Reading FANSAR RAI complete 1&2 BY SIS NERJA'ART Chapter 41 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

biyar saboda sunansu da Alhaji Mu'azu yake ambata a cikin wayar saidai mutum biyu ne bai ganeba toh ammah su wanene? Shin suna raye ko su ma ankashesu? Kanshi ne yajefa ma tambayoyin.

Kasa runtsawa yayi dan kwatakwata daman bai sa ma ranshi yin bacci a lokacin ba nan yayi kwance yana ta 'yan tunane tunane tare da neman hanyar da zai 'bullo wajen ganin ya kamashi da laifin da yake zarginshi da shi, tashi yayi yad'auko wayarshi yana tura duk recording d'in da yake so masu alak'a da case d'in ya dad'e yana turawa dan suna da yawa sosai saida yaza'bi iya wanda yakeso, a cikin kunnuwanshi akayi kiran sallar asuba.


Wajen k'arfe goma yagama shirin shi yaje wajen aiki kasancewar litinin ce yana zaune yana aikinshi nan aka kirashi a waya dubawa yayi ganin private number ne yasa yashare baiyi picking ba wani kiran yasake shigowa a karo na biyu, tsaki yayi sannan yad'auko wayar zai kashe ta gabad'aya dan kar tahanashi yin aikinshi sai kuma yafasa yayi picking batare da yayi magana ba.
Daga chan 'bangaren akace Hello kana ji?
Shuru yayi yana sauraren muryar kamar ya ta'ba jinta k'ara jefo mashi tambaya akayi "wai ko ba Barr Faruk bane"
Saurin d'ago wayar yayi daga kunnenshi yadanna inda zatayi mashi recording d'in maganar sannan yace Hello ina ji.
Au daman kana ji shine zakayi shuru watau har rainin hankalinka ya kai ga haka,,, tsaki yaji anja sannan aka kashe wayar.

Bai damu da hakan ba ya ajiye wayar yacigaba da aikinshi.


Saida yatashi daga aiki sannan yaje yasamu Jawahir tana ganinshi murmushi tasakar mashi tace ina tayaka murna.
Shima murmushin yayi yace murnar me kenan?

"yanayinka da nagani ya sa na gane ka samo wayar"
Matsowa yayi kusa da ita yace Eh hakane na samo kuma duk na saurara saidai mafi yawansu sun mutu dan naji maganarsu da sunan su da aka kira acikin recording d'in.

Fara'ar da take fuskarta ce tagushe tace tabbas hakane duk sun mutu dan dama mutane takwas ne kuma a yanzu shidda daga cikinsu sun mutu, Yaya Aliyu baya cikinsu kawai dai Ammi ta d'auki fansar kasheta da yake da hannu a ciki da kuma niyarshi ta ganin bayana, Mijina Umar ma baya da hannu a ciki, su Abba da abokanshi ne.

Jinjina kai yayi yace na fahimci haka Jawahir saidai akwai wani taimako da nakeso kiyi min.
Taimako kuma? Wane irin taimako ne?,, tajefa mashi tambaya.
"Kar kidamu yanzu zan sanar da ke koma menene.....



_____________


Bayan kwana biyu Faruk yana kwance a d'akinshi Mom tashigo tasameshi zama tayi daga gefenshi tace ya dai Faruk ba dai tunani kake ba?
Murmushi yayi tare da tashi zaune yace No Momcy bacci natashi ne.
Ohk, ina fatan babu wata matsala.
Kallon Mom d'in tashi yayi cike da k'aunarta dan ya san bata son ganinshi cikin kowace irin matsala, girgiza kai yayi yace babu komai Momcy.
Yauwa haka nakeson ji da anjima idan zaka fita zan baka sak'o kabiya kakaima Hajiya Maijidda.

Da mamaki yake kallonta yace Hajiya Maijidda kuma?
Cikin nuna rashin damuwa tace Eh ita tunda kai bakayi da 'yarta wannan ba zai sa mu mudaina zumunci ba dan ka san matsayinta a wajena.
Murmushi yayi yace toh Ammi babu damuwa ai yanzu ma zan watsa ruwa infita sai ma kawai infara zuwa gidan.

