Reading TRIPLETS BOOK 1 and 2 COMPLT BY FATEEMA ZAHRA MUSA PRINCESS TEEMA Chapter 56 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi ta zauna kusa da Ayla tayi shiru tana mamaki, me yasa duk lokacin da ta tambayi Ayla ya akayi ta fita daular mutuwa sai wani abun ya gipta, kuma da alama Ayla bata son sanar da su ta yadda ta fito daga daular mutuwan, dan da farko da suka tambaye ta, tace musu sai sun huta, na biyu kuma tayo yazo, yanzu kuma gashi ta sake tambayar ta daga ita Ayla ɗin har Kausar duk sunyi kamar sun suma, basa jin komai, anya ba wani abu kuwa.

To masu karatu me kuke tunani game da Ayla, Kausar, da kuma Rimsha? Mu haɗu a comments section.

A takaice dai a wannan dare Ayla bata samu damar sanar da su ya akayi ta fita daga daular mutuwa ba, haka zalika ita kuma Rimsha bata dai na tunanin yadda akayi Ayla ta fito daga daular mutuwa ba kuma ya akayi ta kasa faɗa musu ta yadda ta fito.

Kasa barci Rimsha tayi tana tunani, su kuwa Kausar da Ayla tuni sunyi barcin su abun su, sai can tsakiya dare sannan barci ɓarawo ya ɗauki Rimsha tunani cike fal ranta.

A ɓangaren Jelly kuwa, yau gidan babu kowa, Hajiya ta tafi super market yi musu shopping, Nawid yana Katsina gidan kakanni sa, shi kuma Abbo bai dawo ba, ita ka ɗai ce zaune a palon Hajiya, tayi zaman yan bori, ta baje abun ta, kafa ɗaya can ɗaya nan, tayi ɗai-ɗai, ta tasa abubuwa a gaban ta, irin su chocolate, Ice cream, yogurt, soyayyen naman kaza, sweet da sauran su,

Gaba ɗaya ta damalmale wannan ɗan bakin nata da ice cream, har gemun ta, duk sai da ya samu ice cream sai taunan naman kaza take, ga wani cinyar kaza a hannun ta, tana ci tana kaɗa kai tare da lumshe idanun ta irin santi na ɗeban ta. Jikin ta na sanye da wandon jeans pink color da yar riga mai karamin hannu white color, ta sanya turban cap pink mai shegen kyau a kan ta.

Da sallama Abbo ya shigo palon, bata san ma ya shigo ba, dan da alama sai an mata weji, idan ba haka ba zata iya kwacewa, nama yayi daɗi baji ba gani, shi kuwa wani sanyi yaji ya ziyarci zuciyar sa, lokacin da ya ɗaura idon sa a kan ta, kasan cewar yasan Hajiya bata nan, hakan yasa ya kariso cikin palon da sauri

Kusa da ita ya zauna, a kasa kenan, har lokacin Jelly bata san da shigowar saba, hannu yasa ya ɗauki nama ɗaya zai kai bakin sa, cikin sauri ta riƙo hannun sa, ba tare da ta kalle shi ba, tana ta faman kaɗa kai alamar santi idon ta a lumshe tace "Ajiye shi" yar murmushi yayi kafin yace "Baby nine fa" "Kai waye? Nace ka ajiye shi kawai" ta faɗa, har lokacin bata buɗe ido ta kalle shi ba, "Abbon kine fa" sai lokacin ta buɗe ta kalle shi, sakin hannun nasa tayi tana faɗin "Cemin zakayi old man" zaro ido yayi yace "Daga ina yau kuma kika jiyo old man?"

