Reading DAUDAR GORA BOOK 2 BY bilyn Abdull Chapter 32 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Nace ko zaka gwada kashenin muga!!!".


Tai maganar cikin tsananin hargowa tana wani hahhankada kirji a gabansa. Wani irin tafarfasa yaji zuciyarsa nayi, dama a wuya yake, a fusace ya kaima wuyanta wani irin shegen shaka na tashin hankali. Cikin kankanin lokaci manyan idanunta suka sake yowa waje ruku-ruku, ga kakarin mutuwa da ta fara da mutsu-mutsun ganin ta fisge hannunsa da ga kan wuyanta. Sai dai kuma hakan ya gagara, dan karfinsu ba daya ba. Tafiya ya dingayi da ita cikin rufewar ido har jikin bango, ya kara matse wuyan da karfi tare da wajigata ya buga kanta jikin bango. Wata irin wahalalliyar kara ta fasa da ta jawo hankalin Jasrah dake daki kwance ta farka tana nemansa, dan su suna'a falon baki ne kasancewar cikin shigar badda kama Ameera Haifah tazo a nufin bako tasa amintaccensa imata iso saboda baya daga mata waya yanzun. Sai da yazo yaga itace. Gaba daya idon Miran Arshaan da alama ya rufe, dan tuni ya sake jijigata ya buga a bango, jini ko ya samu hanya ya balle.


lya karfi da budewar murya Jasrah ta daddage ta kwalla wata irin kara na firgita, dan ganin jini ya wanke fuskar Ameera Haifah ga Mijinta shake da wuyarta sai ta dauka ta mutu.Wani irin wancakalar da Haifah Miran Arshaan yayi yana duban Jasrah data yanke jiki ta fadi. Har rige-rigen shigowa hadiman masu tsaron sashin keyi, ganinfa abinda ke faruwa tuni wani ya firgita ya kyalla a guje ya sanarma jami' an tsaron gidan dan wannan faninsu ne...✍️[6/1, 1:18 PM] +234 703 445 5862: DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 62


...…….Tofa dan-dan-dan, da alama dama irin wannan damar Iffah ke jiran samu, dan cikin
kankanin lokaci duk da darene masarautar ta dauki dumi, yayinda aka kwashi Ameera Haifah da Jasrah zuwa asibiti, Miran Arshaan kuwa da jikinsa ke tsumar toro gaba daya ya gama
gigicewa, dan sai zuwa yanzu ya dawo a hayyacinsa. Tuni kuwa ya tsure da ganin abinda ya aikata, sai kawai ya bige da borin kunya.
Sudai jami'an babu wanda yace da shi komai,sun tattara komai akan sai zuwa da safe za'a kai
maganar ga Shahan-shan. Abu dai mafi daure kai shine miye tsakaninsa da Ameera Haifah din
har haka a irin wannan tsohon daren, dan a kala fa karfe biyu na dare kenan.










大大










A lokacin da duk ake waccan dambarwar anan ta-kurya ce ke ganawa da manomin ganyayyakin shayin Shahan-shan. A cikin badda kamarta take, dan haka shi bai san wacece ba.Hasalima magana da Jazaa sukeyinta ita dai tana hakimce komai batace ba. Da farko yaso ya, amma ganin wata lukutiyar jakkal da zinare ga barazanar halaka zuri'arsa kunne tuni ya mika wuya akan an gama. Malikat Bushirat tai murmushin basawa ta dauke kanta.Kwalayen ganyen shayin da uwa ta kawo kan ya fara kaiwa sashen Shahan-shan din kafin wanda zasu noma ya tsiro nan ma Jazaa duk ta ajiye masa su har uku..








