Reading TRIPLETS BOOK 2 by Star Lady Chapter 20 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani washe baki take yi. Aafia na son yi mata magana amma ta kasa, har ga Allah abin da Rufee ta yi sam bai yi wa Aafia daɗi ba, ta ji haushin hakan, sai dai ba zata iya ce mata komai ba, already Rufee ta riga ta kai sunan su wajen Malam, ba wanda zai iya mata gardama ko ya ja da maganar ta acikinsu.

"Ke Aafia me ki ke wani kallona haka, kamar na ce ina son Abbin ki? Ni fa kawai jakarsa na agaza mi shi da shi, na kai mi shi ɗakinsa, ko na yi laifi yin hakan? Kuma ai nafa ita Halima bata iya kula da miji bane, shiyasa nake nuna mata example".

Girgiza kai Aafia ta yi, kamar wata wawiya, a sanyaye ta ce "A'a baki yi laifi ba, mu je ɗakina bari na yi wanka" girgiza kai ita ma Rufee ta yi kafin ta ce "A'a zan wuce sai mun haɗu kawai"

(Shegiya kin gama aikin da ya kawo ta, dole kice zaki wuce ai)

Tana kai karshen maganar bata jira amsar Aafia ba ta wuce ta nufi kasa, rai a ɓace Aafia ta wuce cikin bedroom nata.

A ɓangaren Aunty kuwa, Aafia na wucewa, mamanta ta ce "Sadiya me ya haɗa ki da yar taki? Na ji kamar kuna magana mara daɗi wa junan ku" Goge hawayen fuskar ta Aunty ta yi, dan kada mamanta ta gani, saboda kullun tana mata nasiha a kan hakuri da fawwalawa Allah komai.

"Babu komai Inna kawai naga ta dawo ranta a ɓace ne shine nake tambayar ta".

Wucewa Inna tayi ta nufi wani ɗaki dake kusa da Kitchen tana faɗin "To dai ki rinƙa yi mata a hankali dan kin san yarinya ce, ku zauna lafiya da juna". Kasa amsawa Aunty ta yi saboda azaban bakin ciki da ta ke cikin zuciyarta.

A wannan hali Rufee ta sauƙo ta sameta, a tsakiyar falon ta tsaya, ta fara bin Aunty da kallon banza daga sama har kasa.

A wulakance ta ce "ƴan kwanaki suka rage miki" tana kai karshen maganar ta wuce ta nufi hanyar fita daga falon.

Tana fita daidai lokacin daddy'n Jelly ya fito daga part ɗin Irfan, ya nufo cikin gida, zai zo ya yi wa Aunty ya jiki, dan ya ji Abbi ya dawo, kuma dama idan ba dole ba, baya shigowa part ɗin nasu sai Abbi na nan.

Mutuwar tsaye Rufee ta yi tana kallonsa, ga shi kuma yau shigar kananan kaya ya yi, yar ramar da ya yi ma kyau ta kara masa, daddy'n Jelly ba baya wajen kyau, da shi Jelly ke kama, ga golden eyes nasan nan ba'a magana gasu manya-manya kamar ball, ya fi Abbi kyau nesa ba kusa ba, kuma shi idan ka ganshi zaka ce matashi ne, domin kuwa bai da wani shekaru sosai, kuma yana da karamin jiki, auren wuri ya yi, shiyasa ya haifi Jelly.

Rufee ta kasa motsawa har ya zo ya wuce ta, da yake shima ba mai shiga harkar mutane ba ne, sai bai ce mata ko sannu ba ya shiga cikin falo. A sukwane ta juya ta bi shi da kallo har ya kurewa ganin ta.

Afili ta furta "No ya zama dole na kunce aikin da na yi wa Abbi ya dawo kan wanna saurayin, kai kaga kyau iya kyau, tab dole naje wajen malam gobe".

(Tofa ke Rufee ruwan ido ne zai kashe ki, ke kowa kina so anya kanki ɗaya kuwa?)

