Reading TRIPLETS BOOK 2 by Star Lady Chapter 8 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta naje can wani gari na jefar da ita ne?" Ya tambayi kan sa, ɗayan ɓangaren na zuciyar sa ne yace masa "Da kuwa hakan zai fi, dan idan ba haka kayi ba Ummi ba zata fasa aura maka wannan mahaukaciyar kwailar yarinyar ba" tunani kala-kala yake cikin ransa har ya karisa cikin bedroom ɗin nasa.

A ɓangaren Abbo kuwa daga cikin bedroom nasa yana jiyo duk yadda Ummi tayi da Nawid, shi ma tunani yake ta yadda zai ɓullo wa lamarin, ji yake kamar yabi dare ya ɗauki baby ya kai ta gidan shi na Abuja ya ajiye ta a can, sai ya rinƙa biyan bukatar sa da ita, tun da daman a nan bai isa yayi hakan ba, saboda Hajiya, ga shi kuma yana bala'i son ya ga ya keɓe da baby, yana son kasan cewar tare da ita a ɗaki ɗaya. Shi ma tunani cike fal ransa yana tuna yadda zai sa mu mafita.

A ɓangaren Ummi kuwa tunanin bikin Nawid da baby kawai take, dan har ga Allah Ummi tana bala'i kaunar Jelly.
Wayar ta ta ɗauƙo daga cikin jakarta, ta danna kira, sannan ta kara wayar a kunnan ta.

Jim kaɗan a ka ɗa ga kiran "Hello Hajiya Batula ya kike?" Daga ɗayan ɓangaren Hajiya Batula tace "Lafiya lou Hajiya Turai ya su Nawid?" "Nawid yana nan lafiya yanzu ma kiran na shi ne ai" cikin sauri Hajiya Batula tace "Kiran nashi ne kuma? Kaddai ki ce min auren sa ne ya tashi" kyakkyawan murmushi ne ya bayyana a kan fuskar Hajiya Turai, tana murmushi tana faɗin "Eh wlh auren sa ne ya tashi, ina Abla?" "Abla tana school, lallai abu namu maganin a kwaɓe mu, ki ce na kamo hanya kawai" kara faɗa ɗa murmushi ta Ummi tayi kafin tace "Sosai ma kuwa kamo hanya kam mai kyau ma, da wuri kai" "Yaushe ne bikin?" Shiru kaɗan Ummi tayi kafin tace "Eh nan da sati uku haka" "wow lallai dole nan da sati biyu nayiwa Kaduna diran mikiya"

ɗan tsagai ta murmushi ta Ummi ta yi sannan tace "Gaskiya kam abun da yasa ma kenan na kira ki, saboda matar tasa, ki taimaka tun ana sauran sati biyu biki kizo ki fara gyara min ita" shiru Hajiya Batula ta ɗan yi kafin tace "Gaskiya tun ana saura sati biyu kam ba zai yi wu ba, sai dai saura sati ɗayan dai, saboda saura sati biyu biki ina da manyan baki, kuma kinga Abla ma zata dawo hutu daga school, zan yi kokari dai ana sauran sati ɗaya biki nazo, ranan tun safe zan biyo jirgi, kuma ai tsakanin Maiduguri da Kaduna tafiyar ba yawa, jirgin safe zan biyo, ina dirowa mu fara aiki" ɗan canza fuska Ummi tayi alamar bata ji daɗin maganar Hajiya Batulan ba, amma ba yadda ta iya dole ta hakura ta bi yadda Hajiya Batulan tace, dan Hajiya Batula ta kware wajen gyara mata, kuma babban aminiyar tace tun na yaran ta. Ba dan taso ba, ta amsa wa Hajiya Batula da to Allah ya kai mu, sannan suka yi sallama, ta mai da wayar ta ajiye, ta koma ta kwanta, ta ci-gaba da tunanin tana kawata yadda bikin zai kasance a ran ta.

To masu karatu mu leƙo Rimsha mu gani me take aikatawa.