Hummm🥱🚴










**










Zaune take bayan idar da sallar asuba, yanda ta kurama waje daya ido zai baka tabbacin tunani take. Sai lokaci zuwa lokaci da takan saki murmushi, harda cusa kanta cikin kafafunta kamar mai jin kunyar wani da ke gabanta. Ta dan jima a hakan kafin ta mike kamar wadda aka tsikara idonta kan agogon dakin. Tasan yanzu kam yana Gym ne tunda har ya kai yanzu bai shigo ba. Itama tsaf ta shirya cikin kayan motsa jiki ta, sun mata matukar kyau da fidda ainahin surarta komai dam. Dan wani bana ta saka a kanta siriri kalar kayan sannan ta daura talda daura after dress saman sport wears din. Shiru tai tana bin Gym din data shigo da kallo, babu kowa komai ma a kashe yake, da alama banan yazo ba. Fuska ta dan bata da tura baki gaba, har zata koma sai kuma ta tuno randa ta samesa a can sama yana wasan takobi shi da Miran Arshaan. "Yes!" ta fada tana wani kashe ido daya da yin juyi sannan ta nufi can cikin takunta na nutsuwa


Shelanta sunanta da na'urar kofar tayi kamar yanda ta saba duk wanda zai gitta ta cikinta ya sashi dakatawa da jujjuya takobin ya juyo a hankali. Tuni hadiman wajen sun jujjuya bayansu sukam. Yanda take takowa garesa kamar wata tarwada yasa shi gagara cigaba da abinda yake yi.


"Good morning


Ta fada cikin rashin tsoron nan nata na bayyane tana daura yatsanta saman tsintsiyar hannunsa ta zano a hankali ta dire kan kyakykyawar takobin da ya rike rikon kasaita da kwarewa. Da kallo kawai ya bita batare da ya amsata ba. Itama sai bata nuna tasan yana kallonta ba ta zare takobin a cikin hannun nasa fuskarta da murmushi. kin sakar mata yay, sai ma cike da salo yay wani irin juyata bata ankara ba ta dawo saman jikinsa takobin a wuyanta sai dai bai daura a kan fatar jikinta ba. Iffah jitai zatayi fitsari na neman kufce mata tsabar yanda ta tsorata har yana jin yanda jikinta ke tsuma. Dan dukowa yay kansa a kafadarta bakinsa saitin Kunnenta ya furta, "k takamarki tsokala ko?".


Idanunta da ke kawo kwalla ta shiga kikkifatawa da girgiza masa kai a hankali. Cikin rawar harshe ta ce, "Eshaan Akhi na tuba".


"Daga baya kenan".


Ya fada yana kara matsar da takobin jikinta gaf.Sake tsurewa tai. Shiko sai faman danne dariya yake.


"Ki fanshi kanki".


Da sauri ta ce, "Da mi?".


Dan lumshe idanunsa yay ya bude yana mai busa mata numfashinsa a wuyan. A dan salon tabe baki ya ce, "Komai ma".


"Shike nan, shike nan naji na amince, amma dan ALLAH ka janye sau daya fa ake mutuwa, rai daya ne". Yanzu kam kasa daurewa yay sai da murmushi ya subuce masa. Ya janye tare da dauke hanunsa dake saman cikinta ya juyota suna fuskantar juna. Hawaye fa da gaske sun cika mata idanu. Da kyar ya iya gimtse dariyarsa. Idanunsa ya maida ga hadiman wajen da suka juya bayansu tun dazun, dasss daga yatsunsa sau biyu, cikin abinda bai sakkani ba sun bar wajen a ka barsu su biyu. Da baya-baya yaja zuwa table din gefensu kadan,wata takobin ya dakko a cikin kyakykyawan kufanta ya dawo gabanta, hanunta ya riko ya daura mata takobin sannan ya zare abayar ta ya ajiye tare da mata alamar bismillah. Kamar ba ita ta gama hadiyar hawayeba yanzu ta wani dubi takobin shima ta dubesa ta dan murguda baki. Kansa ya maida gefe yana murmushi, tare da ajiye tsinin tasa takobin bisa kasa ya fara zagayata. Yana a tsaye daga bayanta ya juya takobin cikin salon tsokanarta kawai a bazata yaji tama kanta garkuwa. Idanu ya dan waro waje, da bin takobin da kallo kawai ta zuke ta maida masa harin. Cikin zafin nama ya kare kansa shima mamakinta na nan kasheshi.


