Reading TRIPLETS BOOK 2 by Star Lady Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zan iya tafiya ba tare da an mana aure ba, dan ina ganin kamar idan na tafi bappa zai aura mata wani, shine bayan naje munyi sallama da ita, na wuce wajen Bappa na rokesa daya aura min ita kafin na tafi, da farko bappa yaki yarda sai da yaya Imran da yaya Irfan suka sa baki sannan ya yarda na bashi sadaki, a masallaci bayan sallar la'asar aka ɗaura mana aure, daman abun da yasa ban sanar daku ba, na bari sai na dawo ne in ɗauko ta in kawo muku ita, to ina shigo kasar nan kuma na wuce school nasu dan naje na ganta na ɗauko ta na kawo muku ita ku ganta, shine ta ɓata min rai har hakan ta faru tsakanin mu" kallon gefen ido Abba ya masa irin hararar wasan nan ya masa kafin yace "A'a ba dai ta ɓata maka rai ba, dama can da muguntan ka kadawo" ɓuye fuska Akil yayi a jikin Abba yana dariya kasa kasa, cakulkuli Abba ya shiga yi masa yana faɗin "A'a baka isa ba ai sai ka buɗe fuska muga juna ido da ido zai fi, dan rashin kunya ka kwaso zafin ka kazo tsakiyar rana ka sauke a kan ƴata gidan nan duka suna jin ka bakaji kunya ba sai yanzu zaka wani ɓoye fuska to wlh baka isa ba maza ɓuɗe muyi ido biyu" a shagwaɓe Akil yace "Kai Abba ka bari mana ni wlh kunyar ka nake ji" "Eyee kunyata ba, ai dole kaji kunya ta irin wannan ɗanyen aiki daka yiwa ƴata to Allah dai yasa ina da rabon jika" kara ɓoye fuska Akil yayi yana dariya yana jin farinciki

Jin motsin Ammie na zuwa ne yawa dukan su suka yi shiru Abba ya ɗan matsa gefe yayin da shi kuma Akil ya diro kasa daga saman gadon ya nufi hanyar fita

A bakin kofa sukayi karo da Ammie da sauri ya wuce ta ya koma bedroom nasa, kafin ma ta ɓuɗe baki tayi wani magana ya wuce ta, girgiza kai tayi tace "Zamu haɗu ne" ta kai karshen maganar tare da wucewa cikin bedroom ɗin Abba.

Akil kuwa yana shiga ya samu Aafia zaune kusa da Umaisha tana hawaye, kusa da ita yazo ya zauna yana faɗin "Kiyi shiru ki dai na kuka ki tashi kije ɗakin Akila ki kwanta ki huta kafin Akila ta dawo school sai kuyi hira zan kira bappa a waya na faɗa masa kina nan" banza tayi da shi ta ci-gaba da kukan tana mai jin kamar ta shaƙe shi dan haushin ya raba kanwar ta da budurcin ta a banza ba auren ta yayi ba, kuma ga maman sa tana cewa ba zai auri Umaisha ba shikenan ya cuci rayuwar Umaisha a tunanin Aafia kenan.

Ganin taki tashi ta tafine yasa ya miƙe ya riƙo hannun ta ya miƙar da ita, tana kokarin kwace hannun ta a fusace ya ɗaga hannu kamar zai mare ta sai kuma ya dakata, da ɗan karfi yace "Karki fara wuce mu tafi!" ganin ya haɗe rai sosai ne yasa ta hakura tabi bayan sa suka tafi ya kai ta ɗakin Akila ya dawo ya ɗauki jallabiyar sa ya sanyawa Umaisha ya wurzawa kofar ɗakin su key ya dawo ya kwanta kusa da ita yana mai jin matikar farinciki da annashuwa har cikin ransa.

Ita kuma Aafia kwanciya tayi saman gadon Akila tana kallon sama tana hawayen bakin ciki, har barci ɓarawo ya ɗauke ta

Ammie kuwa bala'i ta tsayar wa Abba wai dole yasa Akil ya dai na zancen auren Umaisha dan ba zata taɓa yarda ƴaƴan ta su aurin ƴaƴan talakawa kamar family sa ba, ayya Abba da yake tariga ta shanyesa yana son yan uwan sa amma babu halin nuna musu soyayya, sai kawai ya shiga bawa Ammie hakuri yana ce mata dole Akil ya bar zancen auren Umaisha, ba zai aure taɓa, ya nemi wata, sai daɗi Ammie take ji, bata san Umaisha kam already matar Akil bace.

