Reading FANSAR RAI complete 1&2 BY SIS NERJA'ART Chapter 48 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

natambayeta ko tana buk'atar taimakona?
Girgiza kai tayi tace bana buk'atar taimakonki.
Bushewa da dariya tsohuwar tayi tace cikin ke da Faruk dole sai wani ya riga wani shek'awa lahira.
A rikice jawahir tace ban fahimta ba me zai faru da faruk d'in?
Sake bushewa tayi da dariya saida tayi me isarta sannan tace zasu kasheshi a bayan an yanke maki hukunci a kotu saboda kar susakeshi yatona masu asiri.
Fashewa Jawahir tayi da kuka cikin sauri taduk'a k'asa tace Ammi na rok'eki dan Allah kitaimakeshi kar kibari sukasheshi bai cancanci hakan ba.
Girgiza kai tayi tace bakida ikon neman taimakona batare da yin nadama ba.
'Dago kai tayi fuska sha'be sha'be da hawaye tace indai har akan Faruk ne na amince saida taruntse idanunta cike da takaici sannan tace na yi nadamar kalmar da nafad'a maki kiyi hak'uri insha Allahu bazan sakeba, ina sonki Ammina....dariyar da taji ana kyalkyalawane yasa tayi saurin bud'e idanunta dan gabad'aya d'akin yake amsaba dubawa tayi taga babu Ammin tata saidai muryar dariyar taji tana fita, tana nan duk'e a haka akazo aka fita da su aka tafi da su kotu.
Tana kawowa nan a bayanin nata tanuna inda Faruk yake zaune da sandarta sai gani yayi d'aurin da akayi mashi ya kwance, cikin muryarta me ban tsoro tace zaka iya fita ga k'ofa chan a bud'e nan da minti takwas zata iya rufe kanta, jin haka yasa Faruk yayi saurin mik'ewa duk sai yajishi wani iri dakyar yafara takawa dan a lokacin matar har ta 'bace, bin gidan yadinga yi da kallo bai san inda yakeba da karambani yagano k'ofa yana fita k'ofar tana maida kanta tadatse tsayawa yayi yak'are ma gidan kallo saida yagane anguwar sannan yasamu abun hawa yahau yanufi gidan Barr Nas, ya yi sa'a ya sameshi a gida nan yayi ta murnar dawowarshi wanka yayi yashirya cikin sauri, sannan yace ma Nasir yad'auko mashi ajiyar da yakawo mashi ranar da za'a kamashi dan dama jikinshi ne yadinga bashi kamar akwai abinda zai iya faruwa da shi wannan dalilin ne yasa yad'auki dukkan shedun da yatara yakai ma Barr Nas ya ajiye mashi wajenshi hatta wayarshi da yafi amfani da ita saida yakashe yabashi dan ya san a cikinta ya ajiye abubuwa dadama masu muhimmanci,daga nan suka fito cikin sauri suka nufi kotu dan a lokacin sun makara dan sunsan dole cikin biyu ayi d'aya ko angama shari'ar Jawahir ko kuma ana cikin yi....yana kawowa nan a labarin yace wannan shine abinda yafaru da ni.

Hankalinsu gabad'aya saida yatashi sosai Dad yace tabbas Alhaji Sufyan ya kasance maha'inci ban ta'ba tunanin haka daga gareshiba ace da sa hannunshi aka sace min d'a duk kusancin da ke tsakaninmu ina mashi kallon abokina na k'warai ashe ba haka ba.


Jawahir sai a lokacin tad'ago takalleshi tace ya akayi kasamo Ummah katafo da ita?
Murmushi yayi yace lokacin da naje asibitin naga halin da take ciki nan nanemi taimakon likitocin suka taimaka suka ban ita nacanza mata asibiti inda zata fi samun kulawa dan asibitin da su Alhaji Mansur suka kaita wata k'aramar asibiti ce wadda basuda wadatattun kayan aiki kuma sunyi hakane dan kawai suna so tamutu itama, toh cikin ikon Allah ina maidata chan suka dinga bata kulawa sosai har tafara samun sauk'i, dan tana iya motsa 'bare d'aya na jikinta saisa ma nace atafo da ita tunda tana magana.


