Reading TRIPLETS BOOK 1 and 2 COMPLT BY FATEEMA ZAHRA MUSA PRINCESS TEEMA Chapter 85 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya shiga mota su tafi, sai ta juya tana kokarin buɗe kofar motar zata fita,

Cikin sauri Imran ya riƙo hannunta yana faɗin "Ina kuma zaki je?" Cikin halin nuna ko in kula ta ce "Wajen aiki na zan koma" girgiza kai ya yi yana faɗin ",Haba muna raye a duniyar nan family Nawazudden su yi rayuwar kunci, kai ina a baya ma da kikaga hakan ta faru bamu san in da za mu same ku bane, yanzu kuma gaki na ganki kuma kice zaki tafi, a'a haba ai ke daga nan sai Kaduna, idan duk wani abin da zan mallaka zai kare a kan family Nawazudden to ba zan taɓa danasani ba, daddynku ya taimakemu a rayuwa, ba zan iya kwatanta miki irin taimakon da ya yi mana ba, yau duk wani kuɗin da Abbana yake tin kaho da shi to Allah ne ya bashi kuma sanadin daddyn ku, dan haka yau rana ta yi da zan ramawa His Excellency abubuwan da ya yi mini, nasan ban isa na biya shi dukka ba, amma In Sha Allah zan yi kokari wajen ganin na baki kulawa, kuma na san cewa His Excellency ya fi son ki sama da komai nasa, yanzu dai abubuwa masu mahimmanci guda uku zan fara yi, na farko zan tafi da ke gidan mu, na biyu zan fara neman family ki ina suke, na uku kuma ki zaɓi duk makarantar da kike so a duk kasar da kike so, sai in kai ki karatu can".

Kasa ta yi da kanta tana jin wasu zafafan hawaye na kokarin bin kuncinta, amma haka ta daure ta mai da hawayen nan ta ɗago kanta sama ta fara magana kamar haka "Daddyna ina alfahari da kai, ina mai farincikin kasan cewar ka mutumin kirki, yau ga shi an wayi gari baka duniyar, amma saboda kirkin ka duk in da muka shiga sai an taimakemu, ba wanda za mu zauna da shi kuma mu yi kuka babu, kowa son mu yake yi, saboda kai daddy, saboda kirkin ka da alkharin ka ga mutane, gaskiya zama mutumin kirkima wani babban baiwa ce a duniya da lahira, ko kai baiwar bata taimake ka ba zata taimaki family ka, saboda gaskiyar ka aka kashe ka, aka raba mu da kai, amma ga shi muna cin albarkaci gaskiya da kuma amanar ka, har na koma ga Allah ba zan dai'na yi maka addu'a ba daddy na" ta kai karshen maganar tare da sakin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, matsowa kusa da ita ya yi, ya ɗan riƙo kafaɗun ta yana ɗan jijjigata alamar rarrashi, a nitse ya ce "Ki yi shiru Rimsha ki dai'na kuka kin ji ko? Yanzu dai ki gaya mini kasar da kike son zuwa karatun sai na fara shirye-shiryen tafiyarki" kuka ya ci karfinta ta kasa magana.

Ganin haka yasa Nawid ya ce "prof ka barta ta huta tukunnan, ka kyaleta zuwa gobe ko anjima sai ayi zancen school". Dawo da kallonsa kan Nawid ɗin ya yi yana faɗin "Dr ba zaka gane bane amma ba danu wa yanzu dai ka shiga muje gida, idan munje sai mu karisa magana a can". To Nawid ya amsa da shi sannan ya shiga gidan baya, ya bar Rimsha a gidan gaban.