Tun karfe 6 na safe su ka farka su ka shirya, a tare suka je suka yi wa matar sarki sallama, sannan suka je wajen sarki a ɗakin sa shi ma, suka yi masa sallama, sarki da matar sa basu ji daɗin tafiyar da su Rimsha za su yi ba, dan har ga Allah tun da suka gan su, suka ji kaunar yaran har cikin ran su ya ka ma su, to amma ba yadda za su yi, tun da ba ƴaƴan su bane, dole su kyale su su koma wajen iyayen su, dubu biyu sarki ya basu, sai godiya suke zuba masa, baki har kunne saboda murmushi jin daɗin sun samu kuɗin mota, Rimsha ce ta kulle kuɗin a igiyar rigar ta kusa da in da ta ƙulle goran da duna ya bata

cike da murna suka fito tsakar gida, matar sarki ma ba'a barta a baya ba, ta basu kyautan 500, sosai suka ji daɗi sai murna suke, suka yi sallama, su Rimsha suka nufi waje matar sarki da sarki suka koma cikin ɗakunan su

Su Rimsh sun fito zasu tafi kenan suka ci karo da olohunwa yana ƙoƙarin shigowa cikin gidan, hannun sa riƙe da buta, alamar bayan gari yaje yayi.

Murya kamar na yan shaye-shaye yace "Wow beautiful girl" yayi maganar yana kallon Rimsha, shiru su dukan su suka yi, ba su yi masa magana ba, hannu olohunwa ya kai zai shafi fuskar Rimsha, cak hannun sa ta maƙale ya sanƙare kamar itace, ihu ya fara yi yana kokarin jaye hannun sa baya, amma ina ya kasa, su ma ihu suka yi suka bazama cikin gari da gudu, dan sun tsorata da ihun olohunwa

A guje sarki da matar sa suka fito, olohunwa yana tsaye a wajen ya kasa motsawa, ga hannun nasa sai kumbura yake ya sankare waje guda, su kuwa su Rimsha tsorata da ihun da olohunwa yayi ne yasa su bazama cikin gari suna gudu kamar marasa hankali, a tunanin su, wani abun mugunta zai musu.

Sosai suke gudu basu san in da suka nufa ba, sarki kuma sai faman kokarin janye olohunwa a wajen yake, amma abun yaci tira ko motsa olohunwa sun kasa yi, to kun san halin yarabawa da tsoro ire-iren wayan nan abubuwa, ihu matar sarki ta kurma tana neman a kawo mu su ɗauki. Kan kace me gidan sarki ya cika da jama'a maƙil, sai hayaniya ke tashi kamar gidan biki, sai kokarin ture olohunwa suke daga wajen amma sun kasa, kamar bishiyar da a ka dasa shekara da shekaru haka ya zama a wajen, gashi sai ihu yake ya ka sa magana saboda azaban zogi da hannun sa ke masa, hannun ya kumbura sosai har ya fara fitar da wani irin farin ruwa mai warin bala'i, alamar hannun ya ruɓe.

Su kuwa su Rimsha bayin Allah basu san meke faruwa ba, sai zunduma gudu suke wai kar olohunwa ya kama su, dan Ayla ta faɗa musu olohunwa fyaɗe yake yiwa mata shiyasa ma suka tsorata sosai da shi.

Sun yi gudu sosai, har sai da suka dai na ganin alamar wannan kauye gaba ɗaya, sannan suka tsaya wajen wani bishiyar lemon tsami suna mai da numfashi, suna haki.

Almost 10mins suna tsaye, sannan suka zauna, a kasan bishiyar, da yake akoi ganyen damuna sosai a jikin bishiyar, sai suka sa mu inuwa, wajen akoi sanyi sosai gwanin daɗin zama, haka suka baje

Ayla ta duɓi Rimsha tace "Allah ya cece mu, ba dan haka ba olohunwa fyaɗe zai mana, ɗan iska ne sosai, ga shi da bala'i shaye-shaye" da kyar Rimsha ta iya cewa "Gaskiya kam, amma kuma basu da mutunci in dai haka ne" ita dai Kausar ta kasa magana saboda ta fi su shan wahala, dan ta fi su ƙiba shiyasa ta fi su jin jiki.

