabbata?

Eh yace ,ma police din

Ok toh ai kaji abunda barristr jamal yace ka amince da wannan bata da hannu akan kisan nan kenan a fadada bincike?
Kallo mai tsoratarwa ya bita da shi sannan yace
Ah'a
Ban amince ba
Don haka a kamata

Wani ihu ta buga tana jin wani zafi na hargowa a zuciyar ta shiko police dama jira yake nan ya daura mata hancufs suka fita'"cikin zuciyar sa yace inda talaka ne yaushe ma zan tsaya yarjejeniya bayan ga shaidu ya bayyana"

Ba yadda jamal baiyi ba amma haka fir ashween ya ki shima ..
A karshe Sai da aka tafi da zAhida lokacin wajen kimanin karfe 4 na asubahi

Duk abun ya dame su don For d first time doka ta hau kan su
Gashi zahida ta dage kan cewa bata kashe tania ba
Har mota jabir ya bita yana rarrashin ta cewa washe gari zasu fitar da ita
Amma sam bata jinsa sai kuka
Take tunanin ta ya za'ayi ashween da bakin sa ya sa akamata a wulakance haka

Wasa wasa haka ashween yayi tsayin daka da iya karfin sa har zahida tayi sati guda chur a hannun jamian tsaro ana ta bincike akanta

Hakan ba karamin zame musu abun kunya yayi ba
Musamman ma jamal da kowa ya sani a tarihin sa bai taba fadawa kasa a ko wani irin yanayin case ne wajen murda sharia a kotu ba

Yau ta kasance rana na biyu kuma na kusa da karshe na sauraron kara da shaidu akan zahida
Duk da ashween baya zuwa kotu
Amma lawyer da ya kawo jajirtacce ne wajen aikin sa
don haka ya sa jamal ya rika shan kunya gaban kotu
Yan jarida kuwa sunyi tsayin daka wajen daukar babban al'amarin

Abune na tarihi don a matsayin familyn rodriquez da matsayin barister jamal ba a taba samun case daya so yafi karfin su ba sai wannan

Yawanci jarida ta buga cewa don da chan rodriquez family tafi murqushe na kasa da ita ne shyasa take yawan winning case
Wani fannin kuma sun buga cewa shariar kudi da kudi ake
Saboda haka gar ta san gar "

Rashin samun su nasara yau din ma ya mugun girgiza su duk da ma ba kwarraren shaida akanta tukunna
'Yi shiru baby na im on it "kukan ya isa haka
madam hidayat tace tana shafo kan zahida
A hankali cikin rarraashi

Dago kai tayi tace Mummy..shikenan zai bari akaini prison
Akan wata ? Wayyo Allah na shiga uku,wht will happen to me ,,my beauty"mu..mmy
Pls do something mana ta karashe cikin kuka

Calm down zahida,, Sa hannun ashween akan case din nan ya zama mana babban barazA na
He's got money and words" tunda nake ban taba ganin wannan lawyrs din nashi ba
Amma kar ki damu Zanyi komai ba enda zakije indai ena numfashi ...ena kai,tafada a takaice
Fuska dauke da damuwa

I trust u mummy
Tace sannan ta goge hawayen ta tayi luf kan cinyar ta
Jamal ne ya tinkaro su suit din ma ya rike a hannu Tsaban bacin rai dake tafe da shi
" Me kika aikata haka zahida ?
Ya fada a fusace
Ko kula da yanayin su baiyi ba

Kamr yafa?
Me ya faru kuma jamal
Nan take ya dauko wayar sa ya kunna musu video
40 minutes clip ne na duk abubuwan da suka faru wajen partyn tun kafin zuwan tania har mutuwar ta

Bari hannnun ta ya shigayi tace a ena ka samu wannan?

Bai tsaya amsa ta ba ya dauko wani video 15 minutes clip
Lokacin da take ma tania barazana a shagon ta na spa da na fadar da sukayi a wajen dinner ashween an nuna dai dai ta wanka ma tania mari..

Wtf! Yace a fusace ya bar mata wayar a hannu ya juya baya yana huci

Karbe waya mummyn tayi daga hannun zahida da tuni Zuciyanta ke harbawa sama sama"Kamin bayanin wannan din ma ena ka samu?hjya hidayat ta tambaye sa cikin dauriya

Da kamar bazai amsa ba tsaban bacin rai sai ya danne zuCiyar sa yace Yanzun nan wani unknown number ya turo min akan zasu yi amfani da shi su karya rodriquez family
kinga abunda nake fada miki ko zahida
Duk haukar soyayyar ki da bin mazan ki ya jawo
Gashi Abu kadan na neman tona mana asiri dukan mu
Yhu are ruining my career,. my life zahida

Just stop der jamal haba da Allah hauka ne kuma abun naka? mummyn ta tsawatar masa
Baka ganin hankalin ta atashe ne? So kake ka kashe ta ko me

Bai fasa ba yace" Nima ai nawa a tashe yake mummy tunda mutunci na ya soma zuba gaba daya akan case din nan.

Ko zakice bakiga jarida bane for d past 4 days
Yawancin headline da ni yake farawa
ko yau din nan
Naga wani sabon headline
"The downfall of barister Jarod" me kike so da ni?

Cikin kunan rai yace "Its my dream na zama lawyer how did u xpext me to feel ina ganin yana rugujewa lokaci guda

Shiru ta danyi kafin tace

Please Login or Register in order to submit comment