Reading FANSAR RAI complete 1&2 BY SIS NERJA'ART Chapter 27 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yakawoka inma biyoni kayi kaimin wani wulak'ancin toh babu damuwa bismillah kayi zan iya jurewa saboda duk abinda yafaru laifina ne nice namallaka zuciyata ga wanda bai damu da ita ba, zan iya hak'ura Faruk ko da ace zan rasa rayuwata bazan sake matsa maka ba domin na san bakada laifi a ciki duk abinda yafaru na san mahaifinane yaja min.

Jikin Faruk sanyi yayi sosai yace Nasiba ko d'aya banzo dan inci mutuncinki ba saidai na zone dan inbaki hak'uri sannan inmaido martabar soyayyata.
Da mamaki take kallonshi tana so tayi magana ammah takasa.

Ganin haka yasa Faruk yayi murmushi yace inbanda abun Nasiba taya za'ayi tayi tunanin Faruk zai iya daina sonta bayan ya riga da ya mallaka mata zuciyarshi, Nasiba ina sonki da zuciya d'aya kamar yadda kike sona wallahi nayi maki hakane dan kema kid'and'ani bak'in cikin da kika d'and'ana min a lokacin da kika nisantar da kanki agareni, bana ji zan iya daina sonki Nasiba domin kece Rayuwata.


Wasu irin hawaye ne suka gangaro a fuskarta muryarta tana rawa tace dagaske kake Faruk? Dagaske kana sona zaka aureni?
'Daga kai yayi yace sosai ma indai ba kece kika daina sona ba, ammah a yanzu haka a shirye nake idan kikace inturo sai inturo ayi maganar aurenmu.
'Daga hannunta tayi sama tace Allah nagode maka da kamaido min masoyina, kallonta tamaida ga Faruk tace wallahi bazan iya daina sonka ba Faruk na riga na gama mallaka maka zuciyata idan nabarka taya zan iya son wani.

Ajiyar zuciya yasafke tare da furta Alhamdulillah na yi farin ciki da jin haka daga gareki Nasiba, nima bazan iya son wata ba dan kin riga kin mamaye gabad'aya zuciyata, yanzu dai ina fatan za'a yafe min sannan acigaba da bani kulawa kamar da, komai yawuce mucigaba da nuna ma juna soyayya har zuwa aurenmu.

Murmushi tayi cikin jin dad'in maganarshi tace insha Allahu Faruk na yi maka alk'awalin haka zan cigaba da baka kulawa har k'arshen rayuwata wallahi bakaji farin cikin da kasaka ni ba a yau ji nake kamar a mafarki kadawo gareni.

Su duka dariya sukayi Faruk yace duk farin cikin da zaki shiga na fiki Nasiba yanzu dai kiyi min iso wajen Mummy inshiga mugaisa yau dai zan cire kunya in nemi aurenki dakaina inyaso idan nakoma gida sai insanar da su Dad su kuma su ida nasu.

Wayyoo kar kuso kuga farin ciki wajen Nasiba rasa inda zata sa kanta tayi, haka tanufi hanyar cikin gida tana shiga da gudu ta isa parlor tana k'wala ma Mummy kira, su duka suka d'ago suna kallonta.
Kusa da mummy tazauna cike da farin ciki tace Mummy Faruk ne yazo ya ce zai shigo yanzu kugaisa.

Su duka farin ciki suka nuna nan Mummy tace taje tace yashigo.
Mik'ewa tayi tafita cikin sauri suka bita da idanu, mummy tace kungani ko ai nasan suna k'aunar junansu sosai shima bazai iya barinta ba sai ya biyota.

Su Aunty Sadiya sukace lallai kam ga alama nan mungani.


Tana fita tasanar da shi sak'on Mummy sannan tafad'a mashi batada lafiya, a tare suka jero suka shigo gidan bakinshi d'auke da sallama yashiga parlorn suka amsa mashi har zai zauna a k'asa Mummy tace a'a kar yasaki yazauna yahau kujera dan haka yazauna saman kujera d'an zamowa yayi yagaisheta ta amsa nan yayi mata ya jiki sannan suka gaisa da su Yaya Sadiya da suke zaune gefenta.

Nasiba ko baki k'in rufuwa yayi haka tafita tafara had'a mashi kayan motsa baki.

