Reading FANSAR RAI complete 1&2 BY SIS NERJA'ART Chapter 28 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a matsayin mata agareni.
'Dago kanta tayi takalleshi tana murmushin jin dad'i tace tabbas nima ina cikin farin ciki sosai da ubangiji yamallaka min kai a matsayin miji agareni ina ji a raina na fi kowace mace dace da samun miji irinka,
shima idanu yazuba mata yana mata wani shu'umin kallo.
Saurin maida kanta tayi takwantar a k'irjinshi nan yashafa bayanta yace Nasiba indai har zaki kula da ni toh ni kuma zan nuna maki cewa babu wata mace a cikin duniyar zuciyar Faruk indai ba ke ba.

Wani irin dad'ine taji sosai dan kalamanshi sun ratsata, ahankali tace inko hakane zan baka kulawa wadda babu namijin da yata'ba samun irinshi, fiye da yadda uwa take son d'anta, zan nuna maka tattalin so da k'auna zallah dan Allah Faruk karik'eni amana.
Bakida damuwa da wannan matata yanzu sai kitashi muje anuna min son da ake min wanda yafi wanda uwa take ma d'anta.
Tun kan yarufe baki tayi saurin d'ago kai ta kalleshi, d'aga mata kira yayi nan taturo baki tace nidai a'a.
Kallon agogo yayi yace tunda dai har kika fad'a ya zama dole in gani a ido domin gani ya kori ji kinga ma yanzu dare ya yi muje kawai malama.

K'walla ce tacika mata idanu tace dan Allah kayi hak'uri kaga fa ban warkeba.
Cak yad'auketa yace ai aikin lada ne zakiyi muje kawai amaryata.
Nasiba ji take kamar tafashe da kuka dan ita kad'ai tasan irin wahalar da tasha hannunshi jiya, a bedroom d'inshi yawuce da ita saidai ji tayi ya safketa saman gadonshi nan shima yahau, cike da tsoro kamar zatayi kuka tace dan Allah kar kayi min komai Allah ciwo nake ji.
Shareta yayi yakashe bedside lamp sannan yajanyota jikinshi yarungume, ahankali cikin kunnenta yarad'a mata cewa kikwantar da hankalinki hearty babu abinda zanyi maki bacci kawai zamuyi dan nima ina tausayinki Allah dai yayi maki albarka domin kin faranta min.
Murmushin jin dad'i tayi nan hankalinta yakwanta tagyara kwanciyarta a cikin kunnenta taji yana rad'a mata kalamai masu ratsa gangar jiki ahaka har bacci yayi awon gaba da ita.



____________

Khausar kallon Jawahir tayi da take kwance ta d'age kai sama tana kallon ceiling tace wai ke sister tunanin me kike tun d'azu.
'Dagowa jawahir tayi takalleta tace ni ba tunani nakeba kawai dai ina tunanin rayuwane.
Uhm ko kuma kina tunanin zuwa Katsina dan na ji kince ma Mom da anyi hutun islamiyya zakije masu hutu.
Cikin sanyin jiki tace Khausar bazanje katsina ba a nan zanyi hutuna tunda hutun sati biyu ne aka bamu.
Kai Sister ammah dai da baki kyauta ba kinga ko bikkin Barrister bakije ba muna jarabawa lokacin, kuma yanzu sai kik'i zuwa kiyi masu Allah yasa alkhairi ko d'an man shanu musha, dan ma naga Barrister yanzu tunda yayi aure tsawon kwana biyu baku gaisaba ko fushi yake da rashin zuwanki bikkinshi.

Jawahir runtse idanunta tayi dan itama kanta abun yana damunta ta yi tunanin dalilin dai rashin zuwanta ne yasa tun ranar d'aurin aure da takirashi tayi mashi Allah yasa alkhairi basu sake wayaba, toh ko dai yana fushin da ni dagaske?

Muryar Khausar taji tana cewa yoh wa yasanar maki sai kikira kitambayeshi.
Shuru tayi bata sake cewa komai ba dan bata d'auka a fili tayi maganar ba.



