Reading FANSAR RAI complete 1&2 BY SIS NERJA'ART Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

d'akin wucewa Barr Faruk yayi yashiga tsakiyar d'akin yahangeta zaune kanta sadde a k'asa inda gashi yabaje mata fuska tsaye yayi yana kallonta kafin daga bisani yataka ya isa wajen da take tsugunnawa yayi gabanta ganin har lokacin bata d'ago ba yasa yace Jawahir .
Shuru tayi tak'yaleshi kokad'an bata motsaba sake kiran sunanta yayi ahankali tad'ago kai takalleshi ta cikin gashinta da yake baje a fuskarta idanuwanta yakalla da sukayi jajir kamar garwashi inda fuskarta take a tamke babu fara'a ko kad'an wani irin kallo takeyi mashi,
Barr Faruk tsugunne yayi shima yana binta da kallo a karo na ukku yakira sunanta.
Cikin wata irin murya cike da k'araji tace kabar nan wajen!! tana fad'in haka ta sadda kanta k'asa inda gashin ya ida baje mata fuska.
Mik'ewa Barrister yayi cikin sanyin jiki yawuce zai fita dan tabbas baiga alamun zai samu abinda yake son samuba daga gareta saidai me yake faruwa da ita da gabad'aya tacanza anya kuwa mutum ce ita? Sake juyawa yayi yakalleta yaga still dai kanta yana sunkuye dan haka yawuce yafita, tsaye yayi a daidai k'ofar d'akin yana kallonta ta jikin k'arfunan.

Megadin wajen ne yazo yarufe k'ofar sannan yatsaya gefen Barrister Faruk yace 'Dallab'ai daman nasan mawuyacine a wannan irin lokacin ta iya yi maka magana dan lokutta da dama tana shiga cikin wannan yanayin.
Juyowa Barr Faruk yayi yakalleshi yace in ba damuwa inason samun wasu bayanai daga gareka game da ita.
Barr Bilal da yake mak'ale gefe d'aya yace a'a Oga da dai ka hak'ura kawai mun tafi.
Shareshi Barr Faruk yayi yacigaba da cewa duk abinda kasani a game da ita nakeson ji daga gareka.
Jinjina kai megadin yayi sannan yawuce yakoma wajen zamanshi nan Barr Faruk yabi bayanshi kujera yanuna mashi yazauna nan suka fara juyo sautin kukanta Barr Faruk har zai mik'e nan megadin yace a'a Barrister kar kaje dan kusan kullum sai tayi wannan kukan.
Cike da mamaki yake kallonshi yace toh minene dalilinta na kukan?
Girgiza kai yayi yace wannan ne dai ban saniba abinda dai kawai nasani a game da ita shine....



Wannan littafin na kud'i ne ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 Kacal zai turo MTN card ta wannan number d'in 09035938246 ko katuro 200 ta account number d'innan 5330055604 FIDELITY BANK, idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number d'in 09035938246_

_Ga mutanen Niger zasu tura 300f ta wannan number d'in +22794775574_
_Gareku masoyan gaskiya_


_*GARA B'ASA! GARA B'ASA!! GARA B'ASA!!!* wannan gara'basa anyi tane kad'ai ga duk wanda keson karanta littafin *FANSAR RAI* da *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shaharariyar marubuciyar nan watau *AMINA ABBA UMAR* ga duk mai bukatar karanta duka novel's d'in biyu zai biya *N300* kadai domin samun damar karantasu cikin aminci, gareku masoyan gaskiya muna jiran ku nuna mana k'aunarku ta hanyar biyan *N300* kad'ai, idan duka biyun kakeso zaka turo kud'i ta wannan account number d'in 3092292135 FIRST BANK, ko kuma katin waya Mtn na d'aya daga cikin Numbers d'in nan 09035938246 ko kuma 07030792790, ko 07036073670, sai ka aiko da shedar biya ta d'aya daga cikin numbers d'in, sai munji daga gareku masoyanmu_




