Reading TRIPLETS BOOK 1 and 2 COMPLT BY FATEEMA ZAHRA MUSA PRINCESS TEEMA Chapter 80 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yana son Michael sosai kuma bayan son ya ja baya da shi, hakan yasa ya amsa da to kuma ya miƙe ya bi bayan shi.

Abin mamaki yau zaune a saman dining table suka isko Lion, abin da ba su taɓa gani ba, Lion da cin abinci karfe 7 basu taɓa gani ba, har su kansu bodyguards ɗin sun sha ruwan mamaki, domin wani lokaci abincin dare sai karfe uku yake ci, wani lokaci ma haka yake kwana bai ci komai ba, barema yan kwanakin nan kwata-kwata baya wani cin abinci.

Musharraf bai taɓa zama a saman dining table nasu ba sai yau, ganin Lion ya sa ya sha jinin jikinsa, ji ya yi tamkar ya koma ɗaki, amma ba hali, domin sun riga sun fito idan ya koma Michael ba zai ji daɗi ba.

Kusa da Lion Michael ya zauna yana faɗin "Good evening Lion" tamkar babu shi a wajen, haka Romeo ya kasan ce, ko kallonsu bai yi ba, fruits kawai yake sha, cikin class da kwantatciyar hankali.

"Uncle ɗin James me zaka ci?" Cewar Michael, ɗan satar kallon Romeo ya yi, yana son cewa zai ci komai amma banda namar da Allah ya haramta idan suna ci, shi baya ci, amma kuma yana tsoron faɗin hakan, dan James ya ce masa kada ya yarda ya bari su gane cewa shi musulmi ne.

"Uncle ɗin James why kayi shiru talk now?". Musharraf ya rasa me zai ce, yana tsoron ya ce a bashi komai, azo a zuba masa abin da Allah ya haramata ya ci ba tare da ya sani ba, sannan yana tsoron ya ce kada a saka masa abin da Allah ya haramta ya jawo baban yaki a gidan.

Ganin haka yasa Michael ya ce da bodyguard ɗin su haɗa masa tea kawai, Lion na jin duk abin da suke yi, sai dai ba su isheshi kallo ba ne, dan kallonsu ma ɓata masa ido za su yi.

Bayan bodyguards sun haɗawa Musharraf sun miƙa mashi, shi kuma Michael ya fara ɗura fruits yana shan ruwa mai sanyi. Ya ji yunwa sosai bawan Allah.

Bai wani ci sosai ba ya fara kwarara amai a wajen kamar menene, cikin sauri bodyguards biyu daga cikinsu suka yo kansa, shi kuma Lion zame hannunsa ya yi daga kan fruits da yake sha, ɗaya daga cikin bodyguard ya miƙa masa tissue, ya karɓa ya goge ɗan bakinsa tare da hannunsa, sannan ya juyawa su Michael baya tare da ɗaukar wayarsa dake gefensa ya fara latsawa.

Cikin yan mintuna kalilan sai ga Tga, kusa da Lion ya zo yana faɗin ga shi nan, da hannu Lion ya yi masa nuni da Michael ba tare da ya yi magana ba, sannan ya miƙe ya bar wajen.

Da sauri Tga ya ƙarisa wajen Michael ɗin yana tambayar bodyguards ɗin lafiya me ya sami shi, cikin girmamawa suka ce suma basu sani ba, Musharraf yana son zuwa ga Michael amma yana tsoro, da farko saboda Lion na wajen yasa bai karisa wajen Michael ɗin ba, lokacin da Lion ya tafi kuma Tga ya zo, hakan yasa ya hakura kawai yana ganin Tga ya saɓi Michael suka wuce sama.

Kai tsaye toilet ya kai shi, sannan ya fito ya kyaleshi, da kyar ya iya yin wanka saboda ya galabaita sosai, yinwa ya ke ji over, ga shi ya zo ya sha ruwa mai sanyi da fruits shiyasa ya yi amai.