Sun yi shiru su na zaune, bishiyar na kaɗa musu iska mai sanyin daɗi, har wani lumshe ido suke kamar ma su jin barci

Kaɗan-kaɗan daga can nesa suka fara jiyo hayaniyar mutane, suna nufo in da suke, kasa kunne suka yi suna sauraro su ji, wannan hayaniya ta mecece.

Basu fargaba sai ganin gungun jama'ar kauyen su ka yi sun nufo su, hannayen su riƙe da sanduna wasu kuma suna riƙe da wuƙaƙe, zuba musu ido su Ayla suka yi, sun kasa tashi ma bare su yi yunkurin guduwa, dan su a nasu tunanin ma basu yi laifin komai ba, sun ɗauka wasu can daban yan kauyen suka biyo.

Sun zuba ido suna ganin ikon Allah, har yan kauyen suka iso wajen da suke. Su na zawa ba su yi wata-wata ba suka fara sauƙe musu sandunan hannayen su a jikin su, sosai Ayla da Kausar ke ihu ita kam Rimsha tana zaune shiru, alamar bata san ma meke faruwa ba, ga shi kuma su yan ƙauyen a nasu ganin ido suna duka har da Rimsha, sai dai kuma abun da ba su sani ba sandunan nasu baya taɓa jikin Rimsha

Sosai yan ƙauyen ke dukan Kausar da Ayla, ita kuma Rimsha ga shi dai a zahiri suna sauƙe mata sandan a jikin ta, amma a ɓaɗini ba haka bane, domin ko kaɗan bata ji alamar saukan sanda a jikin ta ba, tana dai ganin jama'ar ƙauyen suna ɗaga sanduna kamar zasu buga mata, sai kuma taga sandar ya ɓace, ga shi sai magana take musu, amma basa jin komai da take faɗa, duka kawai suke kai mu su, a yaren yarabanci suna ce mu su mayu ne, su suka kashe olohunwa

Kausar da Ayla sun daku jikin su duk ya farfashe sai jini yake, bayin Allah, ita ma Rimsha a idon yan ƙauyen jikin ta ya fashe yana jini, amma kuma ba hakan bane.

Sai da yan ƙauyen nan suka ga kamar su Kausar sun mutu basa numfashin, sannan suka kyalesu suka wuce suka bar su a wajen kwance cikin jini.

Suna tafiya wani haske ya fita daga jikin Rimsha ya tashi sama, ya bi bayan yan ƙauyen, wannan hasken na fita Rimsha ta dawo cikin hayyacin ta, ta tsorata sosai lokacin da idon ta ya sauƙa kan su Kausar, cike da tashin hankali ta fara girgiza su, tana kiran sunaye su.

Sosai take kuka ta na kiran su, amma ina ko motsi ba sa yi, kamar sun mutu, juyawa gabas da yamma kudu da arewa Rimsha tayi babu kowa a wajen, kara sautin kukan nata tayi baiwar Allah, sai jan hanci take, hawaye bibbiyu a fuskar ta, banda sunan Allah ba abun da take kira.

"Sannun ki baiwar Allah" taji wani zazzakar murya irin nata sak ta bayan ta, a razane Rimsha ta juya, wata kyakkyawar yarinya ce, yar matashiyar budurwa, wadda ba zata wuce Rimsha ɗin a shekaru ba. Cikin sauri Rimsha ta miƙe tsaye ta kari sa wajen yarinyar tana kuka kamar ranta zai fita, da kyar ta iya cewa "Dan Allah ki taimake ni, yan uwana zasu mutu, suna zubar da jini" tayi maganar cikin ruɗu da kiɗi ma haɗi da tashin hankali mai tsanani.

Sanya fararen hannayen ta yarinyar tayi, ta goge wa Rimsha hawayen fuskar ta, a nitse tace "Ki yi shiru, abun da nazo yi kenan, taimakon ku" ta kai karshen maganar tare da wucewa wajen da su Ayla ke kwance.