"Dama kin iya wasan takobi?".


Ya tambaya da mamaki idanunsa cikin nata Murmushi ta sakar masa da kara zukewa ta kai masa suka ta kasa. Nanma baya yay cikin zafin nama yay wata irin bahaguwar zukewa. Dariya tayi da dire takobinta ta fara zagayashi kamar yanda ya mata dazun, cikin salon dage gira da kashe masa ido daya ta ce, "Zaka cigaba da tsayawa tambayar a ina na iya ne na kaika kasa?". Tsaiwarsa ya gyara da kyau yana murmushi da kamo lips dinsa na kasa ya tura ( paki suka cigaba da zagaye juna. Sai kowa ya yinkuro cikin ragabza akai tsaiwar zakaru. Cikin kwarewa da nuna bajinta ga kowa suka cigaba da wasan mamaki na nan kashe Tajwar Eshaan a zuciya. Duk da ya fita kwarewa yanda ta iya din itama na bashi mamaki matuka.Sai dai ya bita da salon saffa-saffa yanda bazai cutar da ita ba dan karfinsu ba daya bane






Tamkar wanda aka jeho kawai sukaji sallamarsa a kusan tsakkiyar wajen, dan kamar sai da ya matso gab da su ne ma yake sallamar.Da ga shi har Iffahn juyowa sukai, musamman Iffah da kamar wadda ta ma firgita, dan jikinta har rawa yake wajen neman abinda zata yafama jikinta, tsabar yanda ta rikice tama ki ganin after dress din nata. Bata san yanda akai ba, tayaya ma kawai jinta tai a jikinsa, jin kamshinsa ya sata kankamesa da sauri tana kokarin boye kanta.


"Miya kawoka nan babu neman izini? Kabar wajen nan Aam!!" ya fada a matukar tsawace shima yana kankameta da juyawa da ita suka bama Miran Arshaan da yay mutuwar tsaye baya.


"I say out!!!".


Ya sake fada da wata irin mummunar tsawa mai karaji da har jikinsa na girgizawa, ga idanunsa sun yi wani irin kadawar masifa kamar wanda ake kadama gangi. Miran Arshaan har tuntube yake yi tsabar firgicewa da tsawar Tajwar Eshaan din. Bai taba sanin yaron nan dan bala'i bane irin yau. Next surar yarinyar nan ta matukar kidimashi, ashe abinda Jasim kenan ya gani kullum yake cikin sambatu da santin yarinyar, shi manemin matane tun yana da kananun shekaru, yayi mu'amula da mata kabila daban-daban a duniya da bai san adadi ba. A sanda yake ji da rashin ji har order din mata suke ta online, yaga matan ma da sukafi Iffah kira amma wannan jikin dabanne. Ji yake yama kasa cigaba da tafiyar yanda jikinsa ke bari, sai kawai ya samu bango ya manne yana sauke numfashi gudu-gudu. (Humm)


Yanda Iffah taji zuciyarsa na bugawa da sauri- sauri kamar zata ballo kirjinsa ta fito ga tsawar da yayma uncle din nasa ya matukar sake rudar da ita fiye da tsoron ganinta a yanda take da tai gudu. Kanta ta shiga jujjuya masa da kankame hanunsa, sai kuma ta dan dago ta kalli fuskarsa. Ta wani irin kadawar masifa jazur hakama idanunsa gaba daya sun juye mata cikin canjawar kammani. Dole ta maida idanunta kasa jikinta na rawar toro da yanayin nasa. Jitai kawai ya wani irin fisgar hanunta zuwa hanyar kofar da ta shigo, bai tsaya da ita ko ina na bedroom. Yarfar da hannun yay yayi shigewarsa bathroom. Da kallo ta bisa hankalinta a tashe itama, dan ita kadai tasan kalar wutar masifar data gani a cikin idanunsan. Raya mata zuciyarta ta dingayi kawai tabar dakin nan karma ya fito ya sameta...