Shi kuma megadinku buzu wannan aikinki ne dan kece kika samar mana taimako Amminki tasanar da mu inda yake.

Jinjina kai su Dad suka dinga yi mamaki duk ya cikasu.
Barr Junaid yace lallai sharrin su Alhaji Mansur ya fi tunanin duk wani me tunani ashe duk wannan k'ulla k'ullan su sukayi shi sukaja aka kama baiwar Allahr nan.

Dad girgiza kai yayi yace wasu mutanen macen zuciya garesu babu abinda sukasa gaba sai son kansu, kallon jawahir yayi yace tabbas na san mahaifinki dan abokin kasuwancina ne a lokacin da yake raye kamfanina da nashi kusan tare suke tafiya dan ma baza'a had'a ba nashi kamfanin ya fi nawa d'aukaka saboda wasu kayan ya fini saidai shi ba mutum bane me bak'in ciki yana son cigaban mutane nan yasa muka had'a hannu tsakanin kamfanina da nashi muna shigo da kaya tare wani lokacin idan kamfaninshi yana buk'atar rancen kud'i a nawa kamfanin yake zuwa yana ranta nima haka akan wannan ne yasa muka k'ulla abota sosai akan kasuwancinmu dan kowa yana son cigaban d'an uwanshi bamufi wata takwas a haka ba nanemi rancen wasu kud'i saboda wasu kayan aikin injin da nakeso inje Dubai insiyo yad'auki kud'in yabani, koda naje Dubai saida nayi kusan wata ukku sannan nasamu yadda nakeso naturo da kayan ni ban dawoba a wata na biyar ne naturo mashi da kud'inshi daga chan saidai 1 million da tarage ban bashiba, ak'alla saida nayi wata goma sannan nadawo k'asar nan bayan na dawo ne nasamu labarin rasuwarshi nan hankalina yatashi sosai haka nad'auko million d'aya d'in nan naje gidanshi nayi sallama nasa aka kira man matarshi koda tafito nayi mata gaisuwa sannan nabata cheque d'in kud'in, tun bayan rasuwarshi na so mucigaba da kasuwanci tsakanin kamfanina da nashi ammah d'an uwanshi yak'i dan haka nabarshi lokaci guda kamfanin yadaina kawo kud'i yadda yakamata nawa yazo yafi shahara, a haka nak'ara nema muhad'a hannu da Alhaji Mu'azu mumaido ma kamfanin tattalin arzik'inshi ammah yak'i dan gani yake kamar wani cutarshi nakeson yi wannan dalilin ne yasa nafita harkar kamfanin.


Jawahir fashewa tayi da kuka tace tabbas kaine Alhaji Sanin da yazo gida yakawo ma Ammina cheque akan kud'in ne aka nemi a salwantar da rayuwarta

Su duka kallonta suke cike da mamaki Barr Nas yace kamar ya?
Kwashe komai tayi tasanar da su akan mutuwar Amminta nan duk jikinsu yayi sanyi sukayi ma iyayen nata addu'a.

Mom ce tarungumota jikinta tana lallashinta dakyar aka samu tayi shuru sannan Dad yace Jawahir kikwantar da hankalinki mu zamu zauna da ke zamu kula da ke duk abinda kikeso zamuyi maki kid'aukemu a matsayin iyayenki.
'Dago kai tayi takalleshi tayi murmushi tace nagode sosai Dad da wannan karamcin da kukayi min saidai ina so inkoma wajen dangin mahaifiyata zan je incigaba da rayuwata da su tunda suna raye, bazan iya cigaba da zama cikin garin nan ba.

Haba Jawahir mu ma fa zamu zauna da ke tsakani ga Allah bazamu ta'ba cutar da ke ba,,, cewar Faruk

Girgiza kai tayi tace a'a Faruk su ma suna buk'atata na sani kawai dai halin Abba ne yasa suka daina zuwa garin nan, na san ku d'in mutanen kirki ne saidai zamana a nan bazai yuwu ba.