Ɗaure da towel a kugunsa ya fito bayan ya yi wanka, pajama kawai ya sanya a jikinsa, ya lallaɓa ya fito palon kasa.

Bai ga Musharraf ba, kuma bai damu ba, dan yasan ya tafi ɗakin sa ne, saman table ɗin ya sake komawa, domin yunwa yake ji, already bodyguard ɗin sun gyara ko'ina fes, sun goge amai ɗin sai tashin kamshi wajen yake yi.

Zama ya yi tare da basu umarnin su haɗa masa coffee mai zafi, cikin hanzari suka haɗa masa, yau ba shan salo da class, tun da ya kafa ɗan bakinsa a cup ɗin bai sauƙe ba har sai da ya shanye tas, wani daɗi ya ji, lokacin da ya ji cikinsa ta yi ɗumi.

Miƙewa ya yi dan ya kasa iya sake cin komai. Yana kokarin hawa saman bene suka haɗu da Tga yana sauƙowa, nan fa Tga ya ce ya wuce su tafi word room a duba lafiyarsa. Tirjewa ya yi ya ce shi lafiyarsa lou dan haka babu in da zai je, ba yadda Tga ya iya haka ya hakura ba dan yaso ba, sai dan baya son su yi jayayya, dan ya san Triplets gaba ɗayansu ba mai magana ya sauya, ɗan gara shi Micheal ɗin ma, idan abu ya zo da matsala yana iya sauya magana, amma Lion da James ko uban matsalane basu taɓa sauya magana sai dai ayi wace za'a yi, sai dai a mutu.

Wucewa Part nasa ya yi, kai tsaye bedroom ɗin Musharraf ya shiga. Sallah ya isko Musharraf yake yi, saman gado ya haye yana kallonsa.

Bayan ya idar ya yi addu'a ne ya ce "Michael sannu ko" dogon numfashi Michael ya ja tare da saukewa a hankali.

"Uncle ɗin James gobe zan saka John ya karo maka wasu kayan sawa, dan na lura wayan da James ya saya maka basu da yawa sosai" murmushi Musharraf ya yi yana zuba mashi godiya.

Saukowa kasa Micheal ya yi, ya zo ya zauna suna fuskantar juna, a nutse ya ce "Uncle ɗin James, idan kana yin wannan abin da ka yi yanzu yana burgeni sosai, ko zaka koya mini ne?" Cikin sauri Musharraf ya ce mashi "Sallah kake nufi?" Gyaɗa kai ya yi yana faɗin "Wannan abin da na shigo na sameka kana yi yanzu". Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Michael ba'a yin Sallah sai idan mutun ya kasan ce musulmi ne, azumin ma da kaga na barka ka yi saboda nasan kuma kuna yin shi ne, a addinin ku ya halakta, amma shi Sallah wanda ya musulta ya karɓi Kalmar shahada ne kawai yake yin shi".

Shiru ya ɗan yi kamar mai tunani, can kuma sai ya ce "To shi me ma kace? Idan za'a shigeshi kuɗi za'a bayar ne ko me?" girgiza kai Musharraf ya yi alamar a'a, sannan ya ɗora da cewa "Musulunci ba'a shigar shi da kuɗi, kyauta ne". "To ko ma da kuɗin ne ni ka shigar da ni ina so, kuma ina da kuɗi a account na sai na sanya a ciro maka, idan ma yanzu kake so sai na je ɗakin Lion na ɗebo maka, dan shi yana ajiye kuɗi sosai a ɗakin shi".

Tsabar daɗi Musharraf bai san lokacin da ya riƙe hannayensa ba, cike da farinciki ya ce "A'a Michael kyauta ake shiga musulunci, kuma yanzu zan saka ka, amma fa sai ka mini alkawarin ba zaka taɓa gayawa kowa ba, kuma ka yi mini alkawarin duk abin da na koya maka zaka ɗauka kuma zaka rinƙa amfani da shi, sannan ba zaka gayawa kowa ba".