Ta ɗan jima tsaye a wajen tana tunanin ya zata ɓullowa lamarin, kafin ta sa kai ta fice daga gidan, ta fita bakin titin ta tari abin hawa zuwa gida, da waje bata zo da motar ta ba.

Shi kuwa daddy'n Jelly ko a jikinsa, ya je ya gaishe da Aunty ya fito ya koma part nasu.

Allah sarki Aunty ji take kamar zata mutu, Abbi ya dawo bai kula ta ba, ko sannu bai ce mata, kamar bai ganta ba, ga shi kuma ya kara mata wani bakin cikin na yarda da Rufee da ya yi ta karɓar masa jaka.

(To Aunty sai dai muce Allah ya fitar da ke, mu dai bari mo leƙo Jelly muga wani hali take ciki)

💖GIDAN ABBO💖

Zaune Nawid ya ke saman sofa a falo, ya yi shiru yana tunanin yadda zai ɓullo wa abin da ke faruwa, domin har cikin ransa yana zargin Abbonsa.

Ya yi nisa cikin tunani Jelly ta watso a guje tana ihu, a sukwane ya miƙe zai gudu dan ta tsorata shi, har wani kaɗawa hantar cikinsa ya yi, dan har ga Allah bai san zata zo ba, wani sufa ya yi ta saman sofa zai yi waje, kamar wani jikan chinawa haka ya yi, bawan Allah.

Ganin ya da ka tsufa ta saman sofa zai yi waje ne yasa Jelly ta ce "Kai yaya Nawid ashe kai ma ɗan China ne, ashe ka iya firewa".

Cak ya tsaya, a fusace ya juyo dan har ga Allah bai san ita ɗin ba ce.

"Ke ni kam anya ke mutun ce kuwa?" Ya tambaya yana kare mata kallo.

Sanye take da riga da wando, wandon jeans da riga mai dogon hannun, rigar tata kamar bargo haka jikinsa yake da laushi, saboda sanyin da ake yi, sannan rigar a iya kugunta ya tsaya, kayan sun zauna a jikin ta, gata kuma dama da shape sosai, ga shi an fara zama yan mata, komai na daɗa bayyana Masha Allah, kanta babu ɗan kwali, ta saki wannan bakin gashin fulanin nata, ya sha gyara wajen Ummi sai sheki yake yi.

Cikin sauri ya kawar da kansa daga kallonta domin har cikin zuciyarsa ya ji wani yanayi, ganin ta ba dressing mai kyau duk surar jikinta a bayyane ya sanya zuciyarsa wani mummunar tunani a kanta, cikin sauri ya kori sheɗan ya koma ya zauna tare da ɗaure fuska sosai ya ce

"Me ya fito da ke da gudu haka? Ina kuma Ummi?"

Turo ba ki ta yi, kafin a shagwaɓe ta ce "Ummi ba ta nan, ta shiga cikin gida"

"To baki bani amsa ba, me ya fito da ke daga cikin ɗaki da gudu haka, har ma da ihu".

Yar dariya ta yi kafin ta fara bashi labari "Ina zaune ina kallo ne sai naga wata yarinya tana gudu tana ihu wasu maza na binta, suka shiga cikin wani falo, a cikin wani gida, suna shiga falon sai yarinyar ta ɗauko wuka ta fara nuna musu tana faɗin...." Bata karisa maganar ba ta wuce saman table in da aka ajiye wata yar karamar wuƙa cikin kayan fruits.

Yana zaune yana kallonta, da gudu ta yi kansa da wukar tana faɗin "Idan ka matso kusa da ni sai na yanke ka" tana magana tana gyadawa da karfi.

Ganin da gaske wannan zata iya buga masa wukar nan, ta jimi shi ciwo ne ya sanya ya miƙe yana faɗin "Ke baki da hankali ko?"