_Sis Nerja'art✍🏻_
[3/5, 15:59] Sis Nerja'art👰🏻: https://www.facebook.com/105966804349754/posts/105967661016335/?sfnsn=mo

*......FANSAN RAI.......*



_*STORY AND WRITTEN BY SIS NERJA'ART✍🏻*_



*INTELLIGENT WRITERS ASSO....®*
[On Ward Together]


_*DEDICATED TO ZM CHUBA'DO*_


*PAGE THREE*

Tun lokacin da aka kawo ta nan aka rufe a lokacin akwai wasu mata guda biyu masu irin laifinta na kisa an ke'bance su nan su kad'ai aka had'e su d'aki d'aya kasancewar duk wadda zakaga ankawo nan toh ta aikata babban laifi ne wanda za'ayi mata d'aurin rai da rai dan ba'a had'asu da k'ananun masu laifi, tun da aka kawota ban ta6a jin tayi magana da sauran matan biyun da aka had'esu ba dan ina lura da su sosai saidai ita take'be kanta ita kad'ai taraku'be wani lokacin tadinga kuka sosai abinda yafi bani mamaki shine idan dare yayi duk baccin da zanyi infarka sai na ganta zaune idanuwanta suna kallon wacchan yar k'aramar tagar da ke cikin d'akin kafin kaga ta kwanta bacci dawuya, yawanci zakaga ta baza gashin kanta ya rufe mata fuska kamar yadda kashiga kaganta.
sauran matan biyu ganin bata biye masu yasa suka dinga tsangwamarta ammah bata biyesu idan ma aka kawo masu abinci saidai sudauka sucinye subarta bata ta'ba d'aga kai takallesu ba nikuma ganin haka yasa nafad'a ma masu kawo abincin saboda haka ne aka dinga fitar mata da nata daban, akwai wani lokaci da aka kawo masu abinci nan abokan zaman suka cinye nasu daidai ita kuma ta d'auko nata zata ci kawai suka taso suka zo zasu janye Kwanon abincin nata sai tarik'e batare da ta kallesuba ganin haka yasa suka kalli juna suka kwashe da dariya babbar wadda daga ganinta ba alamun imani atare da ita ne tanemi tafizge kwanon da k'arfi ammah sai takasa abun ya basu mamaki ganin da hannu d'aya tarik'e kwanon ammah ta kasa k'wacewa kanta dai yana sunkuye a k'asa a fusace babbar tawanka mata mari.
Ba shiri tad'ago takalleta batare da ta saki kwanon ba ganin batada niyar saki yasa gudar tazo nan suka rufeta da duka suna bugunta ta ko'ina saida mukazo muka janyeta nan aka yi masu bulala akan laifin bugunta da sukayi saidai me wannan bulalar bata shigesuba dan sunji haushin bugun da akayi masu akanta dan haka da dare ma suka k'ara dukanta kafin su kwanta bacci kwanciyar nan da sukayi washe gari ba'a tashi dasuba koda akazo za'a fitar da su wajen aiki me tsanani da ake sakasu nan aka samesu kwance sun mutu ita kuma tana chan zaune k'arshen bango ta had'e kai da gwiwa kowa ya yi mamakin mutuwarsu nan aka fara zargin ko tana da hannu a ciki aka dinga dukanta ana tambayarta tafad'i yadda akayi suka mutu cikin k'araji tace ni ban kashesu ba, cigaba akayi da dukanta saida akayi mata jinajina sannan aka fitar da ita aka yankar mata wani k'aton fili akace tashare ko awa d'aya batayi ana zuwa aka samu wajen fes nan aka bata wanki dayawa akace tayi shima bata d'au lokaci ba aka samu ta gama saboda haka akayi tunanin ko wasu ke tayata dan haka aka tafi da ita kitchen aka bata nik'an markaden da za'a girki tunda tarik'e tafara juya kayan miyar bata tsayaba saida suka nuk'u duk mutanen wajen sukaita mamakin ganin ko alamar gajiya babu tare da ita bayan ak'alla duk rana mutum biyu akesawa sunuka ammah itako ita kadai tayi.