A ranar da marece tana cikin game da wayarta kiran Faruk yashigo tsayawa tayi tana kallon wayar cike da mamaki cikin ranta tace yau kuma antuna da ni kenan.
Har saida takusan tsinkewa sannan tayi picking tare da yin sallama, daga chan 'bangaren Faruk da yake kwance saman cinyar Nasiba amsa mata yayi tare da cewa k'anwata fushi nake da ke.
Murmushi Jawahir tayi tace kayi hak'uri yayana na san na yi laifi kuma na baka uzurina.
'Dago kai yayi yakalli Nasiba da itama take kallonshi nan suka sakar ma juna murmushi sannan yace anya kuwa uzurin nan naki zai kar'bu bayan bakizo kika ga amaryata ba.
Daga chan 'bangaren Jawahir murmushi tayi tace Allah sarki ni, dan Allah Yayana ayi min hak'uri zan zo.
Nasiba ce tace bazan hak'uraba k'anwata har sai kinzo kin goge laifinki.
Murmushi Jawahir tayi dan ta jiyo abinda tace, Faruk ne yace kindai ji abinda tace ko? Bari ma inbaki ita kuyi magana.
Cikin jin kunya tace a'a Yaya Faruk Allah kunyarta nakeji.
Dariya yayi yace nidai babu ruwana gatanan sai k'anwar lauya tasan yadda zata kare kanta,,, wayar yamik'a Nasiba da take ta dariya.
Itama Jawahir 'yar dariyar tayi jin Nasiba ta yi sallama yasa ta amsa tare da cewa Auntyna ina wuni?
"Uhm bazan amsaba fushi nake"
Marairaicewa tayi tace dan Allah kiyi hak'uri wallahi ina son zuwa lokacin exams muke a islamiyya ammah zan zo.
Toh shikenan k'anwata na kar'bi uzurinki ya dai kamata kizo idan kun gama dan ga d'aki nan mun ware nakine kinga sai kiyi mana hutun nan kafin akoma.
Dariya Jawahir tayi tace d'aki kuma Auntyna.
Eh man mu dai muna jiranki.
Faruk ne yace kibarta hearty idan tayi wasa dakanmu zamuje har chan KEBBI mud'aukota.
Jawahir rage fara'ar fuskarta tayi tace zan zo insha Allahu Yayana ayi hak'uri.
Toh shikenan Jawahir sai kinzo muna godiya sosai.
Bakomai Auntyna nima nagode nan sukayi sallama takashe wayar, ta'be baki tayi ta ajiye wayar sannan tamik'e tafito tsakar gida tasamu Inna Mairo zaune tana cin k'uriga nan itama tazauna gefenta tad'iba tafara ci.


Faruk kallon Nasiba yayi da take rik'e da wayarshi yace k'anwarnan tawa gudun garin nan take na lura da ita bata son zuwa.
Cikin sanyin jiki Nasiba tace wallahi Lovely banga laifinta ba saboda abinda su Daddy sukayi mata basu kyautaba sun cutar da rayuwarta sun rabata da duk wani farin cikinta ni wallahi har kunyarta nakeji,,, k'walla ce tacika mata idanu ganin haka yasa Faruk yace Nasiba haka ubangiji yak'addara babu wanda ya isa yacanza k'addararshi.
Cikin muryar kuka tace kaduba kagani lovely duka yarinyar nan nawa take ammah ace jawarci take.
Kinga Nasiba banaso kiyi min 'barnar hawayenki komai yasamu bawa daga ubangiji ne banason kina shiga damuwa
Goge hawayenta tayi nan Faruk yafara lalla'bata yana lallashinta cikin dabara yasamu yarabata daga damuwar da tashiga.

___∆∆∆∆∆____

Dad kud'ad'e yafitar akayo order d'in duk kayan aikin da ake buk'ata inda yazuba ma'aikata sosai a cikin companyn Jawahir aka fara gudanar da aiki nan da nan company yafara ha'b'bakowa dan shi Dad mutum ne mekula sosai da sanin makamar aiki.



A cikin gidan Kaso su Alhaji Mansur da Alhaji Sufyan aiki ake saka su sosai ana wahalar da su babu wanda zai ce ga matsayinsu a da, sunyi nadamar abinda suka aikata sosai dan basusan rayuwa zata juye masu hakaba gashi gabad'ayansu babu wanda iyalanshi yazo dubashi, sunyi bak'k'i sun rame duk sun fita hayyacinsu kullum cikin aibata junansu suke da da sun sani kuka ko ba'a magana musamman idan suka tuna akwai ranar da ma za'a rabasu da rayuwarsu gabad'ayanta.