A gaban su ta tsugunna tare da ciro wani magani daga jakar da take rataye da shi a jikin ta, cikin sauri Rimsha ta ƙariso wajen ita ma, tana hawaye ta tsugunna kusa da yarinyar tana kallon yadda yarinyar ke shafawa su Ayla maganin hannun ta.

"Ki yi shiru Rimsha, ki dai'na kuka kin ji?" Cewar yarinyar, zaro ido Rimsha tayi murya na kerman tsoro tace "Waye ya faɗa miki sunana" cool murmushi yarinyar ta saki, har sai da dimple nata irin na Rimsha ya lotsa, haka zalika murmushi nata yayi sanadiyar bayyanar kyawawan fararen hakwaran ta, har wani haske ke fitowa daga tsakanin hakwaran nata, yarinyar kyakkyawar yarinya ce ajin farko, jikin ta sumul babu ko alamar tabo a jikin, fara ce tas kamar farin turawa ko in ce yan Korea, hancin nan nata ɗan siriri kamar pencil, tana da manya-manyan ido kyawawa, sai dai abun mamaki idan nata sak na Rimsha babu abun da ya ra ba, ita ma sleeping eyes gare ta, haka zalika bakin ta sak na Rimsha babu abun da ya raba. Babu abun da ya fi jan hankalin Rimsha a fuskar yarinyar nan face gashin gerar ta da kuma yanayin shape na fuskar nata, babu abun da ya raba shi da na Rimsha ɗin, sosai Rimsha tayi mamaki ganin wannan halitta mai kama da ita, gashi kuma a tsawo ma ba zata wuci Rimsha ɗin ba, haka a shekaru, a takaice dai banbancin wannan yarinya da Rimsha hasken fata, ita Rimsha fatar ta chocolate color ne, yarinyar kuma fara ce tas, kuma jikin yarinyar bai yi yana yi da jikin ɗan Adam ba, dan baka iya ganin joint na jikin ta, sannan kuma babu tabo ko kaɗan a jikin ta sumul take.

Zuba mata ido Rimsha tayi tana kallon ta, har ta kammala aikin shafawa su Ayla maganain da ta taho da shi, sannan ta miƙe tana faɗin "Nan da minti biyar za su tashi, kuma za su tashi lafiya lou ba tare da wani ciwo ba" ta kai karshen maganar tare da juyawa zata bar wajen, cikin sauri Rimsha tace "mun gode mai taimako"

Wannan cool murmushi nata irin na Rimsha ta saki, har sai da dimple na ta irin na Rimsha ya bayyana a nitse tace "Ba sunana mai taimako ba, sunana Malika" tana kai karshen maganar ta wuce da sauri ta bar wajen, dawo da kallon ta kan su Ayla Rimsha tayi tana faɗin "Allah nagode maka, Malika kema mun gode miki"

Kamar yadda Malika ta faɗa haka su Ayla su ka tashi lafiya Lou, sun yi sumut da su, sai yar waige-waige su ke kamar ma su neman wani abun "Ayla sannun ko, Kausar kema sannu" Cewar Rimsha tayi maganar tana kallon su miƙewa zaune suka yi, suna zare ido kamar ma su neman wani abun, matsowa Rismha tayi ta riƙo hannun Ayla tana faɗin "Ayla akoi in da yake miki ciwo ne?" Girgiza kai Ayla tayi kafin tace "A'a babu" riƙo hannun Kausar ma Rimsha tayi ta tambaye ta, ko akoi in da ya ke yi mata ciwo, ita ma a'a tace, miƙewa Rimsha ta yi tana faɗin "To ku tashi muje ko?" a tare suka miƙe Ayla da Kausar suna jin kamar sun yi mafarkin an mu su duka, abun ya zama musu tamkar a mafarki, ita ma kuma Rimsha bata sanar da su cewa a zahiri ne ba a mafarki ba, sai ta kyale su kawai suka ci-gaba da tafiya.