Cikin sauri Michael ya amsa da ya yi alkawari zan rinƙa rike komai da za'a koya mashi, sannan kuma ba zai taɓa gayawa kowa a gidan ba, kuma zai rinƙa yin duk wani abin da Musharraf ɗin ya ce masa ya yi. Daɗi a wajen Musharraf ba'a magana, duk da cewa dama yasan Michael ba zai yi wuyar karɓar addinin musulunci ba, saboda a halin da yake ciki yanzu ƙwaƙwalwar sa babu komai na kin wata addini a cikinta, sai ma son mutane dake cikinta.

Babu tunanin me zai je ya zo, babu tunanin abin da zai iya fuskanta, ya mance gidan William jacop yake, a tunaninsa Michael zai iya riƙe sirrin, cikin sauri ya yanke hukuncin bawa Michael kalmar shahada, shi kuma Michael cike da murna ya karɓa ya maimaita, sau uku yana maimaita wa, ya ce kalmar ta mashi daɗi over.

(Babbar magana, yau ake yin ta, shin kuna tunanin Michael zai iya rufe wannan sirrin? Kuna tunanin Michael zai iya addinin musulunci? Zai iya Sallah sau biyar a rana? Ya batun tashi sallar asuba? Zai iya kuwa? Zai iya azumi? Sannan zai iya yin basaja, a cikin gida ya nuna musu shi Kristar ne a wajen Musharraf kuma musulmi? Kada ku mance Michael baya karya, bai iya ba kuma bai taɓa yi ba, in fact bai ma san yadda akayi ba, ya ya kuke ganin wannan cakwakiya zata kasance? Yau ake yin ta, ni dai sai dai na ce Allah ya jiƙanka Musharraf)

Farinciki yasa Musharraf ya ringume shi yana hawayen murna, shi Micheal bai ɗauka wani abin arziki ya yi ba, sai bai wani damu ba, mamakin farincikin da Musharraf yake yi ma ya yi.

"Michael daga yau na canza maka suna zuwa Aryan" turo ɗan bakinsa ya yi ya ce "Ni uncle ɗin James bana son Aryan, ba bu daɗi sunan, why zaka canza mini suna ma tukunnan?" Fuska ɗauke da murmushi Musharraf ya ce "Ai dole na canza maka suna, domin sunan ka ba na musulmai bane, kai kuma musulmi ne yanzu" jinjina kai ya yi yana faɗin "Okey tom ka nemo wani suna banda Aryan kam, dan Aryan babu daɗi" shiru Musharraf ya ɗan yi, na yan mintoci kafin ya ce "Yauwa to Asif ya yi maka?" Gyaɗa masa kai ya yi alamar E ya yi mashi.
Yau farinciki a wajen Musharraf ba'a magana, shi kuma Michael mamakin ganin Musharraf a hakan ya jefashi cikin tunani.


Edited




Suna zaune a wajen har lokacin sallar isha ya yi, a tare suka shiga toilet suka ɗauro alwala, Musharraf ya nuna masa yadda ake yi. Bayan sun fito, Musharraf ya yi kokarin nuna masa yadda zai yi sallah, nan fa ya ce aa ai yasan yadda ake yi, abin da dai ake karantawa ne bai sani ba, amma yana kallon friend ɗin James yana Sallah, bayan haka kuma a school nasu akwai musulmai da suke sallah yana gani.

Musharraf bai da mu ya ce to ya kwatanta masa ya gani, haka kuwa ya kwantanta, kaɗan ba yawa Musharraf ya ci gyaranshi sanann ya yi musu jagora ya tada Sallah in da ya ce duk yadda ya yi shima Michael ɗin haka zai yi, ba sai ya karanta komai ba tun da bai iya ba.

