Reading Abban Sojoji Takun Karshe 2&3 complete by Boss Bature Chapter 71 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta kuma yi da wani sabon kukan tamkar ranta zai fita,Sam ta kasa buɗe baki tayi magana,

"Ya Sauke duk wani girman kai nashi,Ya ajiye matsayinshi duk don saboda ke ɗinnan,Don Ya samu soyayyarki,da kanshi ya nemi da in koya mashi soyayya saboda yana son ya faranta maki,Yana kuma son ki gane cewa ba jikinki yake so ba,Zuciyarki yake so,kuma kinyi kuskure da iliminki da hankalinka,kika bari Mijinki yake kwana da baƙin cikinki acikin zuciyarshi!?"

Rass taji gabanta Ya faɗi,girgiza kai Omar yayi,tare da juyawa rai a6ace ya nufi hanyar fita daga ɗakin har ya ruke handle ɗin ƙopar ya kuma juyowa ya kalleta,
  "Ina ƙara tunasar dake,Gobe da Safe zai tafi,shawara ta rage taki,wlh don kina ƴar uwata ne yasa na zauna ina yi maki wannan gargaɗin,Saboda ina sonki dashi,Kuma kema kina sonshi,wannan damarkice ta ƙarshe kiyi tunani kafin nan da safe,nabarki lafiya,"

Yana kai ƙarshen Maganarshi,Ya buɗe kopar ya fuce waje,

Tashin hankali,Wani irin zazza6ine Ya lullu6eta,hawaye ta ko'ina saman fuskarta,wani irin tuƙuƙin baƙin ciki take ji acan ƙasan zuciyarta,sunan Eva ya tsaya mata aranta,saboda ta ta6a jin sunyi magana akanta a lokacin baya shi da Omar,har yake cewa in ma akwai Macen da ya dace ta mallake shi,to itace,

  A hankali ta soma ambaton"Innalillahi wa'inna ilahirraji'un,"

Maganganun Oummansu ta shiga tariyowa acikin kanta,daƙyar ta iya lalla6awa ta haye saman gadon ta kwanta,sosai tashiga raira kuka kamar jinjira jikinta sai kerma yake yi,Wani irin kishine ya rufeta,cikin shesshekar kuka take faɗin"Ya Rafayet zai tafi U.s ya barni,zai je ya aureta,"nutsar da fuskarta tayi jikin pillow tana ta raira kuka,

A daren Ranar Mutun biyu basu runtsa ba,Waɗanda zuciyoyinsu ke cikin halin ha'ula'e,kamar yadda Sgr ya kwana kwance saman gadonshi cikin mawuyacin hali,Haka itama Sehrish ta kwana da tunanin abu biyu,kalaman Oummansu da kuma kalaman Marshal Omar sun tsaya mata aranta,shi kanshi Omar ɗin bai samu isasshen bacci ba,saboda damuwar daya shiga duk akan Ɗan Uwanshi,

Wuraren Sallar Asuba Sehrish tana a kwance kamar matacciya,jikinta duk ya saki,ga zazza6in da take fama dashi tare da matsanancin ciwon kai,daƙyar ta samu ta sauko daga saman gadon ta shiga toilet,agaban Sink ta tsaya tana kallon kanta cikin Mirror,fuskarta tayi jaga jaga da hawaye hada majina,jan bakin data shafa duk ya 6ata fuskar,duk ta harmutsa gashin kanta,tasha kuka sosai,lips ɗinta duk sun kumbura,hancinta yayi jawur dashi saboda matsar daya sha,tajima acikin Toilet ɗin kafin ta samu tayi alwala,

Lalla6awa tayi ta fito daga toilet ɗin ta tunkari wardrobe ɗin kayanta,hijab ta ɗauko tare da darduma ta shimfiɗata,daƙyar ta samu ta tattara natsuwarta kafin ta kabbara sallah,bayan ta kammala Sallar ta zauna tare da ɗaga hannuwanta,tana Addu'a hawaye na shararowa akan face ɗinta,jikinta duk yayi sanyi,A saman dardumar bacci ya ɗauketa,

Baccin bai kaiga yin nisa ba aka soma kwankwasa ƙopar ɗakin,kwan kwan,can cikin bacci take jin bugun ƙopar,firgigit ta farka,zufa sharkaf akan fuskarta tamkar an watsa mata ruwa,bakomai bane ya fado mata aranta ba fa ce Maganar Omar na cewa Yau Sgr zai koma U.s,A hargitse ta miƙe tare da nufar ƙopar tasa hannu ta bude,Amrish ce a tsaye jikinta sanye da hijabi,ganin Sehrish cikin damuwa yasa tace"Meya faru ne?baki da lafiya ne?a ruɗe tayi tambayar,