Hmm ka ji da shi kana so kana kaiwa kasuwa nasan dai kana son ganin Nasiba ne.
Kallon mahaifiyar tashi kawai yake batare d ya ce komai ba.
Nan tamik'e tace idan kafito sai kasameni a part d'ina ka amshi sak'on.
Toh Mom.




Wajen k'arfe biyar ya isa gidansu Nasiba yana shigar da motarshi cikin gate d'in gidan daidai lokacin Nasiba tacinno kan tata motar, da mamaki take kallon motar Faruk cikin ranta taji wani irin sanyi har ta ayyana ko ya dawo gareta, murmushi tayi tace inko hakane zanyi farin ciki sosai, duba fuskarta tayi ta cikin mirror d'in motar taga fes take sannan tabud'e tafita.

Faruk yana yin parking zaune yayi cikin motar sai a lokacin yafara tunanin ta yadda zai iya shiga yakai ma Hajiyar Nasiba sak'o da tun chan baya baiyi tunanin haka ba ko da ya san hakan yana da nasaba da son ganin sanyin idaniyarshi da yakwana biyu baisakata a idanunshi ba, zaune yayi yana kallonta har tafito daga motar tajingine a jikin motar tana kallon tashi motar.

Ganin haka yasa yabud'e yafito hannunshi rik'e da sak'on Mom, tsayawa yayi yana kallonta shima da manyan idanuwanshi su dukansu kowa yana ayyana abu acikin zuciyarshi chan sai Faruk yataka yanufi wajen da take.
Har ya isa bata daina kallonshi ba, sallama yayi mata sai a lokacin tajanye idanunta daga kallonshi tasadda kanta k'asa sannan ta amsa mashi ahankali.
Murmushi yayi yana jin wani irin dad'i a ranshi, muryarta yaji ta gaisheshi, nan ya amsa, daga haka kuma duk sukayi shuru still dai idanunshi suna a kanta gani yayi ta d'an rame, ya shagala da kallonta ita kuma jira kawai take yafad'a mata ya dawo gareta bakinta d'auke da murmushi jin shuru har lokacin bai ce mata komai ba yasa tad'an d'ago tasaci kallonshi karaf suka had'a idanu.

Dabarbarcewa yayi yace am Nasiba daman Mom ce tabani sak'o inkawo ma Hajiya ban saniba ko tana ciki.
Saurin ida d'ago kai tayi takalleshi nan k'wallah tacika idanun cikin ranta tace ashe daman ba dawowa yayi gareni ba, ahakali tabud'e baki cikin murya me kama da ta kuka tace kashiga tana ciki.
Tsaye yayi yana kallonta shi kanshi baiji dad'in hakan ba ko bakomai ai ya kamata ace sun gaisa, cikin k'arfin hali yace Nasiba ina fatan kina lafiya?
'Daga mashi kai tayi alamun Eh.
Ajiyar zuciya yasafke yace ammah na ga kin d'an rame saisa nayi tunanin ko bakida lafiya.
Hawayen da suka taru cikin idanunta ne suka zubo, cikin zuciyarta tace lallai ma Faruk watau tambaya yake ko banda lafiya bayan ciwon da yabar min acikin zuciyata, girgiza kai tayi tace a'a kawai dai...sai kuma tayi shuru.
Kawai dai me?
Memakon tabashi amsa sai cewa tayi kaima naga ka d'an rame ko duk aikin ne?
K'ayataccen murmushin shi me tsada yasakar mata sannan yace ko d'aya lafiya ta lau saidai kece kad'ai damuwata.