Dad yace shikenan Jawahir mun fahimceki ammah kibari kikwana biyu a nan sannan kitafi.
Kallon agogo tayi tace a yau nakeson tafiya.
Faruk ne yayi saurin cewa a'a ba yau ba please kid'an mana kwana biyu kamar yadda Dad yace.
Shuru tayi batace komai ba.
Sallamar mutane da suka jiyo ne yasa gabad'aya suka tashi suka fita suka bar Mom da Jawahir a nan Mom tana k'ara lallashinta.


Mutane ne dayawa sukayo gungu guda sukazo tayasu murnar dawowar Faruk, a setting room d'in Dad suka zauna.

Nan da nan gida yafara cika har mata suka dinga zuwa, Jawahir tashi tayi takoma part d'in Mom tana zuwa takwanta nan da nan tafara baccin gajiya.





A ranar gidan Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan akaje aka tattara duk dukiyoyinsu da duk abinda suka mallaka hatta gidajensu.

Su Nasiba ba k'aramin tashin hankali suka shiga ba sunyi kuka sosai dan gidan da suke ciki ma amsheshi akayi akace za'a maida ma jawahir abunta dan haka suka koma wani madaidaicin gida na mahaifiyarta, yayyenta biyu masu aure saida sukazo suka ci kukansu har suka gode ma Allah, a gidajen sada labarai aka dinga yayata abinda yafaru hatta gidajen talabijin saida aka dinga nuna su Alhaji Sufyan ana fad'in abinda sukayi wannan abun ya yi ma iyalansu ciwo sosai.


A ranar aka had'a duk abinda suka mallaka aka fidda ma jawahir hak'ik'k'inta sauran dukiyar kuma aka damk'ata ga iyalansu.

Da dare aka kira Faruk aka sanar da shi dan washe gari yaje da jawahir adamk'a mata dukiyarta ya amsa da toh.

Mom nan nan take ta yi da Jawahir ammah ita ko ta k'i sakewa da ita magana ma sai tadaina yi masu dan tunda tatashi daga bacci tacanza koda Faruk yaga yanayinta yace subarta kawai wannan ba ita bace dan haka aka k'yaleta ita kad'ai tak'unshe kanta a d'akin Mom, abinci ma akayi akayi da ita taci ammah tak'i yadda aka ajiye mata haka akazo aka d'auka.

Ganin haka yasa Faruk yafara tunanin yadda zaiyi yarabata da Aljanar nan.



Washe gari koda suka tashi nemanta akayi aka rasa a cikin gidan nan hankalinsu yatashi sosai dan ba'a san lokacin da tabar gidan ba, wajen k'arfe goma Malam Nasir (Kakan Faruk) ya iso garin nan yasamesu suna shirin fita nemanta yace sudawo suzauna, bayan sun zauna an gaisa ne yakalli Alhaji Sani yace Faruk ya shaida min komai ta waya wannan dalilin ne yasa nazo dan intaimaka ma yarinyar na san saboda haka ne yasa tabar gidan dan tabbas aljanarta zata san komai akai, jiya ban samu naruntsa ba ina ta aiki akan yadda zan tunkareta kuma Alhamdulillah ina tunanin zamuyi nasara.
Su dukansu amsawa sukayi da masha Allah, Allah Ubangiji dai yasa adace, Dad yace ammah Malam ba a nan gizo yake sak'a ba ai ba'a san inda yarinyar take ba yanzu.

Jim Malam yayi sai chan yace tana da sauran dangi a garin nan?
Faruk yace a'a.
Tunani yafara yi sai chan yace toh gidansu fa akwai wani a ciki?
Nan ma Faruk yace a'a.
Jin haka yasa Malam yace tabbas babu inda zataje sai gidansu a chan ne kad'ai aljanar zata kaita tunda babu kowa a gidan, kallon Faruk yayi yace yi sauri katashi muje chan gidan nasu, kad'auko min wacchan ledar da nazo da ita.
Cikin sauri suka tashi suka fita a cikin motar Faruk suka shiga har da Dad suka tafi aka bar Mom a gida.