****** *******

Jawahir bayan ta dawo daga gidan kitso ganin Baba Malam tayi zaune shi kad'ai a bisa 'yar kujerarshi a k'ofar gida yana sauraren radio, wajenshi tanufa tatsugunna tagaisheshi yace Jawahir har an dawo?.
Eh Baba Malam.
Toh sannunki.
Yauwa Baba.
Ganin yadda tayi yasa yagane akwai magana a bakinta dan haka yace Jawahir kisanar da ni duk abinda yake cikin ranki kar kidamu zan fahimceki.
Ahankali tace am daman Baba wata 'yar alfarmar nake nema a wajenku.
Toh ina saurarenki.
Shuru tayi sai kuma chan tace dan Allah idan ba zan takura maku ba inaso ataimaka asamo min makaranta incigaba da karatuna.
Shuru yayi yana saurarenta ganin daga nan bata sake cewa komai ba yasa yace toh jawahir bazank'i ta takiba ammah da son samune zan fi so ace aure kikayi tunda kinga wanchan mijin naki ya rasu aure shine mutuncinki ammah zaki iya fara karatun kafin Allah yakawo mijin inyaso sai ki ida karatun a gidanki dan ni kinga gaskiya babu d'iyar da nake bari tayi karatu a gidan nan saidai tafara ta ida a gidan mijinta, yanzu haka kinga Khausar da Rashida an tsaida ranar aurensu watanni ukku suka rage ayi bikkin, idan hakan ya yi maki ba matsala.

Jikinta sanyi yayi cikin ranta tace chakwakiya kenan ni ina naga wani manemin aure ni da babu ma aure agabana yanzu na fi son inyi karatu inyaso daga baya idan da rabo zanyi aure.
Ganin ta yi shuru yasa yace Jawahir rayuwarki ta fi had'ari tunda kin ta'ba aure saisa nafison kiyi aure saidai komai lokacine idan Allah ya kawo maki mijin sai ayi auren.
Cike da ladabi tace toh Baba Malam nagode sosai insha Allahu zan kasance me biyayya agareku.
Cikin jin dad'i yace yauwa Jawahir Allah yayi maki albarka.
Amsawa tayi da Ameen tace atashi lafiya sannan tamik'e cikin sanyin jiki tashiga cikin gida, 'bangarensu Khausar tawuce tasameta kwance tana bacci dan haka tafito takoma 'bangarensu.
Tunda tazauna tunanin maganar Baba Malam kawai take wai ya fi son tayi aure ita kuma a yanzu bata shirya ma aureba a tsarin rayuwarta ta fi so tayi karatu tazama wani abu wadda za'ayi alfahari da ita, ammah yanzu taya ma zata iya fara yarda tayi soyayya koda ta san d'an zamanta a garin mutanen da suka dinga zuwa wajenta da sunan so suna da yawa.
Wasu siraran hawaye ne suka gangaro mata ahankali tace Abba kun cuceni duk kune kuka ja min da ace kun barni na cigaba da karatuna da duk hakan bai faru ba, goge hawayen tayi tare da cewa na mik'a ma ubangiji lamurrana domin shi ya fi kowa sanin halin da nake ciki Allah kaza'ba min abinda zaifi zama alkhairi a rayuwata.




******* ********

Faruk da Nasiba soyayyarsu kawai suke sha suna kula da junansu sosai ko da ace Faruk yana wajen aiki tana k'ok'arin kiranshi ko shi yakirata dan kawai suji lafiyar juna.


Faruk yana k'ok'arin zuwa dubo Ummah a asibitin da ake jinyarta har tafara samun sauk'i saidai duk k'ok'arin da suke akanta 'barin jikinta guda ya shanye bata iya komai daga k'arshe ma suka nemi susallameta takoma gida zasu d'aurata akan magani dan bazata ta'ba komawa daidai ba.
Faruk amincewa yayi da hakan nan yasa aka kwashe duk kujeru da kayan d'akin da suje gidansu Jawahir aka kaisu a gidan da taba ummah, gidane madaidaici me d'auke da d'akuna ukku kowane ciki da parlor.

