Reading FANSAR RAI complete 1&2 BY SIS NERJA'ART Chapter 46 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

suke barinshi yayi shima sai kusan mutum ukku sun tsareshi sannan.

******
Wajen k'arfe Taran safe aka fiddo wad'anda za'a yi shara'a akan case d'insu aka saka cikin mota aka nufi kotu inda motocin 'yansanda suka kasance gaba da bayan motarsu, tunda suka fara tafiya matan suka dinga bin titi da kallo masu farin ciki sunayi masu bak'in ciki nayi akan case d'insu dan kowa ya san makomarshi, jawahir ko jingine jikinta tayi a inda take zaune yanayinta kawai zaka kalla kagane tana cikin tashin hankali saidai abinda zai baka mamaki ba wai akan case d'inta tashiga tashin hankalinba ta shiga ne saboda halin da Barrister yashiga akanta, wasu siraran hawaye ne suka gangaro mata tayi saurin sa hannu tagoge, a cikin zuciyarta tana addu'a Allah yasa ko bayan ranta Faruk yaku'buta daga sharrin mutanen nan, ahaka har suka isa HIGH COURT bata saniba saida aka bud'e aka fara fita sannan takusa da ita tata'bota tafito.....


********

Nasiba bayan ta gama sallar asuba da azkhar d'inta gari yana fara haske fitowa tayi dan tagaishe da iyayenta kamar yadda tasaba saidai da ka kalli fuskarta zakaga alamar bata runtsaba, hanyar part d'in mahaifinta tanufa tana isa a parlor taji muryarshi yana waya har zata d'age labulen tashiga sai kuma tafasa taja tatsaya dan yagama wayar abinda taji yana fad'a ne a wayar yad'aga mata hankali sosai saurin sa hannu tayi tatoshe bakinta tare da zaro idanu gabanta wani irin mummunan fad'uwa yayi tayi saurin ja da baya lokacin da taji yana cewa "Haba Alhaji Mansur ai kar kadamu tunda dai Faruk yana hannunmu nasan yarinyar nan ta shiga damuwa sosai saboda ba lauyanta,,, dariya yayi sannan yace ai ya kamata muma muje High court d'innan ayi shara'ar a gabanmu akasheta kowa yahuta kaga shikenan sai mucinye sauran dukiyar hankalinmu kwance.
Eh daman ka fad'a min kunyi magana da Barr M.B jiya toh shikenan koma menene sai mun had'u a kotun".

Saurin juyawa tayi dagudu tabar wajen tare da fashewa da kuka tana isa parlor taci karo da mahaifiyarta da tafito daga part d'inta, kallonta tayi tace lafiya Nasiba.

Jikinta tafad'a tare da k'ara sautin kukanta.

Kingani ko kedai bakijin magana yanzu haka wani laifin kikayi ma Daddyn naki ko? Na fad'a maki kicigaba da addu'a indai Faruk yana raye zaya dawo.
Cikin sheshek'ar kuka tabud'e baki tace Mummy...sai kuma tayi shuru.
Rik'ota Hajiya Maijidda tayi tace shikenan kiyi hak'uri muje inrakaki d'akinki kikwanta kafin agama had'a breakfast insa akawo maki.

Tana a jikin Mummyntata a haka sukaje tarakata har bedroom d'inta saida talallasheta tadaina kukan sannan tatafi.

Nasiba tana ganin ta fita mik'ewa tayi taje tarufe d'akinta tacigaba da kukan maganganun da taji mahaifinta yana yi a waya suna dawo mata, kanta tafara tambaya tana cewa kenan su Daddy sun san inda Faruk yake? Ammah akan me suke magana dukiyar wa zasu cinye?
Ko dai akwai gaskiya akan maganar da Faruk yafad'a akan Daddynta?

Saurin girgiza kai tayi tace a'a Daddyna ba haka yakeba kawai dai suna magana akan wani abun nadaman ammah kuma.....komawa tayi takwanta tare da dafe kanta da taji ya fara sara mata nan hawaye suka cigaba da ambaliya a fuskarta....


__________

Tunda aka shiga kotun waje aka samar masu su kusan hud'u ne suka zauna, mutane ne sosai a cikin kotun, ahankali ahankali ake zuwa lokaci guda kotun tacika mak'il da jama'a ana jiran k'arasowar alk'ali inda gabad'aya ciki da wajen kotun zagaye take da police, a gaba kuma lauyoyin masu k'ara da wad'anda ake k'ara ne zazzaune, goma saura minti biyar alk'ali yafito nan gabad'aya mutanen suka mik'e har saida yazauna sannan kowa yazauna.