Haka aka dinga bata aiki iri-iri duk dan tafad'i yadda akayi suka mutu ammah tak'i akayi duk binciken da yadace ammah ba'a gane dalilin dayasa suka mutuba kuma babu kwakkwarar shedar da tanuna itace tayi kisan dan haka aka kyaleta, kasan abinda yafi bani mamaki wani lokacin ko da ankawo mata abincin yadda aka ajiyeshi haka ake zuwa a d'auka bata ta'bashi ba kuma anrasa me takeci ni kaina nasha inyi la'be ko naga abincin da takeci ammah ban gani gashi duk yadda zakaso tayi magana batayi inma tayi toh ba wata me tsawo bace,


Akwai wani lokaci da aka fita da ita za'a kaita wajen da zata gana da lauyanta Barr Mubarak ana fita tashak'e wata 'Yar aikin gidan nan da take matsa mata sosai dakyar aka samu aka k'waceta duk kacar da aka d'aureta da ita ammah nema tayi tagudu saboda haka ne aka hana fitowa da ita daga cikin d'akinta akace adinga barinta ko da lauyanta ya zo saidai yashiga yagana da ita a ciki, inba court za'ajeba ba'a fitowa da ita sai yau da naga anfito da ita ankaita ta yi aiki bansan dalilin hakan ba, ammah na fi tunanin dan ma'aikatan suna jin haushin yadda ita ake barinta bata aiki.


Ko kad'an baka ta'ba jin maganarta dan hatta lauyoyinta ma haka zasuzo suyi ta faman mata tambayoyi ammah bata basu amsa daga k'arshe ma duk sai rasasu akayi saboda hakane nafara tunanin anya mutum ce.


Ajiyar zuciya Barr Faruk yasafke tare da juyawa yakalli Ceil din da Jawahir take ciki sannan yamik'e yace nagode sosai Baba kuma ni insha Allahu zanyi k'ok'ari wajen ganin ta bani duk wata amsar da tadace.

A'a Barrister kabi ahankali dan akwai had'ari acikin rayuwarta.
Murmushi yayi yace kar kadamu Nan yajuya suka tafi Barr Bilal yana biye da shi yace barrister ka dai ji Komai da kunnenka ina fata yanzu zaka janye kudurinka nason ganin ka taimaka mata.
Girgiza kai yayi yace ina nan akan bakana zan taimaka mata.
Zaro ido yayi yace zaka taimaka mata? Toh nidai ba da niba dan ba abinda zaisa inshiga rayuwarta.
Tsayawa Barr Faruk yayi yajuyo yakalleshi yace ni zan shiga rayuwarta kuma kaima dole kashiga yana fad'in haka yajuya yawuce yanufi chan wajen motarsu.
Tsaye Barr Bilal yayi yabishi da kallo kafin daga baya yabi bayanshi suka shiga mota suna shirin tafiya wani ma'aikacin gidan yazo suka gaisa da su Barr Faruk yace Oga ya sanar da ni zuwanku ina ta jira ashe har kunzo.
'Dan guntun murmushi Barr Faruk yayi yace Eh munzo ai daman ya fad'a min baya nan toh kuma na kira wayarka ban samuba saidai shi ya yi ma sauran ma'aikatan bayanin zuwana saisa ban samu matsala ba.

Yace Eh ai sun san da zuwanka da abinda zai kawoka dafatan dai ka gama?

Eh toh kusan haka ammah zan dawo dan ban samu abinsa nake son samuba.

"Toh shikenan idan ka dawo sai kata'bo ni, godiya barr faruk yayi mashi nan sukayi sallama yaja motar sukabar gidan yarin.