Sun yi tafiya mai nisa kafin su isko wani karamin titi, lokacin karfe goma na safe zai yi.
Sun jima tsaye a bakin wannan ɗan karamin titi kafin su samu wani mota wanda ya ɗauko katako, irin wayan nan taxi ɗin ne, masu kirar mota 206

Cikin sauri Kausar ta daka tar da motar, dan sun gaji da tsayuwa a bakin titi bayin Allah, da farko kamar mai motar ba zai daka ta ba, amma ganin yanmata tsaye a wajen wannan daji yasa ya tsaya, cikin sauri Kausar ta karisa wajen nasa, su kuma Ayla da Rimsha suna tsaye.

Da harshen yarabanci Kausar ta yiwa mai motar magana, a kan ya taimaka ya kai su eyankorin, hakuri ya bata kasan cewar babu filin da zai ɗauke su su dukan su a motar nasa, cikin sauri Kausar tace masa, "Baba zamu zauna a gaba" dawo da kallon sa yayi wajen da Kausar ke nuna masa zasu zauna yace "Ku uku a gaban mota kuma kan kujera ɗaya" da sauri ta gyaɗa masa kai tana faɗin "Eh baba zamu zauna, dan Allah ka taimaka mana, idan ka wuce ba mu san ya za mu yi ba" jinjina kai yayi kafin yace "To shikenan ku shigo mu tafi" da sauri ta juya ta kwalawa su Rimsha kira, da yar gudun su, suka kariso wajen.

Ayla ce ta fara shiga sai Kausar, suka ɗaura Rimsha a saman cinyar su, saboda ita ce karama kuma bata da nauyi, dan yar siriri ya ce, sai kallon su mai motar yake kamar zai yi masu magana, sai kuma ya fasa ya kunna motar kawai suka bar wajen.

Sai satar kallon Rimsha yake ta cikin mirror taxi ɗin nasa, shi dai tun da yake bai taɓa kallon yarinya mai bala'i kyan Rimsha ba, musamman ma idan ta ɗan motsa ɗan karamin bakin ta, dimple nata ya lotsa, subhanallah idan mutun yayi wasa kyan Rimsha sai ya sa shi ya saki kan motar sa, duk da wuyar da ta sha na Daular Mutuwa ga kuma tafiyar da suka yi a dajin nan, duk da haka, ba wani canji a fuskar ta sai ɗan rama kaɗan da tayi, amma kyan ta na nan.

Shiru suka yi ba wan da yayi wa ɗan uwan sa magana, har suka isa eyankorin junction, a nan mai motar ya sauke su, kwance kuɗin dage ɗaure a igiyar rigar ta Rimsha tayi suka bawa mai mota, kin karɓa yayi yace suje dan Allah ya kawo su, sai murna suke, suka masa godiya tare da tsallaka titi suka nufi hanyar ogele, suna tafiya suna hira kaɗan kaɗan, jikin su duk ciwo yake musu.

Gaban wani ɗan ma ɗai-ɗai cin gida suka tsaya, gida ne na mai kuɗi dai-dai gwargwado, gaba ɗaya gidan rufi ɗaya ne, kun dai san yadda ginin yarabawa yake, basu cika yin fencing na gida ba, haka suke barin sa, basu da sirri komai a wangale ake yin sa, a waje suke girki wanke-wanke, wanki da sauran su.

Kausar ce ta sanya hannun ta ta fara knocking na kofar palon, dan na gaya muku dama ba fencing gidan, rufin ɗaku na ne kawai. Daga cikin ɗakin wata murya tace "Tani? Nbowa (waye ne? Ina zuwa)" shiru Kausar tayi tana tunanin yadda zata ga maman ta.