Roban wani Ice cream ɗin ta ɗauko ta buɗe ta fara dumbutsan ice cream ɗin da hannu tana kaiwa bakin ta, har gemun ta duka yana shafa, cike da santi tana kaɗa kai tace "A Tv naji, wai idan mutun ya tsufa old man ake ce masa, dan haka daga yau sunan ka kenan" murmushi yayi ya sanya hannun sa yana shafo wuyar ta, yana faɗin "Idan dai kece zaki cemin old man ɗin ina so ai" a sukwane ta miƙe tsaye tana faɗin "Kwarto jama'a Kwarto" zabura shima yayi ya miƙe tsaye yana faɗin "Ina kwarton yake?!!" Da hannu ta nuna shi tana faɗin "Ga ka nan, wayyo Kwarto" tsawa ya daka mata ganin tana kokarin tara masa jama'a "Ke waye yace miki ni Kwarto ne? Tukun nan ma aina kika ji sunan Kwarto?" Turo baki tayi kafin tace "A Tv naji mana, nagani wata mata da wani mutun yazo zai taɓa ta shine tayi ihu tace kwarto ne, mai neman mata, shine jama'a suka kama shi suka masa duka, kai ma yanzu kazo zaka taɓa ni dan haka kai kwarto ne, wayyo jama'a kwarto nima kuzo ku taimake ni ku kama shi ku masa ɗan iskan duka!!" Da karfi tayi ihu, ganin da gaske take, kuma yasan halin ta, idan duniyar nan duka zai bata, bazata taɓa yin shiru ba sai lokacin da taga dama, dan haka sai ya kwasa a guje yayi cikin bedroom na shi ya banko kofa, yana mai dana sanin barin ta da suke tana kallo, yarinya sai kaifin ƙwaƙwalwan bala'i, kome ta gani a Tv ta riƙe a kwakwalwan ta, amma kuma idan aikin arziki ake koya mata bata ɗaukan komai.

Duk da ya gudu Jelly bata dai'na ihun kwarto kwarto ba, har su maman Afnan suka shigo ihu kwarto take, sai tambayar ta ina kwarton yake suke, amma Jelly taki kula su, dan Hajiya tace kada tayiwa kowa na gidan magana, shiyasa bata kula suba, ihun ta kawai take tana bubbuga kafa a kasa tana yarfe hannu.

Da dai sukaga Jelly fa kamar ta haukace sai suka kama kan su, dan daman suna zargin Jelly da taɓin hankali, to yau dai sun tabbatar, sai tsaki maman Afnan take jelly ta ɓata mata rai, yarinya ita kaɗai a ɗaki ta kama ihun kwarto kamar ba lafiya ba a cewar su.

Ita kuwa Jelly sai da tayi ihun kwarton ta mai isar ta sannan ta koma ta zauna ta ci-gaba da ɗure ɗuren abubuwan da take, idan ka ganta sai ka rantse da Allah ba itace tayi wannan ihu yanzu ba.

30mins da faruwar Abun Hajiya Turai ta dawo cikin gidan daga shopping, har lokacin Jelly na wajen da take zaune tana baje abun ta, shi kuma Abbo yana bedroom na sa kwance saman gado yana tunanin yadda zai yi, dan son Jelly na neman yi masa illa, ta ɗayan gefen zuciyar sa kuma, yana dana sanin fara yunkurin taɓa Jelly da yayi, dan yasan halin ta sai ta faɗa wa hajiya.

Haka kuwa akayi, Hajiya na shigowa ta miƙe ta nufeta da gudu, tana faɗin "Ummi kwarto ya taɓa Ni" jin haka yasa Abbo miƙewa a razane, ya diro kasa daga saman gadon nasa, yazo bakin kofar bedroom ɗin ya laɓe, ya kasa kunne yana jiran yaji me Hajiya zata ce.

"Waye kuma kwarto baby?" Hajiya ta tambaya tana ajiye niƙi niƙin kayan dake hannun ta, "Abbo mana, shine yazo yana taɓa min wuya" zaro ido Hajiya tayi, cikin sauri tace "Wani Abbo kuma?" "Abbon Nawid mana" Jelly ta faɗa tana turo baki "Abbon ya dawo ne?" Cewar Hajiya, eh Jelly ta bata amsa, miƙewa Hajiya tayi ta nufi bedroom ɗin Abbo tana faɗin "Ina zuwa ki jirani"

Nima na tattara kayana nace ina zuwa bari naje na gaida Josephine a New York sai na dawo, bye sai mun haɗu gobe.