Mummy ce cikin k'arfin hali tace dan Allah Faruk kayi hak'uri da abinda yafaru wallahi ba da saninmu bane Alhaji yake aikata wad'annan mugayen halayyar daga ni har 'ya'yana babu wanda yasan haka sai daga baya ashe su ne suka saceka dan Allah kayi hak'uri kar kadubemu da laifin da bamu muka aikata ba.

'Dago kai yayi yakalleta cike da girmamawa yace kod'aya Mummy bana kalkonku da laifin da ba naku bane ai laifin wani baya ta'ba shafar wani nima kaina banyi hakan dan in tozartasu ba saidai nayi ne dan intseratar da yarinyar da aka zalunta sannan daga baya ake shirin ganin anrabata da rayuwarta.

Mummy tace hakane na san haka Faruk wannan dalilin ne yasa na k'ara son Nasiba takasance mata ga miji irinka domin ka cancanci asoka ko dan saboda gaskiyarka.

Su yaya Sadiya sukace hakane muma muna k'ara bada hak'uri Faruk.
Murmushin jin dad'i yayi yace bakomai nagode sosai, daidai lokacin Nasiba tashigo d'auke da k'aton tray ta ajiye gabanshi nan duk suka mik'e zasu bar wajen yace Mummy daman magana nakeso muyi da ke.
Toh Faruk kagama sannan sai muyi maganar.
Kanshi sadde k'asa yace wallahi mummy Alhamdulillah daga gida nake.
Komawa tayi tazauna tace nan ma gidan ne ban yarda ba sai ka ci.
Kallon Nasiba yayi da tatsiyaya mashi lemu a cup tamik'o mashi nan ya amsa tare da sakar mata lallausan murmushi itama tamaida mashi da martani.

Kur'ba yayi ya ajiye sannan yaduk'ar da kanshi k'asa yace daman Mummy akan maganar auren Nasiba ne idan anban dama sai insanar da su Dad inyaso cikin satin nan atsaida rana.

Mummy kallon Nasiba tayi nan Nasiba tamik'e cikin jin kunya tawuce sumi sumi tabar wajen tana ji kamar tanutse saboda kunya.

Murmushi Mummy tayi tace haba Faruk wannan ai abun farin ciki ne agaremu ba damuwa kasanar da su Alhaji kawai akowane lokaci mu ai ashirye muke.
Godiya yayi mata tace bakomai Faruk ai mune da godiya dan kai d'in mutum ne wallahi, dan Allah katayamu godiya a wajen Jawahir akan taimakon da tayi mana kaduba kaga yadda tamaido mana gidan da yake mallakinta da dukiya.
Murmushi yayi yace ai cancanta ce tasa haka mummy kuma ku ai bakuda laifi a ciki saisa itama ta ga dacewar maido maku kayanku.
Jinjina kai tayi tace Allah dai yasaka da alkgairi.
Amsawa yayi da Ameen sannan yamik'e yace Mummy bari inwuce.
Tun yanzu? Baka dai ci komai ba.
Allah mummy a k'oshe nake ne.
Toh shikenan Faruk mungode sosai Allah yasaka da alkhairi dan Allah kagaishe min da Hajiya Nuratu kafin ink'ara samun k'arfin jiki inshigo.
Toh Mummy insha Allahu zata ji.


Yana fita tak'wala ma Nasiba kira nan tafito tabishi a wajen mota tasameshi nan sukayi bankwana kasancewar magrib ta yi nan yaimata alk'awalin kiranta da dare.
Haka suka rabu kowa zuciyarshi fal da farin ciki........









_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:21 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 24*

A ranar farin ciki ne fal acikin ran Faruk da dare tunda suka zauna yin dinner Mom da Dad suna lura da shi da bakinshi yak'i rufuwa saboda farin ciki, su dukansu shuru sukayi suna jira suji ya fad'a masu dalilin farin cikin da yake yi.

Bayan sun gama dinner ne yakalli iyayen nashi yace Dad Mom daman akwai maganar da nakeso muyi da ku.
Su duka sukace toh muna saurarenka.
Sosa kai yayi cikin jin kunya sannan yace daman Mummynsu Nasiba ce tace inturo ayi maganar aurenmu.