Wannan kenan mu leƙa Daular mutuwa mu ga meke faruwa sai mu dawo

👹👹DAULAR MUTUWA👹👹

Gudu Rimsha take sosai kamar zata tashi sama Kausar na biye da ita a baya, kasan cewar cikin ramin akoi hanyoyin da dama sai suka kauce hanyar da suka bi da farko suka kama wata hanyar daban saboda tashin hankali da ruɗu, su kuma su barbushi sunyi gudu mai nisa a wajen basu haɗu da su Rimsha ba, suma su Rimsha ɗin sunyi gudu sosai har suka kasa ci-gaba da gudu basu ga daular mutuwa ba ya ɓace musu, zama sukayi kasa a wajen suna numfashi sama sama kamar ba zasu yi rai ba bayin Allah.

Suna zaune a wajen tun suna ganin haske kaɗan kaɗan har suka fara ganin duhu alamar dare kenan, kasan cewar wajen a karkashin kasa yake ba zaka iya wani banban tashi da yamma ba, danma akoi wasu wurare dake da huji kamar Windows a wajen hakan yasa ake ɗan samun haske kaɗan a wajen, ga yinwa ga kishin ruwa ga gajiya duk abun ya haɗe musu, banda sunan Allah ba abun da suke ambata a zuciyoyin su.

A takaice dai kwana sukayi zaune a wajen, basu samu ganin Ayla ba, suma kuma su Barbushi basu samu damar ganin su Rimsha ɗin ba saboda addua'o'i da suke samu ta ɓangarori daban-daban, dan ko Jehan ta dukufa sosai kwana biyun nan tana yiwa Rimsha addu'a dan kwana biyun tana yawan mafarkin Rimsha ɗin shiyasa ta dukufa da yi mata addu'a sosai, a ɓangaren gwaggo ma haka ne ta dukufa sosai wajen yi ma Rimsha addu'a dan dukkan su kwana biyun nan suna mummuna mafarki a kan Rimsha ɗin, ta gefen guda kuma ga malaman da mum ta bawa kuɗi suyiwa Rimsha saukan Al Qur'ani mai girma suma yau suka gama saukan Al Qur'ani shine ma dalilin da yasa Allah ya bawa su Rimsha damar kuɓuta daga daular mutuwa, sannan ga baba da Mustapha suma ba'a barsu a baya ba sosai suke wa su Rimsha addu'a a zuciyar su, hakan yasa su Barbushi basu samu daman ganin su ba.

Washegari ganin Kausar na kokarin mutuwa ne saboda yinwa da kishin ruwa yasa Rimsha tayi ta maza ta miƙe, Allah sarki itama yinwan take ji amma da ɗan sauran karfin ta tafi Kausar kwari, haka ta tattara karfin ta dukka ta goya Kausar a bayan ta tana jan kafarta a hankali hankali, dan duk kafar nata ya faffashe tun jinin ta na zuba har ya bushe wajen ya dai na zuba, tafiya take kamar zata faɗi kasa dan Kausar ta mata nauyi amma haka ta daure ta cije tana hawaye ta nufi hanyar da sukabi suka zo, ma'ana suka koma in da suka fara tafiya da farko.

Rimsha tayi tafiya mai ɗan nisa da Kausar a goye a bayan ta kafin su iso wata kofar dafaffiyar karfe, da kyar ta iya sauke kausar ta zaunar da ita a kasa, ta sa hannun ta ta kwance ruwan tsafin da duna ya bata wadda ta kulle sa a jikin igiyar rigan ta dan karya faɗi kasa, kamar yadda ya faɗa mata haka ta zuba ruwan kaɗan a jikin kofar sai ga kofar ta buɗe nan take wani haske ya kaure musu ido, lokacin rana ya ɗago tsakiyar duniya, da sauri suka rintse idon su dan sun jima basu ga haske irin haka ba

Sun ɗan jima a haka kafin Rimsha ta buɗe dara daran sleeping eyes nata da sukayi ja sosai, duk sun faɗa kamar ba wayan nan kyawawan idon nata masu kama da audiga dan haske ba, banda zara zaran eyelashes nata dake ɗan taimaka musu wajen fito da su da bazaka taɓa gane su ba saboda wahala da azaba da ta sha