A ranar da aka sallameta gidan yawuce da su itada masu jiyyarta su biyu inda d'aya daga cikinsu yayartace tana aure a chan funtua dan haka suka dawo gidan itada mijinta dan cigaba da kula da 'yar uwartata da a yanzu sai anyi mata komai kamar yadda Faruk yabata shawara.

Ummah kuka tayi sosai lokacin da Faruk yasanar da ita kyautar da Jawahir tayi mata na gidan da mota sai kuma kud'ad'en da tabada abata.
Kuka tadingayi tana cewa kaicona ina ma ace ban zalunci wannan yarinyar ba ko da sau d'aya ban ta'ba kyautata mataba daga ita har mahaifiyarta, yanzu ga shinan yadda rayuwata takoma dan Allah ina zanganta in nemi gafararta.
Faruk yace kar kidamu duk abinda Jawahir tayi maki cancantane yasa hakan sannan zuciyar jawahir mekyau ce akowane lokaci tana da burin kyautata ma mutane kidaina sa damuwa a ranki kinji dai abinda likita yace kafin kubaro asibiti.
Motsa 'barin jikinta me lafiya tayi tace dole inyi kuka Faruk dan na cutar da yarinyar nan fiye da tunanin wani me tunani sai gashi rayuwa ta juya min na rasa komai nawa a yanzu itace take taimakona dan tarufa min asiri.

Lallashinta suka dinga yi tayi shuru nan Faruk yadamk'a masu komai sannan yasa aka kawo masu kayan abinci sosai wanda yafitar da kud'inshi yasiyesu dan kawai saboda su.
Haka suka dinga yi mashi godiya suna shi mashi albarka har yatafi.


*BAYAN WATA UKKU*

Nasiba ce tafito daga kitchen d'auke da Cup a hannunta jikinta sanye cikin kayan bacci tanufi d'akin Faruk, tana shiga zaune yake ya d'aura laptop a saman cinyarshi yana wani aiki, daga gefenshi tazauna tace wash sannu lovely.
Batare da ya kalletaba yace kema sannunki hearty.
Hmm kaine da sannu kaida tun d'azu kake faman aiki yauwa lovely dan Allah akwai maganar da nakeso muyi da kai.
Janye laptop d'in yayi tare da janyota yad'aura bisa cinyarshi sannan yace ina saurarenki hearty wace magana kikeson muyi?
Murmushi tayi tamik'a mashi cup d'in da tashigo da shi tace toh kasha wannan kajik'a mak'oshinka sannan muyi maganar.
Amsa yayi bai musaba yasha saida yashanye kunun ayar da takawo mashi tas sannan yace toh ina saurarenki.
Kwantar da kanta tayi a k'irjinshi sannan cikin sanyin murya tace dan Allah Lovely kataimaka muje Kebbi wajen Jawahir muganota ko da wuni guda ne tunda ita har yau bata lek'o mu ba.
Jan hancinta yayi yace kedai baki gajiya, toh ai ita yakamata tazo taganki.
'Bata fuska tayi kamar zatayi kuka tace dan Allah Lovely kataimaka muje mu ai sai mukwashe ladar zumuncin.
Hmm tunda kince haka shikenan kibari sai weekend sannan muje wuni guda mudawo.
Rungumeshi tayi tace nagode sosai Lovely Allah yasaka da alkhairi, ai kam saidai kawai mubata mamaki dan bama zata san zamuje ba.
Hamma yafara yace kinga tashi muje mukwanta dan ni nan na gaji aikin ma bazan ida shi ba sai zuwa gobe.
Shagwa'be fuska tayi tace toh saidai kad'aukeni muje.
Cicci'barta yayi yace toh ya zanyi ai dole inyi yadda kikeso amaryata.
Dariya tayi tace a'a ni yanzu ba amarya bace ai na kwana biyu.
Baice mata komai ba saida yadireta saman gado sannan yace toh ke micece?
Maimakon tabashi amsa sai ma juyawa da tayi tana murmushi dan haka shima yakwanta daga bayanta tare da kashe masu haske.....






_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:21 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 25*

Ana saura kwana ukku suje Kebbi Nasiba tamatsa mashi suka je gidan su Dad, sunyi farin ciki da zuwansu nan Mom tadinga nan nan da ita dan tana son Nasiba sosai, a chan suka wuni sai dare sannan Faruk yaje zai d'akkota.