Har Imran ya tada mota cikin sauri ta ce "Ba zai yi wu in biku ba, saboda kaga aiki nake yi, sai na gama biyawa Jehan kuɗin da ta karɓa tukunnan". Abin ma dariya ya bawa Imran, cikin zola lace "Ashe first lady ta girma". Sanya kyawawan hannayenta ta yi ta rufe fuskarta tana turo ɗan baki, zuba mata ido Imran ya yi na ɗan lokacin kafin ya ce "Ke dai ba in da kika baro Madam a kamanni," ya kai karshen maganar yana mai do da kallonsa kan Nawid dake gidan baya yana fama da latsa waya.

"Dr fita dan Allah ka karɓi account number Ibraheem ɗin nan ka sanya masa 1m mu samu mu tafi da wuri, kasan First lady mu daman akwai ta da gaskiya da amana kamar His Excellency, idan ba ku biya wannan kuɗin ba ba zata taɓa barinmu mu bar nan ba".

Ita dai shiru ta yi tana binsu da kallo ta kasan ido. Tuna cewa 1 million Imran ya ce a bawa Ibraheem sai ta ce "Kuɗin shi 500k ne ba 1m ba" fuska ɗauke da murmushi ya ce "E na sani amma shima dole yaci albarkacin ya taimaki family Nawazudden, ni abin da ma ya fi bani mamaki ya akayi basu iya gane Jehan ba? Ya akayi ta yi aiki a nan kuma manyan mutane suna zuwa nima ina zuwa kuma bamu taɓa haɗuwa ba?". Nawid ne ya cafki zancen da cewa "Ai yanzu da na san asalin wace ce Jehan sai na gane a baya da fake face take amfani, nima na yi mamaki da kuka ce Jehan Nawazudden ce ta yi aiki a nan, wlh ba dan daga wajen yar uwarta na ji zancen ba, da ba zan taɓa yarda ba, domin ni ba asalin fuskar ta na gani ba, da asalin fuskarta ce ai da tuni na gane ta na ɗauketa in je in haɗa ta da baby uwar dirama, amma kasan abin da ya ke bani mamaki kuwa?"

Girgiza masa kai Imran ya yi alamar a'a bai sani ba "Jehan Nawazudden tun tana primary 6 lokacin da ta fara media lokacin na kamu da son ta, kasan ita ko ka mata dm bata reply, naso yarinyar nan kamar hauka, amma bani da hanyar da zan iya ganinta, hakan yasa na danne na hakura ina dakon so, sai ga shi yau an wayi gari na haɗu da ita a wani irin yanayi da ba zamu ina gane juna ba, kai wannan abu ya mini ciwo sosai, ba zan taɓa mantawa da shi ba".

Yar dariya Imran ya yi yana faɗin "Baka sanar da ni bane ai ni dana kai ka har cikin gidan su, His Excellency yana da kirki sosai, yana kuma kaunata fiye da tunaninka, ni bana zama a palon baki ma idan naje, kai tsaye palon gidan nake shigewa kamar ɗan gida, lokacin da na koma school ne abubuwa suka ja baya, amma duk yaran sa ba wanda bai san ni ba, kuma kamar yadda kaga Jehan a Media bata yi wa mutane magana, to haka take ko a gida ma, bata yi wa mutane magana sam, idan naje ga mai yi mini magana nan first lady, daga ita sai Aunty Aisha da Madam, ita kuma wannan mage sarkin son jiki ce, kulkun tana jikin daddynta, ko ba haka akayi ba?" Ya kai karshen maganar yana dariya yana leƙo fuskarta.

Murmushi ta yi har sai da dimple nata ya lotsa, tabbas ta gane Imran amma sai dai lokacin da yake zuwa gidansu tana karama bata kai haka ba.

Fita daga motar Nawid ya yi zuwa cikin restaurant ɗin, kamar yadda Imran ya ce haka ya yi, ya karɓe Account number Ibraheem ya sanya mashi kuɗin, sannan ya juya zai ta fi, cikin sauri Ibraheem ya miƙa mashi wayar Rimsha yana faɗin "ga phone ɗin ta" karɓa Nawid ya yi, sai zuba godiya Ibraheem yake yi, da haka suka yi sallama.