Koda ya fito bayan tsahon lokaci da ya dauka a bayin bai nema Iffah ba dan yana bukatar kadaici saboda ya shiga bacin rai, shi mai kishi ne, tabbas yanada matukar kishin da yake ji akan yarinyar nan zai iya badda mutum. Wata irin tsanar Miran Jasim da Miran Arshaan yake ji irin wadda bai taba ji a kansu ba a dukkan abubuwan da suka aikata masa a baya, ga wani irin sara masa da kansa yake yi na ciwo. Jikin window ya karasa hannunsa goye a bayansa batare da ya cire ko bathrobe din jikinsa ba yana kallon sararin samaniya da ke hada was irin manyan bakaken giza-gizai na hadari, du da safiyar tayi sosai garin yaki washewa sai ma rinewa yake sake yi kamar za'ai wata sabuwar magriba. Kiran waya ne ya shigo, ya share kamar bai jiba, aka sake kira nan ma kamar zai share sai kuma ya nufi wayar a fusace ya daga. Sai dai yay shiru baice komai ba. Da ga can Sayeed Fayzul-haq ya gaishesa cike da girmamawa.Haushin kowa yake ji, duk da bashi yay lefin ba ya samu rabonsa. Dan maimakon amsa gaisuwa a dake ya ce, "Ya akai". Dan rikicewa Sayeed Fayzul-haq yayi, amma sai cikin dauriya da sake kankan da kai ya shiga masa bayanin abinda ke faruwa tsakanin Miran Arshaan da Ameera Haifah tun a daren jiya. A zafafe ya ce, "Kaima jami'ai magana su kamashi a hadashi da dayan sakaran, a saka na'urar daukar magana cikin akin kurkukun kuma.Itama Haifah din Doctors su sallameta idan babu wata matsalar data shafi lafiayarta jami'an tsaro su rufeta",. Daga haka ya ajiye kan wayar yana huci. Duk yanda yake kokarin rike kansa da bin komai a sannu ya fahimci ba haka makiyansa suke bukata. Fushinsa suke son gani, ainahinsa suke bukatar ya nuna musu. Ya barsu da yarinyar nan ne kawai domin shi din shugaba ne, shugaba kuma da hadiyewa aka sansa, amma tunda so suke shi ya fito musu a Eshaan In Haysam Abdul-majeed Aliy Qutb din sa to yanzu ne wasan zai fara..












😆🥱TOFA ran yan maza ya baci, al'ummar kasar ruman kuyi takanku mai RUMAN dinne da kanshi 🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴🚴
[6/1, 1:18 PM] +234 703 445 5862: DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 64


Tunda aka shigo da Arshaan dakin kurkukun da ke makwaftaka da juna da na Miran Jasim sukema juna kallon kallo, duk da dai shi Jasim bai ko motsa da ga zaman takurewa waje dayan da yay ba, su dukansu dakin babu yawaitar haske, sai dai ta dan hasken da ke lekowa sukan iya gain junansu. Sun kwashe awa guda a haka kafin Jasim ya mike cikin dan tangadi, dan baya cin abincin da ake bashi ga raunikan da ya jima kansa duk an masa tretiment dinsu. Jikin karfen da ya raba dakin nasu ya tsaya, sai kuma ya kece da wata irin dariya kamar wanda hauka ya kama. Cikin bacin rai da kunar zuciya Arshaan ke kallonsa, sai dai baice komai ba har yayi ya gama yay shiru dan kansa. "Oh!! Kai dama a tunaninka Jasim ne kawai ta karewa Arshaan? Lallai kai jaki ne bazan gaji da maimaita fada ba, why da ace uwarka na raye zuwa yanzu nayi imanin bakin cikin haihuwar wawa da tai irinka ne zai zama ajalinta. Kai anya ma kuwa bada cikinka ta shigo gidan nan namu b


"Jasimmmmm!!!!!!!".