A hankali ta fara bin wajen da kallo, bata ganin komai sai bishiyoyi masu cikar ganye, juyowa tayi tasa hannu zata ɗago Kausar ta goyata, Kausar tayi sauri dakatar da ita ta hanyar yunkurawa da kan ta ta miƙe, rungume juna sukayi dan su tallafawa juna suka fara jan kafafun su da kyar da kyar zawa wajen wurin

Sai kuma me, kungurmin daji ne sosai a wajen wadda baka gane gabas baka gane yamma, ga dogayen bishiyoyi masu abun tsoro, lokaci guda tsoro ya dira musu a ransu, tunani suka fara yi gara musu cikin daular mutuwa da wan nan wajen, domin koba komai cikin daular mutuwa akoi mutane nan kuma fa, sai karan tsuntsaye kuma da alama ba za'a rasa yamun dawa a wajen ba, macizai kam ma guarantee ne sai an same su ba adadi a wajen.

Shin nan ɗin ma wace kasa ce? Wani gari ne? Tashin hankali

Masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu


TRIPLET'S💞






# BOOK 2📚📙✍️


💔💔Episode 3💔💔


💔RIMSHA💔


A hankali suka fara kutsawa cikin dajin nan suna tafiya suna tangal tangal kamar zasu faɗi kasa, saboda wahalar da suka sha, duk sunyi wani iri dasu, sun koɗe futu futu, kamar ba su ba, kamar wayan da aka tono su daga rami, ko aka kwato su daga bakin kura, har wani duhun wahala sukayi, gashi sun manne junan su sosai saboda tsoro.

A wannan lokaci da suka fito sun samu damar kiran sunan Allah a baki, gaba ɗaya dark black curly hair Rimsha ya cukurkuɗe kamar bashi ne wannan kyakkyawan bakin gashi mai shekin ba, mai tashin kamshi, yanzu ya dawo duk dattin, kuran daular mutuwa ya buɗe shi, sai warin datti suke saboda wanka ma da ruwa kawai suke ba sabulu, bare kuma mayukan gyaran jiki, ita kam Kausar daman ba gashin gare taba, abunku da kan yarbawa basu da gashi sosai aguiguye kan nata yake, sai dai itama fa ba laifi tana da kyan ta daidai gwargwado.

Sunyi tafiya mai ɗan nisa kafin su iso wani katon rafi mai cike da ruwa, Allah sarki bayin Allah daman kishin ruwa suke ji kamar zasu mutu, suna ganin ruwan sukayi saurin isa wajen, suka kafa bakin su kamar shanu suka fara shan ruwan, basu damu ruwan da datti ko babu ba, su dai burin su kawai su sha ruwa.

Sosai suka sha ruwan sai da sukaji cikin su na musu barazanar fashe wa sannan suka dakata. Sai kuma me cikin sune ya fara murɗa musu, saboda yinwa da ya musu yawa, gashi sun zo sun ɗirka ruwa ciki empty ba abinci.

Kwanciya sukayi a bakin yafin cikin ciyayi dake wajen, suna murkusoso suna juyin azaban ciwon ciki, dukan su babu mai tallafa ma wani, saboda dukan su suna neman tallafi a wannan yana yi, kowannen su ta kan sa yake.

Almost 30mins suna haka kafin su sami ciwon ya ɗan lafa musu. A hankali Rimsha ta miƙe zaune tana kallon Kausar, sai kuma hawaye suka fara bin kuncin ta, lokacin da ta kalli Kausar Ayla ce ta faɗo mata a ran ta shiyasa take kuka. Kausar bata lura da kukan da Rimsha ɗin keyi ba saboda ita bata gama dawowa cikin hayyacin taba.

Sun ɗauki lokacin mai ɗan tsawo a wajen kafin su lallaɓa su tashi su ci-gaba da tafiya, basu san in da suka dosa ba tafiya kawai suke suna fatan Allah ya fitar da su daga wannan bala'i bakin dajin lafiya kar wani naman dawa ko wani abun ya kama su.

Ita dai Kausar bata tsorata da dajin sosai ba, kasan cewar ita bayarbiya ce, kuma asalin kasar yarbawa mafiyawancin gida jen su a cikin ɗan daji daji suke, sai dai ba mai girman wannan ba, ita kuwa Rimsha rainon madara da Ice cream su chocolate bata san wannan wahala ba, gata daman da tsoron bala'i Jehan ta fita jarunta sosai.

A takaice dai sunyi tafiya har rana ta kusa faɗuwa amma basu ga alamar karshen wannan daji ba, daga karshe da suka gaji, kasan wata itaciyar mangoro mai girman gaske suka samu suka zauna a wajen suna sauke numfashi.