Sehrish bata tsaya jin amsarta ba,duk hankalinta ya tashi,ta gefen Amrish tabi da gudun gaske ta nufi babban falon gidan,babu kowa duk basu tashi daga bacci ba,Upstairs ta haye har tana tuntu6e wurin taka matattakalar,Idanuwanta sun makance tana tsoran ta rasashi,a fujajen ta faɗa part ɗinsa,shigarta falon keda wuya,Sai ga Sgr Ya turo trolley a hannunshi,Ya kammala shirin shi tsaf zai tafi Airport,Jikinshi nasanye cikin jeans da T-shirt,fuskarshi sam babu annuri akanta,ga hannunshi daya jima rauni,

Cikin sanyin Murya ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet,"ɗagowa yayi da idanuwanshi akan fuskarta,ita kanta ta tsorata da ganin launin idanuwanshi,Sun yi jawur dasu gwanin ban tsoro,tsantsar 6acin raine acikinsu,bai amsa kiran sunanshi da tayi ba,tamkar ma baisan da zuwanta ba,janyo trolley ɗinshi yayi kaitsaye ya nufi hanyar fita daga falon inda take a tsaye,tayi tunanin zai kula ta,amma ko kallo bata ishe shi ba,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,tuni hawaye sun wanke fuskarta,Yana ƙoƙarin bi ta gefenta ya wuce,a hanzarce tayi saurin sanya hannu ta ruko damtsen hannunshi,
  Muryarta na kerma tace"Ya Rafayet,idan ka tafi ni kuma fa?ya kakeso nayi da rayuwata"?

Runtse idanuwanshi yayi"ki sakarmun hannuna,tunkafin ranki ya 6aci,"A kausashe yayi maganar,

"Na yarda kayi mun duk wani hukunci da ya dace dani Saboda bani da hankali,amma dan Allah kada ka tafi ka barni,"
  Tana kai ƙarshen maganar,ta faɗa saman faffaɗan kirjinshi ta rungumeshi sosai tare da fashewa da matsanancin kuka,har cikin zuciyarshi yake jin kukan nata,
   "Ya rafayet am sorry,bazan ƙara ba,"cikin shessheƙar kuka tayi maganar,lokaci guda kuma ta ɗauke ɗuff,a hankali ya buɗe idanuwanshi tare da sauke su akanta,tayi tighting ɗinshi sosai,kamar ance za'a ƙwace mata shi,
Nauyayyiyar ajiyar zuciya ya shiga saukewa,wani irin sanyine ya ratsa zuciyarshi,sakin trolley ɗin hannunshi yayi tare da ruƙota,ya ɗago da kanta daga jikinshi,da alama ta sume,fuskar nan tayi jaga jaga da hawaye,ta jigata sosai,jikinta yayi zafi sosai,tsantsar sonta da ƙaunarta ne acikin zuciyarshi,kamar ya haɗiyeta cikin cikinshi haka yake ji,
  Gaba ɗaya ya sa6eta saman kafaɗarshi,ya juya da ita zuwa bedroom dinshi,a saman katafaren gadonshi ya sauketa,ya gyara mata kwanciyarta,ya kasance tana fuskantar ceilling,hijabin jikinta ya cire mata,ganin yadda take zufa,a gefe ya ajiye hijabin,ya sauko daga saman gadon ya fita palour,within minute ya dawo hannunshi ɗauke da bottle water mai sanyi,gefen gadon ya zauna bayan ya buɗe murfin ya tarfa ruwan a hannunshi ya yayyafa mata shi asaman fuskarta,nan take taja dogon numfashi haɗi da sauke ajiyar zuciya ajere,tunkafin ta buɗe idanuwanta,ta soma sambatu"ya rafayet kada ka tafi ka barni,bazan iya rayuwa batare dakai ba,'