Lokacin da ya dawo mota ya same su, Rimsha ta ɗan saki jiki suna hira da Imran, domin tun abaya ta sanshi, kuma ko ba'a faɗa mata ba tasan mutumin kirki ne, domin daddynta baya alaka da mutanen banza, duk wanda ka gani tare da daddy to yana da kirki sosai, ba mutunne wanda za'a yar ba, ba zata taɓa manta lokacin da Jehan take cewa bata son ganin Imran ba, a lokacin ya zo gidan su, daddyn su ya ce In Sha Allah in dai yana da rai sai ya aura mata Imran tun da ta raina shi, ranar wuni kuka Jehan tayi wai an kaskantar da ita, ko da wasa daddy yake yi bai yi mata adalciba, ya haɗa ta da bawansu.

(Kai Jehan duniya, ka ji wai bawan su🤔)

Kallonta Imran ya yi yana faɗin "First lady zamu iya tafiya?". Cikin girmamawa ta ce "Yaya Imran tun da ka ganni a nan ai kasan dole akwai wayan da nake karkashin kulawar su ko? Amma shine zaka ce mutafi ban sallame su ba?" "Afuwan our first lady yi mana jagora zuwa gidan su mu zuba musu godiya".

Shiru ta ɗan yi tana tunani ko zata iya gane hanyar, dan kwana biyun da ta yi, Sadiq ne yake kawo ta kuma da yamma ya dawo ya ɗauke ta, sai dai ta gaya musu sunan anguwar kawai idan sun kai nan zata iya gane gida, haka yasa ta juya ta sanar da shi sunan anguwar, kallon Nawid ya yi alamar ko ya san anguwar, dan shi ba garinsu bane.

Gyaɗa masa kai Nawid ya yi alamar ya sani, ba ɓata lokaci ya tashi motar, Nawid na nuna musu hanya suka nufi gidan su Sadiq.

Kamar Kullun zaune suka isko Yusuf a kofar gida yana aikin nashi, wato sa wa mutanen da suka zo wucewa ido, ita kuma Hanan tana aikin tuyar awararta, Sadiq na gare ji bawan Allah.

Kusan a tare Rimsha da su Imran suka fito, sai kallon su Yusuf yake yi.

Tun daga ɗan ne sa Rimsha ta ce "Yaya Yusuf ya kake zaune a ranan nan?" Washe baki ya yi dan a tunaninsa Rimsha ba zata kula shi ba, dan ta zo da masu mota, Allah sarki bai san cewa ita Rimsha ba bakuwar arziki bace, a cikinta ta taso dumu-dumu.

Ba tare da ɓata lokaci ba ta yi musu sallama ta fito, mayafi maman Sadiq ta ɗauka ta rakota har wajen motar, gaisawa suka yi da Imran cikin mutunci da girmama juna, sannan ya zuba mata godiya sosai da sosai suka yi sallama, ya ciro 200k ya bata yana kara yi mata godiya. Da farko taki karɓa, amma daga baya daya matsa mata sai ta karɓa ta yi mashi godiya, ita kuma Rimsha ragowar 4k da ya rage a hannunta ta ɗauko ta bawa Yusuf dan shine abokinta.

Ɗan kwana biyun nan da tayi sun yi sabo sosai, dan Yusuf ma yana da hankali. Da haka suka yi sallama, Rimsha ta shiga mota kamar zata yi kuka, Imran ya buɗe gidan baya ya sanya mata trolley ta sannan ya shiga mazaunin driver ya ja motar suka kama hanyar Kaduna, Dr Nawid sai fama da latsar waya yake yi.

(Nima kuma na haɗa kayana na nufi wajen Jehan yar amana)


💖ABUJA💖

Kata faren gida ne mai girman, wadda da kaga gidin kasan arziki ya zauna wa mamallakan wannan gidan. Hawa ɗaya ne, zaka iya saka gidan a jerin gidan manyan masu kuɗi na faɗin Nigeria.