Court Reporter ne yamik'e yayi sallama tare da yin addu'a bayan anshafa ne sannan yace a yau 2 ga watan Afurili (April) wanda yayi daidai da 7 ga watan Rajab......Shara'a ta farko da zata kasance a yau itacs Shari'ar Maimuna Ahmad wadda ake zargi da zuba ma mijinta guba a cikin abinci yaci yamutu daga k'arshe dangin mijin sukayi k'ararta bayan antabbatar masu da guba ce takasheshi, juyawa yayi yakalli Alk'ali yace Allah yagafarta malam wannan itace shari'ar tamu ta farko, jinjina kai Alk'ali yayi nan court reporter yaje yamik'a ma alk'ali file d'inta.


Dattijon Alk'alin gyara zaman farin glass d'inshi yayi a saman fuskarshi sannan yaduba file d'in ya d'au kusan minti biyar a duk'e sannan yad'ago kai yace kotu tana buk'atar ganin Maimuna ta bayyana a gabanta.

Jawahir da tunda taji za'a fara karanto k'ara taruntse idanunta dan a tunaninta shari'ar ta ce za'a fara'a bata bud'eba sai da taji ta kusa da ita ta fara kuka ahankali sannan tabud'e takalleta da alama itace Maimuna nan wasu police mata guda biyu sukazo suka jata suka tafi da ita wajen da aka tanadar ma me k'ara da wanda ake k'ara dan sutsaya.

Alk'ali d'agowa yayi yakalleta sannan yaduk'a yafara 'yan rubuce rubuce sai kuma yad'ago yace kotu tana buk'atar ganin lauyan me k'ara da na wadda ake k'ara.

'Daya daga cikin lauyoyin da suke zaune ne a layin gaba yamik'e yayi sallama sannan yace sunana Barr Mu'ammar nine lauyan da yake kare wadda ake k'ara sannan yakoma yazauna, Barr Junaid da yake zaune ya yi zugum bai ma san abinda ake tattaunawa ba saboda hankalinshi yana wajen abokinshi da ya'bata tsawon kwanaki hud'u, Barr Bilal ne yad'an zunguroshi da biron hannunshi sannan yadawo hayyacinshi saurin mik'ewa yayi yai sallama sannan yace sunana Barr Junaid nine lauyan da yake kare mek'ara.

'Dago kai Alk'ali yayi yakalleshi sannan yaduk'a yayi 'yan rubuce rubucenshi.

Yad'ago kai yace kotu tana so maimuna tabayyana mata gaskiya a game da kisan da ake zargin ta yi ma mijinta ta hanyar ciyar da shi guba.

Sheshek'ar kuka tafara yi saida megabatar da k'ara yamik'e yasake maimaita mata jawabin alk'ali sannan cikin inda inda tace bani bace nakashe shi dan lokacin da yamutu bana gidan.

Alk'ali ganin ta yi shuru bata sake cewa komai ba yasa yaduk'a yayi 'yan rubuce rubuce sannan yad'ago yace shin ko Lauyan wad'anda suke k'ara yana da shedar da zai bayyana ma kotu wadda zatasa tagamsu da cewa maimuna ce tayi kisan bayan a yanzu maimuna ta nuna ba itace tayi kisan ba.

Mik'ewa Barr Junaid yayi yace tabbas ina da ja ya maigirma mai shara'a inaso kotu taban dama ind'an yi wasu tambaboyi ga maimuna.
Kotu ta baka dama,,, cewar alk'ali.

Fitowa Barr Junaid yayi yanufi wajen da take tsaye yace malama maimuna shin ko zaki iya sanar da mu kina ina a lokacin da mijinki yamutu?
Inda inda tafara yi tace na je gidan 'yar uwata ranar ban gida nima saidai nadawo natarar da gawarshi.

Murmushi Barr Junaid yayi yace shikenan abinda kika sani?
'Daga kai tayi alamun eh.

Juyawa yayi yakalli alk'ali yace ya megirma me shara'a maimuna bata amsa laifinta ba saidai duk na kusa da ita sunsan cewa itace tayi kisan.