Gudu Faruk yadinga yi da motar har suka isa gidan suna zuwa suka tarar da gate d'in a bud'e dan haka a gaban gidan sukayi parking d'in motarsu suka fito Faruk yace nan ne gidan mushiga, har ya wuce zai shiga malam yayi saurin rik'oshi yace a'a kar kushiga kujira, nan suka ja suka tsaya, addu'a yayi sannan yace sushiga suna shiga filin gidan itacene suke ta kad'awa ga ganyaye a k'asa duk sun bushe, su dukansu bakinsu d'auke da addu'a suka nufi hanyar da zata sadaka da cikin gidan suna shiga tsakar gidan wata irin k'ara sukaji me had'e da iska, nan suka ja suka tsaya kallon d'akunan sukayi sukaga kowane rufe yake, dariya ce sukaji ta fara tashi a d'aya daga cikin d'akunan dan haka cikin sauri suka nufi d'akin kafin su isa k'ofar d'akin ta bud'e kanta sai duhu sukaga ya bayyana a ciki, malam ne yace masu kowa yacigaba da addu'a kar yadaina dan haka suka nufi d'akin, Faruk wayarshi yad'auko yakunna touch sannan suka shiga, a k'arshen bango suka ganta tsaye bisa iska k'afafuwanta sun nannad'e gashin kan nan ya mik'e tsaye ga bakin nan na jirkice, idanuwanta k'ara fitowa sukayi waje k'wayar kamar ba zaune take a cikin idanun ba, gabad'aya halittarta ta canza, kallonta suka tsaya suna yi cike da mamaki, Faruk ne yayi k'arfin halin cewa Jawahir ya akayi kikazo nan?
Wata irin murya sukaji me kama da gurnanin zaki ana cewa taya zan zauna bayan kunaso kurabani da rayuwata bazan ta'ba barin duk wanda yaso yarabani da duniyarnan ba.

Malam nuni yayi ma Faruk alamun yayi shuru sannan shi yace ya zama dole kirabu da yarinyar nan kidaina wahalar da ita hakanan.
Bushewa tayi da dariya tare da matsowa bisa iska har lokacin bata safka k'asa ba tace hakan ba zai ta'ba yuwuwa ba babu wanda zai rabani da d'iyata ko wanene yaso haka sai na ga bayanshi.

Malam na jin haka ya amshi ledar da take hannun Faruk yabud'e yad'auko wata roba k'arama wadda take d'auke da wani ruwa a ciki, sannan yad'auko wata leda me d'auke da wani farin abu kamar gari, bud'e ledar yayi yad'ebo farin abun yayi bismillah yawatsa mata, wata irin k'ara tasaki sai gata ta fad'o tim k'asa, hasken d'akin ya dawo.

cikin sauri yabud'e robar yawatsa mata ruwan, nan tasake sakin wata k'ara me k'arfi wadda tasa saida suka toshe kunnuwansu saboda kar k'arar ta lahanta masu dodon kunne, cikin k'araji tace kar kakuskura kasake watsa min ruwan nan banaso kadaina, wanene kai????

Malam kallonsu Faruk da Dad yayi yace kuje kurik'e man ita, su duka suka nufi wajen da take kafin su isa hannu tad'aga tanunasu sai gasu kamar anyi wurgi da su su biyun sun fad'a chan gefe.

Ganin haka yasa malam yafara karanta ayoyin Allah dak'arfi sannan yafara zagaye d'akin yana d'ibar ruwan yana watsawa nan tadinga ihu tare da yunk'urin ja da baya, Faruk ne yafara mik'ewa dakyar yanufi inda take malam wurgo mashi garin maganin yayi yace yawatsa mata a saman kanta nan ya amsa ya watsa mata tasake sakin wata k'arar sannan tasulale k'asa asume, ganin haka yasa malam yai saurin isa wajenta yace ma Faruk yabud'e mashi bakinta, nan yafara k'ok'arin bud'ewa dak'yar yasamu yabud'e mata nan Malam yazuba mata ruwan maganin a ciki, yagoga mata na garin a fuska, bud'e idanunta tayi tare da k'wala k'ara tature Faruk da ke rik'e da ita nan tabank'are jikinta tare da bud'e bakinta gabad'aya nan wani irin farin hayak'i ne yadinga fita daga bakin, idanuwanta duk sukayo waje, hayak'in yana gama fita kallonsu tayi d'aya bayan d'aya sai kuma tamaida idanunta tarufe tadaina ko da motsi.
Faruk yace Malam me yafaru da ita bata motsi ko ta suma?
Malam da yake kallonta girgiza kai yayi sannan yakalli su Faruk yace ba suma tayi ba tana raye bazata ta'ba tashiba har sai anyi abu d'aya.
Cikin rashin fahimtar maganarshi sukace bamu ganeba Malam
Jinjina kai yayi yace tabbas layar da aka sa ma gawar ne a kusa da iccen suri aljannun da suke cikin iccen ne suka tado fatalwarta kuma tana rayuwa ne a cikin hak'ark'arin jawahir wannan dalilin ne yasa take amfani da jikinta da ruhinta, sannan wannan fitar da tayi zata iya dawowa nan da 'yan awanni kad'an idan har ba'ayi saurin zuwa k'abarinta aka tono wannan layar ba dan a yanzu haka layar tana nan cikin k'abarin da antone aka k'one shikenan fatalwar zata koma bazata sake bayyanaba.