Sun yi Sa'a har suka idar da sallah ba wanda ya shigo cikin ɗakin, bayan sun idar da sallah ne, Musharraf ya zauna ya fara koya masa wasu abubuwa daya kamata ya fara iyawa

(To fa me kuke tunanin makomar Musharraf idan har zakunan gidan suka gane ya musuluntar da Michael wato Asif a yanzu? Hmmmm a kwai dai chakwakiya, ni dai na haɗa kaya na domin na je na gani ya Rimsha take, ta farfaɗo ne ko yaya)

💖💖NIGERIA 🛬💖💖

💖💖KATSINA STATE💖💖


Cike da tashin hankali maman Sadiq ta zuba mata ruwa, bakin ta ɗauke da kalmar shahada tare da salatin annabi ta farfaɗo. Baiwar Allah zuciyarta tamkar zai buga ya faso kirjinta ya fito waje.

Hakuri maman Sadiq ta yi ta bata, haka ta hakura ya zata yi, a halin da take ciki yanzu mutuwa shine abinda kawai ta fi buƙata, a cewarta ta ga ji da wannan bakar rayuwa mai cike da bakinciki.

After some hours👌

Bayan ta ɗan warware, har wanka ta yi, sannan ta nemi Yusuf da ya rakata wajen da ake wanke kai, gashinta ya yi datti sosai zata wanke. Nan Yusuf ya sanar da ita sai sun shiga cikin gari sannan za su samu shagon wankin kai. Buɗe trolleynta ta yi ta sanya wayarta a ciki sannan ta ɗauki hijabinta har kasa tare da face mask ɗin ta suka tafi bayan sun sallami maman Sadiq kenan.

Ahmad ya kira wayarta dan ya ji ko ta isa lafiya, amma ina shiru bata ɗauka ba, ya mata miss call ya kai goma, ta sanya wayar a silent bata ji ba, ya shiga damuwa sosai, sai tunani yake kadda ace wani abin ne ya sameta a hanya, ya yi kokarin kiran layin Ayla, amma a kashe, daga karshe dai ya hakura zuwa dare ya ce sai ya sake gwadawa.

Ita kuma Rimsha kuɗin mashi ta biya musu zuwa cikin gari.
Da suka je, a cikin kuɗin da Ahmad ya basu 20k ɗin nan, a ciki ta zari 2k ta biya aka wanke mata, dark black curly hair ta, ba karamin kyau ta yi ba, daga nan suka wuce wajen gyaran kafa, bata yi wani tunani ba kawai ta hau kashe kuɗin hannunta a wajen gyara, har da wani cewa a mata kunshi, ai kuwa kunshi mai kyau suka mata suka karɓi 3k, ta yi kyau kam iya kyau kamar ka saceta ka gudu da ita.

Rimsha tana bala'i son gyaran jiki da sauransu, tana da bala'i tsabta, ko nawane zata iya kashewa a kan gyaran jiki, haka ita ma Jehan akwai ta da bala'i tsabta, sai dai Rimsha ta fita.

Bayan an mata komai ta fito tsab, sai ta ce da Yusuf su tafi, shi kuma duk in da ta je yana biye da ita, haka kawai ta burge shi, saboda tafi jehan saukin kai da girmama mutane, domin kuwa ita tun farkoma yaya ta kira shi, saɓanin Jehan da take ce musu dirty boys.

Kamar yadda suka zo haka suka koma a kan mashin, sai dai kowa da na shi mashin ɗin, naira 7500 Rimsha ta kashe, wankin kai da gyaranshi 2k, wankin kafa da yanke kumba (farce) shi kuma 1500, kunshi 3k sai kuɗin mashin zuwa su biyu 500 komawa ma 500 saboda kowa da mashin nashi.

Suna komawa gida suka isko maman Sadiq a kitchen tana ta faman hura wuta, ɗaki Rimsha ta shiga ta cire hijabinta tare da yafa gyalen abayar jikinta ta fito ta kama wa maman Sadiq aiki, ta fara share tsakar gidan. Sai mamaki maman Sadiq take yi, sai tambayar kanta take yi ya akayi Rimsha ta iya aiki Jehan bata iya ba, kuma Jehan ce babba, sai dai babu mai bata wannan amsa, haka ta share zance ta ce da Rimsha ta koma ɗaki ta zauna, kada ta damu zata yi aiki, kin yarda Rimsha ta ya, ba yadda maman Sadiq ta iya haka ta kyaleta ta kama mata aikin.