Lauyan wadda ake k'ara ce yayi saurin mik'ewa yace ya me girma me shara'a ya kamata a tsawatarwa lauyan wanda suke k'ara yagyara jawabanshi dan sunyi muni ga wadda ake k'ara.

'Dagowa Alk'ali yayi yakalli Barr Junaid yace kagyara bayaninka.

'Dan duk'ar da kai yayi cikin girmamawa yace na gode, sannan yad'ago yace ya megirma me shara'a inaso kotu taban dama ingabatar da shedu.
Kotu ta baka dama.

Godiya yayi yace malam zubairu me gadi da Talatu me aikin gidan sune sheda.

Alk'ali ne yace kotu tana buk'atar ganin Malam Zubairu me gadi gidan Sadik'u da Talatu me aiki sun gurfana a gabanta.

Su dukansu suka fito nan aka sa su sukayi rantsuwa akan zasu fad'i gaskiya sannan aka tambayesu suka bada shedar cewa babu inda taje a ranar tana gida inda 'yar aikin gidan tak'ara da cewa a gabanta ta ga me d'akintata ta fiddo wani abu cikin leda ta zuba a cikin abincin wanda yaci yamutu.


Maimuna na jin haka tafashe da kuka tace talatu sharri zaki ja min Allah ya isa ban yafeba, police d'in da suke bayanta tsaye ne suka daka mata tsawa tayi shuru, Barr Junaid cewa yayi sukoma suzauna sannan yamaida kallonshi ga alk'ali yace ya megirma me shara'a bayan wannan shedar ina da shedar report d'in da likita yabada na mutuwar mamacin inda ya rubuta ya ci guba sannan an d'auko abincin da yaci anduba anga akwai guba a ciki.

Alk'ali ajiye biron hannunshi yayi yace ina sheda?
Barr Junaid d'auko wata farar takardar yayi yaje yamik'a ma alk'ali yace ya me girma me shara'a wannan itace shedata sannan a cikin file d'in mamacin ma akwai shedar hakan, nan yaje yad'auko file d'in yakawo ma alk'ali yace jiya na amsoshi a asibiti.


Dubawa alk'ali yayi sannan yad'ago yakalli wadda ake k'ara yace shin ko kina da ja akan wannan shedun da aka samo?
Shuru tayi tana cigaba da kuka ganin haka yasa lauyanta yamik'e yace ina da ja ya megirma me shara'a abinda lauyan masu k'ara yafad'a ba gaskiya bane.

Cikin kuka tace tabbas hakane nice nakasheshi saboda bana sonshi iyayena ne suka aura min shi, wallahi nice nakashe shi.

Alk'ali yace kin tabbata kece?
'Daga kai tayi alamun Eh.

Duk'awa yayi yai 'yan rubuce rubuce sannan yad'ago yace Alhamdulillah kin amsa laifinki bayan duk bayanai sun nuna hakan dama, dan haka kotu zata yanke maki hukuncin zaman gidan kaso har k'arshen rayuwarki domin laifin da kika aikata na kashe mijinki wannan shine adalcin kawai da zamuyi.


Kuka tacigaba da yi cike da tashin hankali nan aka tafi da ita.


Jawahir wani irin tausayinta taji ganin yadda take kuka saidai me matar itace me laifi babu yadda za'ayi.

Haka me gabatar da k'ara yamik'e yasake bayani akan k'ara ta biyu aka fito aka fara yin shara'a.


Jawahir tana nan tsaye saida akayi ma mutane hud'u inda wasu aka yanke masu hukuncin kisa wasu kuma aka maidasu gidan yari, ita d'in kanta ta san dole cikin biyu za'ayi guda ko kisa ko yanke hukuncin k'arashe rayuwa a gidan kaso, wasu siraran hawaye ne suka gangaro mata cikin zuciyarta tace Barr Faruk rayuwarka kawai nakeji ba wai abinda zai faru da ni ba, ina ma ace Ammi zata taimaka taku'butar da kai.



Ana gama wad'annan shari'o'in megabatar da k'ara yamik'e yace sai shari'ar da takasance ta k'arshe a wannan ranar itace shari'ar Jawahir Muhammad Maikud'i wadda ake zargi da yin kisa na mutane d'aid'aya har mutum bakwai, inda dangin mamatan suka shigar da k'ara,, sannan yaje yamik'a ma alk'ali file d'in,
kotun kacamewa tayi da surutu saida alk'ali yad'an buga tebirinshi sannan akayi tsit,


Duk'awa yayi yafara duba file d'in ya d'auki lokaci yana dubawa sannan yad'ago yace kotu tana buk'atar ganin Jawahir wadda ake k'ara ta bayyana a gabanta.