Saurin mik'ewa Faruk yayi yace ni zan je intone k'abarin kujirani bari inje ind'auko megadinsu yarakani mak'abartar.
Malam yace toh kutafi da ashana da kun tono ku k'oneta kar kubaro wajen baku k'onetaba Faruk ya amsa da toh nan yawuce cikin sauri yatafi.....








_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:21 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 22*

Yana barin gidan chan gidan da yasafke buzu megadi lokacin da yad'akkoshi daga Marad'i dan yazo yabada sheda yawuce ya yi sa'a daidai lokacin yafito daga cikin gidan, ganin motar Faruk yasa yanufo wajen cikin hausar shi da bata fita sosai yace hannu da zuwa Alhaji hannu.
Murmushi Faruk yayi yace yauwa buzu megadi ashe na yi sa'a da fita ma zakayi.
Washe baki yayi yace eh na d'an fitone zanga gari kafin gobe inkoma garinmu.
Allah sarki, yanzu shigo mota inmaka wata tambaya.
Bai musaba yabud'e motar yashiga yace toh Alhaji ai dun yanda kashe haka za'ayi.
Yanayin maganarshi tana ba Faruk dariya har saida yayi murmushi sannan yace yauwa tambayar da zanyi maka itace: dan Allah kana iya tuna mak'abartar da aka binne Hajiya Khausar bayan ta rasu?

Yatsa yasa yadafe kanshi irin yana tunanin nan sai chan yace Eh aradu har k'abarinta na sani kusa da wani iccen giginyane akwai tudu a wajen ban mancewa har lokacin nayi tuntu'be a wajen nafad'i bayan mun rufota har yanzu akwai tabon gurjewar da nayi a gwiwata bari ma kaganshi.

A'a kabarshi ba sai na ganiba yanzu fad'a min mak'abartar muje dan inason ganin k'abarinta.

Angama oga nan yafad'a mashi Faruk yaja motar dagudu yanufi anguwar da mak'abartar take suna zuwa suka samu waje daga chan k'etare sukayi parking d'in motarsu suka tsallako, megadin mak'abartar suka samu suka gaisa nan Faruk yafayyace mashi komai akan abinda yakawoshi, da fari megadin be yarda ba dan ya yi tunani wani abu sukeson yi ne kawai.

Ganin haka yasa Faruk yace na san baka yarda da maganataba saboda duniyar nan ta yanzu ta 'baci matsafa sunyi yawa suna amfani da wani sashe na jikin gawa suna tsafi da shi, wallahi ni ba wannan yakawoni ba idan baka yarda ba muje tare ayi komai a gabanka.
Jin haka yasa megadin ya amince suka je tare buzu megadi tsaye yayi yana tunanin inda zai gane k'abarin saboda tsawon shekaru ukku kenan da binneta, gefe gefen mak'abarta yafara bi dan ya san tabbas daga gefe yake, megadi ganin haka yasa yace da hak'ura kukayi dan kusan shekara ukku ai babu abinda zaku samu saboda bayan ita mutum dubu nawa aka binne a wajen.
Jikin Faruk sanyi yayi dan ya san gaskiya megadi yafad'a.