Duk sunyi tsuru tsuru dasu gwanin ban tausayi, ji suke gara musu daular mutuwa da wannan azaba da suke ciki a yanzu, ba abinci, ba motsin ɗan Adam, sai kukan wasu halittu wanda basu san menene ba ne, a daular mutuwa kuma ana basu abinci sau ɗaya a rana kuma suna ganin mutane saɓanin nan.

Suna zaune a wajen har barcin wahala da gajiya ya kama su, zaune manne da junan su sukayi barci bayin Allah, sun sha wahala, ga ba abinci, babu wajen kwana, ba wani motsin ɗan adam a wannan daji, abun ya haɗu ya cakuɗe musu.

To su Rimsha sai dai muce asuba ta gari, bari mu koma Washington DC mu gani ko zamu dace.

💞💞 WASHINGTON DC💞💞

Ya kasa motsawa daga wajen, sannan ya kasa cire fuskar sa daga kan fuskar Michael, dan ji yake kamar idan ya raba fuskar sa dana Michael zuciyar sa zata iya fasa kirjin sa ta fito waje, yaki bari ayiwa Michael sutura dan har zuchiyar sa bai yarda da cewa Michael ya mutu ba.

Duk dakiya da taurin zuciya irin na soja, sai da wayan nan jibga jibgan sojojin suka ji zuciyar su ta raunata, sai da sukaji mugun tausayin ogan su ya kama su, har wani fuskar tausayi sukayin yau.

A hankali hankali kunnen sa ta fara jiyo masa wani abun da ji yake tamkar gizone kawai kunnen sa ke masa, kara nitsuwa yayi dan ya tabbatar wa da kan sa shin abun da yake ji da gaske ne ko dai karya ne.

Tabbas gaskiyane sautin bugun zuciyar Michael ne ke fita a hankali hankali. A sukwane ya raba fuskar sa dana Michael ɗin, ya mai da kan sa sai tin kirjin Michael dan ya tabbatar da abun da yake ji, kasa kunnen sa yayi sai tin wajen bugun zuciyar Michael.

A sukwane ya ɗago yana faɗin "Call doctors for me!!" Yayi maganar da karfin gaske

Ji kake dap dap wayan nan jibga jibgan sojojin sun fita da gudun gaske dan suje su kira likita,
_shi kuma hannu yasa ya tallaɓo kan Micheal ya ɗan ɗago shi dan ya samu damar yin numfashi da kyau, dan kan sa yayi kasa sosai daman.

Kusan gaba ɗaya manya manyan likitocin dake cikin asibitin ne suka biyo bayan sojojin nan, da gudun gaske suka shigo cikin room ɗin.

Har likitoci nan suna rige rigen saka hannu, su karɓi Michael daka hannun Romeo, dan ko ba a faɗa musu ba sun san kiran da Romeo ya musu kenan.

Cikin kankanin lokaci suka dukufa aiki a kan Micheal babu kama hannun yaro, gefe guda Romeo ya koma ya tsaya yana shafa kyakkyawa dark black curly hair sa, yana cizan lallausan laɓɓan sa, tare da furzar da iska mai zafi daga bakin sa, a zuciyar sa yana yiwa ɗan uwan sa addu'ar Allah ya tashi kafaɗun sa.

Abun ka da kwararrun likitoci, ga kuma kayan aiki na zamani masu inganci, sannan ga kuɗi, dan in baka da kuɗi ko da kayan aiki ba mai kula ka.
Cikin ƙanƙanin lokaci suka bawa Michael taimako sosai, ɗaya daga cikin taimakon da suka bashi shine sunyi kokarin wajen gyare wajen da yake bleeding, daman wajen kan sane ta baya kunnen sa ya fashe, sai kuma gefen cikin sa nan ma yaji ciwo sosai, wajen na bleeding.

Ba karamin daɗi sojojin nan suka ji ba, dan ko ba komai hankalin ogan su zai kwanta, idan hankalin ogan su ya kwanta, suma hankalin su zai kwanta su samu nitsuwa, sai dai abun da basu sani ba shine, ogan su fa hankalin sa ba zai kwanta ba, dan ko ya gama da case ɗin Michael akoi James a site.