Turo baki ta yi kafin ta nufi saman table ta mai da wukar tana faɗin "To ai zan nuna maka yadda matar ta yi ne, wai ma yaya Nawid kai komai na yi, ban maka ba, komai na yi sai ka zageni" "Dole na zage ki, yanzu na ce ki nuna mini yadda matar ta yi ne?" Ya yi maganar yana kokarin gyara zaman shi.

"Dama ai ba kai zan nunawa ba, gwada kaya na nake yi ko zan iya nima, kai ne nan ka tsayar da Ni kana tambayata me yasa na fito ina ihu, to abin da na fito gwadawa kenan".

Haushi ma ya hana shi yin magana, dan in ya ce zai biye mata tsab zai karya ta koma ya sumar da ita gaba ɗaya, yarinya kamar sheɗan ya mata fitsari a kai, cewarsa.

Ganin ya mata shiru ne yasa ta juya zata wuce cikin ɗaki, bata kai ga karisa juyawa ba idon ta ya sauƙa kan wani ɗan karamin kwaro dake tafiya a kan ƙafarsa, irin karon nan ne dake bin sanyi.

Da karfi Jelly ta ɗaga kafarta ta sauke masa a kan nasa, har wani kara ya bada, Nawid bai san lokacin da ya saki ihu ba, domin bai lura da lokacin da ta ɗaga kafar tata ba, hankalinsa na kan wayarsa dan ya ce baya son sake ganin ta a irin dressing da taken nan, shiyasa ya ɗauke kansa daga kallonta.

Jin ya yi ihu yasa ta ce "Yaya Nawid kai fa Allah kamar mace kake, kai rago ne, yanzu kashe kwaron ka ke yi wa kuka? Allah sai na maka irin ta Ram Charan yake ko waye, wannan dai na cikin Tv nan, sai kana barci na ɗebo ruwa yana tafasa a wuta na zuba maka, yadda Ram ya yi wa abokinsa a Tv bayan sun ɓata".

A fusace Nawid ya miƙe zai wanka mata mari Abbo da ya shigo tun ɗazun kyan Jelly da dressing tata sun ja hankalin sa ya kasa magana, kuma ya kasa karisowa cikin falon, ya tsaya kawai ya zubawa Jelly ido, sai da ya ga Nawid zai mare ta sannan ya ce

"Kada ka kuskura ka taɓa ta, baka ganin yarinya ce kuma bata da lafiya".

Sosai Nawid ya kara yin mamaki "wai ba jiya Abbo ya ce yarinyar nan tsintaciyar mage bace, baya son ta baya kaunar ta, me kuma yasa ya dawo bayan fage yana kareta" Nawid ne ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa.

Wucewa Jelly ta yi tana turo baki tana kunkuni ciki-ciki, ta shige ɗaki abinta, shima Abbo zuwa ya yi ya wuce zuwa na shi ɗakin.

Nawid kam ya kasa magana tunani kawai yake a kan Abbo, sannan ga in da Jelly ta dakesa ya masa zafi sosai, dan da iya karfinta ta take masa kafar nasa.

Yana zaune a wajen Har Abbo ya sake fitowa, dama Abu yazo ɗauka. Ko sannu bai ce da Nawid ba, ya sa kai ya fice abinsa.

Yana fita ba jimawa Ummi na shigowa bakinta ɗauke da sallama, ka sa amsa mata sallamar Nawid ya yi.

Bata wani damu ba tazo ta zauna kusa da shi tana faɗin "Baka fita zuwa asibiti bane Nawid?"

Da kyar Nawid ya iya ce mata "E Ummi ban fita ba".

"Lafiya Nawid na ganka cikin wani yana yi?" Ta tambaya tana kare masa kallo.

Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe kafin ya ce "Ummi dan Allah ki fahince ni ba wai zan miki gyarane dan kin gaza ko wani abu makamancin hakan ba, na san ke mace ce mai hankali, ilimi, addini, da kuma hakuri, to amma a wannan fannin kin kaza, bana ganin laifin ki saboda baki taɓa haihuwar ƴa mace ba, sannan kuma kema ke kaɗai ce mace a wajen kaka, baki taso kinga yadda ake kula da ƴaƴa mata ba, wannan dalili yasa ni bana ganin laifin ki".