Police d'in matan nan ne guda biyu suka fito da ita tatsaya a wajen da ake tsayawa, me karanta k'ara yace ya me girma me shari'a wannan itace Jawahir.
'Dago kai alk'ali yayi yakalleta nan yashaidata sannan yacigaba da cewa kotu tana son ganin lauyan masu k'ara da na wadda ake k'ara.

Barr MB ne yamik'e yayi sallama sannan yace sunana Barr Mahamud Bello nine lauyan masu k'ara,, sannan yakoma yazauna.

Shuru babu wanda yasake mik'ewa daga cikin lauyoyin, Barr Junaid dafe kanshi yayi tare da runtse idanunshi saboda tsananin tashin hankalin rashin abokinshi dan shi kanshi shara'ar da sukayi ta maimuna ya san ya yi k'ok'ari sosai a yadda ya iya yinta saboda tashin hankalin da yake ciki.
Me gabatar da k'ara ganin babu wanda yamik'e daga cikinsu yasa yak'ara cewa kotu tana son ganin lauyan wadda ake k'ara.

Jawahir idanu tazuba ma lauyoyin lokaci guda tasafke idanunta k'asa dan ta san babu lauyanta a ciki.

Me gabatar da k'ara ne yasake maimaitawa nan Barr MB yamik'e yakalli alk'ali yace ya me girma ne shara'a lauyan wadda ake k'ara ya gudu saboda baida bayanan da zai kare wadda ake k'ara da su.
Karaf a kunnuwan Barr Junaid lokaci guda yamik'e a harzuk'e yace k'arya ne ya me girma me shara'a lauyanta ba guduwa yayi ba akwai dalili me k'arfi da yahana bayyanarshi, kallon Barr Mb yayi yace ya kamata kadinga gyara kalamanka sannan yakoma yazauna.

Barr MB d'an rissinawa yayi sannan yakoma shima yazauna.

Alk'ali da yake kallonsu bayan sun zauna ne yace shin ko akwai wanda lauyan wadda ake k'ara yawakilta a cikinku?
Su duka shuru sukayi nan yasake cewa ko akwai wanda zai kare wadda ake k'ara?
Nan ma shuru.

Dan haka yaduk'a yayi 'yan rubuce rubucenshi sannan yad'ago yakalli jawahir yace Malama Jawahir kamar dai yadda shari'ar tamu ta baya takasance tsawon shekara d'aya har yau kin kasa amsa laifukanki akan zargin da akeyi maki shin ko a yau zaki iya kare kanki kafin kotu tazartas da hukunci na k'arshe?

'Dago kanta tayi takalli alk'ali sannan tamaida idanunta ga d'unbin jama'ar da suke zaune wajen kowa idanunshi akanta suna jira suji abinda zata fad'a, karaf idanunta suka safka akan mutum biyu.
Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan murmushin mugunta suka sakar mata.
Idanu tazuba masu bata ko k'yaftawa musamman ma Alhaji Sufyan nan hawaye suka fara gangarowa daga cikin idanunta, tana ji kamar taje tashak'esu

Alk'ali sake maimaita mata tambayar yayi ammah bata ma san yana yi ba, saida police d'in wajen suka d'an ta'bota sannan tadawo hayyacinta.

Ganin bata ce komai ba yasa alk'ali yace shin ko Lauyan masu k'ara yana da k'wak'k'warar shaidar da zata ida bayyanar ma kotu cewa jawahir ce tayi kisan?

Mik'ewa Barr MB yayi yace tabbas ina da ita ya me girma me shara'a inaso kotu taban dama ind'anyi ma jawahir wasu 'yan tambayoyi.
Dama alk'ali yabashi nan yawuce yanufi inda jawahir take tsaye....