A kofar wannan gidan motar Hajiya da ta ɗauko Jehan ta tsaya tare da danna horn. Horn ɗaya mai gadi ya wangale mata gate ɗin gidan, cikin kwarewa ta danna hancin motar cikin gidan, kallon gidan nan Jehan take yi tana tunanin anya gidan nan ba wani abu kuwa, ace irin wannan haɗaɗen gida kuma azo ayi shi a keɓaɓen waje kamar haka? Dole a dasa mashi ayar tambaya, Jehan akwai kwakwalwa da kaifin basira abin ba'a magana.

Tana tsaka da tunani ta tsinkayo muryar Hajiyar tana faɗin "Jehan mu je ko?" Kallonta Jehan ta yi kafin ta fito daga cikin motar, zuciyarta sai ayyana mata abubuwa da dama dangane da wannan gida take yi, domin wannan gida bai yi kama da gidan masu gaskiya ba, ya fi kama da gidan marasa gaskiya, ita kanta Hajiyar bata yi kalar masu gaskiya ba.

Jehan bata karasa shi ruɗani da tantama a kan wannan gida ba har sai da suka shiga cikin palon gidan, a irin kallon da take yi wa wannan Hajiyar bata yi kala da mace mai aure ba, to waye ya bata wannan gida? Sannan me yasa za'a yi wannan gida a wajen keɓaɓe haka?.

Suna shiga wani ɗan karamin yaro da bai wuci shekara biyar ba, kamaninsa ɗaya da Hajiyar nan, ya taso da gudu ya yi wajen Hajiyar yana faɗin "oyo mummy". Rungume shi ta yi a jikinta, ita ma tana faɗin "Oyoyo ɗan lele na".

Mamakine ya sake kama Jehan, kenan Hajiyar nan ta yi tafiya daga nan Abuja har zuwa Katsina ta bar wannan yaron shi kaɗai a cikin gidan ne? Dan da alama ba wani motsi mutun a cikin gidan, wannan yaron shi kaɗai ne a ciki, sai mai gadi dake bakin gate.

A karo na biyu ta lula duniyar tunani sai tsinkayo muryar Hajiyar ta yi tana faɗin "Jehan ga waje ki zauna mana, ki saki jikin ki fa, zuwa dare zan kai ki wajen aikin kin ji?".

Ba musu ta zauna saman luntsumemen sofar dake wajen, har yanzu zuciyarta bai dai na mamakin dukiyar da aka narka wa gidan nan ba, ta dai zuba ido ta ga me zai faru.

Saman sofa ita ma Hajiyar ta zauna tana sauƙe numfashin a hankali hankali, shi kuma ɗan lele da gudu ya nufi cikin ɗaki ya ɗauko cake ya fito yana faɗin "Mummy i want to play with this cake".

"Go ahead mana my ɗan lele" ta faɗa tana ƙoƙarin fito da wayarya daga cikin jakarta.

Kusa da Jehan ɗan lele ya zo ya zauna, tare da fara ɗaban cake ɗin yana shafa mata a fuska, kamar ta ce mashi ya yi mata hakan.

"Ɗan lele me yasa kake ɓata mata fuska da jikinta haka? Ka bari mana, baka ga bakuwa bace?" turo baki ya yi yana faɗin "A'a mummy ni ina son ɓata mata ko ina a jikinta ne".

Murmushi Hajiya ta yi tana faɗin "To ɗan lele na, amma da ka barta ai".

Wani mugun kallo Jehan tabi Hajiya da shi, a ranta taka maimaita abin da Hajiyar ta faɗa, wato ɗan lele ya ci gaba da ɓata mata jiki, su ga su ƴaƴan masu kuɗi, komai suka yi daidai ne, basa laifi.