Dad kallon Mom yayi takalleshi suka bushe da dariya yace Daman Nuratu ban fad'a makiba kurabu da shi dakanshi zai koma sushirya kansu.
Murmushi Mom tayi tace ai gashinan yanzun na gani daman ban tsaya 'bata lokacina ba wajen yi mashi fad'a.
Toh ai yanzu gashinan dai kin gani dan nasan wannan soyayyar tasu ta riga ta gama bin jinin jikinsu dan ma dai d'an nan naki ya cika taurin kai, ammah dai yanzu shikenan Faruk fad'i yaushe kakeso aje nema maka auren?

'Dago kai yayi cikin jin kunya yace ni Dad?
Uhm hum muna saurarenka.
Duk'ar da kanshi yayi ahankali yace cikin satin nan.
Su dukansu sunji dad'in hakan da yace sukace toh shikenan babu damuwa insha Allah nan da kwana biyu zasu tura a tsaida ranar aure kawai.
Cike da farin ciki yace nagode sosai Mom and Dad Allah yasaka da alkhairi, Allah yak'ara girma.
Sukace Ameen.
A karo na biyu suka tambayeshi ko wata nawa yakeso asa bikkin.
Mik'ewa yayi tsaye saida yafara tafiya sannan yace kar yawuce wata biyu please,,, yana fad'in haka yawuce cikin sauri yanufi part d'inshi, muryar Dad ce yajiyo yana cewa kar kasamu damuwa yadda kakeso haka za'ayi Son.

Yana shiga d'akinshi wanka yayi yai shirin kwanciya sannan yakira Nasiba a waya da itama tun bayan tafiyarshi bakinta yak'i rufuwa saboda farin ciki nan hankalin mahaifiyarta da 'yan uwanta yakwanta dan a yanzu sun gane duk Faruk ne dalilin damuwarta ba wai rashin mahaifinsu kawai ba.


Hira suka sha sosai a waya a nan ne yake sanar da ita yadda sukayi da su Dad nan itama tayi ta murna, soyayya suka sha sosai sai da dare yaraba tsaka sannan sukayi bankwana suka kwanta tare da yi ma juna alk'awalin had'uwa gobe.


Bayan kwana biyu Dad yasanar da su Malam da Su Aunty Kilima nan abokan Dad su ukku da d'an uwanshi sukaje suka nema ma Faruk auren Nasiba a wajen wani k'anen mahaifinta Malam sulaiman mutumin kirkine sosai nan ya amince aka tsaida rana nan da wata biyu masu zuwa.

Haka aka koma aka fara shirye shiryen aure inda Faruk yak'ara gyara gidanshi da zai tare da amaryarshi nan da wata biyu.



A chan 'bangaren Jawahir hankalinta ya kwanta sosai zamanta a wajen dangin mahaifiyarta dan tana samun kulawa yadda yadace gabad'ayansu kowa nan nan yake da ita dan haka tasaki ranta kud'ad'e tafiddo daga account d'inta dayawa taraba biyu taba kakanninta rabi sauran rabin kuma taraba ma yayyen mahaifiyartata sukaita mata godiya inda motar tabarta da sunan duk wanda zai fita yana iya d'auka yafita da ita ammah yayyen mahaifiyartata basu amimce da hakan ba su dakansu suka koya mata mota dan tadinga tuk'awa dakanta.
Khausar d'iyar Baba Musa itace tsararta dan haka suka k'ulla abota sosai Jawahir tana sonta saboda sunan mahaifiyarta gareta islamiyyarsu aka sata nan tafara karatu hankali kwance inda a cikin zuciyarta taci burin cigaba da karatunta na high institution.
A 'bangare guda kuma suna waya da Faruk da su Mom dan kusan kullum sai sun gaisa, a wajen Mom ne take jin labarin sa ranar auren Faruk nan tayi Allah yasa alkhairi, abun ya tsaya mata a rai sosai koda suka gama waya da Mom kiran Faruk tayi lokacin yana wajen aiki ya yi busy dayawa bai d'agaba saida yagama aikinshi sannan yakirata a waya, lokacin tana kwance suna kallo ganin me kiran yasa tatashi zaune tare da yin picking tayi sallama.
Amsa mata Faruk yayi yace k'anwata ina fata kina lafiya.
K'walla ce tacika mata idanu tace Yaya Faruk shine har akayi maka baiko tsawon sati biyu ammah baka fad'a min ba hakan da kayi ka kyauta ma k'anwarka?