Arshaan ya fada cikin karaji da wani irin girgiza karfen tsakanin nasu kamar zai babbagesa,amma da yake a gine yake cikin kasa ko gezau shegen baiyi ba. Ka dan Jasim yay baya yana dage hannaye sama kamar wanda yay surrunder, sai kuma ya sake kwashewa da dariya kamar zai fadi ya sake dafe karfen yana fadin, "Shegen kaya ashe kasan abinda kake. To to naji uwarka anan ta haifeka, sai dai wlhy bazan daina tantama ba nikan kodan kasancewarka kasurgumin annamimi, butulu,sannan rago mai labewa a bayan mace domin kubutar da kai. Shin nawa ta siyeka ne har haka?"


"Yanda aka sayo uwarka a gidan karuwai. Why da ga yau idan ka sake kuskuren zagin uwata, sai na maka lahanin da sai ruhin uwarka ya dawo duniya yana mai cikin garari Jasim.Wawa jaki kawai maybe ma uwar takace ta shigo mana da cikinka da ga wajen dan tsautsayi kawai. Ko an fada maka bamusan tarihin tushenta bane a gidan.


"Amma kasan zan iva kasheka na binne gawarka a cikin kurkukun nan ko? Idan ka manta bari na tuna maka wanene Jasim in Abdul- majeed Aliy Qutb, domin ni a gareka sai dai kallo sai kuma hange daga nesa koda bakin cikina zai ajalinka. Ko an fada maka ban san kulle-kullen da ka jima kanayi a kaina bane?, Kana goyamun baya domin in mun kauda shi nima ka kaudani, sai dai kuma kayi kuskure, domin kafin kaga biri shi birin ya ganka dan hau. Da ido daya Jasim ke barci,sannan a tafin hannuna kake, zakuma ka tabbatar da hakan nan gaba jadan". Ya kare maganar yana wata yar iskar dariya cikin rangaji harya koma wajen zamansa ya sake zama rigija yana dariyar har lokacin.


Shiru Miran Arshaan baice komai ba, sai dai yana tsaye kamar gunkin da aka ajiye dan tarihi idanunsa nabin Jasim din da kallo, da alama dai tattaro abin fada yake, ko kuma maganar Jasim din ce dai ke masa kaikawo dan bai taba tunanin yasan da wannan burin tattare da shi ba.












** BAYAN KWANAKI BIYAR **










Kwanaki biyar kenan da mika su Arshaan suma a makargama, Jasim kuwa sati guda. Sai dai kuma Tajwar Eshaan bai sake cewa komai ba game da su, hasalima a yau da ake saran ganin watan azumin ramadana ya dauka hutun fitowa fada har sai bayan salla. Tare da daura Sayeed Fayzul-haq akan komai dan zaije Umrah shi da iyalinsa kamar yanda ya sanar.Tabbas a wannan karon babu wasa a cikin al'amarin Tajwar Eshaan din, dan haka kowa ya shiga taitayinsa har su manyan masarautar. Duk da akwai abubuwan fada a bakinsu har game da karasa zaman shari'ar da aka fara amma sun gagara cewa komai har ya gama jawabin fara azumi da gamashi lafiya yay musu bankwana.


A lokacin da Tajwar Eshaan ke can yana bankwana da jama'ar fada anan Iffah ce cikin babban bitalmanin kasar ruman bisa jagorancin babban dan Sayeed Khairul-Bashar mai suna Abdul-Shakhur in Khairul-Bashar tana bada umarnin ware kayan masarufi nau'i-nau'i domin dorasa a jagorancin rabawa talakawan kasa. Sai matasan masarautar da ta saka shi Abdul- Shakhur din ya samo har su hamsin da zasu jagoranci sauran jihohi da wanda za'a kai wasu kasashen da yaki ya samarwa yan gudun hijira da ma iftila' in rayuwa na talauci.


Wannan al'amari ya matukar jjiga kunnen duk wanda ya samu labari a cikin masarautar, dan abinda bai taba faruwa bane, duk da duk azumi akan fitar da kayan masarufi a dan kai jihohi suma kuma ana da kasune ga Tajwar na jihohi bawai a wakilta wasu suyi aikin ba a cikin masarautar. Sannan a duk shekara tun ba hawan Tajwar Eshaan din Malikat Bushirat ce ke da wanna karfin ikon matsayinta na mahaifiya ga Shahan-shan. Sai kuma a yau labarin ya canja akaga Zawjata-almilk kan komai cikin kuma sauyi.