  Ajiye bottle din yayi saman drawer,kafin ya hau saman gadon gaba ɗaya,a dai dai saitin fuskarta yakai tashi fuskar,zuba mata ido yayi yana kallon yadda take ta sambatu
  "Reesh!You know you love me, but why kike wahalar dani"?he said calmly,jin muryarshi yasa ta buɗe idanuwanta,sunyi luhu luhu cike tab da ƙwalla,
   A hankali take kallonshi,yayin da shima yake kallonta,batare da kyaftawar ido ba,tamkar zasu haɗiyi junansu,saboda tsabar so,
   Ganin tana ƙoƙarin sake fashewa da kuka,yasa shi yin saurin toshe mata bakinta,da tafin hannunshi"its ok,u don't ave to cry,tunda gani a kusa dake,"
  Lumshe idanuwanta tayi tare da sake buɗesu akan fuskarshi,zame hannunshi yayi daga kan fuskarta,
"Ya rafayet,Am really sorry,pls don't leave me,i can't survive without you,"
Kalamanta ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya sukeyi ba,
  "why reesh?kin tada mun hankalina,ko bacci bana iyayi just because of you,kin fusata ni sosai,kin sanyani zubar da hawayena,'
  Girgiza mashi kai tayi"Bazan ƙara ba,"
  "Kin yarda cewa inasonki?ba jikinki nakeso ba?kuma kin amince zaki rayu dani a matsayin Mijinki Uban ƴa'ƴanki"?
  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,
Kafin tace"na aminta dakai,Na yarda da irin son da kake yi mun,kuma ina namen yafiyarka,akan misunderstanding din da muka samu,ban kyauta maka ba,its all my fault,nice ƙarama koba haka ba,kai ɗan uwana,Yayana kuma Mijina,nice a ƙasa dakai,amma ban duba hakan ba......"
  Bata kai ƙarshen maganar ba,ya dakatar da ita,ta hanyar sanya yatsanshi ɗaya asaman lips ɗinta,
   "Komai ya wuce a wurin,nima ina neman yafiyarki akan laifin da nayi maki,"
  Kallonshi kawai take yi,ba ƙaramin mamaki Sgr ya bata,ta ƙara yarda da irin son da yake yi mata,ya canza mata ba kamar da ba,
  "Nima komai ya wuce A wurina,amma pls,ka fasa tafiya U.s din,idan ma zaka tafi ƙafata ƙafarka,don bazan bari na rasaka ba,"
  Ƙayataccen murmushin gefen fuska Sgr ya sakar mata,gaba ɗaya ya tafi da tunaninta,natsuwa tayi tana kallon kyakkyawan murmushinshi,ƙurawa juna ido sukayi wani irin kallon so suke jefawa junansu,

A wannan yanayin na shauƙi,Marshal Omar ya faɗo bedroom ɗin,Yazo da niyar ya lallashi Sgr akan ya fasa tafiyarshi,tun a palour yaci karo da trolley an ajiyeshi,yana zuwa bakin ƙopar ɗakin,ba zato ba tsammani ya hango romeo da juliet,abun ya bashi mamaki,Yadda ya samesu,manne da juna,sun ƙurawa juna ido,kamar zasu cinye junansu,Ƙayataccen murmushi marshal Omar ya saki,yadda kasan wani zautacce,Su suke yin soyayyar amma yafi su jin daɗinta,a hankali Ya furta Alhamdulillah Ya Allah,Na gode maka daka cikama ɗan uwana burinshi,Nima Ya Allah ka cikamin burina na ganin na mallaki hosana,A matsayin matata,Uwar ƴa'ƴana,Ya Allah ka dawwamar da farin ciki acikin zukatanmu,Ya Allah ka ƙara haɗa kan masoyan nan,ka albarkance da samun zuri'a ɗayyiba,

Bai bari sun ganshi ba,juyawa yayi da sauri yabar part ɗin,A ƙopar palourn Ya tsaya tare da zura hannu cikin aljihun wandonshi,Ya zaro wayarshi,Layin hajiya azeema ya dannawa kira,sae faman sakin murmushi yake yi,kamar wanda Akayiwa Albishir da gidan Aljanna,yafi kowa farin cikin wannan ranar,