Ayya k'anwata yi hak'uri wallahi ba haka bane ina ta so infad'a maki mancewa nakeyi.
"Ammah ai kusan kullum muna yin waya kawai dai bakaso kafad'a min ba sai gashi ita Mom ta fad'a min"
Kiyi hak'uri Jawahir ba haka bane ai zan zo.
"Uhm Allah yasa alkhairi kayi zamanka kawai,,, tana fad'in haka takashe wayarta.
Faruk sake kira yayi ammah batayi picking ba murmushi yayi yace lallai ana fushi da ni

Jawahir kasa samun sukuni tayi a ranar ba dan komai ba sai dan abinda Faruk yayi mata su Innah damunta sukayi da tambaya akan abinda yake damunta tace bakomai.
Tun daga ranar indai Faruk zai kirata a waya bata d'agawa koda itama bata jin dad'in hakan da takeyi mashi saidai tana fushi da shi akan abinda yayi mata.


++++++++++++

A 'bangaren Hajiya Maijidda kud'i tafitar sannan tasiyar da k'addarorinta tayo ma d'iyartata order d'in kayan d'aki na gani na fad'a set biyu sannan tasiya mata kayan kitchen dan itace uwa da uba har a lokacin babu wanda yalek'a Alhaji Sufyan daga cikinsu bare susan halin da yake ciki dan su kansu kunyar tunkarar gidan yari suke da sunan sune iyalanshi.



______Wasa wasa haka aka ci wata guda ana saura wata guda bikki Mom taje itada Aunty kilima k'anwar mahaifinsu Mom suka had'o lefe na gani na fad'a akwati goma sha biyu akayi mata anzuba duk wani abu da yadace sannan aka kai lefe.

Su Mummy da danginsu Nasiba sun yaba sosai da irin kayan da aka zubo mata nan suka bada tukaici me tsoka su ma.


* * *
Faruk ganin har lokacin Jawahir bata kulashi ba yasa yashirya ranar wata asabar yaje Kebbi batare da ya sanar da ita ba.
Yana isa yakira Baba Nura yaje yad'auko shi suka nufi gidan.

A waje suka gaisa da Baba Malam sannan suka shiga ciki suka gaisa da Innah a d'akinta yazauna nan takawo mashi fura me sanyi yasha, su Baba Musa duk zuwa sukayi suka gaisa nan aka cika mashi gabanshi da abinci da balango, furar yanark'a sosai dan ta yi mashi dad'i.
Hira sukayi sosai da su Baba Malam da su Baba Nura duk wannan bidirin jawahir tana cikin gida wajen su Khausar batasan abinda ake ba har saida su Faruk sukayo sallar la'asar sannan Baba Nura yashiga cikin gida yasamesu zaune suna hira kallon Jawahir yayi yace kizo kugaisa da bak'o gashichan ya zo tun d'azu.
Bak'o kuma?,,, jawahir tatambaya.
Eh kishiga yana chan 'bangaren su Innah.
Amsawa tayi da toh nan tamik'e tajawo hijab d'inta tasaka, Khausar tace wai wanene yazo?
Oho nima ina sani Baba Nura bai fad'a min ba saidai kitaso muje mugani.

Dariya Khausar tayi tace babu inda zanje dan wannan bak'on da alama na musamman ne lallai garinmu ya amsheki nan da nan anyi mana sabon kamu eyyen ba.
Harara Jawahir tadoka mata tace kinga Khausar kidaina wannan maganar ko kin mance ni matar aure ce.
Ta'be baki khausar tayi tace wallahi ba mecewa haka idan ba ke kika fad'a ba kuma ma auren da babu shi yanzu.

Tsaki Jawahir taja tawuce tatafi batare da ta bata amsaba tana jiyota tana cewa agaishe man da surukin namu ammah tayi shuru.