Tana tsaka da tunani, ɗan lele ya ɗebo cake yana kokarin cusa mata a cikin hancinta. Wani gigitatcen mari ta sakar mashi, wadda ya sanya shi tafiya ta baya baya, ya buga kai da jikin table, da karfi ya fasa ihu mai raza kwakwalwar mai sauraro, ita kuma Jehan miƙe wa tsaye ta yi, rai a matukar ɓace ta ce

"It seems like you have not been morally train in this house, and I will give you instantly, be get prepare"

(Toh fa ɗan lele ga maganin ka nan ta zo gidan, sai ka shirya.🤣)

A zafafe Hajiya ta miƙe cikin tsawa ta fara magana, da karfi-karfi "Akan me zaki mare shi Jehan? Dan ya saka miki cake a jiki? Baki ganin yaro ne shi?!!".

Ko kallon in da take Jehan ba ta yi ba, shi kuma ɗan lele sai kuka yake yi yana birgima a kasa, irin dai sangartattun yaran nan.

Komawa Jehan ta yi ta zauna saman sofa tana ɗaure fuska, domin a cewar ta bata da lokacin ɓata bakinta wajen bawa Hajiyar nan amsa.

Da kamar Hajiyar zata sake yin magana, amma kome ta tuna sai ta fasa ta ɗauki wayarta da jakarta tare da ɗan lele suka wuce sama bene.

Kallon banza Jehan ta bisu da shi kafin ta dawo da hankalinta kan binciken da tunanin a kan gidan.

Hajiya kuwa tana shiga cikin ɗauki ta rarrashi ɗan lele, bayan ya yi shiru ne sai ta ɗauki wayarta ta danna kira.

Jim kaɗan a kayi picking call ɗin, kamar tana gaban wadda take waya da shi, cikin girmamawa har tana wani yin kasa da kai ta fara magana "Allah ya taimake ki ranki ya daɗe, yau fa Allah ya yi zan cafki kuɗi yadda ya kamata" shiru ta ɗan yi da alama tana sauraron abin da ake faɗe a ɗayar ɓangaren ne, ma'ana tana sauraron abin da wadda ta kira ɗin take faɗe.

Bayan wasu yan sakannin da ba su 30 ba, sai ta cigaba da cewa "Wlh ranki ya daɗe yarinya ce bata san komai ba, kuma idan kin ganta ko ke sai kin ruɗe kyakkywa ce, amma fa nasan idan kika ganta zaki iya gane yar wace ce, yarinyar Nawazudden ce, kin san sun yi haɗarin mota ya rasu, to ashe familynsa suna Katsina dana je duba kanwar kawata ɗin nan da abin ya sha kan taaaaaa, to a nan naga Jehan". Shiru ta sake yi tana sauraron abin da ake faɗe a ɗayar ɓangaren bayan ta kai aya.

Bayan ɗan lokaci kamar minti ɗaya sai ta ce "E da farko da fake face take yawo, nima ban gane taba, sai da na ce zan ɗauketa shine iyayen nata suka gaya mini gaskiya, sai na ce to ta cire fake face ɗin dan yanzu mutane ai sun fara mantawa da ita, wasu ma sun mance da ita, dama kin san Jehan akwai kyau iya kyau, wlh zaki samu kuɗi bana wasa ba" dakatawa ta yi dan jin me wacan ɗin zata ce.

Bayan ta gama ji sai ta ce "To shikenan kamar dai yadda aka saba, shabiyun dare na cika daidai zan kawo ta, amma fa kin san bata san komai ba kada ki bari su zinariya su taɓata har sai kin dawo, sai ki ɗaurata a kan hanya da kanki". Shirun minti biyu ta sake yi kafin ta kwanshe da dariya ta ce "Gaskiya na ji daɗi, amma da an kara mini wani abu a saman 1 million ɗin, kin ga fa budurwace". Dif ta ji an katse kiran ma'ana kenan ciniki ya faɗa Millon ɗaya aka sayi Jehan.