A lokacin da kiran Omar ya shiga,Hajiya azeema na kwance bata farka daga baccin asuba ɗin data koma ba,ringing ɗin wayartane Ya tayar da ita,hannu takai saman side drawer ta ɗauki wayar,ganin sunan daya bayyana akan screen ɗin wayarna yasa ta cewa"to fa,Omar ne ke kira tunda safe,to Allah yasa muji alkahiri,
  Ta ambaci hakan tare da ɗaga kiran nashi,ta manna wayar a kunnanta,
  Gaisawa suka fara yi kafin tace"Ya Andace ko kuwa har yanzu ba canji"?
  Muryarshi da alamun farin ciki atattare da ita,Yace"Congratulation Mommy azeema,munyi winning,"tunkafin Ya karasa maganar tace"Alhamdulillah Ya Allah,'ta ambaci hakan yayin da take miƙewa zaune,
  "Omar shaƙa mun naji,wlh aƙagare nake,Meya faru,sun shirya,Sehrish ta janye maganar sakin,"
  Dariya omar yayi sosai,jin yadda take ta jero mashi tambayoyi,
  "Aunty ae yanzu haka daga part dinsa nake,Na same su manne da juna,maganar saki ta ƙare,Zama na har abada,"daga haka Omar ya kwashe duk abunda ya faru tundaga daren jiya har zuwa yau da safe daya same su,Ya sanar da ita,
  Saboda tsabar farin ciki,Saukowa tayi daga saman gadon hannunta manne da wayar,Ta shiga yin rawa,tsantsar farin cikine akan fuskarta,
  "Mommy,suna buƙatar wasu abubuwa da zasu ƙara danƙon soyayyarsu,amma kafin nan,Yanzu dai suna buƙatar lafiyayyen breakfast,don jiya ɗan uwana baici komai ba,"
  Murmushi hajiya azeema tasaki kafin tace"in sha Allah,Yanzu zan tafi kitchen don in shirya masu,"
  "Yawwa aunty,mun gode sosai,sai munzo yin godiya nida rafayet,"
  "Haba dai,ae duk yiwa kaine,kada ka wani damu kanka,Amma ya tsakaninka da hosana?Ba tada matsala"?
  Omar yace"Nikaɗai zan iya da hosana,Bata da matsala,"
  Jinjina kai tayi"shikenan omar,duk da haka zan dage damtse wurin ganin na koya mata abubuwan da suka dace,"
  "Thank so much auntynmu,mai son ganin farin cikinmu,"
  Murmushi ta saki"yanzu bari naje na shirya masu breakfast din"
   Daga haka su kayi sallama dashi,Ajiyar zuciya ta sauke fuskarta ɗauke da murmushi ta ajiya wayar sama drawer,

A hanzarce ta nufi hanyar fita daga ɗakin,tana kokarin buɗe ƙopar ɗakin,Amrish ta turo ƙopar,jikinta sanye da jallabiya black colour ta yafa mayafi akanta,
  "Amrish har kin shirya kenan"?
Ɗaga mata kai tayi"eh mommy,"
  'Meya faru naga fuskarki kamar da alamun damuwa attare da ita,"
  Cike da damuwa amrish tace"ɗazu da zan shiga ɗaki,naci karo da sehrish,fuskarta sharkaf da hawaye,wlh na shiga damu sosai,bansan inda ta dosa ba,har tambayarta nayi ko bata da lafiya,Amma bata tanka mun ba,sai dai kawai naga ta watsa da gudu..."
  Hannu hajiya azeema tasanya tare da shafa gefen fuskarta"Calm down ur mind,A halin Yanzu sehrish tafi ki ƙoshin Lafiya,tana cikin farin ciki,babu abunda ke damunta,don haka kema ki kwantar da hankalinki,"
Ajiyar zuciya amrish ta sauke,haɗi da yin murmushi,
  "Muje waje,bari nayiwa wani magana acikinsu sai ya kaiki gidan,"
  Ta ƙarasa yin maganar,tare da yin gaba,Amrish tabi bayanta,
  Suna saukowa Babban Falon,Sai ga kanal Yusif ya fito daga part ɗinsu sai faman sauri yake yi,jikinshi sanye cikin shadda brown colour,wani irin ƙamshine ke fita ajikinshi,
  "Yawwa yusif"hajiya azeema ce ta kwala mashi kira,A hanzarce ya juyo 6angaren da suke,ganin hajiya azeema yasa shi sakin murmushi,da sauri ya tunkari wurinta,yana ƙarasawa ya soma gaisar da ita"Ina kwana Auntynmu,An tashi Lafiya,"
  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Lafiyalou,Alhamdulilla,Ina zaka je naga kana ta faman zumbula sauri,"
  "Inaso zanje dubo jikin abokina ne,An farmakesu ne wurin aiki da aka turasu,yanzu haka yana asibitin yaya rafayet,acan aka kwantar dashi,
  "Allah sarki,bawan Allah,Allah ya bashi Lafiya,"acewar hajiya azeema,
  Kallon Amrish yayi,ta sunnar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta,
  "Wannan fa,ina zuwa"?
Da sauri tace"Ina kwana yaya yusif,"
  "Lafiya lou,"cike da jin kunyarshi amrish ta amsa mashi,
"Tana so zataje kwaso kayanta ne a gidansu,ni nace ta shirya zanyiwa wani magana yakaita gidan,"
"Ba damuwa,Zan sauketa,in yaso saina wuce asibitin,kafin ta kammala kwasar kayan,sai na dawo na ɗauketa,"
Wani irin farin cikine ya lullu6e amrish,
  Godiya hajiya azeema tayi mashi"nagode ssai,Sai kun dawo,"
  Gaba yayi amrish tabi bayanshi,bayan sun fita,Yace ta tsaya ya dauko motarshi,Jim kaɗan sai gashi yayi driving ɗin motar,har zuwa inda take a tsaye,buɗe motar amrish tayi kafin ta shiga daga ciki,yana a diver seat tana a gefen shi,karya kwana yayi,kafin ya fisgi motar da gudun gaske ya fuce dasu,