Tana shiga part d'in inna fuskarta kicin kicin tawuce tanufi inda inna take zaune tace wai inna wanene yazo?
Kishiga ciki man sai kigane ma idanunki.
Jawahir tsayawa tayi cikin ranta tace wallahi indai har wajena akazo zan wulak'anta mutum dan ni samari basu gabana, muryar Inna taji ta ce bazaki shigaba sannan tawuce tashiga.

Tana d'age labule bakinta d'auke da sallama nan sukayi ido biyu da Faruk batasan lokacin da murmushi yasu'buce mataba cikin sauri ta ida shiga d'akin tace lah yaya Faruk kaine kazo ashe shine baka fad'a min ba?
Murmushi yayi yace taya zan fad'a maki bayan k'anwartawa fushi take da yayan nata saisa nazo dan in goge laifina.

Waje tasamu tazauna nan tagaisheshi ya amsa tatambayeshi su Mom yace duk suna lafiya lau.
Amaryar fa ko ma ince Auntyna?
Murmushi yayi yace tana nan lafiya lau itama tana gaisheki, nidai yanzu ayi hak'uri adaina fushin nan da akeyi da ni na amsa laifina insha Allahu bazan sake ba.
Turo baki tayi batare da ta ce komai ba.
Ahankali yace please my k'anwa kiyi hak'uri wallahi na shafa'a ne.
Juyawa tayi gefe guda sannan tace shikenan na hak'ura.
Yauwa kokefa har na ji dad'i ina fata babu wata matsala?
Girgiza kai tayi tace babu.
Ajiyar zuciya yasafke yace toh yanzu yaushe zakizo katsina? Ya kamata kizo kafin bikki dan wata d'aya kinga yarage.
Kicin kicin tayi da fuska tace zan zo sai mun gama exams islamiyya dan next week zamu fara.
Toh menene na had'e fuska? na ji ba damuwa idan kun gama sai azo kinga ayi hidimar bikki k'anwar ango tana kusa.
Murmushi tayi tace hakane yayana.

Faruk janta yayi da hira sukaita yi har wajen k'arfe biyar sannan sukayi sallama kud'i yafiddo sosai yabata yace ta sayi abinda takeso tunda baiyo tsara ba, da dafari har ta k'i amsa tace akwai kud'i a wajenta shareta yayi yabar mata su nan sannan yaje sukayi sallama da su inna da Baba Malam su ma ya ajiye masu kud'i sosai su Yaya Nura ne suka kaishi airport yabi jirgin k'arfe biyar da rabi yakoma katsina.

Jawahir ta yi farin ciki sosai da zuwanshi haka taje talabarta ma khausar zuwan yayan nata da kud'in da yabata dan su Baba Malam taba su k'in amsa sukayi, a wajensu taga invitation d'in Faruk na d'aurin aure nan tayi Allah yasa alkhairi dan daman ya fad'a mata ba'a kaida bugo IV na 'yanmata ba lokacin da yazo saisa bai tafo mata da nata ba, batama yi tunanin anbugo na d'aurin aureba saida taganshi.




*BAYAN SATI UKKU*

Gidajen biyu aka fara hidima sosai inda kud'ad'e aka dinga ruwanu dan ma amarya ta ce ba wani program d'in da zatayi saboda yanayin da suke ciki saidai wa'azi kawai ta amince ayi.

Amarya Nasiba ta sha gyara ta yi gwanin kyau sai salk'i take da kaganta kaga amarya saboda kyaun da tayi na amare.


Ana saura kwana ukku bikki suna zaune a harabar gidansu suna hira da Faruk tace Lovely wai dan Allah Jawahir ta zo garin nan ne?
Girgiza kai yayi yace a'a.
Cike da mamaki take kallonshi tace meyasa toh sai yaushe zata zo? Zata dai halarci bikkinmu ko?
Toh wannan ne ban dai saniba dan ance min suna exams a islamiyya kinga kenan ba damar tazo.
Cikin nuna tausayi tace Allah sarki Jawahir baiwar Allah wallahi yarinyar nan tana bani tausayi gata mutuniyar kirki,, k'walla ce tacika mata idanu tace duk su Daddy sune silar jefata cikin wannan yanayin ta rasa kowa nata wace irin rayuwace wannan, taya zata kasance cikin farin ciki?