Karku manta idan Allah ya kai mu ranar Jumma'a da rai da lafiya, zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci, dan in ɗan huta in samu kwakwalwata tayi fresh, in ji daɗin zubo muku zafafan page's masu tashin kai, ina godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci 🥰

Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu .
[11/11, 8:52 PM] +234 906 579 6460: 💞💞TRIPLET'S💞💞





💔💔Episode 9-10💔💔



"Waye kuma kwarto baby?" Hajiya ta tambaya tana ajiye niƙi niƙin kayan dake hannun ta, "Abbo mana, shine yazo yana taɓa min wuya" zaro ido Hajiya tayi, cikin sauri tace "Wani Abbo kuma?" "Abbon Nawid mana" Jelly ta faɗa tana turo baki "Abbon ya dawo ne?" Cewar Hajiya, eh Jelly ta bata amsa, miƙewa Hajiya tayi ta nufi bedroom ɗin Abbo tana faɗin "Ina zuwa ki jirani"

Abbo na jin Hajiya ta nufo bedroom na sa, sai yayi sauri ya haye saman gadon sa, ya kwanta tare da lumshe ido kamar mai yin barci, har da wani yin mumfashi irin na mai barci za

Da sallama ɗauke a bakinta Hajiya ta shigo cikin bedroom ɗin, shiru Abbo yayi bai amsa mata ba, kamar mai barci, saman gadon ta haye ta zauna tana faɗin "Abbon Nawid har kayi barci ne?" Shiru ya mata bai yi magana ba, ganin haka yasa tayi tunanin ko barci yake, dan haka sai ta sauƙa ƙasa, ta fito daga cikin bedroom ɗin.

Tana dawowa palo ta tarar da Jelly ta mata aika-aika, ta zazzage mata duk wayan nan niki-nikin kayan da ta shigo da su a jaka, ta haɗe su waje guda, sai faman bubbuɗe kwalayen take, tana fitar da duk wasu abubuwa dake ciki.

"Baby me yasa baki ji ne?" Hajiya ta faɗa a raunane, dan jikin ta duk a mace, ta gaji sosai, kasan cewar tana da kiba da tayi tafiya kaɗan take gajiya.

Saman sofa tazo ta zauna tana faɗin "Tattara komai da kika fitar ki mai da shi" turo baki Jelly tayi tana faɗin "Ni Ummi ban iya ba" kwanciya Hajiya tayi tana faɗin "Wash Allah na gaji" ci-gaba da watsa kayan Jelly tayi abun ta, tana neman abubuwan ci kawai taci, shiru Hajiya tayi bata sake tanka mata ba, dan a gajiye take, ba zata iya rigimar jelly yanzu ba.

Tsab Jelly ta fitar da komai daga cikin kwalin sa, na ledoji ma ba'a bar su a baya ba, sai da ta yaje duk ledojin ta fito da abubuwan dake ciki, wayan da ake ci duk ta tara a gaban ta, irin su chocolate, sweet, popcorn, chips da sauran kayan kwaɗayi da maƙulashe da Hajiya ta sayo mata.

Yage ledar popcorn tayi, ta fara dumbuza tana kai wa bakin ta, Hajiya kuwa tana kwance idon ta a lumshe, saboda gajiya, bata san aikin da Jelly ke yi ba. Bayan ta gama da popcorn ta ɗauko wani leda mai ɗauke da chin-chin a cikin sa, yage shi shi ma tayi, ta fara cin chin-chin ɗin.

Kaɗan taci wannan chin-chin ɗin ta ajiye sauran tana faɗin "Ba daɗi kamar an wanke kan wancan matar, maman Afnan take kowa, kan ta a gwaguye ba gashi, sai masifa kamar sheɗaniya" Hajiya na jin ta, amma ba ta tanka ta ba.