Kamar yanda labarin ya isa kunnen kowa kuwa yaje ga Malikat Bushirat din da take zaman tsara yanda zatai fitar da wanna abinci bisa tsarawar uwa kamar kowace shekara. Ba kuma a bada abincin ma sai bakwai da azumi, sai kuma gashi yau ana gobe saka ran daukar azumi za'a fara rabon. Kayan da aka fitar kuma sun ninka wanda ita take sakawa a fitar sau dari. Dan duk wani abinci dake shekara ta uku a cikin bital mali Iffah tasa an fito da shi ana da kasa a hannun wakilan. Su kuma kasancewar matasa masu zafin nama da son dama su nuna tasu baiwar amma basu da wanna damar sun bata goyon baya dari bisa dari, duk da kasancewarta karama a shekaru kuma sun bata girmanta matsayin Zawjata-almilk, to kwarjini da cikar kamalar ta da barazana ma bazai bari ko kaso kawo mata wargi ka iya aikata hakan ba.


Tsaf numfashin Malikat Bushirat ya dauke na wucin gadi lokacin da Jazaa tazo mata da mummunan labari. Ta wani zuba idanunta kamar mai son gano gaskiyar maganar a jikinta. Kafin ta yunkura ta mike cikin wani irin zafin rai ta shiga bedroom din ta. Cikin kankanin lokaci ta canja shiri, tana kokarin fitowa Jasrah ta shigo dakin da sallama, dan tunda aka sallamota da ga asibiti nan sashen ta dawo take zaune, a kallo daya datai mata ta fahimci bacin rai dake tattare da ita. Itama yanzu take jin labarin komai a bakin hadiman sashin, dan haka ta biyota daki sanin yanzu yayar tata zata birkice. Ita mamaki take da yanda gaba daya yanzu wasu halayenta ke neman canjawa. Tunda ta dawo sashen kokarin ganin ta fahimtar da ita wacece Iffah take amma taki fahimtarta, gashi kuma yanzu Iffahn ta sake dangwalo wani al'amarin.


"Akia Please kiyi hakuri, zuwanki wajen yarinyar nan a yanzu bashine mafita ba, sai dai maya zubar miki da mutuncinki. Ni a ganina nemanta ya kamata kiyi bayan tabar wajen sai muji dalilinta na zartar da hukuncin da kece ke zartar da shi, ko kuma ki tuntubi Abni kiji tunda dai bazatai komai bada saninsa ba".


"Bani hanya Jasrah".


Ta fada a zafafe kamar ma bataji mi Jasrahn ta fada ba. Cikin dakewa itama Jasrah tace,"Bazan barki ki fitaba gaskiya Akia, kiyi tunani abinda kike son aikatawa. Akia na miya canjaki haka? Bayan kuma a baya ba hakan kike ba. Karfa ki manta shekaru kusan hudu muna kuka akan matsalar dake zagaye da mu ta mutuwar matan Abni, amma a yanzu UBANGIJI ya kawo mana iyakar komai, a kanta komai ya canja har mutane suka fahimci makarkashiya ake masa sabanin da da shi kai tsaye kowa ke zargi. Kamata yay mu rungumi yarinyar nan muyi farin ciki da kasancewarta mata ga danmu bawai bore ga duk yunkurinta ba. Matsalarmu da ita dama can akan abinda muke zargin ta aikata ne, amma yanzu mun fahimci ba haka bane ba, to mizaisa bazamu manta komai ba mu maidata komai dinmu kodan farin cikin da yaronmu ke samu da ga gareta.