Suna a parlor zaune suna hira ita da Mom nan Faruk yakalleta yace sutafi dare ya yi.

Amsawa tayi da toh sannan tace Ammah kafin mutafi ina son zamuyi wata magana da su Mom daman tun d'azu naso yinta sai kuma naga Dad ya fita.
Muryarshi sukaji ya ce toh gani na dawo me za'a fad'a min
Su duka juyawa sukayi suka kalleshi sukai murmushi Mom tace ashe kana kusa.
Shima murmushin yayi yace Eh wallahi wani meeting ne yatsaida ni saisa kuka ji ni shuru har wannan lokacin ban dawo ba.
Sannu da zuwa sukayi mashi nan yashigo yazauna yana cewa wace magana ce d'iyartawa takeson yi da mu?

Faruk kallonta yayi yai murmushi sannan yamaida kallonshi ga iyayenshi yace wai maganar zuwan da zamuyi Kebbi zata fad'a maku batasan munyi maganar ba.
Eh toh kusan itace ammah ba ita bace.

Mom tace toh shikenan d'iyata fad'a mana fatana dai ba matsala bace kuka fara samu da mijin naki?
Duk'ar da kanta tayi cikin nutsuwa tace Mom Dad dan Allah alfarma nake nema wadda na san wajenku ne kawai zan iya nemanta.
Da mamaki suke kallonta sukace wace irin alfarma ce Nasiba kifad'i kowace irice insha Allahu zaki sameta.
Shuru tayi na d'an lokaci sai kuma chan tace dan Allah so nike kurok'ar man Faruk ya auri Jawahir.

Su duka idanu suka zuba mata mamaki k'arara a fuskarsu, Faruk ne yayi k'arfin halin cewa Nasiba wannan wace irin magana ce kikeyi kinsan abinda kike fad'a kuwa?
'Dagowa tayi takalleshi idanu cike da k'walla tace tabbas na san abinda nake fad'a Faruk ina son kataimaka ka auri Jawahir domin ko bakomai ta cancanci hakan ya kamata muyi duba da rayuwarta ita d'in yarinya ce me k'arancin shekaru tana buk'atar auren miji wanda zai bata kulawa sosai wanda zatayi farin cikin kasancewa da shi a matsayinta na marainiya na tabbata kaine kad'ai zata iya aura tasamu wannan gatan domin kai ka san halin da take ciki zaka tausaya ma rayuwarta.
Mom ce tayi k'arfin halin cewa keko Nasiba miyasa kikayi wannan maganar har kikeso mijinki yak'ara aure?
Hawaye ne suka gangaro daga idanunta tace Mom banaso inkasance mace me son kanta dayawa na san ina son Faruk kuma ina da kishi saidai ina ji a raina kamar idan Jawahir bata auri Faruk ba banyi ma kaina adalci ba domin shine kad'ai namijin da yadace ya aureta.
Wani irin kallo yawurga mata yace kar kisake wannan maganar kitashi mutafi gida tunda bani nace maki ina buk'atar k'ara aureba kuma duka wata nawa da yin bikkinmu har zaki wani ce ink'ara aure sannan Jawahir da kike gani matsayin k'anwa take a wajena ba wai sonta nake ba.

Had'e hannuwanta tayi waje guda alamun rok'o tace dan Allah Faruk kar kak'i amincewa da auren Jawahir wallahi na amince zan zauna da ita da zuciya d'aya domin ita d'in zuciyarta mekyau ce, shin ni idan nice zan so ace wani nawa ya fad'a irin halin da Jawahir take ciki? Ya kamata kayi tunani rayuwarta tana buk'atar tallafi duk yadda zataji dad'in zama a wajen kakanninta bazai ta'ba kai zaman da zakayi da ita ba domin na tabbata zaka bata duk kulawar da tadace, na maka alk'awali zamuyi zaman lafiya da ita zamu kasance abun koyi ga duk sauran mata har ayi alfahari da mu,,
Kasa cemata komai yayi saidai kallon mamaki da yakeyi mata.