Haka Jelly ta rinƙa cin abin da zata iya ci, wanda ta ji ba daɗi kuma haka zata bar shi, a watse a wajen, ta yage ledar.

Suna cikin wannan hali Nawid ya shigo bakin sa ɗauke da sallama, waro ido Hajiya tayi tana kallon sa, hannun sa riƙe da yar karamar trolley ɗin sa mai kyau, ya dawo daga Katsina.

Saman kujerar kusa da Ummi ya.zo ya zauna yana ta faman washe baki, murmushi baki har kunne, Jelly kam kamar bata san da shigowar sa ba.

"Nawid lafiya kake wannan murmushi haka? Ko dai kakan ka ya maka wani kyautan ne?" Ummi ta tambaya tana tsare shi da ido, baki har kunne saboda murmushi yace "Ummi na samu mata ne wlh, shiyasa nake cikin farin ciki, shiyasa ma ki kaga na dawo da wuri dan na sanar dake, farinciki ya hana ni na cika satin da nace zan yi, dole na zo na sanar dake" zaro ido Ummi tayi kafin tace "Mata kuma? Ai na ka sami matar?" Kara faɗaɗa murmushin sa yayi tare da ɗan duƙar da kai ƙasa yace "Ummi a Katsina take, tana aiki a restaurant ɗin gwaggo Auta"

kara zaro ido Ummi ta yi kafin ta miƙe zaune tace "Lallai Nawid, ita kuma baby fa?" Zaro ido shi ma Nawid yayi yace "Ummi baby kuma?" "Kwarai da gaske baby fa" Ummi ta ba shi amsa with her full confidence

Tashin sense lokaci guda yaji duniya ta tsaya masa cak, har wani yanan duhu yake gani na gilmawa a idon sa, nan take yaji duniya na masa wani irin juyi, kan sa na sara masa, da karfi karfi, kamar zai rabe biyu, zancen zuci ya fara yi, "ko na rasa mata a duniya ba zan auri baby ba, yarinya bata da hankali, bata da kan gado ko kaɗan, kamar ni dr Nawid a ce wannan mahaucikayar ce matata, kai ina hakan ba zai yi wu ba, yarinyar da bata san kan ta ba, ita da kan ta, sannan ace ni in aure ta, muyi zaman mata da miji da mahaukaciya" wani irin zufar ne ya fara gan garo masa daga gefe da gefen kunnen sa, kasa ya duƙar da kan sa yana tunanin abun yi

"Nawid menene naga ka canza lokacin guda haka?" Cewar Ummi,
furzar da iska mai zafi yayi daga bakin sa, kafin yace "Ummi ni a kanwa na ɗauki baby, ko kaɗan babu son ta a rai na, dan Allah Ummi kiyi hakuri, kada ki sanya na auri ta, wlh idan na aure ta, na san zan cutar da ita ne, dan bana son ta" salati Ummi tasa tana tafa hannu, har ta kai karshen salatin "Nawid yanzu ni kake cewa baka son baby? To tun da baka son baby zaɓi na, ni ma bana son wanda ka kawo kake son aura, har zan ce maka ga zaɓi na kace baka so lallai ka girma"

zamowa ƙasa daga saman sofar Nawid yayi ya zube gwiwowin sa a kasa, cikin raunanniyar murya cike da tashin hankali yace "Ki yi hakuri Ummi, ba wai bana son baby ba ne, ina son baby amma a matsayin kanwa, dan Allah Ummi ki fahince Ni, ki so zaɓi na, ki bari na aure ta, wlh tana da kirki sosai"

Oho Allah ko yaushe Nawid ya zauna da Jehan har yasan tana da kirki, kai jama'a hmmm maza mutanen mu😹.

Ummi za tayi magana Jelly dake zaune tana faman cinye sauran naman ta na ɗazun tace "Yaya Nawid kar ka damu, ni ma bana son ka ai, tun da baka so na, Ni ma haka ne" guntun tsaki Ummi taje kafin tace "Ke baby ta shi ki kwashe kayan cimar ki, ki wuce ɗakin ki" ba musu ta tashi ta tattare kayan ciman ta, da wanda ta fara ci ta ajiye da kuma wanda ma bata samu daman ci ba, duk ta kwashe ta wuce ɗakin ta tana turo baki.