(Nikuma na tattare kayana sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu a gidan Abba, wato wajen yaya Akil🙃 amma dai kawai cakwakiya, yanzu muka fara shiga cikin ainahin labarin, sai ku gyara zama Ma'assalam✍️🥱)

Kafin na tafi bari na yi muku tambaya, wace ce Hajiyar da ta ɗauki Jehan? Ina kuma ta kai ta? Me yasa ta ba su address na karya? Me hakan yake nufi? Ina su mum suka tafi? Ya makomar Rimsha? Ina jiran amsa.🤣[11/17, 12:27 PM] +234 906 579 6460: 💖💖TRIPLET'S💖💖


💖💖GIDAN ABBA💖💖


Aafia suna shiga ɗaki, Akila ta ce mata tana zuwa bari ta ɗebo ruwan zafi ta haɗa mata tea, ai kuwa Akila na fita Aafia ta tashi cikin sauri ta lallaɓo zuwa palon su Akil, kamar wata ɓarauniya haka take tafiya.

Tana shiga ta ɗauki wayarta dake saman sofa cikin sauri ta fice. Tana komawa ɗakin Akila ta fara neman layin Rufee.

Ai kuwa kamar jiran kiran Rufee take yi, bugu ɗaya ta ɗaga, murya kasa kasa A'afia ta ce "Kiyi hakuri Rufee, gobe zamu haɗu a school kin ji?" Daga ɗayan ɓangaren Rufee ta ce "Ba komai kada ki damu, yanzu dai abin da nake so da ke ki turomin hoton wannan da ya bugemun nan idan kina da shi" to A'afia ta amsa da shi, sannan suka yi sallama, cikin sauri A'afia ta shiga WhatsApp ta tura mata duka wasu hotonan Akil da take da su a wayar.

Bayan ta kammala ta ajiye wayar ta kwanta tana tunanin yadda za'ayi ta iya zama a wannan gida tare da Akil, dan ta san takura mata zai yi, saboda ya fi yaya Irfan tsanani, ya fi su Imran duka tsanani, gara Imran sau dubu a kanshi, shine karami amma idan ranshi ya ɓaci, Imran da yake babba ma lallaɓashi yake yi, yana da bala'i zuciya sosai.

A wannan yanayin Akila ta dawo ta sameta, saman bedside drawer ta ajiye cup ɗin kakkauran tea din da ta haɗa mata, sannan ta ce "Aunty Aafia ki ta shi ki sha kin ji ko?"

Tamkar da gunki Akila take yi, Aafia ta ki kula ta, ko sannu bata ce da ita ba. Allah sarki Akila baiwar Allah, ta yi tunanin ko dai A'afia bata ji me ta ce da kyau ba ne, sai ta sake maimaita maganar. Tsawa A'afia ta daka mata wadda ya sanyata wucewa ta fice daga ɗakin.

Kallon banza Aafia ta bita da shi, har ta kurewa ganinta, sannan ta ja dogon tsaki tare da runtse ido, a cikin zuciyarta tana jan wa Akil Allah ya isa na dukan da ya yi mata.

After some hours👌

Bayan sun ci Abinci dare sun kammala komai sun kwanta, Aafia tana tsaka da barci ta ji wani bala'i yunwa ya addabawa rayuwarta, cikinta sai kugi yake yi mata, har wani irin murɗa mata yake yi, ba shiri ta tashi zaune a tsakiyar gadon, wutar ɗakin a kashe ko ina duhu, hakan yasa ta laluɓi wayarta dake saman bedside drawer, ta kunna hasken. A hankali ta zuro kafafunta kasa tare da sauƙowa gaba ɗaya daga saman gadon, sannan ta nufi palo.

Ko da ta je palo ba kowa, kai tsaye wajen switch ta nufa ta kunna wutar, nan take haske ya gauraye palon baki ɗaya.