Daddy kuma yana can gida yana fama da kokarin ceto rayuwar pastor, Tga John Jay duk suna gida hankalin su a matukar tashe, dan Tga ya sanar da su John abun da ya faru da Michael, sau biyu John yana suma, suna zuba masa ruwa yana farfaɗowa, kafin ya samu kan shi, saboda John yafi su Jay shakuwa da Michael, dan tare suke tsula tsiyar su a School, kuma mafi yawancin lokuta tare suke fita suje wajaje daban daban, irin su party da sauran su, shiyasa John yafi su Jay shiga tashin hankali, kuma duk wannan suma da yake yana farfaɗo dan bai yardan wa zuciyar sa Michael ya mutu bane, idan ya yardan wa zuciyar sa, kila mutuwa zai yi ma gaba ɗaya, dan son da yakewa Michael ba sone na wasa ba.

Good 3 hours doctors suka ɗauka a kan Micheal suna bashi kulawa yadda ya dace. Sai da suka tabbatar sun masa duk wani abun da ya dace, sun tabbata ya fita daga haɗari, sannan suka nemi iznin komawa office nasu daga wajen Romeo, Romeo ya basu izinin komawa kam sai dai yace likitoci uku su tsaya kusa da Michael su lura da shi sosai, kar su kuskura su fita daga room ɗin, hakan kuwa akayi, likitoci uku ne suka tsaya a kan Micheal sauran kuma suka koma bakin aikin su, kowannen su ya koma cikin office na sa.

Romeo bai bar hospital ɗin nan ba sai wajen 11 na dare, sannan ya wuce gida, amma kafin ta tafi sai da ya sanar da likitocin a kan gobe za'a mai da Michael gida wasu daga cikin likitocin su bisu gida suje suyi jinyar sa a can, dan su daman family William jacop basa zuwa asibiti, asibitin da kan ta take zuwa ta same su, ma'ana likitocin suke zuwa gida suyi jinyar su, yanzun ma Romeo bai san lokacin da aka kawo Michael hospital bane da ba zai yarda ba, sai dai ya ɗauko likitoci azo gida a kula da shi, yanzu kuma ba halin su ɗauki Michael a yau ne, saboda na'urori da aka dasa mashi, da sauran kayan aiki, dole dai su hakura sai gobe zasu samu daman ɗaukan nashi zuwa gida.

Jibga jibgan sojoji 30 Romeo ya sanya su tsaya a hospital ɗin, dan kula da Michael. Cikin ɗakin da Michael jibga jibgan sojoji 6 ne aciki dan bashi kyakkyawan tsaro, ga kuma kwararrun likitoci uku a zaune kusa da shi, abun ku da masu hannu da shuni, abun ba'a magana sai dai muce Masha Allah. Bakin kofar ɗakin kuma sojoji huɗu ne, sauran sojojin kuma suka kewaye asibiti gaba ɗaya.

Ko da Romeo ya koma gida, zaune su Tga suke gaba ɗayan su a palon kasa, bai bi ta kan kowa ba ya wuce da sauri ya nufi sama, saboda jinin Michael dake jikin rigan sa, baya son dad yaga jinin, za'a samu matsala idan ya gani.
Dad na tambayar sa ina Michael, amma bai kula dad ba, saboda bai son tsayawa har dad yaga jinin, yanzu sai ya birkice musu, shima dad ganin Romeo bai tsaya ya bashi amsa ba, sai yayi tunanin ba lafiya, dan haka sai ya miƙe da sauri ya bi bayan Romeo.

Koda ya shigo bedroom na Romeo, Romeo baya ciki, sai dai saukan ruwa dad yaji daga toilet, alamar wanka Romeo yake yi kenan, zama dad yayi a gefen gado yana jiran fitowar sa, dan yaga cikin kwayar idon sa ko zai ga wani abun.

Romeo na fitowa kallo ɗaya yayiwa dad, ya kawar da kan sa yana faɗin "My dad what are you doing here?" Tun da daddy yaji Romeo na tambayar sa me yakeyi a nan, sai yaji wani irin dan bai taɓa masa makamanciyar tambayar nan ba, daga nan yasan ba lafiya ba, a gefen shima Romeo duk sai yaji wani iri, bai san lokacin da yayiwa daddy wannan tambayar ba, ganin dad ya sa shi ya shiga ruɗune dan yasan halin dad sarai, zai tsare sane da tambayoyi, shiyasa tun bai fara yi masa tambayoyin ba shi yayi saurin tambayar me dad yake yi a nan.

Kamar wani mara gaskiya da sauri ya wuce dressing room nasa, yau ko shafa mai ɗin ma ba zai yi ba tun da dad na ɗakin, daddy kuwa ya zuba masa ido yana kallon sa yana mamakin me ya firgitar masa da lion nasa lokaci guda ne haka, duk yayi wani iri da shi, abun da dad bai taɓa ganin makamancin haka a tattare da lion ɗin ba sai yau.