Tunda yakoma gida tunanin labarin da megadi yabashi da yanayin da yaga jawahir a ciki yake tabbas har cikin ranshi yana da niyar taimakonta saidai me shima ya fara tantama akan hakan.
Wayarshi yad'auko yakira shugaban me kula da gidan yarin yace gobe zai dawo zai tattauna da Jawahir dan yanason more information game da case d'inta sannan asa agyarata asa tayi wanka wannan gashin nata agyara mata shi.
Dariya Mahadi yayi yace toh Barrister angama ammah wannan gashin nata ko angyara shi dakanta take yamitse abunta ammah shikenan za'ayi.


Bayan sun gama wayar fitowa yayi yasamu Hajiya Nuratu a parlor tana waya zuwa yayi yazauna a gefenta har tagama wayar takalleshi tana murmushi tace Son ka fito?
Murmushi yayi yace Eh Momcy d'azu ai na shigo lokacin kina sallah
Ohk ina fatan dai ka ci abinci.
Yatsina fuska yayi yace Eh Momcy na ci.
Ba dan ta yarda da maganarshiba tace Allah dai yasa dagaske kake dan nasanka bakason cin abinci.
Allah first love na ci.
"Toh shikenan na yarda d'azu mukayi waya da Nasiba ta ce kwana biyu baka je wajentaba meyasa?
Dan guntun murmushi yayi yace Momcy aiki ne yaimin yawa wata shara'a ce tasha min kai sosai saisa ma yanzu kikaga kullum ina gida ammah zan kirata a waya.
Gyad'a kai tayi tace toh shikenan Allah dai yataimaka yashige mana gaba.
Barr Faruk yace Ameen Momcy Daddy ya dawo ne?
"A'a ya dai ce min yau zai dawo idan tafiyar ta samu inko bata samuba sai jibi"
Allah yamaidoshi lafiya Momcy bari inje ina wani aikine in d'an ida.
Toh Son badamuwa Allah yataimaka.
Ameen Momcy.




Washe gari wajen k'arfe sha d'aya kasancewar weekend ne yashirya yaje gidan yari dan yagana da Jawahir a office d'in shugaban yasafka kasancewar abonki shi ne sosai bayan sun gaisa ne Mahadi yace Barrister wai dagaske zaka tsaya ma Jawahir maikudi a wannan shara'ar tata?
Murmushi yayi yace Eh insha Allahu ina da burin haka.
Shuru yayi sai chan yace kuma kana gani babu wata matsala.
Ta'be baki yayi yace bana tunanin haka.
Shikenan bari insa akawo maka ita nan,,,wayarshi yad'auko yakira wata ma'aikaciyarsu suna gama wayar yakalli Barr Faruk yace abokina gatanan za'a kawota bari ind'an fita ana jirana a waje zan turo ma'aikacinmu ko akwai abinda kake buk'ata kafin intafi?
Murmushi yayi yace bana buk'atar komai maybe kafin kadawo na gama abinda nake na tafi.
Mahadi yace Eh gaskiya ina tunanin haka dan zan dad'e ammah kakula.
Hannu yamik'a mashi sukayi musabaha yatafi.