Saman table ta nufa, abin mamaki abinci ne a jere kala-kala a saman table ɗin, jolof rice, white rice and beans with steew, ga su indomie ne, gasassun kaji, ga soyayyu a gefe, abinci dai kala-kala, kuma dukka anyi serving nasu a cikin plate, sai ta shin kamshi suke zubawa kamar me,

Saboda tsabar yunwa dake cinta, cikin hanzari ta zauna tare da ɗaukar spoon, cikin natsuwa ta fara cin jolof rice, wani irin ɗanɗano na musamman ta ji a bakinta, lokacin da ta kai abincin, ɗanɗano ne wadda bata taɓa jin mai daɗi irin shi ba, har wani lumshe idanuwanta take yi, abincin ya yi daɗi over.

Cikin natsu take cin abinci, tana tsaka da ci ta kware ta fara tari, kamar daga sama wani kyakkyawar hannu ya ɗauko wani kyakkyawar glass cup mai ɗauke da ruwan sanyi dake wajen, ya miƙa mata, sai faman tari take yi, ganin an miƙo mata ruwa yasa ta karɓa cikin sauri ta kafa a bakinta ta fara sha.

Shi kanshi ruwan wani irin ɗanɗano ne mai zaki ga daɗi, tas ta shanye ba tare da ta sani ba. Bayan ta shanye, sai ta ci-gaba da cin abincinta cikin kwanciyar hankali.

Da zarar bakinta ya ɓaci za'a sanya tissue a goge mata, kwata-kwata bata yi tunanin waye mai mata hakan ba, bata ma san ana yi mata ba.

A ɓangaren su Ammie kuwa, tana tsaka da barci ta ji ana taɓa ta, cikin tsiwa ta ce "Kai Abba Akila ba zaka daina tashin mutun daga barci bako? Wlh kada ka sake yi mini haka, ni bana son jarabar tsiya..." Bata kai ga rufe bakinta ba a ka sake taɓata, hannunta ta kai ido a rufe ta bude hannun wanda yake taɓa tan, a tunaninta Abba ne.

Can kuma aka sake taɓa ta, dogon tsaki ta ja, ta miƙe zaune a tsakiyar gadon tare da fara surfa masifa tsakiyar dare, dan lokacin karfe 2 na dare zai yi.

Abba ne a tsaye a kanta ta gani, amma a nata ganin ne Abba a zahirin gaskiya kuma ba Abba bane, domin Abba baya ɗakin ma kwata-kwata sai Allah kaɗai yasan ina ya tafi.

"Abba Akila wai meyasa baka da imani ne wani lokacin? Yanzu ba zaka barni na kwanta na hutawa rai na ba?..." Bata kaiga rufe bakinta ba, ya ɗauketa da wani mahaukacin mari mai razanar da kwakwalwar duk wanda a ka yi wa shi.

Ji take yi dif komai ya tsaya mata cak, har wani bala'i duhu ta gani ya gilma mata ta cikin idanuwanta.

Ihu ta kurma tare da miƙewa ta damko kwalar rigar Abba da idanuwanta ke nuna mata.

"Har ni zaka mara? To wlh baka isa ba". Ta kai karshen maganar tare da ɗaga hannu zata wanke masa fuska da mari, abin mamaki ko da ta kai mashi marin, sai ta mari iska, bata ji komai ba, sake kai masa wani marin ta yi, shima sai ta ji iska ta mara.

Sau uku tana gwada marin, amma ina ko sau ɗaya bata sami damar taɓa fuskar ba, nan fa ta fara tsorata, jikinta ya fara kerma, cikin sauri ta saki wuyar rigar mutumin tana ja da baya-baya.

Ina bai bari ta yi nisa ba, ya damko wuyarta, nan fa ya fara yar carafke da ita a cikin ɗakin, kamar ba mutum ya riƙe ba, haka ya rinƙa wurgi da ita yana sake caf kota, sannan ga wasu siraran bulalu guda uku, wadda suke zane mata jikinta idan ya ɗaga ta sama, sai ihu take yi, amma babu wanda ya kawo mata agajin.