Zuba masa ido Ummi ta yi tana kallon cikin kwayar idanuwansa masu ɗauke da damuwa turun.

Ci gaba da magana ya yi "Ummi dan Allah ina so idan zaki fita anguwa, koma ina ne ki fita tare da baby, kada ki barta ita kaɗai a cikin gidan nan, yin hakan babban haɗari ne, wlh ko jiya a asibiti sai da na yi wa yarinya yar shekara 3 ɗinki saboda fyaɗen da wani azzalumi ya mata, kuma kinga gidan ba mu kaɗai bane ga su Sadiq suna nan, ba wai ina zarginsu ko wani abu bane, a'a kawai dai kula ce, ka kula da kayan ka, ya fi kazo kana cikiya, kuskure kaɗan za ka yi a tarbiyar ƴa mace ya zama mata babban illa, kuma zai iya zama sanadiyyar tarwatsewar rayuwar ta gaba ɗaya, sannan Ummi dan Allah wasu dressing ɗin baby ta dai na yin su, kinga yanzu ta fara zama cikakkiyar mace, koda a gida ne ta daina saka su, saboda bamu san wani irin bako za mu yi ba, kuma idan kika duba mai son abinka ya fika dubara".

Sosai Ummi ta ji nasihar Nawid har cikin ranta, dama bata taɓa kawo hakan a ranta ba, kuma dama haka ne wani abin sai an nusassheka ka ke iya gane hakan, ta yi kukan zuci a kan abin da ya faru da yarinyar da Nawid ya yi wa ɗinki jiya, ta kuma kudiri niyyar kula da Jelly sosai fiye da a baya, ta wani ɓangaren kuma ta ji daɗi sosai, domin a tunanin ta Nawid ya fara son Jelly shi ya sa ya fara kishinta.

"Nawid na san ba iya wannan ne abin dake damunka ba, ka faɗa mini gaskiya me kake ɓoye min" Ummi ce ta sake jefo masa tambaya tana tsare shi da ido.

Dogon numfashi ya ja tare da sauƙewa a hankali, sannan ya fara magana "E Ummi ba shikaɗai ke damu na ba, akwai wani matsala dake cin min tuwo a kwarya, ke mahaifiya tace, bani da kamar ki, ba zan iya ɓoye miki komai ba"

Cikin sauri ta ce "Menene wannan kuma? ina jinka faɗa mini"

Juyowa ya yi suna fuskantar juna sosai, ya riƙo hannayenta cike da kaunar ta ya fara magana

"Ummi ki yi hakuri da abin da zan faɗa, amma ya zama dole na gaya miƙi, wata kila ke kina da hanyar iya maganin abin" tsare shi da ido kawai ta yi tana kallon sa, tana jiran ta ji me zai faɗa.

"Ummi ina zargin Abbo kamar yana da wata manufa a han baby" zaro ido sosai Ummi ta yi, har haɗe words ta ke wajen cewa "Wani irin manufa kuma Nawid?".

"Ummi yanzu idan a ka ce miki Abbo yana son baby ya za ki yi?" Dariya sosai Ummi ta yi, kafin ta ce "Nawid har yanzu kai yarone" "Yaro kuma Ummi?"

Gyaɗa masa kai ta yi, tana faɗin "E mana Nawid banda kai yaro ne tayaya Abbonka zai so baby? To ma idan ya sota ya yi yaya da ita? Kada fa ka manta Abbonka matansa huɗu, bayan gidan nan akwai nasu Zainab ka sani, ina hakan ma ba zai yiwu ba".