Lokacin da suka hau titin a tsanake yake yin driving ɗin,har suka isa unguwarsu,adai dai ƙopar gidansu Amrish yayi parking ɗin motar,juyawa ya ɗanyi gefen da take ya saci kallonta,tare da cewa
  "Zan dawo na ɗauke ki,nan da 30 minutes,ina fata bazaki gaji da jirana ba,"
  Murmushi ta ɗan saki tare da kallonshi,suka haɗa idonsu dashi,tayi mamakin irin sanyin kyan dake gareshi,mai matuƙar jan hankali,musamman kwantaccen sajen gefen fuskarshi,
  "Nagode sosai,Ya yusif,sai ka dawo,a gaishe mun da mara lafiyan,"
  Mayar mata da martanin murmushi yayi"ki kulamun da kanki,"
  "Kaima haka,"tana ambaton hakan ta buɗe motar ta fuce,

A buɗe ta samu ƙopar dake jikin gate ɗin gidan,hannu tasa ta tura ƙopar ta shiga daga ciki bakinta ɗauke da sallama,murmushi ta saki lokacin da tayi arba da baba mai gadi,zaune saman tabarma,Ga tray agabanshi mai ɗauke da soyayyun kaji,Ga kayan marmari,Ga kuma lemu acikin cup  hada kankara acikinsa,duniya tayi kyau,
  "Assalamu akaikum,"jin muryarta yasa baba mai gadi yin hanzarin kai idanuwanshi kanta,washe baki ya soma yi,ya miƙe ya nufeta"Allah sarki Amrishi,yau kece da kanki,ashe ba rabon in rigaki zuwa,don yanzun nan nake cewa da zarar na kammala yin karin kumallona,naba furannin can ruwa,Zan shirya inzo har gidanku in duba ki,"
  Zuƙunnawa amrish tayi tare da gaisar dashi,ba ƙaramin daɗi yaji ba,shi kanshi ya lura da irin sauyawar da tayi,don da lokacin bayane ko kallo bai ishe taba,balle har ta gaishe dashi,"
  Bayan sun kammala gaisawa,tace"dama,nazo kwasar kayan sawata ne,"
  "Oh to,bari na ɗauko maki key ɗin,"yakai ƙarshen maganar,tare da juyawa ya nufi cikin ɗakinsa,jim kaɗan ya dawo hannunshi,ruke da key ya miƙa mata,tasa hannu buyi ta kar6a kafin ta wuce cikin gidan,

Komawa baba mai gadi yayi saman tabarmar ya zauna,sae faman washe baki yake yi,duk murnar ganin amrish,A fili yace"Mutanan kirki,gashi har zun canza yarinyar nan,Kai Allah dai ya saka masu da mafificin Alkhairinsa,nima ata dalilin Yaron nan da muka taimaka,Sunyi mun alheri,mahaifinsu ya dunƙulo kuɗi har dubu ɗari shida ya damƙa mun,gashi yanzu inata Cin kaji,"sai faman sambatu yake yi,

Amrish kuwa bayan ta shiga gidan,bedroom ɗinta ta shige,ta kwashi kayanta acikin trolley,hada agogon diamond ɗin junaid ta haɗo don ta mayar mashi da abunshi,a falo ta zauna tana jiran dawowar kanal Yusif,har kitchen ta shiga ta dafa indomie ta zubota acikin plate ta zauna saman Sofa,tana ci tana tunanin Kanal Yusuf,

*Boss Bature*

Bayan tafiyar Amrish da kanal Yusif,juyawa hajiya azeema tayi izuwa kitchen,Anan ta samu abu tare da Mommy da saude suna girke girken breakfast ɗin gidan,gaisawa suka fara yi,kafin ta shiga shirya masu lafiyayyen abinci,mutun biyu ta shirya mawa,Na Omar da kuma Na Sgr,Har ɗaki taje ta kira hosana don takai mashi abinci,a lokacin suna kwance saman gadonsu,ita da jahad,Hajiya azeema tazo mata da maganar,hada bata shawarar tayi mashi kwalliya,ta sanya kaya masu kyau,dama kamar jira take yi,cike da zumuɗi ta sauko daga saman gadon ta faɗa toilet don tayi wanka,komawa kitchen hajiya azeema tayi ta ɗauki na Sgr da sehrish Ta nufi Uptairs dashi,