Barr Faruk wayarshi yashiga latsawa chan yajiyo yanayin tafiya kamar ana jan mutum d'ago kai yayi yakalli k'ofar wasu matane biyu jaye da wata yarinya andaureta da kaca hannuwa da k'afafuwa dakyar take tafiya har suka shigo da ita, ido Barr Faruk yazuba mata yana kallonta cikin ranshi yace wacece wannan?
Matan ne sukace 'Dallabai gata Oga yace akawota.
Kallon matan yayi yace wacece wannan? Jawahir fa nace akawo min?
wannan ai itace jawahir din",,cewar d'aya daga cikin matan.
Kallonshi yamaida ga yarinyar da aka shigo da ita take tsaye kanta sunkuye a kasa doguwa ce kalarta farace ko ma ace me haske sosai daga gani wahala ce tadisar da ita fuskarta me round ce hancinta dogo ne ba chan ba bakinta madaidaici koda tana cikin yanayi na wahala ammah hakan bai hana agane kyaunta, Jinjina kai yayi yace shikenan zaku iya bamu waje.
Tsawa suka daka mata sukace bazaki tsugunna ba?
Ahankali tazame k'asa ta tsugunna still dai kanta na sunkuye a kasa bata d'agoba, juyawa matan sukayi suka fita Inda wani ma'aikaci yatsaya daga bakin k'ofar yadda yana hangensu.
Barr Faruk zuba mata idanu yayi yana kallonta tana kallon ankwar da take hannunta Ahankali yakira sunanta.
D'ago kai tayi tana mashi kallon mamaki batare da ta amsaba.
Numfasawa yayi yace Jawahir sunana Barr Faruk Sani Maishadda.
Wani irin kallo tayi mashi cikin dasashiyar murya tamaimaita Sani Maishadda!
Da mamaki yake kallonta yace kin sanshi ne?
Wani irin murmushi tayi mai wuyar fassarawa sannan tace menene yakawo ka wajena?
Ta6e baki yayi yace ba komai bane yakawo ni sai dan inaso intaimaka maki idan kika bani duk wani bayani da yadace zanyi k'ok'ari wajen ganin na fitar da ke daga cikin gidan nan.
Lokaci guda fuskarta tacanza takoma kwata-kwata babu annuri tace bana buk'atar taimakon ka,
Baki buk'atar taimako na saboda wane dalili nifa so nake intaimaka maki kifita daga gidan nan ammah idan har kika ban damar haka.
Idanu tak'ura mashi tana kallonshi sai kuma chan tajuyar da kanta gefe d'aya tace bazaka iya taimaka min ba kabarni kawai ink'arasa rayuwata ahaka kar kajefa rayuwarka cikin hatsari dan shiga rayuwata daidai yake da ruguza duk wani farin cikin rayuwarka.
No Jawahir kidaina cewa haka akowane lokaci ni me tsayawa ne bayan gaskiya kuma nasan ke bakida hannu a cikin kisan nan.

Fashewa tayi da wani irin firgitaccen kuka tace wannan ba gaskiya bane Barrister kar kasaki kayi gigin shiga rayuwata gudun kar kayi silar rasa taka rayuwarka.
Mik'ewa yayi tsaye yamatso kusa da ita yace ban damu da rayuwataba Indai akan gaskiya zanyi aikina.
Cikin wata irin razanannar murya tace tabbas zaka aikata babban kuskure idan har kanemi kataimaka min zaka iya rasa rayuwarka kamar yadda lauyoyi biyu suka rasa tasu rayuwar.
Cike da mamaki yake kallonta ganin yadda lokaci guda tahargitse yace jawahir kodai kina da hannu acikin mutuwar su Barr muhsin?
K'ara sautin kukanta tayi tace ina gargad'inka kar kayi gigin shiga rayuwata katafi kawai.
Matso da kujerarshi yayi yazauna a gabanta yace na ji zan tafi ammah inaso kifad'a min gaskiyar lamari akan kisan da akayi shin kina da hannu a ciki?