Shiru Nawid ya ɗan yi kafin ya ce "Amma Ummi ai abin da Abbo yake a kan babay ne abin ya yi wa sosai". Miƙewa tsaye ta yi tana faɗin "A'a ba wani yawa, kawai ɗoukin soyayyar yaya mata ne ke ɗibarsa, kada ka manta bamu da ƴa mace fa, kawai kaunar ta ya ke yi, dan haka ka dai na kawo tunani mara kyau a zuciyar ka, ka yi mana fatan alkhari kawai" ta kai karshen maganar tare da nufar ɗakinta tana faɗin ina babyn ma take, tazo na shiryata mai kunshi zata zo ta yi mata.

Shidai Nawid ya kasa magana tunani yake a zuciyar sa "Lallai Ummi kin yi nisa, yanzu in banda ke da abin ki, Abbo yana da mata huɗu, ƴaƴan sa mata sun kai shida dukka bai yi ɗouki a kansu ba sai kan baby tsintaciyar mage, anya Ummi ba amiki wani abin ba kuwa?". Sai zan cen zuci yake yi bawan Allah, abin ma yaso ya wuce tunaninsa.

(Nan na barosu na haɗa kaya na zuwa, wajen Jehan)


💗💗Super restaurant💗💗

Sai karfe 6 na yamma Jehan ta baro restaurant, sai sauri take ta nufi bakin titi dan tarar abin hawa zuwa asibiti, daga bayanta ta ji murya ana faɗin "Sannunki yan mata" kin juyawa ta yi, ta ci gaba da tafiyarta kawai, dan ba komai take kulawa ba.

Cikin sauri ya sha gaban ta, matashine wadda ba zai fi shekara 23 ba. Kallon sama da kasa ta masa, kafin a wulakance ta ce "Lafiya ka tare min hanya?"

Yar murmushi ya yi tare da fito da wayarsa kirar Tecno camon 11 yana faɗin "Wlh yan mata kin yi mini ne, idan ba damuwa ki zuba mini shaɗatar ki a nan" ya yi maganar yana miƙo mata wayarsa.

Tsabar bakin ciki ta ɗan jima kafin ta ce "Sai ka rasa uban waye yake koyawa yaran nan wasu abubuwan, zaka wuce ka je ka yi firsari ka je ka kwanta dare ya yi ne ko sai na ɗauki bulala na zane maka jiki? Yara kanana sai wani iya shege, yanzu ni ce zan baka number ta, lallai yaron nan" Da turanci ta yi maganar.

Kasan cewar yana jin turanci hakan yasa ya gane me take nufi, ya sha ruwan mamaki, cikin sauri ya fara bin jikinsa da kallo, ya tsurawa gaban sa ido yana son gane me Jehan ta gani ta ce masa yaro.

Wucewa ta yi abinta, ta bar shi a nan tsaye yana yan dube dube a jikinsa.

Mashin mai taya biyu ta tara ta hau zuwa asibiti, kamar kullun yauma ta sayowa su gwaggo abinci a restaurant nasu, dama kullun idan zata dawo zata sai takeaway guda uku, Sadiq ɗaya, gwaggo ɗaya, sai maman Sadiq ɗaya, ita bata wani damu da cin abincin dare sosai ba, Sadiq yana sayo mata maltina ta sha ta yi barci abinta.

Kamar kullun tana isa asibiti Sadiq yana isowa, a tare suka jera zuwa cikin asibitin, sai murna Jehan take, an ce gobe mum zata farfaɗo.

Allah sarki gwaggo ta rame sosai kamar ba ita ba, kusa da ita Jehan ta zauna, tana kallon fuskar mum ɗinta.

Mum kamar ba mai jinya ba ta yi ƙiba sosai, saboda karin ruwa da jini da aka mata.

Gaishe da gwaggo Jehan da Sadiq suka yi, sannan suka tambayi jikin mum, da fara'a gwaggo ta amsa, Jehan zata sake yin magana wata hamshakiyar Hajiya wadda da ka ganta kasan nera ta zauna mata, tasha kwalliya da sarkan gold, ta zuba abin hannu shima na gold, ga wani dankareren lace da ta sanya a jikinta abin ba'a cewa koma.