Sun kai 3mins tsaye a wajen kafin nan wata mata wadda da ka ganta kaga bahaushiya, kuma kaman ta ɗaya da Kausar, ita ce tazo ta buɗe kofar tana faɗin "Kilode (menene)"

Ihu ta kurma lokacin da idon ta ya sauka kan fuskar Kausar, rungume ta Kausar tayi, ita ma matar ta rungume Kausar tana faɗin "oh oluwa" kun san dai yadda shaukin soyayya tsakanin uwa da ƴa yake, musamman a ce sun jima basu haɗu ba, abun ba'a cewa komai, dukan su hawaye suke sun rungume juna, sai ihu iya Kausara take tana kiran oluwa oluwa, kan kace me makota sun tattaro cincirindon dan suzo su ji lafiya iya Kausara ke ihu haka.

Ganin Kausar yasa suma suka fara na su ihun murnan, su Rimsha sun tsorata sosai da jin yadda suke ihu, basu san yarabawa bane, yarabawa idan suna magana cikin kwanciyar hankali ma sai ka ɗauka faɗa ake, saboda Allah ya zuba musu murya mai sauti, har sama idan suna magana, ina ga kuma abun murna ya samu, ai shikenan kuma sai dai wanda bai saba ji ba ya toshe kunne

Gaba ɗaya sun cike anguwar da ihun Kausara ta dawo Kausara ta dawo, wannan ya ja Kausar ta nan wannan ya ja ta ta can, farinciki a wajen su ba'a magana, babu wanda ya kula da Rimsha da Ayla, Allah sarki bayin Allah sai bin su kawai suke da ido, sun ga abun da yafi karfin su.

Almost 20mins ana wannan ihun murna na dawowan Kausara kafin iya Kausara ta jata zuwa cikin gida tana faɗin suje tayi wanka taci abinci sannan tazo ta basu labarin ina ta ɓata, suma makotan kowa ya wuce gidan sa, suka bar su Rimsha tsaye sun rasa madafa, sai zare ido suke gwanin ban tausayi.

Har sun shige cikin gida, Kausar ta fito da gudu tana faɗin "Iya friends ɗina" bin ta da ido iya Kausara tayi tana kallon ta, har ta fito wajen palon.

In da ta bar su Rimsha tsaye wajen ta fito ta same su, sun kasa ko motsawa Allah sarki, tunanin nasu iyayen kawai suke, ita Rimsha tana tunanin ita ma idan ta koma gida kila haka su Jehan za su yi mata, ita kam Ayla ƙoƙarin ɓoye hawayen dake ƙoƙarin zubo mata take, dan ganin Kausar cikin yan uwan ta, ya jefa ta cikin tashin hankali, dan ita ba ma ta da yan uwan bata da kowa sai maman ta kawai.

Suna tsaye sunyi jugum jugum babu wanda ya kula su, Kausar tazo ta jawo hannayen su tana faɗin "Kuzo muje?" Bin ta su kayi zalalau-zalalau zuwa cikin gida, duk jikin su a mace, ji suke kamar su yi ta kuka kada su dakata

"Kausar su waye wayan nan?" Iya Kausar ta tambaya cikin harshen Hausa "Iya friends ɗina ne tare muka zo ai" kallon tsab iya Kausar ta musu kafin tace "Ban gane tare kuka zo ba? Ina za su je?"

Saman sofa dake cikin palon Kausar ta zauna tana faɗin "Iya nan mana suka zo, basu da kowa ne shiyasa" tsawa iya Kausar ta daka mata "Dan basu da kowa, sai ki kwaso su ki kawo ma na su? Tukun nan ma daga ina kuke?" Cikin sauri Kausar tace "Daga Daular Mutuwa muka fito"