Ganin yadda tafara hawaye yasa cikin sanyin jiki yace Nasiba duk abinda kikaga ya samu bawa to daga ubangiji ne babu wanda ya isa yatsallake k'addararshi, kuma a yanzu Jawahir tana rayuwa me dad'i a wajen dangin mahaifiyarta.
Duk da haka Lovely ta yi rashi.
Kinga Nasiba kidaina sa damuwa a ranki Jawahir batada matsalar komai, mubar wannan maganar yanzu kud'in da naturo maki sun isa ko kuna buk'atar k'ari.

Girgiza kai tayi tace bana buk'atar k'ari na wajena sun isheni dan ni ba wani taron da zanyi.
Shikenan rabin ran duk yadda kikeso haka za'ayi.
Murmushi tayi tace nagode sosai Lovely.

Hirarsu suka cigaba da yi cike da shauk'i da k'aunar juna har saida aka fara kiran sallar magrib sannan sukayi sallama yatafi gida.


Ranar alhamis aka gabatar da wa'azi wanda mutane d'aid'ayane suka halarta sakamakon rashin gayyar da amarya tayi ko ma ace ita da danginta sukayi duka abokanta mutum ukku tagayyata sai 'yan uwa, amarya ta yi kyau sosai anyi wa'azi me ratsa jiki inda aka ci aka sha.

Ranar juma'a kuma akayi ma amarya lalle, inda ranar asabar aka d'aura auren faruk Sani Maishadda da amaryarshi Nasiba Sufyan Mai Nasara akan sadaki mafi daraja wanda dubban mutane suka halarci d'aurin auren kasancewarsu 'ya'yan manya yasa aurensu yazagaye cikin garin katsina da gidajen yad'a labarai ko da rabi da kwatan mutanen duk na 'bangaren ango ne dan amarya basu wani yi gayyaba saidai dangi, abokan mahaifinta ma wasu sun halarci d'aurin auren, ango baki k'in rufuwa yayi saboda farin ciki ga jama'a da suka dinga mashi Allah yasa alkhairi su Barr Nas da Barr Junaid manyan abokan ango sin sha babbar riga sune suka dinga haba haba da jama'a.



Gidajen biyu cike suke da jama'a ana ta hidima abunka da bikkin masu kud'i haka aka dinga fiddo naira.

Mutanen Kebbi tun ranar juma'a suka iso Katsina ammah banda su Jawahir da suke jarabawa a islamiyya itama ta so zuwa saidai Exams d'in tahana dan an d'aga masu ita ne da tuni sun gama a lokacin baifi guda hud'u sugama ba, Mom bataji dad'iba koda sukayi waya tace tazauna tayi jarabawarta inyaso idan sun gama sai tazo tayi masu hutu da hakan Jawahir ta mince, saidai takira ango tayi mashi Allah yasa alkhairi.


A 'bangaren Nasiba ta sha kyau har ta gaji dan gyarane ta sha shi saidai da kaganta ka san tana cikin damuwa wanda ba komai yaja hakanba sai tunanin rabuwa da gida da zatayi tafuskanci sabuwar rayuwa, Nasiha iri iri tasha a wajen mahaifiyarta da dangin iyayenta.

Da marece angwaye suka zo da motoci aka d'auki amarya aka kaita a chan gidan angonta da ke chan Goruba Road, gida ne na gani na fad'a dan tun daga tsarin ginin zuwa kayan da aka zuba mashi komai ya ji, shi kanshi Faruk part d'inshi iyayenshi sun tsara mashi sosai dan duk kayan da suke ciki saida aka kwashe aka canza mashi sabbi abunka da d'an gata.

'Yan kawo amarya sunyi santin gidan da tsarinshi inda wasu daga cikinsu suka dinga ma gidan vedio, Nasiba dai tana zaune a tsakiyar royal bed d'inta k'udundune cikin mayafinta inba hawaye ba babu abinda take.

Bayan sallar magrib jama'a suka fara watsewa yarage daga amarya sai yayyenta da k'awarta d'aya me suna Amrah, Amrah aminiyar Nasiba ce tun tashinsu hatta karatunsu tare sukayi a school guda babanta wani hamshak'in me kud'i ne zama a iya cewa yana cikin mak'arraban gwamnati, su suka sake gyara mata gida tas aka kunna turaren wuta.