Tassss! Kake jin saukar lafiyayyen mari a fuskar Jasrah, idanu kawai ta rumtse tana mai kauda kanta, yayinda Malikat Bushirat ke wani irin huci. Abune da bai taba faruwaba, dan ko sanda Jasrah a karama bata taba dukanta ba, shagwabata tai kamar yar data haifa ba kanwa ba, ta kyautata rayuwarta tai mata raino kamar Kwai a cikin cokali. Idanunta da sukai jazur ta bude, ta dan girgiza kai tana murmushi mai ciwo. "Zan iya amsar duk hukuncin da zakimun Akia dan ke uwa ce a gareni ba yar uwa kawai ba. Amma why bazan taba barinki ki zubar da mutuncinki ba". Tana gama fada ta zare key din kofar ta fice da sauri ta maida kofar ta kulle
gaba daya. Duk kiran sunanta da Malikat Bushirat keyi cikin karaji batako kulata ba tai shigewarta dakin dake matsayin nata a yanzun tana hawaye. Ita kam ta fara shiga rudani akan canjin halayen yar uwar tata, ta sara mike damunta a yanzu. Anya ba masu son cutar da Eshaan bane suka dawo kanta suka saka kiyayya a tsakaninta da yarinyar nan. Ita kam yanzu ta fahimci Iffah, tanajin kaunar yarinyar a ranta kamar tun a da can farko, matsalar data biyo baya ma a dalilin abinda suke tunanin ita ta aikatane. Amma yanzu kunyar haduwarsuma take ji. Dan bata san da bakin da zata fara rokonta gafara ba. Amma koba komai ALLAH ya sakama yarinyar tun ba'aje ko'ina ba, tunda gashi wanda ta yarda da shi fiye da kowa da komai yau shine kecin amanarta da matar dan uwansa, wannan wace irin mummunar kaddara ce. Hawaye masu zafi suka silalo mata, dan abune dake mata matukar kuna da zafi a zuciya tunda ya faru, ga kunyar fitama da takeyi dan ko hadimai shune suke mata akaikaice matsayin matar mai neman tsohuwar matar Shahan-shan……..✍️
[6/1, 1:18 PM] +234 703 445 5862: DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 66


."UBANGIJI ya halicceki mace bayan akwai maza da yawa dake kwaikwayo son zama macen amma basu isa komawa ba. Ya halicceki kyakykyawa, bayan awai wasu da yawa da kyawun da bai kai naki ba suke fafutukar nema ta hanyar sabama UBANGIJI suna amfani da abinda yace haramunne garesu. Ya baki lafiyar jiki babu ta inda kika nakasa. Bayan ga dubunki can su nakasar itace jarabawarsu. Ya baki lafiya
matsayinki na yar adam. Bayan ga dubunki can kwance a asibitoci da gidaje basu da kudin shan magani, masu kudin ma basu isa iya sayawa kansu lafiya ba koda sun kai karuna dukiya. Ya azurtaki cikin nagartaccen addini, bayan ga dubunki can na bautar wanin ALLAH cikin batan da su a karan kansu basu san bata bane ba. Ya azurtaki da tarin dukiya. Bayan akwai dubunki da abincin yini daya ma gagararsu yake ci saboda basu da kwabo na saya. Ya azurtaki a cikin katon gidan aure dana haihuwa, karkashin kyakykyawar nasaba bayan akwai dubunki da a kan titi ko cikin bukka suke rayuwa badan kin fisu ba. Ya azurtaki da karfin iko na mulki, bayan akwai dubunki da su wanna matsayin naki suke kwadayon kaiwa, ke wasu ace ma su din hadimanki ne kawai farin ciki yake sanyasu. Ya azurtaki da ilimin addini dana zamani, bayan akwai dubunki da suke zagaye da jahilci, wasu ko suna son karatun rashin mai tallafa musu Yasa suka hakura suka zama masu aikata miyagun laifuka koda zukatansu basa so, sai dai basu iya banbance abinda ya dace da wanda zai dace da tasu rayuwar. Ya azurtaki da da daya tilo tamkar da dubu da nagartaccen mijin da duniya bazata taba mantawa da su ba, bayan akwai mata da yawa da su jarabawarsu mazajen aurensu ne da yayan da suka haifa. Duk da ya miki wadannan abubuwane badan kinfi sauran halittun duniya

Please Login or Register in order to submit comment