Dawo da kallon ta, kan Nawid Ummi tayi "Nawid idan dai har kana son auran wancan, tofa sai ka fara auran baby, zan sanar da Abbon ka, nan da 3 weeks masu zuwa a ɗaura muku aure a wuce wajen, idan yaso daga baya sai ka auri wan can, amma fa ka sani ba zaka kawo min wadda zata takurawa baby ba tom" kasa kasa yace "To shikenan Ummi Nagode" sannan ya miƙe ya ja trolley sa zuwa bedroom na sa murna ya koma ciki, yana tafiya yana tunanin hanyar da zai bi ya gujewa auren baby, "ko dai na ɗauke ta naje can wani gari na jefar da ita ne?" Ya tambayi kan sa, ɗayan ɓangaren na zuciyar sa ne yace masa "Da kuwa hakan zai fi, dan idan ba haka kayi ba Ummi ba zata fasa aura maka wannan mahaukaciyar kwailar yarinyar ba" tunani kala-kala yake cikin ransa har ya karisa cikin bedroom ɗin nasa.

A ɓangaren Abbo kuwa daga cikin bedroom nasa yana jiyo duk yadda Ummi tayi da Nawid, shi ma tunani yake ta yadda zai ɓullo wa lamarin, ji yake kamar yabi dare ya ɗauki baby ya kai ta gidan shi na Abuja ya ajiye ta a can, sai ya rinƙa biyan bukatar sa da ita, tun da daman a nan bai isa yayi hakan ba, saboda Hajiya, ga shi kuma yana bala'i son ya ga ya keɓe da baby, yana son kasan cewar tare da ita a ɗaki ɗaya. Shi ma tunani cike fal ransa yana tuna yadda zai sa mu mafita.

A ɓangaren Ummi kuwa tunanin bikin Nawid da baby kawai take, dan har ga Allah Ummi tana bala'i kaunar Jelly.
Wayar ta ta ɗauƙo daga cikin jakarta, ta danna kira, sannan ta kara wayar a kunnan ta.

Jim kaɗan a ka ɗa ga kiran "Hello Hajiya Batula ya kike?" Daga ɗayan ɓangaren Hajiya Batula tace "Lafiya lou Hajiya Turai ya su Nawid?" "Nawid yana nan lafiya yanzu ma kiran na shi ne ai" cikin sauri Hajiya Batula tace "Kiran nashi ne kuma? Kaddai ki ce min auren sa ne ya tashi" kyakkyawan murmushi ne ya bayyana a kan fuskar Hajiya Turai, tana murmushi tana faɗin "Eh wlh auren sa ne ya tashi, ina Abla?" "Abla tana school, lallai abu namu maganin a kwaɓe mu, ki ce na kamo hanya kawai" kara faɗa ɗa murmushi ta Ummi tayi kafin tace "Sosai ma kuwa kamo hanya kam mai kyau ma, da wuri kai" "Yaushe ne bikin?" Shiru kaɗan Ummi tayi kafin tace "Eh nan da sati uku haka" "wow lallai dole nan da sati biyu nayiwa Kaduna diran mikiya"

ɗan tsagai ta murmushi ta Ummi ta yi sannan tace "Gaskiya kam abun da yasa ma kenan na kira ki, saboda matar tasa, ki taimaka tun ana sauran sati biyu biki kizo ki fara gyara min ita" shiru Hajiya Batula ta ɗan yi kafin tace "Gaskiya tun ana saura sati biyu kam ba zai yi wu ba, sai dai saura sati ɗayan dai, saboda saura sati biyu biki ina da manyan baki, kuma kinga Abla ma zata dawo hutu daga school, zan yi kokari dai ana sauran sati ɗaya biki nazo, ranan tun safe zan biyo jirgi, kuma ai tsakanin Maiduguri da Kaduna tafiyar ba yawa, jirgin safe zan biyo, ina dirowa mu fara aiki" ɗan canza fuska Ummi tayi alamar bata ji daɗin maganar Hajiya Batulan ba, amma ba yadda ta iya dole ta hakura ta bi yadda Hajiya Batulan tace, dan Hajiya Batula ta kware wajen gyara mata, kuma babban aminiyar tace tun na yaran ta. Ba dan taso ba, ta amsa wa Hajiya Batula da to Allah ya kai mu, sannan suka yi sallama, ta mai da wayar ta ajiye, ta koma ta kwanta, ta ci-gaba da tunanin tana kawata yadda bikin zai kasance a ran ta.