_____****______


Barr Faruk hankalinshi atashe yake a ranar duk k'ok'arin da yayi dan yakwance kanshi kasawa yayi yana nan zaune inda aka d'aureshi idanunshi suna a kan agogo har k'arfe tara da rabi tabuga, kallonsu yayi yaga suna zaune su biyu dan sauran ukkun basunan sun fita tare da ogansu gashi wad'anda sukafi rashin mutuncin ne suke zaune babu damar yarok'esu, runtse idanunshi yayi ahankali yace kiyi hak'uri Jawahir banda yadda zanyi in ceceki wannan itace k'addararki saidai ina maki fatan Allah yatseratar da ke,,, bud'e k'ofar da akayine yasa yai saurin bud'e idanunshi sai ganin d'aya daga cikinsune yashigo d'auke da takeaway, sauran yaji sunce ya dai bahbah wani abu aka kawo mana?
Zuwa yayi ya ajiye masu kowa takeaway guda yace wani aiki ne mukayi da oga yau mun samu kud'i sosai cikin kud'in ne yace ink'ara siyo mana breakfast tunda bamu k'oshiba, su dukansu dariya sukasa sukace dakyau, nan yakoma yazauna kusa da su, su kuma suka d'auka suka fara ci, Barr Faruk yana kallonsu suka ci abincinsu shi ko ba'ayi mashi ko tayi ba.
Faruk wasu irin hawaye ne masu gumi suka gangaro mashi saboda tsananin tausayin halin da Jawahir zata shiga yau, runtse idanunshi yayi yana cigaba da yi mata addu'a a cikin zuciyarshi.
Jin su yayi shuru dan haka yabud'e idanunshi sai gani yayi mutane biyu daga cikinsu sun hankad'e kai saman kujera suna bacci inda d'ayan yake zaune yana kallonshi.
Mamakine yakamashi cikin ranshi yace daga gama cin abinci sai bacci.

Bai ankaraba kawai sai gani yayi babu mutumin a wajen, mamakine ya ida kamashi yace ikon Allah ina mutumin nan yayi?

Murya ce yajiyo a bayanshi me firgitarwa wadda sautinta tacika d'akin gabad'aya yaji ance "barka da wannan lokacin Barr Faruk"
Yunk'urin waigawa yayi dan yaga me magana ammah yakasa saboda d'aurin da akayi mashi.

Ji yayi anbushe da wata irin mahaukaciyar dariya wadda tasa saida yad'an firgita, muryarce yaji tana cewa wannan aikina ne Barrister.
Dakewa yayi yace wanene nan? Ko ma wanene yabayyana min kanshi!! Shuru yaji nan yasake maimaitawa nan ma shuru dan haka yatabbatar da babu kowa d'akin.
Runtse idanunshi yayi tare da safke ajiyar zuciya.




**** *****

Barr MB kallonta yayi yace Malama Jawahir a iya binciken da mukayi mun gane cewa kin kashe Alhaji Mu'azu da 'ya'yanshi biyu wanda d'aya daga cikinsu mijine a gareki kinyi kisan ba dan komai ba sai dan kawai kina so kigaje dukiyar da ke gareshi.
Da mamaki tajuyo takalli Barr MB, bai damu da mamaki da yagani a fuskarta ba yacigaba da cewa, a lokacin da aka tuntu'bi Megadin ku ya bada shedar cewa daman kin dad'e kina yunk'urin kashe yayan mahaifin naki da shi da iyalanshi wannan dalilin ne yasa itama me aikin gidanku tagudu takoma garinsu saboda tsoron gargad'in da kika ta'ba yi masu a lokacin da suka ta'ba ganinki kin nufi d'akin kawun naki da wuk'a a hannunki lokacin yana bacci zaki kasheshi sai gashi 'yar aikin ta shigo ta ganki, a dalilin haka tatsorata takoma gidansu sannan shima megadinku bayan ankamaki da muka samu wannan bayanin daga wajenshi mun sake nemanshi dan musamu k'arin bayani ammah ya tsorata ya gudu ya koma garinsu chan Marad'i, shin ko zaki k'aryata wannan?

Baki tasaki tana kallonshi ganin yadda yake ta zubo mata k'arya.
Ganin batace komai ba yasa yacigaba da cewa sannan su kuma abokan mahaifinki kin kashesu ne saboda dalilin kun siyar masu da companynku wanda saboda karayar arzik'i yasa kuka rabu da shi shine daga baya kika dinga kashesu saboda kisamu kimaido companyn a hannunki, wannan bayanin mun sameshi a wajen sauran wad'anda suke da hannu wajen sayen companyn.....