Lokacin da hosana ta fito daga toilet,ɗaure da towel a chest ɗinta,Jahad na zaune saman gadon ta manna wayarta akan kunnata,Da alama da junaid suke waya,akan idonta hosana,Ta zauna gaban mirror tana kwalliya,kamar aljana haka ta koma,amma tayi kyau ba laifi,matsalarta bata iya shafa janbaki ba,dam6arashi takeyi,bayan ta kammala kwalliyar,Ta shirya kanta cikin riga da skirt na lace milk colour,ganin tana ta kiciniyar ɗaura ɗan kwali ta kasa,hakan yasa jahad tayi rejecting ɗin wayar,ta sauko daga saman gadon ta nufeta,Da taimakon jahad, Hosana ta ɗaura kallabin,ta kuma gyara mata makeup ɗinta,asaman kafaɗarta ta yafa mayafinta,juyowa tayi tare da kallon Jahad tace"idan naje kai mashi abincin ya zance mashi"?
  Murmushi jahad ta saki tare da cewa"bangane me kike nufi ba?ko kina nufin kalaman soyayya,"
  "Eh su nake nufi,"
Dariya jahad ta ɗanyi kafin tace"yanzu lokaci ya qure,ki bari idan kika dawo sai in koya maki,"
  Girgiza kai hosana tayi"a'a wlh,nidai ki rubutamun ko a paper ne,in naje sai in dinga karanto mashi,"
  Fashewa jahad ta kuma yi da dariya,daƙyar ta tsagaita da yin dariyar tace"Its okey,amma karki bari yaga takardar,ki 6oyeta,"ta amsa mata da toh,
A paper jahad ta rubuta mata kalaman soyayyan,sai murna take yi,ninke takardar tayi,a cikin bra ɗinta,ta soke takardar,da gudu ta fuce daga ɗakin,

Murmushi jahad ta saki tana girgiza kai tace"Yau ya omar zaisha kallo,don nasan saiya ganota,"

Toilet ta shiga,after some minutes ta fito ɗaure da towel,jikinta duk lemar ruwa da alama wanka tayi,hannunta na ruƙe da short towel tana goge sumar kanta,

Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,batare da tambayar wanene ba,tace"Come in,"duk a tunaninta oummansu ce,

A hankali ya turo ƙopar ɗakin,jikinshi sanye da Jallabiya,batare da jahad ta juyo ta kalleshi ba,tace"Oumma,kin gamu da hosana kuwa?Yanzun nan ta gama kwalliya wai zataje kaima Ya Omar abinci,ba don na gyara mata janbakin data shafa ba,da shi kanshi ya Omar ɗin sai ya razana.....'sai surutu take yi,

Murmushi kawai junaid ke saki,Ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,sai kallonta yake yi,koda taji oumman tasu bata tanka mata ba,Sam bata kawo komai arantaba,

Cikin sanɗa junaid yake tafiya harya ƙarasa bayan jahad ya tsaya,ƙamshin turarenshi ne ya dakar mata hancinta,lumshe idanuwanta tayi tare da sake buɗesu a hankali tace"hmmmm ina nake jin ƙamshin turare mai daɗi kamar na baby junaid ɗina,
  Kwantar da kanshi yayi saman kafaɗarta,aikuwa a firgice ta zabura zata gudu,yayi hanzarin ƙanƙameta sosai,cikin sanyin murya ya furta sunan da yake kiranta dashi"My juliet,its me ur Romeo,"
  A ruɗe tace"Junaid kayi hauka ne,Yaushe ka shigo cikin ɗakin?yanzu idan wani ya shigo ya ganmu a haka fa?ko kaya ban sanya ajikina ba,daga ni sai towel,"
  A shagwa6e junaid yace"meyasa kikayi rejecting call ɗina,batare da iznina ba?
  ɗaure fuskarta ta ɗanyi kafin tace"Am Sorry my romeo bazan ƙara yin hakan ba,but pls ka tafi kada wani ya shigo ya same mu a haka,"
  Maimakon ya tafi saiya ƙara ƙanƙameta sosai,yana shaƙar ƙamshin jikinta"Kamar nayi bacci Allah,kina jin abunda nake ji kuwa"?shiru tayi batare da tace mashi komai ba,Gaba ɗaya ya kashe mata jikinta,
  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Babyna,pls ka tafi,idan na kammala shiryawa,zanzo na same ka,'
  ashagwa6e junaid yace"i won't go anywhere,an fa biya sadaki,ki bari kawai na taimaka maki ki sanya kayan,tun yanzu mu fara practicing kafin a shafa fatihar auranmu,A sanyamun ke a ɗakina.......'
  Baikai ƙarshen maganarshi ba,Oummansu ta turo ƙopar ɗakin da ƙarfi,bakinta ɗauke da sallama,aikuwa a guje daga junaid ɗin har jahad,suka faɗa cikin toilet,tare jan ƙopar suka rufe,Tashin hankali,Tsoro yasa jahad tabi junaid toilet,Komai zai biyo baya,Ga Oumma ta shigo ɗakin..........'