To masu karatu mu leƙo Rimsha mu gani me take aikatawa.

Tun karfe 6 na safe su ka farka su ka shirya, a tare suka je suka yi wa matar sarki sallama, sannan suka je wajen sarki a ɗakin sa shi ma, suka yi masa sallama, sarki da matar sa basu ji daɗin tafiyar da su Rimsha za su yi ba, dan har ga Allah tun da suka gan su, suka ji kaunar yaran har cikin ran su ya ka ma su, to amma ba yadda za su yi, tun da ba ƴaƴan su bane, dole su kyale su su koma wajen iyayen su, dubu biyu sarki ya basu, sai godiya suke zuba masa, baki har kunne saboda murmushi jin daɗin sun samu kuɗin mota, Rimsha ce ta kulle kuɗin a igiyar rigar ta kusa da in da ta ƙulle goran da duna ya bata

cike da murna suka fito tsakar gida, matar sarki ma ba'a barta a baya ba, ta basu kyautan 500, sosai suka ji daɗi sai murna suke, suka yi sallama, su Rimsha suka nufi waje matar sarki da sarki suka koma cikin ɗakunan su

Su Rimsh sun fito zasu tafi kenan suka ci karo da olohunwa yana ƙoƙarin shigowa cikin gidan, hannun sa riƙe da buta, alamar bayan gari yaje yayi.

Murya kamar na yan shaye-shaye yace "Wow beautiful girl" yayi maganar yana kallon Rimsha, shiru su dukan su suka yi, ba su yi masa magana ba, hannu olohunwa ya kai zai shafi fuskar Rimsha, cak hannun sa ta maƙale ya sanƙare kamar itace, ihu ya fara yi yana kokarin jaye hannun sa baya, amma ina ya kasa, su ma ihu suka yi suka bazama cikin gari da gudu, dan sun tsorata da ihun olohunwa

A guje sarki da matar sa suka fito, olohunwa yana tsaye a wajen ya kasa motsawa, ga hannun nasa sai kumbura yake ya sankare waje guda, su kuwa su Rimsha tsorata da ihun da olohunwa yayi ne yasa su bazama cikin gari suna gudu kamar marasa hankali, a tunanin su, wani abun mugunta zai musu.

Sosai suke gudu basu san in da suka nufa ba, sarki kuma sai faman kokarin janye olohunwa a wajen yake, amma abun yaci tira ko motsa olohunwa sun kasa yi, to kun san halin yarabawa da tsoro ire-iren wayan nan abubuwa, ihu matar sarki ta kurma tana neman a kawo mu su ɗauki. Kan kace me gidan sarki ya cika da jama'a maƙil, sai hayaniya ke tashi kamar gidan biki, sai kokarin ture olohunwa suke daga wajen amma sun kasa, kamar bishiyar da a ka dasa shekara da shekaru haka ya zama a wajen, gashi sai ihu yake ya ka sa magana saboda azaban zogi da hannun sa ke masa, hannun ya kumbura sosai har ya fara fitar da wani irin farin ruwa mai warin bala'i, alamar hannun ya ruɓe.

Su kuwa su Rimsha bayin Allah basu san meke faruwa ba, sai zunduma gudu suke wai kar olohunwa ya kama su, dan Ayla ta faɗa musu olohunwa fyaɗe yake yiwa mata shiyasa ma suka tsorata sosai da shi.