Daidai wani iccen giginya dake kusa da wani d'an rami buzu megadi yatsaya yace alk'ur'an nan ne wajen ga ma k'abarin nan kusa da giginyar nan.

Megadin mak'abartar ne yace ka tabbata nan ne dan gaskiya an kwana biyu ba'a binne mutane a wajen ba dan duk gawar da aka binne saidai washe gari azo atadda k'abarin a bud'e ko ansake rufewa haka yake faruwa wannan dalilin ne yasa gabad'aya aka daina binne gawa a wajen.
Sake kallon wajen yayi yace wallahi nan ne ban manceba.

Jin haka yasa Faruk yace tunda ya tabbata da nan d'inne toh mutone wajen mugani ta yuwu aga gawar.

Megadin mak'abartar amincewa yayi nan suka duk'a suka fara tonen k'abarin babu komai a cikinshi sai k'asa haka sukaita tonawa daga k'arshe ma sai farin yashi suka fara gani, ganin haka yasa Faruk yaduk'a yasaka hannunshi yafara lalubawa cikin yashin yana cewa indai har wajen nan ne toh tabbas zamuga layar, cigaba yayi da lalube ganin baiji komai yasa yasa suka cigaba da tone ramin har said sukayi mashi zurfi sosai sannan suka kwashe k'asar ciki, suna cikin kwasar k'asar ne buzu megadi yakwaso da wani abu bak'i nan yanuna ma su faruk.

Me gadin mak'abarta ne yad'auko abun yana dubawa nannad'e yake da zare yace to menene wannan ko dai layar ce?
Buzu yace anya kuwa ai laya ba bak'a bace.
Wurgi yayi da shi yace wani dai abun ne daban kunga ahak'ura kawai k'ila ma ba nan bane tunda kusan shekara ukku ai ya isa amance.
Faruk ne yayi saurin zuwa yad'auko abun yace tabbas raina ya bani wannan ce layar bakuga an nad'e da zare ba, bari inbud'a muga abinda yake ciki, nan yafara warware zaren saida yawarware tas yaga da fata aka had'a an d'inketa nan suka warware d'inkin sai ga wani siririn gashi guda d'aya a ciki, cire gashin sukayi suka bud'e layar nan wani bak'in hayak'i yafito daga ciki, sunan Khausar ne tun daga sama har k'asan layar, faruk yace kungani ko wallahi itace aljihunshi yafara lalube zai d'auko ashana nan sukaga wata irin isaka ta taso me k'arfi wadda tasa gabad'aya iccinan da suke cikin mak'abartar suka fara kad'awa su kansu iskar saida taso tayi masu yawa.

Faruk saurin fiddo ashanar yayi yafara kyastawa saidai saboda iska da ya kyasta sai tamutu, saida yakyasta ashana kusan guda goma tana mutuwa ganin haka yasa megadi yace saidai muhad'e waje guda mukare yadda iska bazata shigaba da wannan shawarar sukayi amfani nan suka had'e wata irin k'ara suka dinga ji tana tashi a wajen ahaka suka kyasta ashanar, muryace suka juyo ana cewa kar kak'ona kabari zan tafi bazan sake dawowa ba kabarni ina gargad'inka kar kak'onata!!!
Saurin cinna wutar yayi a jikin layar tafara ci, k'abarin khausar saida yad'an girgiza nan wani bak'in hayak'i yafito daga ciki, layar na kusa cinyewa a hannunshi yayardata a k'asa daidai lokacin iskar da take wajen tadaina kad'awa komai yatsaya chak, jinjina kai megadin mak'abarta yayi yace lallai Annabi ya yi gaskiya tsafi gaskiya ne yana kama mutum yanzu daman da abinda aka k'ulla ma wannan baiwar Allah saisa tun bayan ita babu wanda aka sake rufewa a cikin k'abarin nan dan ko anrufe mutum wahala za'asha sai ma ancanza mashi waje.
Buzu megadi yace wallahi da gaskiyarka haka abun yake, kallon faruk yayi yace yanzu shikenan bazata sake kashe kowaba Jawahir ta dawo daidai
Hamdala faruk yayi nan suka maida k'asar ramin suka rufe sannan suka wuce godiya sukayi ma megadi sosai sannan suka tafi.