Ji tayi kamar a mafarki yafad'a mata haka shi kanshi saida yaga tsantsan mamaki a tattare da fuskarta, saurin sa hannu tayi tagoge hawayen da suke fita tace anya Faruk hakane ba kawai ka fad'a min bane? Na tabbata da ace kana sona da bazaka ta'ba banzatar da ni ba.
No Nasiba ko d'aya ban banzatar da ke ba kawai dai banda yadda zanyi ne saboda Daddynki ammah ni ko a yanzu yajanye k'udurinshi..
Tarar numfashinshi tayi tace ammah dai Faruk wannan bai dace yazama hujjar da zaka iya hak'ura da ni ba kaidai kawai kace min ka daina sona, bayan ka dasa min ciwon da har yanzu ya kasa warkewa a cikin zuciyata.
K'ara matsowa yayi saitin fuskarta yace Nasiba da sannu zani dawo gareki kikwantar da hankalinki.
'Dan guntun murmushi tayi sannan tace wane lokaci ne wannan ko har sai na bar duniya?
Please kidaina wannan maganar bazaki mutu ba insha Allahu nan da 'yan kwanaki kad'an zan dawo gareki, kallon k'ofar gidansu yayi sannan yace kinga amsa inbaki kishigar ma Mummy da shi.
Wani irin dad'i taji akan maganarshi ko bakomai yanzu ta tabbatar Faruk zai dawo gareta, kasa 'boye farin cikinta tayi har saida yabayyana, tace dagaske kake Faruk?
Maido kallonshi yayi akan fuskarta sannan yace insha Allahu Nasiba dan bana ji zan iya cigaba da rayuwa batare da ke ba, nasan Daddynki yana nan bazan shiga gidan ku ba dan banso muhad'u dan Allah ki amsa kikai mata.

Kallon motocin da suke wajen tayi taga dukkansu suna nan dan haka ta san tabbas Daddy yana gida, bata musaba ta amshi ledar.
Murmushi yayi yace yauwa na gode, nan yajuya zai tafi, bud'e baki tayi kamar zatayi magana sai kuma tafasa.
Ja yayi yatsaya tare da juyowa yakalleta yace please Nasiba akwai wani d'an taimakon da nakeso kiyi min.
Murmushi tayi tace toh ba damuwa, menene kakeso ko ma menene kafad'a zanyi maka.
Rasa yadda zai ce mata yayi dan bayaso tazargi wani abu, ganin ya yi shuru yasa tace kai nake sauraro.
Am daman dan Allah Number d'in Alhaji Mansur nakeso kisamo min a wajen Daddynki ammah dan Allah kar kibari yagane ni zaki ba.
Murmushi tayi tace indai wannan ne kar kadamu zan samo maka.
Shima murmushin yasakar mata yace Nagode sosai My Wife to be sai na jiki.
Wayyo farin ciki tsantsa Nasiba tashiga batasan lokacin da tamaimaita kalmar ba, nan yajuya yafara tafiya, ji take kamar tatsaidashi ammah takasa.
Shi kanshi wani irin dad'i yake ji ko bakomai ya ba idanunshi abincin shi, ko da ya san ya yi k'ok'ari sosai wajen controlling kanshi bai nuna mata irin yadda yadamu sosai d'innan ba, ko da ya san k'asan zuciyarshi shi kanshi ciwone da baida magani indai ba ya ga anmallaka mashi Sanyin idaniyar shi ba.

Yana isa wajen motarshi har ya bud'e zai shiga yajuyo yakalleta yasakar mata lallausan murmushi itama maida mashi martani tayi sannan tanufi cikin gida.


Tana shiga dagudu tanufi hanyar part d'in Mummy tana k'wala mata kira, ja tayi tatsaya a parlor lokacin da tagansu zaune ita da Daddynta,
Daddyne yace Nasiba wannan irin kira haka me yafaru? Ko ta samu ne?
Murmushi tayi tace bakomai Daddy.
Yace ke dai fad'amin shalele ko ansamo mana wani sabon siriki?
Kunya ce takamata tayi saurin mik'a ma Hajiya Maijidda ledar da Faruk yabata tace Hajiyata ga sak'onki sannan tajuya dagudu tanufi part d'inta.

Ba Daddy ba hatta Hajiya maijidda saida tadara, duba ledar tayi ganin sak'on Hajiyar Faruk ne yasa tayi murmushi tace watau yau ta had'u da abin k'aunarta saisa tashiga farin ciki, har ta bud'e baki zata sanar da mijin nata dalilin farin cikin d'iyar tasu nan wayarshi tafara ruri, mik'ewa yayi yafita yana cewa ganinan zuwa.