Sun yi gudu sosai, har sai da suka dai na ganin alamar wannan kauye gaba ɗaya, sannan suka tsaya wajen wani bishiyar lemon tsami suna mai da numfashi, suna haki.

Almost 10mins suna tsaye, sannan suka zauna, a kasan bishiyar, da yake akoi ganyen damuna sosai a jikin bishiyar, sai suka sa mu inuwa, wajen akoi sanyi sosai gwanin daɗin zama, haka suka baje

Ayla ta duɓi Rimsha tace "Allah ya cece mu, ba dan haka ba olohunwa fyaɗe zai mana, ɗan iska ne sosai, ga shi da bala'i shaye-shaye" da kyar Rimsha ta iya cewa "Gaskiya kam, amma kuma basu da mutunci in dai haka ne" ita dai Kausar ta kasa magana saboda ta fi su shan wahala, dan ta fi su ƙiba shiyasa ta fi su jin jiki.

Sun yi shiru su na zaune, bishiyar na kaɗa musu iska mai sanyin daɗi, har wani lumshe ido suke kamar ma su jin barci

Kaɗan-kaɗan daga can nesa suka fara jiyo hayaniyar mutane, suna nufo in da suke, kasa kunne suka yi suna sauraro su ji, wannan hayaniya ta mecece.

Basu fargaba sai ganin gungun jama'ar kauyen su ka yi sun nufo su, hannayen su riƙe da sanduna wasu kuma suna riƙe da wuƙaƙe, zuba musu ido su Ayla suka yi, sun kasa tashi ma bare su yi yunkurin guduwa, dan su a nasu tunanin ma basu yi laifin komai ba, sun ɗauka wasu can daban yan kauyen suka biyo.

Sun zuba ido suna ganin ikon Allah, har yan kauyen suka iso wajen da suke. Su na zawa ba su yi wata-wata ba suka fara sauƙe musu sandunan hannayen su a jikin su, sosai Ayla da Kausar ke ihu ita kam Rimsha tana zaune shiru, alamar bata san ma meke faruwa ba, ga shi kuma su yan ƙauyen a nasu ganin ido suna duka har da Rimsha, sai dai kuma abun da ba su sani ba sandunan nasu baya taɓa jikin Rimsha

Sosai yan ƙauyen ke dukan Kausar da Ayla, ita kuma Rimsha ga shi dai a zahiri suna sauƙe mata sandan a jikin ta, amma a ɓaɗini ba haka bane, domin ko kaɗan bata ji alamar saukan sanda a jikin ta ba, tana dai ganin jama'ar ƙauyen suna ɗaga sanduna kamar zasu buga mata, sai kuma taga sandar ya ɓace, ga shi sai magana take musu, amma basa jin komai da take faɗa, duka kawai suke kai mu su, a yaren yarabanci suna ce mu su mayu ne, su suka kashe olohunwa

Kausar da Ayla sun daku jikin su duk ya farfashe sai jini yake, bayin Allah, ita ma Rimsha a idon yan ƙauyen jikin ta ya fashe yana jini, amma kuma ba hakan bane.

Sai da yan ƙauyen nan suka ga kamar su Kausar sun mutu basa numfashin, sannan suka kyalesu suka wuce suka bar su a wajen kwance cikin jini.

Suna tafiya wani haske ya fita daga jikin Rimsha ya tashi sama, ya bi bayan yan ƙauyen, wannan hasken na fita Rimsha ta dawo cikin hayyacin ta, ta tsorata sosai lokacin da idon ta ya sauƙa kan su Kausar, cike da tashin hankali ta fara girgiza su, tana kiran sunaye su.

Sosai take kuka ta na kiran su, amma ina ko motsi ba sa yi, kamar sun mutu, juyawa gabas da yamma kudu da arewa Rimsha tayi babu kowa a wajen, kara sautin kukan nata tayi baiwar Allah, sai jan hanci take, hawaye bibbiyu a

Please Login or Register in order to submit comment