Hannuwanta biyu masu d'aure da ankwana tasa tadafe kanta da su dataji ya fara sara mata k'ara tafasa da dukkan k'arfinta wanda yasa saida gabad'aya d'akin ya amshi shi kanshi Barr Faruk saida yada d'e kunnuwanshi har tagama k'arar idanuwanta yaga lokaci guda sun juye sun canza ta yi wata kala da ita.
Barr Faruk d'auko wata Newspaper yayi ya ajiye a gabanta yace me zakice a nan?
Ido tazuba ma hoton da yake manne jikin newspaper d'in kafin daga baya tajanye idanunta daga kallonta.
Barr Faruk yace shin gaskiya ne wannan bayanin da akayi na hotonki da aka buga akan kin kashe mutane bakwai ciki har da nakusa da ke?
Zumbur Jawahir tamik'e tsaye tare da ja baya kad'an tace ina sake gargad'inka kar kayi gigin shiga rayuwata kabari kawai ayanke min hukuncin kisa domin hakan shine kawai zai kasance *FANSAR RAI* kagaugauta zare hannunka acikin lamurra na banso kaima kajefa kanka cikin wahalalliyar rayuwa, dan taimakona daidai yake da barazana da rayuwarka,,,saurin dafe kanta tayi da taji ya sara mata.
Daidai lokacin matan suka shigo sukace 'Dallabai 20 minutes d'in da aka baku ta cika.
D'aga kai yayi cikin sanyin jiki yace kutafi da ita.
D'ago kai Jawahir tayi takalleshi sannan tajuya suka riketa suka tafi.
Ajiyar zuciya Barr Faruk yasafke tare da mik'ewa tsaye yafara zagaye d'akin maganganunta suka dinga tariyo mashi a k'walwa cikin ranshi yace kenan tana nufin da hannunta acikin kisan nan duk da akayi? Saidai taya hakan zai kasance bayan ita me k'ananun shekaru ce? Tunowa yayi da irin kallon da tayi mashi lokacin da za'a tafi da ita sai yaga gabad'aya idanuwanta sun canza sunyo waje, ahankali yace anya yarinyar nan mutum ce?
Wayarshi ce da tafara ringing takatseshi daga tunanin da yakeyi dan haka yad'auki key d'in motarshi yaficce cikin sauri saboda wannan Kiran ya san cewa Alk'ali ne yake nemanshi a court.



_Wannan littafin na kud'i ne ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 Kacal zai turo MTN card ta wannan number d'in 09035938246 ko katuro 200 ta account number d'innan 5330055604 FIDELITY BANK, idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number d'in 09035938246_

_Ga mutanen Niger zasu tura 300f ta wannan number d'in +22794775574_
_Gareku masoyan gaskiya_


_*GARA B'ASA! GARA B'ASA!! GARA B'ASA!!!* wannan gara'basa anyi tane kad'ai ga duk wanda keson karanta littafin *FANSAR RAI* da *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shaharariyar marubuciyar nan watau *AMINA ABBA UMAR* ga duk mai bukatar karanta duka novel's d'in biyu zai biya *N300* kadai domin samun damar karantasu cikin aminci, gareku masoyan gaskiya muna jiran ku nuna mana k'aunarku ta hanyar biyan *N300* kad'ai, idan duka biyun kakeso zaka turo kud'i ta wannan account number d'in 3092292135 FIRST BANK, ko kuma katin waya Mtn na d'aya daga cikin Numbers d'in nan 09035938246 ko kuma 07030792790, ko 07036073670, sai ka aiko da shedar biya ta d'aya daga cikin numbers d'in, sai munji daga gareku masoyanmu_








_Sis Nerja'art✍🏻_
[3/6, 15:07] Sis Nerja'art👰🏻: https://www.facebook.com/105966804349754/posts/105967661016335/?sfnsn=mo


*......FANSAN RAI.......*



_*STORY AND WRITTEN BY SIS NERJA'ART✍🏻*_



*INTELLIGENT WRITERS ASSO....®*
[On Ward Together]


*DEDICATED TO ZM CHUBA'DO*



*PAGE FOUR*


Suna janye da jawahir suka maida ta d'akinta suka wullar da ita ciki suka maida k'ofar suka gark'ame, Jawahir had'e kai da gwiwa tayi tafara fitar da kuka Marar sauti wata irin k'ara tafara ji me kama da kukan hadari saurin mik'ewa tsaye tayi tafara waige waige jin k'arar daga saman d'aki take yasa tayi saurin d'aga kanta sama wata irin razanannar k'ara tasaki tare da sulalewa k'asa tafad'i a sume.