A ɓangaren ita kuma A'afia, sai cin abincinta take yi. Abin mamaki shine bayan ta koshi ta tashi zata ta fi, kamar daga sama taga wasu mutane su biyu masu kamanni irin na Abba sun bayya a kujerun gefe-gefen ta, ma'ana sun sanyata a tsakiya, tsabar tsorata yasa ta kurma ihu, tana kokarin guduwa, suka yi maza suka danneta suka fara bata abincin nan a baki.

Ji take yi cikinta na mata barazanar fashewa saboda ƙoshi, amma sun ki kyaleta sai da suka ɗura mata abinci na wuce misali, sai ihu take yi ba wanda ya iya kawo mata agaji dan ba mai iya jinta.

Sabo tsabar rashin mutunci irin na dodannin nan sai bayan sun kammala ɗura mata abincin nan son ransu, sannan suka fito mata da ainahin suffar abincin da taci dan ta gani.

Kai kai kai wai iya zubillah, wasu irin manya-manyan tsutsotsi ne sai yawo suke cikin plate ɗin, sauran plate ɗin kuma akwai mai ɗanyen nama, akwai nai hanjin mutun ba'a wanke ba, shi kan shi ruwan da ta sha kakkauran jinine mai kaurin gaske.

Ai daga wannan lokaci Aafia bata sake motsi ba, nan take numfashi ta ya ɗauke ta sume a wajen, tana suma suka ɓace abin su, kamar yadda suka ɓace kuma haka duk wani abu na su ya ɓace.

A ɓangaren Hajiya Umaiya kuwa, yau Abba ne ya mata duka ita kaɗai, sai ihu take yi tana tambayarsa shin me ta yi masa, amma ina bai yi magana ba, domin ba asalin Abba bane, sai Allah kaɗai yasan in da asalin Abba suka kai shi, lilis suka yi wa Ammie kafin su ɓace su barta da azaba. Sai bayan awa biyu da tafiyarsu sannan ta samu azaban ya sake ta, ta samu ta yi barci, amma fa Abba bai dawo ba har barci ya yi awon gaba da ita.


A ɓangaren gidan Abbi kuwa.

Sun yi kaura lafiya, sun koma tsantsararren gidan su mai bala'in kyau da girma, hawa biyu ne, ya tsaru iya tsaruwa, Irfan ya kashe kuɗi wajen zuba musu tsan tsararrun furnitures masu bala'i kyau da tsada, kai kace gidan wani gwamna ne saboda haɗuwa.

Ansha walima da sadakar abinci, su Imran duk sun haɗu a part ɗin Irfan, sai murna ake yi.

Misalin karfe uku Aunty ta ce Ayla ta ɗauki abinci ta kai wa su yaya Irfan part ɗin su, domin yau cikin gidan a cike yake da yan Walima, kuma yaya Irfan ya ce yanzu ya kamata su dai na cin abinci a Palo gaba ɗayan su, su za su rinƙa ci a part nasu saboda yanzu Abbi baya zama da su, kada wata matsala ta sake faruwa, Aunty ta amince da hakan kuma ta ji daɗi.

Ayla ta yi wankanta fes, ta shirya cikin ɗaya daga cikin dogayen rigunanta, ta fito tas kamar ba ita ba, amma babu wani abin da ta fi yawan tunawa kamar Rimsha, ai na za su sake haɗuwa, shikenan sun rabu, idan ta tuna hakan sai ta yi kuka.

Jiki ta gaba ɗaya a mace ta ɗauko katon kular abincin, mai aikinsu kuma ta biyota da kular miya da kuma basket na su kayan latus da su plates and spoons.

Zaune daddyn Jelly yake a palon Irfan yana latse-latse a wayarsa, ya yin da shi kuma Irfan yake cikin toilet a bedroom nasa yana wanka, lokacin da ta shigo kuma, a lokacin Imran ya fito ya zo ya zauna a sofar kusa da daddy.

Gabansu ta zo ta ajiye abincin, ta yi musu sannu tare da gaisuwa, ta miƙe zata

Please Login or Register in order to submit comment