Wata irin k'ara jawahir tasaki takai hannu cikin zafin nama tashak'e mashi wuya tace wallahi k'arya kake min, meyasa zakayi min k'arya.

Idanuwanshi waje sukayi saboda zafin mak'ara nan yafara neman yak'wace kanshi, police ne suka 'ban'bareshi daga hannunta alk'ali yace yakamata kisan a inda kike nan kotu ne ya zama dole kidinga ladabi.
Barr MB mik'a ma alk'ali takardun hannunshi yayi nan ya amsa yaduba sannan yad'ago yakalleta yace ga shaidar siyar da company da kukayi wanda a yanzu yake mallakin mutum biyu sannan ga duk bayani akan kisan da kikayi ko zaki iya kare kanki a gaban kotu me adalci?
Wasu sabbin hawaye ne suka gangaro mata tayi saurin runtse idanunta, Alk'ali sake maimaita mata yayi, ahankali tagirgiza kai alamun a'a.
Buga table Alk'ali yayi yace tunda bakida shedar da zaki kare kanki kotu ta yanke maki hukuncin.....tun kan alk'ali ya ida fad'a Jawahir tasulale tazauna k'asa d'irshen tare da fashewa da kuka dan ta san kisane kawai zai biyo baya gashi bata cika burinta ba.......







_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:15 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 20*

K'ofar Kotun ce aka turo da k'arfi aka shigo wanda hakan yaja hankalin duk mutanen da suke cikin kotun suka juya dan ganin wanda zai shigo, shima kanshi Alk'ali bai ida fad'in hukuncin da yayanke ma Jawhir ba, wanda yabud'e k'ofar ne yashigo inda daga bayanshi sukaji murya ana cewa Ya Megirma me shara'a kar ayanke mata hukunci na zo da hujjoji masu k'arfi da zan bayyana ma kotu wanda zaisa agane batada laifi acikin kisan da akayi.


Jawahir na jin muryarshi saurin d'ago kai tayi tana kallonshi cike da mamaki, sanye yake cikin kayan aiki shi da nakusa da shi watau Barr Nas.

Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan saurin mik'ewa sukayi tsaye mamaki duk ya bayyana a fuskarsu k'arara sukace kai daga ina kake ya akayi kazo nan?

Kallonsu Barr Faruk yayi yai murmushi sannan yataka yanufi wajen alk'ali yana cewa agafarceni ya me girma me shari'a.
Alk'ali gyara zaman farin glass d'inshi yayi sannan yace watau sai yanzu kaga damar zuwa, kotu zakayi ma wasa da hankali bayan a farko baka zo ba saida kotu zata zartas da hukunci sannan.

Matsowa yayi yace agafarceni ya me girma me shara'a babban daliline yahanani zuwa wanda idan kabani dama nagabatar da hujjata zan sanar da kotu dalilin.

Jinjina kai Alk'ali yayi yace kotu ta baka dama, kowa yakoma yazauna.

Nan duk aka zauna, Jawahir mik'ewa tayi tsaye daga duk'en da take tana kallonshi, shima kallonta yayi sannan yamaida kallonshi ga Alk'ali yace Allah yagafarta malam nagode sosai, a yau zan gabatar da shedun da natattara akan zargin da akeyi ma Jawahir ammah kafin nan inaso kotu tafara bani dama infara tattaunawa da wadda ake k'ara.
Alk'ali yace ta baka dama.
Juyawa yayi ga jawahir sannan yace shin malama jawahir ko zaki taimaka kifad'a ma kotu yadda kike da Alhaji Mu'azu da su Alhaji Tanimu?
Shuru tayi tana kallonshi, nuni yayi mata alamun tayi magana sannan tace Eh Alhaji Mu'azu yayan mahaifina ne su kuma abokan mahaifina ne bayan rasuwarshi suka koma tare da yayan mahaifin nawa.
Jinjina kai yayi yace dakyau sannan yajuya ga alk'ali yace Allah yagafarta malam hujjata ta farko da zan fara gabatarwa itace Marigayi Alhaji Mu'azu da Abokan mahaifinta su takwas kenan sunyi amfani da damarsu sun kashe mahaifinta da mahaifiyarta dan sugaje dukiyarshi ban fad'i hakan ba saida natabbatar da shedata.
Kotun ce tafara kacamewa da hayaniya jin abinda yafito daga bakin Barr Faruk, saida aka nutsar da mutane sukayi shuru.
Juyawa Faruk yayi yakalli k'ofa yace kushigo.
Wani buzu ne yashigo nad'e da rawani a kanshi sai wata dattijuwa tana tura wata mata a saman wheelchair, jawahir idanu tazuba ma matar ahankali tace Ummah, matar ma kallonta tayi nan hawaye suka gangaro mata.