*Boss Bature*
[3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: Tsayawa abu tayi cike da mamaki take kallon ƙopar toilet din,don taji lokacin da aka banko ƙopar da ƙarfi aka rufeta,bata kawo komai aranta ba,tuni sun kammala breakfast din,jikinta ne baiyi mata daɗi,shine tashigo ɗakin don tayi wanka kota jin daɗin jikin nata,

Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,duk tabi ta ruɗe baiwar Allah,junaid kuwa,koda suka faɗa toilet ɗin,wata irin zufa ce ke kartowa a kan fuskar kowannansu,sun ƙurawa juna ido,
  Muryarshi na kerma Yace"Jahad,dan Allah ki taimaka,ki fiddani daga cikin toilet ɗin nan,wlh idan oummanku ta ganmu atare zata sa a fasa bani auranki ne,"
  Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya kakeso inyi junaid!duk laifinka ne,nayi maka magiya akan ka tafi amma kaƙi tafiya,yanzu duk wanda ya ganmu cikin toilet atare a irin wannan yanayin me kake tunanin zaiyi tsammani"?
  Tayi tambayar tana kallonshi,fuskarshi duk a hargitse,sai faman cizon yatsanshi yake yi,
  "Jahad na shiga ukuna,Wayyo Allah.....'
Bai kai ƙarshen maganar ba,ta sanya tafin hannunta,ta toshe mashi bakinshi,
  Cikin raɗa tace"Kayi shiru,kada agane cewa akwai mutun a toilet ɗin,"
  Shiru su kayi,yayin da suka ƙurawa junansu ido,lumshe idanuwanta ta ɗanyi batare data buɗesu ba,ba zato ba tsammani,taji ya faɗa mata,sosai ya qanqameta,hankalinta ya ƙara tashi,aruɗe ta shiga faɗin"junaid wai menene haka?wlh zanyi ihu kowa yaji muna acikin toilet ɗin nan,"
  "Jahad tsoro nake ji,dan Allah ki barni a haka,bazan ta6aki ba,"yana magana yana ƙara matseta ajikinshi,tarasa yaya zatayi dashi,ga Oumma acikin ɗakin,
  Batayi aune ba,taji yana goga lips ɗinshi saitin nipple dinta,kokarin kamawa yakeyi,A firgice jahad ta soma kiciniyar kwace shi,yaƙi sakinta,Ya ƙanƙameta yana faɗin"Wai menene haka jahad,so kika asirin mun ya tonu,
  A ƙule tace"bana son iskanci junaid,bazaka iya hakuri a ɗaura auran ba,"
  Da buɗar bakinsa sai cewa yayi"ae an biya sadaki,tun yanzu mu fara practicing," haushine ya isheta,saboda ƙarya yake yi,ba'a biya sadaki ba,Yana fakewa da hakan don ya samu tadinga yi mashi biyayya,
  Gartsa mashi cizo tayi asaman kafaɗarshi,abunka ga shagwa6a66en,Ya fasa ƙara tare da faɗin"Wayyo Allahna,Ta cije ni,"a gigice Jahad ta toshe mashi bakinta,ta janyoshi ta rungume don ta samu yayi shiru,

Abu dake acikin ɗakin,Abun ya ɗaure mata kai,domin kuwa tajiyo muryar mutun acikin toilet ɗin,bakin ƙopar ta nufa,ta ɗan tsaya tare da sanya hannu ta ƙwanƙwasa ƙopar"akwai mutun"
Gabansu ne ya faɗi,tuni ido ya raina fata,
"Junaid mun shiga uku,"tayi maganar,idanuwanta cike ta da kwalla
  "Wai bakowa ne"?oumma ta ƙarayin tambayar,junaid yayi shiru ya lafe a ƙirjinta,jikinshi sai kerma yake yi ga tsoro ga iskanci cike dakai,
  Muryarshi na kerma yace"Jahad,kice mata kece,"
Jin haka yasa jahad ta ɗanyi gyaran murya,
  Ajiyar zuciya abu ta sauke tare da cewa"Lafiya naji kina ihu"?tayi maganar don ta gane wacece,
  Ƙasa ƙasa da murya jahad tace"Lafiyalou oumma,na sanya ruwan zafine,ban surka dakyau ba,"
  Jinjina kai abu tayi"ki ƙara surkashi mana,"
  "To oumma,"