Biyawa yayi yasafke buzu megadi gidan da yake nan yatambayeshi gobe da k'arfe nawa zai wuce yace da asuba, kud'i yafiddo sosai yabashi yace yayi kud'in mota da tsaraba nan buzu yayi ta mashi godiya har da fita daga cikin mota yaduk'a yana godiya.
Faruk yace bakomai shine da godiya da yayarda yabiyoshi suka zo katsina.



A chan 'bangaren Jawahir Malam addu'o'i kawai yake yi mata, har a lokacin bata motsi sai wata irin zufa da take kwarara daga fuskarta jikinta zafi yayi sosai kamar me zazza'bi dan hucin zafin har su suna jinshi, daidai lokacin da Faruk ya k'ona layar taja dogon numfashi nan tafara atishawa, saida tayi ta fi goma.

Dawowar Faruk gidan ne tafarka tatashi zaune tana binsu da kallo daga k'arshe tasafke idanunta akan faruk da yashigo a daidai lokacin ahankali tabud'e baki tace me yake faruwa da ni? Kun rabani da Ammina ko?

A'a Jawahir ba rabaki mukayi da ita ba.
'Dan guntun murmushi ne tayi sannan tamik'e dak'yar tafito tsakar gidan duk su ma suka fito, wani part ne taje tabud'e tashiga taja tatsaya a tsakiyar parlorn lokaci guda tafara hawaye tajuyo takalli Faruk tace nan shine part d'inmu ni da Yaya Umar d'ina a nan muke rayuwarmu ammah Ammi tazo tarabamu wannan dalilin ne yasa nakasa cigaba da sonta, na sani kun rabani da ita bazan ta'ba damuwaba, kallonta tamaida ga Malam tace nagode sosai Malam.
Faruk cikin sanyin jiki yace Jawahir kakana ne wannan.
Murmushi tayi ahankali tasake cewa nagode.

Saurin goge hawayen da suke kwarara a fuskarta tayi sannan tafito daga d'akin tace ya kamata inje Kebbi inason ganin dangina wad'anda su kad'ai suka rage min dangi a duniya.

Dad yace a'a jawahir kibari sai kin samu sauk'i sannan kitafi, mu zamu rakaki wajen danginki.

Malam yace tabbas hakan yakamata dan nima kaina akwai wasu magunguna da zan d'aurata akansu na tsawon kwana biyu.

Faruk yace to kinji abinda yace dan Allah kizo mukoma gidanmu na tabbata mom zata kula da ke sosai.

Ita kanta ta san jikinta yana mata ciwo dan haka ta amince, ammah saida tafara shiga part d'in Abba taduba duk wasu file babu su, kallon Faruk tayi tai murmushi tace su Abba sun mutu ni kuma antafi da ni prison ummah tana asibiti sunyi amfani da duk wannan damar sun zo sun kwashe duk wani abu me amfani, saidai wannan ba shine a gabana ba, a yanzu na fi farin ciki da natabbatar su ma zasu mutu.
Faruk yace haka ne ina tayaki murnar samun 'yancin kanki jawahir.

Murmushi tasake yi a karo na biyu tace nagode.



A cikin motar da sukazo duk suka shiga suka koma gida, nan Malam yakawo maganin da yazo da shi yabata yace tadinga sha kullum sau ukku a rana na tsawon kwana biyu ne, godiya tayi mashi tare da su Dad, nan mom tadinga nan nan da ita.

Da marece Faruk yasanar da ita neman da akeyi mata akan dukiyarta tace bazata iya zuwa ba yau saidai zuwa gobe shima d'in yayarda da hakan dan saboda batada lafiya.
Bacci tadinga yi a ranar sallah kad'ai take tadata da kuma ta yi sai takoma.

Malam yace abarta duk na gajiya ne da kuma yanayin da take ciki.

Nan yakawo tsarabar da yakawo masu yabasu yayi masu nasiha da wa'azi dan duk zuwan da zaiyi ko idan sukaje sai ya yi masu nasiha akan suji

Please Login or Register in order to submit comment