Kariso wajen na su ta yi, tana faɗin "Hajiya Aisha wayan nan kuma su waye ne?" Ta yi maganar tana nuna Jehan da Sadiq, Nan gwaggo ta gaya mata ƴaƴan ta ne. Murmushi Haniyar ta yi tana faɗin "Kai amma suna da kyau sosai wlh" shiru gwaggo ta yi bata sake magana ba, su Jehan da Sadiq ba wanda ta tanka matar a cikin su, shi Sadiq dama ɗan abi yarima ne a sha kiɗa, duk abin da Jehan ta yi, shi yake yi shima, to da ya ga Jehan bata kulla matar ba, shine shima ya ki kulata.

Cikin gwababɓen fulatanci Jehan ta tambayi gwaggo wace ce wannan Hajiya, nan gwaggo ta gaya mata, kanwar Hajiyar ce a ka kwantar a ɗakin kusa da su tana jinya, yau Hajiyar tazo daga Abuja duba jikin kanwar tata.

Shiru Jehan ta yi bata sake cewa komai ba, gaba ɗayan su shiru suka yi kowa da abin da yake tunani

Yau sun jima sosai a asibiti, sai wajen karfe 10:20 sannan suka sallami gwaggo Jehan ta bata abincin ta suka wuce zuwa gida, sun bar gwaggo tare da wannan Hajiya suna hira.

Yau kasan cewar sun yi dare ko da suka fita bakin titi basu sami abin hawa ba, hakan yasa suka fara ta fiya da kafa, suna yi suna hira, har suka ci karfin tafiyar ba tare da sun sani ba.

Basu ankaraba sai sukaga har sun kusa isowa anguwarsu, hakan yasa suka ce bari su karisa da kafa kawai.

Sun ci gaba da tafiya suna hira, sun zo daidai hanyar da zata shigo da su anguwarsu wasu jibga-jibgan mutane masu bakin kaya da kuma bakin marks a fuskar su, suka tare su.

Daga Jehan har Sadiq sai da suka kusa sakin fitsari a wandon su, nan take jikinsu ya fara kerma, ga shi wayan nan mutane za su kai su goma, ga shi baka iya gane ko ala'mar kamannin su, saboda dare ne sosai akwai duhu, kuma koda ma ba dare bane, sun rufe ko'ina a cikin su, ba zaka gane su wanene bane.

Ɗaya daga cikin su ne ya matso kusa da Jehan ya fara magana kasa kasa "Ke ina wayar da kika yi recorded na oga Farooq? Ki bamu wayar ko kuma mu kasheki a nan, kuma mun kashe banza" Wani wahalallen yawu ta haɗiye, nan take zufa ya fara karyo mata, ina amafanin karyar da ta yi, ta tambayi kanta.

Tana kokarin yin magana, suka ji jiniyar motar yan sanda sun zo wucewa, a guje wayan nan mutane suka bar wajen, ita kuma Jehan da sauri ta juya ta nufi hanyar komawa asibiti, tana sauri tana tunani a ranta ta ja wa kanta bala'i, a tunanin ta komai ya wuce, ta tseratar da Hanan, sai ga shi ita kuma ta jefa kanta cikin bala'i.

Da sauri Sadiq ya bi bayanta, har suna haɗawa da gudu, Sadiq ya ce "Jehan me kuma zai mai damu asibiti? Tun da sun tafi mu wuce gida mana" girgiza kai ta yi tana faɗin "A'a Sadiq ba zancen komawa gida, tun da ka ga sun tare mu a nan to tabbas sun san gidan mune, Farooq ya gaya musu in da gidan mu yake, shi ya sa suka zo suka tsaya a bakin unguwar mu, yanzu dole asibiti zamu koma, zan je in sanar da su gwaggo meke faruwa" tana magana tana kwaɓawa da turanci.

Haka suka sake takawa da kafa har zuwa asibiti, dan ba abin hawa, kasan cewar kauye ne da wuri suke shiga.