(Toh fa babbar magana🤔)

Bayan ta kammala wayar ta ajiye ta miƙe ta sauƙo Palo, yadda ta bar Jehan ɗin haka ta dawo ta sameta, shi kuma ɗan lele dama tun lokacin da ta fara waya ya fice abin shi.

Da kanta ta kawowa Jehan lafiyayyen abinci har da ruwan sha, har cikin zuciyarta Jehan tana tantama a kan wannan matar, amma da yake tana jin yunwa sai ta sauƙo ta ci abincin, bayan ta kammala Hajiyar ta nuna mata ɗaki akan ta shiga ta kwanta ta huta zuwa dare sai suje wajen aikin. Ba musu ta wuce zuwa ɗakin, ita ma Hajiya ta wuce ta koma sama abinta, ranta fes yau ta kawo mai tsoka an bata 1 million.

After some hours 👌

Karfe 12 na dare daidai motar wannan Hajiya ya fito daga gidan ta ya miƙi wani hanya, kai daga ganin irin wannan fita kasan babu gaskiya ko kaɗan a cikinta, ita kan ta Jehan sai mamaki take yi, anya ba wani abin a kasa kuwa? Kamar wasu munafukai, fita tsakiyar dare, kai ba'a kulla gaskiya a wannan lamarin ba kwata-kwata.

Sun yi tafiya mai ɗan nisa kafin su iso wani sihir tatcen gida cikin gidan.

(Tofa gida kuma cikin gida?🤔)

Da farko idan ka shigo gidan zaka yi tunanin normal gida ne kaman ko wani gida, sai dai ba hakan bane, ginin gaba anyi shine kamar normal gidan mutane, while daga baya kuma ta ciki aka yi wani irin tsantsarerren gida wadda kusan rabin shi a cikin kasa yake, hakan yasa ba zaka sami damar ganin wannan ginin daga ta waje ba, sannan ta bayan wannan ginin sirrin akwai wani gini shima mai kama da gidan mutane, a takaice dai gini a kayi kamar normal wadda ya kewaye wannan ginin sirrin dan kada a gane me yake ciki, idan har ba shigo da kai akayi ba, ba zaka taɓa tunanin cewa akwai wannan gini a wajen ba.

Horn ɗaya Hajiyar nan ta yi masu ganin wajen suka wangale mata tampatsetsen gate ɗin gidan.

Kutsa hancin motarta ta yi zuwa cikin gidan, a parking space nasu ta yi parking sannan ta fito tare da faɗin Jehan ta fito su tafi.

Ba musu Jehan ta fito suka kama wani ɗan hanya a wajen suka fara tafiya, ginin farko akwai wutar lantarki a wajen, haske ko ina, amma da suka ratsa cikin gidan zuwa gini na biyu sai taga wutar ginin na biyu daban dana farko, wuyar wajen green ne da kuma blue ba su da haske sosai, sannan ginin dake kewaye da wannan suna da tsawo sun kare wannan ta yadda ba wanda zai iya ganin wannan daga ta wajen.


🏬*A company of quality Prostitutes*🏬

Shine abin da Jehan tagani an rubuta a kofar shiga wajen, mamaki ne ya kara bayyana a kan fuskar ta, amma ta kasa yin magana domin bata ma san me zata ce ba.

Wani kafataren palo suka fara cin karo da shi, palon ya ji komai da ake buƙata, sai dai an yi wa palon tsari irin na office ne, idan ka ga palon zaka yi tunanin office ne, amma fa ya haɗu sosai da sosai, saman sofa suka zauna, daga gefe a cikin palon, wani kyakkyawar table ne mai ɗan girma sai kuma office chair a wajen, da alama dai wajen manager company ne.