Nasiba tana shiga d'akinta saman gadonta tafad'a tare da jawo pillow tarungume a k'irjinta fuskarta tana d'auke da k'ayataccen murmishin da tunda taga Faruk take fitar da shi, ahankali tace nagode faruk tabbas a yanzu na tabbatar zaka dawo gareni, lumshe idanunta tayi tare da k'ara matse pillown a k'irjinta tana jin farin cikin da rabon da taji irinshi tun lokacin da aka fasa baikonsu da Faruk...










_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:14 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 13*

...Nasiba ce zaune a parlon Daddynta da dare ita da iyayen nata suna kallo ammah ita duk hankalinta ba a wajen kallon yakeba tunani kawai take tana neman hanyar da zatabi tasamo number d'in Alhaji Mansur batare da Daddynta ya ganeba, a gefe d'aya kuma tambayar kanta take shin me yasa Faruk yake son tasamo mashi number d'in? Chan kuma a fili tace ko dai akan maganar aurenmu ne yakeso suyi magana.

Muryar Hajiyarta ce taji ta ce lafiya Nasiba kike magana ke kad'ai?
Murmushi tayi dan batasan maganar ta fito fili ba dan ma Allah ya taimaketa ahankali tayita, girgiza kai tayi tace a'a ba magana nakeba Mummy, juyawa tayi takalli Daddynta da hankalinshi yake a kan news d'in da yake kallo gyaran murya tayi tace am Daddy dan Allah ka ara min wayarka.
Juyowa yayi yakalleta yace Nasiba me zakiyi da ita ba dai wayarki babu credit ciki ba?
Girgiza kai tayi tana murmushi tace a'a Daddy Number d'in Yaya Maryam zan d'auka na yi loosing d'in contact d'inta.
Mummy ce tace ai dama sauk'i tunda number ce kikayi loosing ba taki wayar ba.
Turo baki tayi tace kai Mummy ni yaushe rabon da inyada waya anfi shekara biyu.
Daddy ne yamik'a mata wayarshi yace amsa rabu da ita shalele anfad'a mata da da yanzu d'aya ne bataga da bambanci ba.
Amsa Nasiba tayi tana dariya tace Allah Daddy ita Mummy da abu ya wuce sai tadinga tuno ma mutum
Kibarta Shalele na ma kusan canza maki sabuwar waya.
Mummy murmushi tayi tace oho dai na baku zuwa gobe ai sai anji ku indai Nasiba ce.


Fakar idanun iyayenta tayi tashiga cikin contact d'in Daddy tad'auki number d'in Alhaji Mansur sannan tamik'a ma mahaifin nata wayarshi.



Zama tayi na kusan mintuna biyar sanna tayi masu sallama tatashi takoma part d'inta cike da farin ciki, saida tahau saman gado sannan talalubo number d'in Faruk.




A chan 'bangaren Faruk bayan ya gama shirin shi na bacci yana kwance saman gadonshi yana tunanin abar k'aunarshi yana jin wani irin dad'i a ranshi akan had'uwarshi da ita, shi kanshi ya san yana son Nasiba sosai ya yi k'ok'ari sosai da har ya iya danne son nata a yau bai nuna mata ya yi missing d'inta ba, murmushi ne yasu'buce mashi lokacin da yatuno yadda suke nuna ma juna soyayya kafin wannan abun yafaru, lumshe idanunshi yayi ahankali sannan yace Nasiba kina raina a kowane lokaci, yadda kike missing d'ina nima haka nake naki, ina fata akwai lokacin da komai zai zo k'arshe muyi aure.....yana cikin haka wayarshi tafara ringing tashi yayi zaune tare da d'aukota saman bedside ganin Nasiba ce yasa yai murmushi tare da yin picking, daga chan 'bangaren tayi mashi sallama ya amsa nan kuma duk sukayi shuru sai chan kuma takauda shurun ta hanyar cewa ina fata ka koma gida lafiya?
Lafiya lau Nasiba.
Wani irin haushi taji ganin a yanzu wai Faruk ne yake kiranta da sunanta ko dai ya daina sonta ne? Wasu siraran hawaye ne suka gangaro mata cikin sanyin murya tace am daman na kira ne infad'a maka na samo number d'in.
Kai masha Allah na ji dad'i sosai Baby ina fata dai baki bari Daddy yagane ba?
'Dan guntun murmushi tayi cikin ranta tace wai kuma Baby dan na samo mashi abinda yake so, sai kuma chan tace uhm uhm bai gane ba.
Toh shikenan kituro min kinji?
Shuru tayi batace mashi komai ba, sake maimaita mata yayi nan ma shuru.