Barr Faruk bayan ya je wajen Alk'ali sun sake tattaunawa akan case d'in Jawahir nan ya amshi file d'inta yaduba akan dai laifin kisan ake zarginta list d'in mutanen da takashe yabi.

Yana gama dubawa wasu information yad'auka akan mutanen sannan yatashi yatafi koda yakoma office d'in shi kiran Barr Bilal yayi a waya yace yanaso yaje yasamo mashi hotunan wad'anda ake zargin Jawahir ta kashe, Jim Barr Bilal yayi cikin ranshi ko baisoba dan a rayuwarshi bayason abinda zaisa yashiga Case d'in Jawahir, ba dan ya soba ya amsa mashi da toh zaiyi k'ok'arin hakan.
Barr Faruk yace yatabbatar koma me ake kar yawuce zuwa gobe da safe.
Barr Bilal ya amsa da insha Allahu.

Suna gama wayar yatashi yakama hanyar gida yana isa a parlour yasamu Hajiya Nuratu zaune a main parlor tana ganinshi tayi murmushi tare da cewa sannu da dawowa Son
Shima murmushin yayi yamatso yabata peck a goshi yace yauwa first love dafatan na dawo na sameki lafiya?
Lafiya lau ya aikin?
Alhamdulillah Momcy muna ta fama.
"ai na gani Son dan yanzu kullum busy kake Allah ubangiji dai yataimaka"
Barr Faruk yace Ameen First love
Wai son ka je gidansu Nasiba kuwa?
Murmushi yayi yace a'a Momcy yau dai nakeson zuwa.
Shikenan son ya dai kamata kaje dan Allah kadaina wannan zurfin cikin naka kana son Nasiba ammah sai kadinga basarwa kadinga bata kulawarka ta hakane zata gane kana sonta.
Murmushi yayi yace Toh Momxy insha Allah zanci gaba da k'ok'arin hakan.
Allah yayarda dan wallahi idan har kayi wasa da damarka karasa Nasiba babu ruwana.
Dariya yayi yace insha Allahu ma bazan rasataba Momcy kema nasan ai bazaki bari inrasata ba.
Toh ya zanyi tunda kana ta ja mata aji ai sai inzare hannuna aciki.
Marairaicewa yayi yace kai momcy keda zakiyi min fatan insameta yanzu ma bari inshiga ciki inshirya inzo inyi lunch zuwa anjima sai inje ingano Masoyiyata.
Momcy cikin jin dad'i tace toh shikenan Son idan zakaje sai kayi min magana zan baka sak'o kakai mata Barr Faruk ya amsa da toh momcy nan wuce yanufi hanyar part d'inshi da kallo Hajiya Nuratu tabi d'an nata cike da so kafin daga bisani tamik'e itama tanufi part d'inta.




Barr Faruk bayan ya shiga part d'inshi wanka yayi yashirya yafito yayi lunch bayan sallar la'asar ne yad'auki key d'in motarshi yabiya part d'in Momcy yafad'a mata zai tafi gidansu Nasiba wata Leda tad'auko dank'are da kaya tabashi tace yakaimata.
Murmushi yayi ya amsa yace toh momcy mun gode Allah yak'ara girma da bud'i.
Itama murmushin tayi cikin jin dad'i tace Ameen son.



Yana fita motarshi yabud'e yasaka kayan a bayan mota sannan yabud'e mazaunin megadi yashiga yaja motar driver yahangeme mashi gate yabar gidan dagudu.