Wani katon hoton ne ke manne a jikin bangon kusa da table ɗin ta sama, hoto ne wadda ko ba a faɗa maka ba kasan cewa wannan hoton mamallakin wajen ne, irin hamshaƙan matan nan ne, wadda Naira ta zauna musu, farace tas amma kana gani kasan farin bilicin ne, ga hancin nan nata kamar me a bage a kumatun nata, ga kofofin hancin nata a buɗe kana hango har canciki, amma a haka ta zo ta damɓara hujin hanci ta kuma saka wani katon yan kunne, abin ba kyan gani ita a dole ta yi kwalliya, a dake take saman wani haɗaɗɗen kujera irin na gidan sarautar nan, tana hakimce ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya, kai daga ganin wannan matar kasan ba sauƙi, dan ga shi a hoton ma fuskarta babu alamar annuri ko kaɗan, inaga kuma anzo zahiriyya? Ta ci uban make up a fuskarta, ga eyelashes da ta tabka a ido kamar bindin kaza, duk da wannan kwalliya da ta sha, hakan bai hana ka ganin muninta a filliba, mummuna ce sosai, daga gani wannan kabilace ba hausa fulani ba ce.

Ta shagala da kallon wannan hoton tana mamaki sai sinkayar Muryar hajiya ta yi tana faɗin "Jehan ta shi ku je ko" cikin sauri ta dawo da kallonta kan Hajiya, sai ta ga wata matace ke tsaye a kan su, ta shiga duniyar tunani kwata-kwata bata ga shigowar matar bama.

Matar irin Hamshaƙan tantiran yan duniyar nan ne, ta wani ci uban make up ga eyelashes ita ma a idonta kamar bindin zakara, ta ci matsu riga t-shirt da wando guntu zuwa gwiwarta, kayan sun matseta over, idanunta a buɗe garau suke, babu alamar kunya bare tsoron Allah, kai daga gani kasan bariki ya yi musu katutu, da alamama bariki ta kusa yayesu ma, amma kuma a shekaru ba zata wuci 35 years ba.

Ba musu Jehan ta miƙe ta bita, domin dama ta ƙagu ta shiga cikin gidan nan dan ta ga me suke aikatawa a cikin shi, sannan kuma aikin me zata yi. Suna shigewa cikin gida Hajiyar nan ta tashi ta fita zuwa wajen motarta, ta shiga ta bar gidan baki ɗaya ta koma gidanta.

Ita kuma wadda ta tafi da Jehan, bayan sun shiga cikin gidan, ɗakuna ne a gere a gere, a rufi ɗaya kamar hostel na student, ko wani ɗaki da number a jikin shi. Daidai tsakiyar wajen suka tsaya matar ta ce "Shekarun ki nawa?". "16 to 17 Jehan ta bata amsa.

Wucewa gaba matar ta yi ba tare da ta sake yin magana ba, bin bayarta Jehan ta yi har suka je wajen wani ɗaki da aka sanya number 17 a kofar ɗakin, da hannun matar ta nuna mata ɗakin a kan ta shiga, ba musu ta buɗe kofar ɗakin ta shiga bakinta ɗauke da sallama.

Ɗaki ne kamar ko wani ɗaki, sai dai kuma gadaje huɗu ne a cikin ɗakin, shiru ta yi tana kallon yan matan dake kwance a saman gadaje biyu daga ciki gadajen.

Shiru ta tsaya ta kasa gaba ta kasa baya, kawai kallon ɗakin take yi. Kamar daga sama ta ji an taɓata ta bayan ta ana faɗin "Barka da zuwa gidan farinciki". Cikin sauri ta juyo da yake wutar ɗakin nasu green color ne baka iya ganin fuskar mutun da kyau, sai Jehan bata sami damar gane wace ce ta yi mata magana ba.

Hannunta yarinyar ta ja zuwa saman ɗaya daga cikin bed ɗin ɗakin, sannan ta miƙe ta canza musu wutar ɗakin zuwa blue light dan su samu damar ganin juna. Bayan ta kunna ta dawo ta zauna kusa da ita tana faɗin "Garama ki saki jikin ki domin ba bu wani abin da kamewa zata

Please Login or Register in order to submit comment