Juyawa tayi takalli Mom da Dad tace dan Allah ina rok'onku kusa baki a ciki Dad na san ku zaku fahimci abinda nake nufi wannan dalilin ne yasa ban ta'ba mashi maganar ba sai yau da muke zaune a gabanku wallahi tun kan muyi aure da Faruk nasa ma raina ba zan ta'ba zama ni kad'ai da shi ba zai kasance mijinmu ni da Jawahir domin wannan shine adalcin rayuwa ko bakomai mahaifina yana cikin mutanen da suka ruguza mata duk wani farin ciki nata, dan Allah Dad kutaimaka kufahimci abinda nake nufi.

Jinjina kai Dad yayi yace tabbas Nasiba ke mace ce me adalci kinsan abinda yakamata, banyi niyar shiga cikin maganar nan ba na fiso kuje kuyi shawara a tsakaninku idan shi ya amince zai aureta to mu bamuda matsala yadda duk kuka tsara daidai ne ko Hajiya?.
Mom da take kallon Nasiba cike da mamaki d'aga kai tayi tace hakane Alhaji suyi shawara a tsakaninsu kawai zai fi.
Fashewa da kuka Nasiba tayi tace dan Allah Dad kutaimaka kusa baki a ciki na tabbata kune kad'ai zakuyi mashi magana yasaurareku wallahi idan har bai auri Jawahir ba banyi ma rayuwata adalci ba ta rasa mijinta a lokacin da take buk'atar shi kuma duk ta silar su mahaifina dan Allah na rok'eku Mom kuce wani abu.
Ganin yadda take kuka yasa su dukansu suka ji tausayinta Dad yace kidaina kuka hakanan Nasiba, sannan yamaida kallonshi ga Faruk da yahad'e fuska idanunshi suna a kan waya yana dannawa kamar baisan abinda ake tattaunawaba Dad yace toh kai Faruk ka ji abinda matarka tace tana neman wannan alfarmar.
'Dagowa yayi yakalli mahaifin nashi yace Dad ni fa ban da burin auren mata biyu.
Duk da haka Faruk tunda matarka ce tanemi kayi auren sai kataimaka kayi bare ko bakomai Jawahir ta cancanci ka aureta.

Ammah Dad duka aurenmu fa wata ukku da yinshi.
Toh ai ba matsala bane.

Faruk juyawa yayi yakalli mahaifiyarshi da jikinta yayi sanyi sosai nan tad'aga mashi kai alamun Eh.
Duk'ar da kanshi yayi k'asa yama rasa abida zaice ganin iyayen nashi duk sun goya ma maganar Nasiba baya.

Nasiba idanu tazuba mashi tana jira taji abinda zai ce har lokacin hawaye basu daina fita daga idanunta ba.

Jin ya yi shuru yasa Dad yace kai muke saurare Faruk.
Sai da yayi kusan minti ukku sannan yace shikenan na amince.

Saurin rik'oshi Nasiba tayi tace dagaske ka amince zaka aureta?
Harararta yayi yace tunda kun nuna kuna son hakan.
Janye hannunta tayi daga rik'on da tayi mashi cikin sanyin jiki tace dan Allah kar kayi duba da abinda mukeso kataimaka kaima kaso auren a cikin ranka insha Allahu zakayi alfahari da mu.
Toh wai Nasiba ita d'in Jawahir tace maki batada wanda take so?
Jim tayi sannan tace na tabbata insha Allahu bata da shi.
Jinjina kai yayi yace shikenan ammah da sharad'i guda idan dai har tana da wanda takeso dole mubarta ta aureshi,,, Cewar Faruk.

Tace toh shikenan na yarda da wannan.
Dad da Mom dai idanu suka zuba masu suna kallonsu cikin ransu suna jinjina ma k'ok'arin Nasiba dakanta take neman mijinta yak'ara aure wanda itama d'in basu dad'e da yin auren ba.

Nasiba godiya tayi mashi sannan tajuya tayi ma su Mom su ma godiya.
Addu'a su Dad suka dinga yi mata dan tabbas sunsan d'an nasu ya yi dacen mata dan samun irinsu Nasiba a yanzu sai an tona, mik'ewa Faruk yayi yai ma su Dad sallama sannan yace kisameni waje ina jiranki.
Itama mik'ewar tayi tai masu sallama sannan tabi bayan Faruk da tuni ya yi gaba.