Ajiyar zuciya yasafke yace Nasiba kiyi hak'uri duk yadda kikeji nima kaina ina ji ba wai na daina sonki bane wallahi ina k'aunarki sosai saidai banda wani za'bi da zan iya hak'ura da case d'innan bayan alk'awali nayi akanshi kuma kema kinsan girman alk'awali.

Fashewa tayi da kuka tace ammah Faruk ka san ina sonka shine karabu da ni..
Katseta yayi yace kidaina cewa haka Nasiba wallahi ko d'aya ban rabu da ke akan son raina ba kuma har yanzu ina nan akan bakana zan dawo gareki a duk lokacin da muka gama shara'ar nan kikwantar da hankalinki kin ji ko?
Rage sautin kukanta tayi tace shikenan Faruk ina nan ina jiranka dan Allah kar kabarni.
Murmushi yayi yace kar kidamu da sannu zan baki mamaki dan banaso aja lokacin bikkin mu, nidai fatana kidaure kicire duk wata damuwa a ranki kikwantar da hankalinki sannan kidaina kirana a waya kar parents d'inki sugane har yanzu muna tare ransu ya'bace kibari mubi komai a sannu Nasiba.

Cikin jin dad'in kalamanshi tace toh shikenan Hearty duk yadda kakeso haka za'ayi.
Lumshe idanunshi yayi tare da sakin murmushi sannan chan k'asan mak'oshinshi yace kece rayuwata zan kasance da ke akowane lokaci acikin zuciyata, kikwanta kiyi bacci.
Ita kanta lumshe idanunta tayi tana fitar da murmushi me sauti "Nagode sosai Hearty hak'ik'a nayi farin ciki da jin kalmar nan a yau zanyi baccin da rabon da inyi irinshi tun muna tare shikenan sai dasafe.
Sallama sukayi suka kashe wayar kusan a tare suka manna wayoyinsu a bisa k'irjinsu suna murmushin farin ciki, kowa na jin soyayyar d'an uwanshi tana fizgarshi.


Chan Faruk yaji shigowar text yad'aga wayar yana dubawa sai ganin number d'in Alhaji Mansur yayi ta turo mashi.

Murmushin jin dad'i yayi cikin ranshi yace kin gama min komai My Life, nan yatura mata " Thanks my wife to be insha Allah, Good Nyt, kiyi bacci me dad'i.

A karo na biyu tasake lumshe idanunta cikin jin dad'i tace Night too My Everlasting,,, tana manne da wayar a k'irjinta a haka tayi bacci.


Achan 'bangaren Faruk tashi yayi yagama duk abinda zaiyi sannan yakoma yakwanta.


Washe gari yana zaune a parlorn d'akinshi yana kallon kwallo inda a saman d'an teburin da yake gaban kujerar da yake zaune fruit salad ne yana sha, sai wajen k'arfe sha d'aya yagama kallon yamik'e yad'auko wayarshi da yajona charge yakoma inda yake zaune kasancewar ranar bazaije wajen aiki ba, Number d'in Alhaji Mansur yalalubo yakira, har saida takusan tsinkewa sannan akayi picking, sallama yayi daga chan 'bangaren Alhaji mansur ya amsa a dak'ile tare da tambayar wanene.
Faruk bai damu da yanayin da ya amsa shi ba yace am Barr Faruk ne daman na kira ne intambayeka dan Allah in ba damuwa ina zan sameka dan akwai magana me muhimmanci da zamuyi.
Tun kan yarufe baki yaji muryar Alhaji Mansur cikin fad'a yana cewa babu wata magana me muhimmanci indai ba janyewa kayiba kabari aka kashe yarinyar chan kamar yadda takashe wasu.
Murmushi Faruk yayi dan yanayin yadda yayi maganar ta so tabashi dariya ammah yadanne sannan yace koma menene kaban dama muhad'u sai mutattauna.