Yadda suka bar gwaggo da Hajiya haka suka dawo suka same su, cike da tashin hankali Jehan ta sanar da gwaggo abin da ta aikata, na karyar da ta yi wa Farooq na tayi recorded na muryan sa yana yiwa Hanan maganganun banza, ga kuma abin da karyan ta zamar mata.

Sosai gwaggo ta shiga tashin hankali ta kuma yi mata faɗa sosai, a kan ba yanzu ba ko gaba ta guji yi wa mutun karyar abin da ta san bata aikata ba, ga shi yanzu ta ja musu bala'i.

Sun shiga tashin hankali sun rasa mafita, idan suka ce Jehan ta koma gida, to tabbas wayan nan mutane za su iya bin dare su mata yankar rago, domin Farooq ba shi da mutunci ko kaɗan, zamanta a asabiti kuma ba zai yi wu ba, hakan ya sa suka fara neman mafita ta hanyar shawara.

A nan ne wanann Hajiya ta ce musu idan ba damuwa zata tafi da Jehan zuwa gidan ta, daga nan zata sama mata aiki a gidan masu kuɗi, ko wani wata za'a rinƙa biyan ta dubu ɗari, idan anyi mata salary Hajiyar zata rinƙa turowa su gwaggo.

Babu tunani babu komai gwaggo ta miƙawa Hajiyar nan Jehan domin ita burinta kawai Jehan ta tsira da ranta, bata son wani abin ya sameta, rubuta musu number wayarta Hajiyar ta yi tare da address ɗinta na Abuja da kuma gidan iyayenta dake nan Katsina. Gwaggo ce ta karɓa takardar sannan suka yi wa Haniyar godiya, gwaggo ta ce Sadiq ya koma gida da safe Hajiya zata wuce da Jehan Abuja, kwata-kwata sun manta da zancen aikin Jehan, sun kuma mance da Ibraheem na bin su bashin kuɗi.

(Toh fah, haka za ku yi wa Ibraheem, shi yana can yana kokarin yadda zai lallaɓa Jehan ta samu ta yi aiki ta biya shi hakkinsa, lallai akwai cakwakiya)

Haka Sadiq cike da tsoro ya koma gida yana ta tunanin Jehan, ya yi sa'a daya bi hanyar mutanen basa nan, sun gudu, saboda yan sanda dake zagaye a wajen dan maka yan shaye-shaye, ita kuma Jehan a asibiti ta kwana a kan gobe za su wuce Abuja da Hajiya ta kai ta gidan aiki. Sai dai bata ji daɗin rabuwa da su gwaggo ba, amma bata da mafita dole ta bi Hajiya.

To bari dai mu leƙo Washington DC mu dawo

💓💓Washington DC💓💓


Zaune suke gaba ɗayan su a palon kasa, ban da Lion da kuma James da baya nan, sai uncle herry dake asibiti shima baya nan, Jay ma yana wajen punishment nasa, dan yau tun safe ya dasa daga in da ya tsaya.

Dukkansu kowa za abin da yake yi, Tga da John sun kafa kai a kan wayoyinsu suna latsawa, shi kuma daddy yana kallon News a makeken Tv su, while shi kuma Michael yana buga game a system. Dukkan su kayan shan iska ne a jikin su, barim ma Tga shi ko riga ma bai saka ba, daga shi sai gajeren wando, ya bar wayan nan dama daman damtsen hannun nasa a wajen, ga sarkan kros daya sanya a wuyarsa, sai sharholiyar su suke banda Jay.

Cikin nitsuwa Musharraf ya sauƙo daga sama izuwa cikin palon. Sannu ya musu sannan ya wuce zai zauna saman sofa.

Dukkan su ba wanda ya amsa sannun na shi. Tsawa Tga ya daga masa wadda ya sanya gaba ɗayansu ɗagowa "What brought you here?!!"

Kallon Musharraf Michael ya yi sanna ya dawo da kallon sa kan Tga da yake ta wani cika yana batsewa, Allah Sarki Musharraf har jikin sa ya

Please Login or Register in order to submit comment