Suna fita Mom kallon Dad tayi tace oh Alhaji kaga ikon Allah wallahi Nasiba yarinyar kirki ce ta san abinda yakamata.
Jinjina kai Dad yayi yace ai kedai bari gaskiya Nasiba ta yi kuma nima kaina na ji dad'in hakan da tayi dan tuni nayi ma Faruk sha'awar auren Jawahir dan nasan zasu dace kuma ko bakomai shi zai kula da maraicinta.
Ammah Alhaji yanzu kana ganin shi Faruk d'in zai aureta kalli fa yadda yanuna baya sonta.
Murmushi Dad yayi yace Hajiya kibarni da shi kawai.
Mom tace toh shikenan Alhaji Allah dai yatabbatar mana da alkhairi.
Amsawa yayi da Ameen.



Tunda suka shiga mota suka kama hanyar gida Faruk shuru yayi Nasiba ko ganin yadda yad'auke kai yasa tayi shuru dan ta san fushi yake da ita.

Suna isa gida d'akinta tawuce, zama tayi bakin gado tadafe kanta nan wasu siraran hawaye suka gangaro mata saurin gogesu tayi tamik'e taje tayi wanka tai shirin kwanciya sannan tafito tanufi part d'in Faruk.
Tana shiga tasameshi kwance murmushi tayi tace Lovely har ka kwanta kenan?
Shuru yayi nan tataka ta isa wajen gadon takwanta daga bayanshi tana kwanciya yakai hannu yakashe hasken d'akin.
Matsowa tayi kusa da shi cikin sanyin murya tace Lovely dan Allah kayi hak'uri idan har abinda nayi ya 'bata maka rai wallahi banyi hakan da wata manufaba nayi ne saboda hakan shine dacewa.
Muryarshi taji ya ce Nasiba a wajenki ne hakan yake dacewa watau shine zaki d'auki maganar da kika tsara kije kifad'a ma iyayena koda ace ni bana da ra'ayin hakan ke tunda kinaso dole kenan inyi ke awajenki hakan kin min adalci.

Fashewa tayi da kukan da tun tuni yake cinta ammah tadanne shi sai a lokacin tasamu damar yin shi, cikin kuka tace dan Allah Faruk kayi hak'uri banyi hakan saboda son zuciya ba, nayi ne kawai saboda ina tsoron alhakin abinda mahaifina yayi mata yahau kanmu banda kwanciyar hankali a duk lokacin da natuna mahaifinmu ya bamu munci da hak'in wata ya suturtamu da hak'in wata ya salwantar da ran wasu, dan Allah Faruk kataimaka ka auri Jawahir ba dan halinaba na san kai mutumin kirki ne kuma me fahimta zaka fahimci abinda nake nufi dan Allah kayi min wannan taimakon ko da ace shine taimako na k'arshe da zakayi min a duniya, na maka alk'awali zamu zauna lafiya tamkar 'yan uwan juna please Faruk kataima min,,, nan tasake fashewa da wani sabon kukan.

Wani irin tausayinta ne yad'arsu a ran Faruk, juyowa yayi yafuskanci inda take tare da rungumota jikinshi cikin lallashi yace Nasiba kidaina kukan nan bana so kinsan dai banason jin kukanki, shikenan na amince zan aureta ammah da sharad'i d'aya.
Saurin d'agowa tayi takalleshi tace wane irin sharad'ine dan Allah kafad'a min insha Allahu zan kiyaye.
Idanu yazuba mata yana kallon cikin idanuwanta sannan yace sharad'in shine idan har Jawahir tana da wanda takeso dole kijanye daga k'udurin nan dan bazan ta'ba amince ma aurenta ba idan tana son wani na daban domin gudun kar incutar da ita.
'Daga kai tayi tace ba damuwa na amince da wannan sharad'in.
Gyara mata kwanciya yayi a jikinshi yace toh shikenan yanzu muyi bacci dan ni bacci nake ji.
Toh nagode sosai Lovely Allah yasaka da alkhairi Allah yabarmu tare.
Amsawa yayi da Ameen daga nan kuma babu wanda yak'ara cewa komai daga cikinsu kowa da abinda yake tunani a cikin ranshi.


***********
Ranar juma'a Faruk yakira Baba Nura

Please Login or Register in order to submit comment