Har wani bonsin iya Kausar tayi jin an ambaci sunan Mutuwa, dafe kirji tayi tana zare ido tace "oloni Kausara Mutuwa kuma?" Gyaɗa mata kai Kausar tayi tana faɗin "Eh iya Daular Mutuwa" "kaiii Kausara ki dai na kiran Mutuwar nan, wannan suna mai sanya tashin hankali haka, tukun nan ma ai na kuka samu wannan suna?" Tana magana tana zare ido ta dafe kirji "iya gaskiya na faɗa miki daga Daular Mutuwa muka fito, Daular da ba'a shiga a fito a raye, mu Allah ne ya tsare muna da sauran kwana" hannu biyu duka iya Kausar ta ɗaura a kan ta, ta kara zaro idon nan waje, nan take ta birkice musu kamar wadda notir ɗin kan ta ya kwance, cikin sauri ta dawo kusa da Kausar ta zauna, kun san dai yadda yarabawa suke idan suka tsorata "Yanzu Kausar Mutuwa ma har da Daula yake da shi? Na shiga uku ni jummai, Kausara anya kinji me kika faɗa kuwa?" Gyaɗa mata kai Kausar tayi, sannan ta fara bata labari cikin Daular Mutuwa da yadda suke yanka mutane, a zabure iya Kausar ta miƙe da karfi tace "Kai kakai kakai Kausara bari bani wannan labari, bar shi kada ni ki kashe ni, ke basu kashe ki a Daular Mutuwa ba ni kuma zaki kashe ni a nan da labari, ni wlh bana son ji, ya isa haka, bayin Allah sannun ku eyeee wannan bala'i haka, gaskiya na tausaya mu ku" tana magana tana zare ido kamar idon ta zai faɗi kasa, dariya Kausar tayi tace "Iya wannan fa baki ji ko kwata daga cikin labarin abun da muka gani a Daular Mutuwa ba, har da masu canza ido fa" ihu iya Kausara ta kurma tana faɗin "oloni Kausara zan wurgaki waje idan baki dai na kiran wannan bala'i ba, ki dai na kira mun Mutuwa tsirarar ta a nan" abun ma dariya yaso bawa Rimsha da Ayla, ganin yadda iya Kausar ta birkice musu lokaci guda, daga jin sunan Daular Mutuwa, wanna da ita aka kai Daular Mutuwa tsoro da fargaba ne za su kashe ta, mata sai bala'i tsoro, ji yadda take zare ido, tana bahaushiya amma zaman ta da yarabawa yasa ta dawo sak su, ta koyi ɗabi'un su da komai nasu, idan ba kaga fuskar ta na hausawa ba, bazata taɓa cewa bahaushiya bace, duk wani attitude nata na yoroba ne yanzu.

Iya Kausar kam daga jin zancen Daular Mutuwa sai ta nitsu tayi hankali har da yiwa su Rimsha sannu. "Iya ina boder Jami'u?" Cewar Kausar "Baki tambayi dadyn ki ba, kina tambayar boder Jami'u ko?" Dariya Kausar tayi kafin tace "Ai zan manbaye shi ina suke?" Tayi maganar tana miƙe wa ta nufi wani ɗaki mai kama da kitchen "Daddy'n yana Lagos, Jami'u kuma yana cikin Ilorin" iya Kausar ta bata amsa, already Kausar ta shige cikin Kitchen abun ta.

Tukunyar abinci ɗungurungum na shi ta ɗauko , ta dawo palon ta yi zaman yan bori a kasan carpet, ba wanke hannu ba komai ta fara dumbulan abincin tana kai loma bakinta,

"Kausar ba zaki kira friends na ki su zo ku ci bane?" Cewar iya, kallon su Kausar tayi, duk sun yi tsuru-tsuru da su, kamar wasu marayu, kamar biri yana jin matsanancin yinwa, haka suka yi da fuskokin su "Ayla kuzo kuci abinci mana" ta faɗa tana tura abinci a baki, jolof rice ne ya ji kayan haɗi sai kamshi yake, dan ba karya yarabawa sun kware wajen iya girki

Haushi yasa Rimsha tace bazata ci ba, dan a ganin ta Kausar ta wulakanta su ne, ga shi tana jin matsananciyar yunwa saboda jiya ma bata iya cin abincin da matar sarki ta ba su ba, amma ba zata ci abincin nan dake gaban Kausar ba, dan Kausar ta raina su, kuma har ga Allah ita Rimsha bata ɗaukan wannan wulakanci, karku manta duk da

Please Login or Register in order to submit comment