Toh shikenan zan turo maka adress d'in Guest House d'ina sai kazo kasameni.
Cikin jin dad'i Barr Faruk yace toh shikenan sai na jika,,, bai jira jin abinda zai ce ba yakashe wayar tare da saving d'in recording d'in da yayi,
gudar wayarshi yad'auko yakunna muryar da yake tunani ta Alhaji Mansur ce yasake saurare tabbas ya ida gasgatarwa da tashin ce, yana nan zaune sai ga message ya shigo wayarshi yana dubawa yaga Alhaji Mansur ne, murmushi yayi yace dakyau haka nakeso nan yamik'e yashige bedroom d'inshi bai dad'eba yafito hannunshi rik'e da key d'in motarshi fuskarnan ya dad'eta da bak'in glass d'aukar wayoyinshi yayi yafita yabar gidan.



Yana isa k'ofar gate d'in gidan duk security's suka taso suka nufo wajen motarshi ganin haka yasa yagane bazasu barshi yashiga ba nan suka fara tambayarshi me yazo yi? batare da ya basu amsaba yad'auko wayarshi yakira Alhaji Mansur yana yin picking yace gani a k'ofar gidanka wad'annan k'attin da katara sun hanani shigowa.
Ba su da akace ma k'atti ba hatta shi kanshi Alhaji Mansur ya ji ciwon abun dan de kawai yana so yasan abinda yakawoshi saisa yadanne fushinshi yace basu waya muyi magana.
Mik'ama d'aya daga cikinsu wayar yayi yace oganku yana son magana da ku.
Amsa yayi yakanga a kunne nan sukaji yana cewa ohk sir angama, mik'a ma Barr Faruk wayar yayi sannan yabada umurni aka hangame mashi tank'amemen gate d'in yashigar da motarshi parking yayi yafito nan d'aya daga cikinsu yayi mashi jagora zuwa cikin gidan, Faruk ko kanshi d'aurewa yayi ganin makeken Guest House d'in Alhaji Mansur ahaka har suka isa wani tank'amemen parlor inda Alhaji Mansur d'in yake zaune ya kame sai hura hanci yake.
Sucurity d'in komawa yayi inda Barr Faruk yayi sallama yashiga, amsawar ma cikin tak'ama aka yi mashi, murmushi kawai Faruk yayi yaje yazauna saman kujerar da take opp d'in wadda Alhaji Mansur yake zaune cikin tak'ama yazauna tare da d'aura k'afa d'aya saman d'aya, koda Alhaji Mansur yakalleshi saida yaga ya yi mashi k'warjini, zare glass d'in da yake fuskarshi yayi sannan yace sannu Alhaji.
Cikin isa ya amsa da yauwa ka ce kana son ganina ko?

Murmushi yayi yace Eh saboda inaso ka amsa min wasu tarin tambayoyi da ke gareni.
Da mamaki yake kallonshi yace wane irin tambayoyine haka?
Ta'be baki yayi yace ba wasu tambaboyi bane masu wuya kawai dai akan case d'in mutuwar su Alhaji Muhammad Mai kud'i ne.

Gaban Alhaji Mansur wani irin mummunan fad'uwa yayi yai saurin gyara zaman shi tare da kallon Faruk yace ban fahimceka ba me kake nufi?
Murmushi yayi yace daman bazaka fahimceni ba saidai yanayin yadda kafirgita ya sa na gane ka d'an fahimci wani abu, ammah dai kar kadamu da wannan na san dai Alhaji Muhammad abokinka ne kai da su Alhaji Tanimu toh abin mamakin bayan mutuwarshi kuka koma kuka k'ulla abota da yayanshi Alhaji Mu'azu, saidai hakan baisa kuyi tunanin ko za'a iya zarginku da wani abu ba? Ko ma ace akwai wani abu da kuka shirya ku d'in?

Zumbur Alhaji Mansur yamik'e tsaye cikin fushi yace ban ganeba me kake nufi, wannan ai zancen banza ne ka zo ne daman dan karaina min hankali?

Murmushi yayi a karo na biyu sannan yace kaga Alhaji da ka zauna munyi magana cikin kwanciyar hankali ba sai an jiyo abinda muke tattaunawa ba.