Barr Faruk ne yanuna buzun yace wannan shine megadin gidan Alhaji Mu'azu wannan kuma uwar d'akinshi ce.

Alk'ali d'agowa yayi yakallesu sannan yace ma megadin kotu tanaso kafad'a mata gaskiya akan abinda kasani a game da gidan Alhaji Mu'azu.

'Dage kanshi sama yayi yace eh zan fad'i gaskiya ni nine megadin shi kuma wannan yarinya tun bayan mutuwar iyayenta Alhaji yake azabtar da ita yana cin dukiyarta shi da abokanshi, akwai wata rana ina zaune a wajen gate ina sauraren radio Alhaji yafito zai shiga mota yafita nan naji yana waya yana cewa zai san hanyar da zaibi yafito da ita suje banki yasa taciro mashi kud'i daga account d'in mahaifinta, toh bayan nan na ta'ba jin suna magana da wani abokinshi yana cewa zai siyar mashi da wani gida da yagano k'anen nashi yana da shi baisan da gidan ba sai bayan mutuwar d'an uwan nashi, sannan a game da mutuwar d'an uwan nashi a ranar da aka shigo aka kasheshi Alhaji Mu'azu najiyo yana magana da wasu a waje ban dai ji abinda yake cewa ba saidai na ji ya ce masu ga makullin gidan nan, toh kuma da makullin aka bud'e gidan aka shigo aka kasheshi, d'aga hannunshi yayi sama yace wallahi wannan shine abinda nasani banyi maku k'arya ba.
Alk'ali jinjina kai yayi sannan yaduk'a yacigaba da rubuce rubucenshi yace Barrister muna saurarenka.
Faruk juyawa yayi ga Ummah yace Hajiya munaso kifad'a ma kotu matsayinki a wajen Alhaji Mu'azu da duk abinda kika sani akan kisanshi.

Goge hawayen fuskarta tayi tare da motsa 'bari d'ayan jikinta da yake da lafiya sannan murya chan k'asa tafara magana ganin haka yasa aka d'auko mata lasifika aka kanga wajen bakinta fara jawabi tayi tace nice matar Alhaji Mu'azu kamar yadda kotu taso zan fad'a mata gaskiya maganar gaskiya tabbas ni da mijina mun cutawa yarinyar nan kuma ya ci dukiyarta wannan shine abinda nasani sannan itace takasheshi da 'ya'yana biyuuuuu, kyarma tafara yi tana jijjiga nan wasu nurse guda biyu sukayo saurin zuwa wajenta dan dama tare da su sukazo, alk'ali yabada izini afita da ita amaidata asibiti nan suka tafi da ita.

Barr MB me yamik'e a fusace yace ya megirma me shari'a ya kamata kotu tagaggauta hukunta lauyan wadda ake k'ara akan zuwa da yayi har asibiti yazo da marar lafiya wanda a halin yanzu ya ja ta shiga wani hali, wannan ba daidai bane.
Alk'ali d'agowa yayi yace Barr MB yace koma kazauna, komawa yayi cikin sanyin jiki yazauna


Barr Faruk cigaba yayi da cewa shedata ta gaba da zan bada itace Marigayi Alhaji Mu'azu da Abokan mahaifinta su takwas sunyi amfani da damarsu sun kashe mahaifinta da mahaifiyarta dan sugaje dukiyarshi ban fad'i hakan ba saida natabbatar da shedata, wayarshi yad'auko yakunno recording d'in duk maganganun da yatura na wayar da su Alhaji Mu'azu yayi da abokanshi d'aya bayan d'aya yakunna ma alk'ali yasaurara, gabad'aya kotun tayi tsit ana saurare, akan lokacin da suke had'a plan zasu kashe Alhaji muhammad da kuma kisan da sukayi ma mahaifiyar jawahir sannan wajen ciro kud'i dan su mallaki dukiyarta duk ya saurara

Alhaji Mansur ne yayi saurin mik'ewa yace wannan k'arya ne sharrinshi ne kawai.

Kallonshi

Please Login or Register in order to submit comment