Cikin k'ank'anin lokaci ya isa Malali Quarters a daidai k'ofar gidan Alhaji Sufyan Mai Nasara yayi horn nan megadi yataso cikin sauri yalek'o ganin motarshi yasa yai saurin hangame mashi tankamemen gate d'in gidan yashiga.
A daidai inda ake parking d'in motocin gidan yai parking yad'auko wayarshi yayi dialing d'in wata number, saida takusan tsinkewa sannan akayi picking tare da yin sallama akace Hello Lovely.
Lumshe idanunshi yayi dan sosai yakejin dad'in sunan da take kiranshi da shi yace Sweetheart kifito ganinan nazo.
Daga chan 6angaren Nasiba tace ohk ina zuwa.
Katse wayar yayi tare da Jingine kanshi jikin kujerar yana jiranta tafito.

Tayi kusan minti biyar sannan tafito tana tafiya tana yauk'i, Nasiba chocolate colour ce bak'inta mekyau ne batada tsawo sosai saidai yar duma duma ce idan tana tafiya jikinta gabad'aya yake motsawa koda take bak'a ammah tana da kyaunta daidai ita idanuwanta dara dara ne, a nutse take takowa sanye cikin gown din material red da bak'in veil har ta iso wajenshi baisan ta zoba knocking tayi ma glass d'in motarshi nan yabud'e idanunshi tare da bud'e mata gaba fuskarta d'auke da murmushi tashigo tare da yin sallama.
Shima murmushin yayi yana binta da kallo dan sosai tayi mashi kyau.
Kallonshi tayi cike da shauk'in so tace lovely kallon fa?
Lumshe idanunshi yayi yabud'e yace Sweetheart kinyi kyau sosai.
Uhm nagode ammah fa fushi nake da kai.
Zaro ido yayi yace da nayi maki mi?
Juyawa tayi takalli window tace Komai ma kayi yau kusan kwana ukku baka kirani a wayaba kuma rannan munje gidan shine ko kafito mugaisa.
Cikin kwantar da murya yace Ayya sorry sweetheart kinsan yanayin aikin namu yanzu kullum busy nake fara aikin nan da nayi a High Court natarar da aiki dayawa yana jirana yanzu haka shara'ar da na amsa zan tsaya ma mutane sun kai goma banda ma wad'anda namaida nace bazanyi ba saisa kusan kullum banda lokacin kaina cikin research nake.

6ata fuska tayi tace gaskiya lovely tun bakayi nisa da aikin nan ba ya fara fita a raina dan ko munyi aure nasan sai ka fi ba aikinka muhimmanci akaina.
Girgiza kai yayi yace wannan ba hujja bace Nasiba shi aiki daban haka shima aure daban yake ina sonki Kamar yadda nasan kema kina sona kar kidinga sa damuwa a ranki akan haka koda bayan aurenmu ni nasan yadda zan kula da ke batare da nashiga hak'k'in kiba.
Ajiyar zuciya tasafke tace hakane lovely saisa a kullum nake k'ara jinka acikin raina dan Allah kar karabu da ni komin daren dad'ewa.
Murmushi yayi yace kar kidamu insha Allahu muna tare babu abinda zaya rabamu.
Allah yasa, bismillah kazo mushiga cikin gida.
Girgiza kai yayi yace a'a muyi hirarmu a nan.
Kai lovely narasa meyasa bakason shigowa cikin gida kai wai kunyar Ummi ita babu ruwanta tana d'akinta ma.
Ni bazan fa shigaba sweetheart nan dai nakeso muyi hirarmu.
Shikenan lovely duk yadda kakeso haka za'ayi.



Nan suka zauna suka dinga hira cike da k'aunar juna kafin daga bisani sukayi sallama kamar kar su rabu sukeji yad'auko kayan da Mom tabada yabata yamik'a mata nan tayi mashi godiya takoma cikin gida shikuma yafizgi mota yakama hanyar gida tuk'i yake a nutse yana tafiya nan yafara jin motsi a bayan motarshi ta mirror yakalla ammah baiga kowaba ji yayi kamar anwane glass d'in bayan motar dan haka yayi saurin waigawa ganin

Please Login or Register in order to submit comment