'Daga murya yayi yace kowa yajiyo man ina ruwana, watau ni kake zargi ko kenan?

Shima mik'ewar yayi yace ni ba zarginka nakeba tambayoyi suka kawoni wajenka kuma ya kamata ka amsa min su, shin ya labarin kud'ad'e, gidaje, filayen marigayi Alhaji Muhammad da suke hannunku ko kun ajiyesu ne sai d'iyarshi ta fito daga gidan kaso sannan kumallaka su a wajenta tunda kawunta wanda kuke tayawa ajiyewa ya rasu?


Alhaji Mansur mutuwar tsaye yayi yana kallon Faruk da tsantsan mamaki jin kalaman da suka fito bakinshi bayan babu wanda yasan wannan sirrin sai su kad'ai toh ina yaji hakan?

Yana cikin tunanin yaji muryar Faruk ya cigaba da cewa sannan takardun kamfanin yarinyar chan ya kamata ace kun damk'a mata abunta, filayen da gomnati tasiya ma a wajenku ko tana da alak'a da su?

A fusace cikin d'aga murya yace ya isheka haka Barrister! ya isa!!! Watau ni zakazo kaci ma mutunci dan kawai mahaifin Nasiba ya hanaka auren d'iyarshi ni zaka ja ma sharri? Toh wallahi ya zama dole indamk'a ka a hannun hukuma dan bazan lamunci hakan ba da girmana a gari kanemi kazubar min da shi, duka dukiyar muhammad nawa take da har zamu so mucita kaduba girman Guest house d'ina wanda ko rabin girman gidana bai kai ba shin wannan bai isa yazama shaidaba akan cewa na fishi dukiya? Bazan barkaba dole kotu tashiga ciki,,, wayarshi yad'auko yana shirin lalubo number.

Murmushi Barr Faruk yayi yace kiran wayar da zakayi daidai yake da tona ma kanka asiri, shin zaka iya tuna wata mota sabuwa fil da Alhaji Muhammad yasiya wadda kaci burin kamallaketa Wadda cikin motocinka babu kamar ta? Ko zaka iya tuna wayar da kukayi da Alhaji Mu'azu akan son mallakar dukiyar jawahir da take cikin account d'in mahaifinta?..

Wayar da take hannunshi ce tasu'buce tafad'i nan yafara zufa 'yan cikinshi saida suka kad'a, wuta tad'auke mashi d'if saida yayi kusan minti biyar suna kallon kallo da Barr Faruk sannan yayi k'ok'arin saita kanshi sannan cikin inda-inda yace ina kaji wannan? wanene yafad'a maka hakan?

Tsayawa Barr Faruk yayi yana kallonshi ganin haka yasa Alhaji Mansur yanufoshi a harzuk'e yana cewa tambayarka nake kabani amsa!

Ja yayi da baya yace ka ga kar kamatso min nan ni tambayarka nayi kuma amsa nakeso.

Idanuwan Alhaji Mansur jajir sukayi saboda 'bacin rai cikin fushi yanuna mashi hanya yace fitar min daga gida tun kan insa afitar da kai ta k'arfi, wannan cin fuska ya yi yawa ace katako har cikin gidana kaci min fuska, kai wanene a garin nan da har zakayi min haka?

Ta'be baki yayi cikin nuna rashin damuwa yace na ji zan fita kuma ni ba kowa bane saidai inaso kasani na san abubuwa da dama agame da duk abinda kuka aikata, sannan kashirya zan k'ara dawowa gareka dan neman amsar wad'annan tambayoyin kai har ma da wasu na daban, murmushin gefen baki yayi sannan yace na barka lafiya,,, yana fad'in haka yajuya yafita.


Alhaji Mansur tsaye yayi yakasa ta'buka komai mamaki duk ya gama cikashi nan kuma yafara zagaye d'akin yaje yadawo haka yaitayi cikin ranshi yana tunanin wanene yasanar da Barrister duk wannan to kodai yarinyar chan ce? Toh ammah ita kanta batasan abinda duk muka shiryaba, saidai ya kamata inyi wani abu a nan, komawa yayi yazauna yad'auko wayarshi yalalubo wata number bata dad'e tana ringing ba akayi picking ko

Please Login or Register in order to submit comment