Dad na zaune har lion ya gama shiri cikin kayan barci masu kyau da tsada, ya dawo cikin bedroom ɗin sai tashin fitinannen kamshi yake, sai wani ɓoye fuskar sa yake bai son suyi ido huɗu da dad, dan yasan dad akoi kaifin basira, duk da matsalar da yake da shi, yana da basirar gane abu da kallo ɗaya, suna haɗa ido zai gane lion na cikin damuwa.


"What is wrong with you my lion?" Dad ya jefo masa tambaya
Tamkar saukan aradu haka yaji tambayar dad

Juyowa yayi ya kalli dad kallo ɗaya, sannan ya kau da kan sa gefe, a nitse yace "Nothing My dad, have you noticed any change from me?"
_miƙewa dad yayi yazo kusa da shi yana faɗin "tell me the truth my lion, what is wrong with you? I knew there is something wrong with you, because I have seen some changes on your face" Ji yake kamar ya fasa ihu, saboda tsananin tashin hankali da yake ciki, tambayoyin dad suna sawa yaji tamkar ana caka masa mashi a zuciyar sa, abubuwa sun haɗe masa, bai san in da James yake ba, ga kuma Michael kwance a gadon asibiti rai a hannun Allah, tsananin ciwon da jikin sa ke masa ma kawai ya ishe shi, ba sai ya samu kari ba, ko ina na jikin sa ciwo yake masa, sakamakon ciwon da Michael ke ciki da kuma ɓatar James.

Jin yayi shiru ne yasa dad yace "why are you hiding something to me, I'm i not your Father?" Rungume daddy yayi yana ɓoye fuskar, dan saboda dara daran idon sa har sun canza launi, bai son daddy ya gani, "My lion please t... Bai bari dad ya kai karshen maganar ba yayi saurin rufe masa baki yana faɗin "Babu wani abun da na ɓoye maka My dad, just kawai I'm feeling headache ne" kokarin raba jikin su dad ya fara yi, dan ya samu damar ganin cikin kwayar idon lion, amma ina lion yaki yarda da hakan, dan ya rungume dad sosai, yau ga ikon Allah.

Da dai dad yaga lion bai da niyar sakin sa, sai yace "Sorry muje na baka drugs" "No dad ba sai ka bani ba, I I'll take it by myself" yayi maganar with full confidence, ta yadda dad zai yarda eh da gaske babu komai ɗin.

"Where is Michael and James, since morning banga James ba, Michael kuma tun ɗazun da yayiwa pastor wannan abun, ban sake jin motsin shi ba" har wani dum dum kirjin Romeo ya bada bugu, shi damuwan sa ɗaya, idan daddy ya san halin da James da Michael suke ciki, mawuyacin abune su ɗauke sa da rai a daren nan, zuciyar sa zata iya bugawa, dan Triplets na sa, sune duniyar sa, sune rayuwar sa, gashi ba isshesshen lafiya ke gare shi ba, ga tsufa, yana da saurin rikicewa a kan abu, abu kaɗan yake birkita shi.

"James baya nan, ya tafi Spain, Michael kuma yana white house" Romeo ya bawa dad amsa yana raba jikin su,
"Me James yaje yi Europe? Kuma why bai faɗa min ba?" Wucewa Romeo yayi, ya haye saman bed nasa yana faɗin "Ni na aiki James Spain akoi abun da zai karɓo min a can" shiru dad ya ɗan yi, kafin yace "Okey let me call his number" "No dad, no need ka kira shi, saboda yana tsaka da min aiki, idan ka kira shi za'a iya samun matsala" yayi maganar yana kokarin jawo wayar sa da system nasa, to dad yace masa tare da matsowa kusa da shi ya manna masa kiss a goshi, shima lion ɗin juyowa yayi, ya mannawa dad kiss a kumatu, daga nan sukayi sallama dad ya nufi hanyar fita daga bedroom ɗin, zuba masa dara daran blue eyes nasa lion yayi yana kallon sa cike da so da kauna.

Har ya kai bakin kofa zai fita, sai kuma ya dakata tare da juyowa, a sukwane lion ya kawar da kallon sa gefe, dan kar dad ya zargi wani abu
"Ya kamata ka dai na cin abinci tsakiyar

Please Login or Register in order to submit comment