Sai wajen k'arfe tara su angwaye sukazo tun kafin su shigo su Aunty Sadiya suka sa'be suka tafi aka barta tadinga kuka hatta Amrah tafiya tayi saboda kiran da aka dinga mata a gida.

Nasiba kuka tadinga yi har angwaye suka shigo duk surutan da suka dinga bata ma san abinda suke cewa ba dan hankalinta baya wajensu, Faruk ko rawar jiki yadinga yi yanaso sutafi subar mashi amaryarshi ammah suka k'i saida yaja Barr Nas gefe yace ya kamata yace sutafi hakanan dare yakeyi, shi ko Barr Nas mi zaiyi inba dariya ba koda suka dawo yakalli su Barr Junaid yace toh ku sai kuzo mutafi tun kan ango yabiyomu da ta'barya su dukansu dariya sukayi Barr Junaid yace ai naga alama angon nan ya k'agara mutafi dan ina lura da irin kallon da yake mana, toh arufe mana taro da addu'a kafin muwatse tunda mun rako ango gidanshi lafiya.
Faruk shuru yayi yak'yalesu suka dinga mashi shak'iyanci.

Cikin abokansu ne d'aya daga ciki yayi masu addu'ar zaman lafiya sannan sukayi masu sallama suka tafi Faruk yarakasu saida suka bar gidan sannan yarufe yadawo yasamu amaryarshi a inda yabarta har lokacin k'udundune take cikin mayafi tana sheshek'ar kuka.
Daga gefenta yazauna tare da yin sallama ahankali, jin shuru yasa yakai hannu yayaye mayafin nan tayi saurin runtse idanunta yace haba Hearty miye abun kuka a ciki yau fa ranar farin ciki ce agaremu godiyarmu yakamata mununa ma ubangiji akan wannan ranar da yanuna mana.
Shuru tayi nan yad'ago fuskarta yana goge mata hawaye saida yatabbatar ta daina kukan sannan yasata taje tayi alwallah sukayi sallah bayan sun gama sunyi duk abinda yadace daga nan yafita yakoma part d'inshi dan haka Nasiba tasamu damar yin wanka koda d'ar d'ar kawai take gabanta yana ta fad'uwa tana fitowa tashirya cikin sauri tagama duk abinda zatayi tahaye gadonta takwanta bata dad'e da kwanciya ba taji Faruk ya bud'e k'ofa ya shigo saurin runtse idanu tayi kamar me bacci tana ji yahau gadon yakwanta gefenta muryarshi taji saitin kunnenta yana cewa Hearty ba dai kinyi bacci ba?.
Shuru tayi nan yai murmushi tare da janyota jikinshi yana cewa ban yarda ayi wannan baccinba dan yau ranar farin ciki ne agaremu ya kamata mununa ma juna irin son da muke fad'a muna yi ma juna, shafata yafara yi
Saurin tura kanta tayi cikin k'irjinshi nan yai murmushi tare da kai hannu yakashe bedside lamp daga nan wasa yacanza.....



Washe gari Faruk lalla'bata yadinga yi nan tadinga narke mashi tana zuba shagwa'ba, breakfast daga gidansu Faruk aka aiko masu da shi tun kan sutashi bacci, tare sukayi wanka suka shirya sannan suka fito sukayi breakfast Nasiba tana ta narkewa shi ko sai rawar jiki yakeyi akanta.


A ranar bai lek'a ko k'ofar gida ba yana nan manne da matarshi indai ba masallaci zai je ba, sai magrib sannan yafita nan Nasiba tasamu damar shirya kayanta.


Bayan sallar isha'i Faruk yadawo gida nan sukayi wanka suka yi dinner sannan suka zauna a parlornshi suna kallo, Nasiba manne mashi tayi a jiki inda shi kuma idanunshi suke a lumshe kamar me bacci gabad'ayansu babu ma meyin kallon, fuskarshi taji ya tura cikin gashin kanta tare da k'ara matseta a jikinshi nan itama tak'ara narke mashi, muryarshi taji ahankali kamar me jin bacci yana cewa Hearty ina k'aunarki da dukkan zuciyata tabbas sonki a cikin jinin jikina yake ji nake kamar a mafarki yau nine tare da wadda nafi k'auna

Please Login or Register in order to submit comment