Juyawa abu tayi maimakon ta fita daga ɗakin,Sai ta zauna gefen gadonsu,Tana jiran jahad ta fito itama ta shiga toilet ɗin tayi wanka
  Hannu tasa ta 6an6are junaid daga jikinta,hannu yasa tare da dafe cikinshi,ya ɗan ɗago da dara daran idanuwanshi yana kallonta,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,
  Kamar wani ɗan iska,Ya kashe mata ido ɗaya,tare da zuro harshen shi yana lasar gefen le6ensa,
  Abun ya bata haushi,jarabar junaid tafi ƙarfinta,ita duk a tunaninta yayi hankali tunda an rabashi da sihirin jikinshi ashe dama can tunfil azal,Ɗan iskan kanshi ne,
  Harara ta wurga mashi,tare da cewa"Wlh zan fasa auren,"
Bubbuga ƙafarshi ya ɗanyi,Ashagwaye yace"wlh da nayi maki lalata,kinga dole ki amince ayi auran,"
  Har sai da gabanta ya faɗi jin abunda yace,hankali atashe take kallonshi"nashiga uku junaid'
 
  Lamarin shi ya fara bata tsoro,ƙura ido tayi tana kallonshi,jiki asanyaye tace"Junaid,kana shaye shaye,"
  Girgiza kai yayi"wlh ko taba ban ta6a sha ba,"
 
Abu dake zaune gefen gadon tana jiran fitowar jahad,kunnuwanta suna jiyo mata ƙusƙus acikin toilet din,
  "Jahad,surutun me nake ji acikin toilet ɗin nan,ke da waye"?
  Aruɗe tace"babu kowa oumma,"jinjina kai abu tayi"kiyi sauri ki fito inaso in shiga,"
  Rass taji gabanta ya faɗi,amarairaice ta kalli junaid"Ya zamuyi,"
  "Nima kaina bansani ba jahad,pls ki nema mana mafita,"
  Shiru su kayi na wani lokaci,can taga yana nannaɗe jallabiyar jikinshi,tayi tunanin wata dabara zaiyi hada saurin cewa"Junaid,ka gano mana mafita ne"
  Batare daya kalleta ba,yace"fitsarine ya matse ni.....'
Tunkan yakai ƙarshen maganar,tayi hanzarin buge hannunshi"ashe baka da hankali,agabana zakayi,"
  "To sai me,wlh ya matse ni,in ba so kike inyi a wando ba,"zuba mashi ido tayi tana kallon ikon Allah,
  Ganin yana kokarin xame short ɗin ya curo abunshi yasa tace"Nashiga uku"!da ƙarfi tayi maganar,Abu dake zaune a ɗakin a firgice ta mike ta nufi toilet ɗin tana faman kwala mata kira"Jahad lafiyarki kuwa?wai me ke farune?tun ɗazu nake ta jin surutu acikin toilet ɗin nan,Zaman me kikeyi ne,Ya isa ace kin fito,"
  Hankali atashe Jahad tace"Babu komai oumma,Yanzu zan fito,kan famfo ne ya lalace,ruwa duk ya fallatsarmin,Shiyasa kika ji ina magana,Yanzu zan gyara shi,ba wuya,"
Jinjina kai abu tayi"ok ina jiranki,"komawa tayi gefen gadon ta zauna tana jiran fitowarta,

  "Dan Allah junaid,kada kayi fitsarin nan,"a ƙule yace"ji wani ikon Allah,Nace dole saikin kalleni ne,ki juya baya mana,wlh sai nayi,"da sauri ta juya mashi baya,ta kifa kanta da bango,tana jin sautin fitar fitsarinshi,abun ya bata mamaki,kwata kwata junaid baida kunya,bata ta6a tunanin haka yake ba,tabbas zata sha wahala a hannunshi,don ba ƙaramin jarababbe bane,

Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,da sauri abu ta miƙe ta nufi ƙopar tana tambayar wanene,daga waje akace"Mommyn junaid

Please Login or Register in order to submit comment