Reading Abban Sojoji Takun Karshe 2&3 complete by Boss Bature Chapter 137 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abu da suke faɗi acikin kunnanta,amma bata ɗago ta kallesu ba,har yanzu dae bata dawo dai dai ba,


Daƙyar su Omar suka lallashe su,kafin daga bisani Abbansu yace"Jahad yanzu ke muke sauraro!munaso muji irin rayuwar da kukayi a hannun mutumin nan!"

Duk wannan abun dake faruwa akan kunnan Haroon,ya jima da shigowa batare da sanin kowa ba ya la6e yana jin labarin da abusufyan ke ba su jahad,na rayuwarshi da mahaifiyarsu,hankalin shi yayi mugun tashi,gaba ɗaya ya tsorata ya rikice,wata irin zufa ce tashiga gangarowa a fuskarshi,bakomai ya razanar dashi ba face ganin Ƴan ukun gaba ɗayansu sun haɗu acikin gidan kuma ga Ubansu da kanshi ya gane cewa ƴa'ƴanshi ne wannan alama ce dake nuna cewar asirinsu ya kusa tonuwa,
Tuni zufa tasoma tsastsafo mashi acikin jikinshi,sharkaf ta jiƙa t shirt ɗin jikinshi duk kuwa da ba zafi,jan ƙafarshi yayi tare da lalla6awa cikin sanɗa ya wuce bedroom ɗinshi,
Zagaye ya shiga yi acikin ɗakin,gaba ɗaya jikinshi sae faman rawa yakeyi,yama rasa inda zai tsoma kanshi kamar wani zautacce haka ya koma,a fusace ya dunƙule hannunshi tare da kai ma madubin ɗakin naushi,nan take glass ɗin jikinshi ya tsastsage ya zube ƙasa,
Hannunshi ya shiga fitar da jini,ko kaɗan baiji xafin hakan ba,raɗaɗin da zuciyarshi ke yi mashi yafi raɗaɗin glass ɗin daya shige shi,
Da ƙarfi ya furta"That's impossible!ƙaryane ba gaske bane!!wlh bazan rasa rayuwata ba!dole na rayu ko da kowa zai rasa ranshi,zanyi komai zan yi don ganin na kwaci kaina!!
Yana magana yana sakin huci,idanuwan nan nashi sunyi jawur dasu luhu luhu,
Cikin sauri ya zura hannunshi tare da ciro wayarshi daga cikin aljihun jeans dinshi ya danna ma wata number kira,cikin sa'a aka ɗaga kiran!
Wata irin muryace ta karaɗe kunnanshi mai tsoratarwa"Ba saida nace maka karka sake kira na ba!Tun farko ya mukayi dakai?
hankali atashe haroon yace"Ni ba wannan maganar tasa na kira ka ba!ka faɗamun taya akai kukayi gangancin barin yaran nan har suka haɗu da danginsu!!!!!!!
"Wasu yara kenan!"
Haroon yace"Ƴan ukun nan!na gansu da idona acikin gidan nan!yanzu haka gasu can a falon gidan nan sun taru suna jin labarin rayuwar yaran nan!
Nan take muryar mutumin da suke waya dashi ta canza,
"Wai kana nufin hosana!jahad!sehrish!duk sun haɗu anan cikin gidan naku ko mi"?
A ƙule haroon yace"Eh mana!akansu nake magana,wlh kowa yayi ta kanshi!saboda yarinyar nan dole ta ambaci sunanka acikin labarin da zata bayar kuma kasan cewa muddin waɗannan namun dawan guda biyu sukaji mugayen abubuwan da kuka aikata dole su binciko ka duk inda ka shiga kuwa,kuma koda a ƙarƙashin ƙasa ka 6oye,!

Fashewa da dariya mutumin yayi kafin ya tsagaita da yin dariyar yace"Baza su ta6a iya gano ni ba!nafi ƙarfinsu nesa ba kusa ba!zanyi amfani da ƙarfin sihirina wurin dakatar da tunaninsu.......'
Tun kan ya ƙarasa maganar haroon ya daka mashi tsawa tare da cewa"Ya Isa haka!!zancen ku iri ɗaya da ita!daga kai har ita daga anyi magana sai kuce ƙarfin sihiri,zakuyi amfani da sihiri ku asirce mutun!angaya maku cewa kowane lokaci sihiri ke yin tasiri ne!sam babu Allah aran kowannanku don haka babu wanda zai tsira acikinmu!ko ka manta da irin mutuwar da mahaifinku yayi ne?duk wani sihiri da kuke taƙama dashi ae a wurinshi kuka gado shi,akan idon kowannanku yayi mummunar mutuwa sakamakon farmakar shi da kakanmu salahuddeen sukayi,ku baku da tunani ne?me yasa shi a lokacin baiyi amfani da ƙarfin sihirin shi ba don ya hana kanshi mutuwa?ko don saboda ya tsufa ne yasa nashi sihirin baiyi aiki bane?

Gaba daya haroon ya rufe shi da faɗa ta inda yake shiga batanan yake fita ba,ba don komai ba sai don saboda yasan cewa bazai kai labari ba,sun ja mashi bala'e da masifa,
Wata irin gigitacciyar tsawa mutumin ya daka mashi wadda tayi silar dawowarshi cikin hayyacinshi,yayi tsit yana faman sauke ajiyar zuciya,
"haroon!ya kamata ka iya bakinka!kasan dawa kake magana!duk wannan tada jijiyoyin wuyan da kakeyi bazai hana kaga mutuwarka ba!zaifi kyau ka mayar da hankali wurin ganin ka sama ma kanka abokan tafiya,kada ka yarda wannan abun ya tayar maka da hankalinka,babu wanda ya isa ya ta6a ka acikinsu,!abu ɗaya kawai mukeso awurinka!muddin ka aikata hakan komai yazo ƙarshe zaka tsira kuma muma zamu tsira,sannan farin cikin gidansu zai tarwatse na har abada,......................'
Natsuwa haroon yayi yana sauraron bayanan da mutumin yake kora mashi,sae amsa mashi yake yi da to,toh
Alamar ya amince da abunda suke so ya akaitan,


Acan main palour ɗin kuwa,kowa ya kasa kunne yana sauraron Jahad,

****




*

Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*




*Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari*,


2 pages ne hada na monday

*CIGABAN LABARI*

Abu ba ƙaramar wahala tasha ba a hannun Ya sayyadi,daga ita har yaran bai raga masu ba,tun yana 6oye mata mugayen halayenshi,har ya fara bayyana mata su,babban tashin hankalin da ta fara fuskanta a wurinshi shine shigo mata da Manyan Alhazan da yake yi acikin gidansu,in suka shiga ɗaki sai suyi fiye da 6hrs basu fito ba,wani sa'in har gurnani take ji ya cika gidan tamkar namun dawa na yaƙi,wannan abun ba ƙaramin razanar da ita yake yi ba,kuma duk in ta tambayeshi me suke zuwa yi a wurinshi sai yace mata *Wala tajassasu*kuma ta tsaya a iya matsayinta kar tace zatayi mashi shisshigi irin na mahaifinta,tarasa uban me sukeyi acikin ɗakin,abun ba ƙaramin damunta yake yi ba,tun tana iya jurewa har dae wata rana ta yi masu la6e a window ɗin ɗakin shi,a ranar abu taga tashin hankalin da bata ta6a gani ba da idonta tunda uwarta ta haife ta,wani irin yunƙurin amai ne yazo mata da gudun gaske tabar leƙen sun da takeyi ta koma bakin fanfo tana kwarara amai tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito,agaban fanfon ta zuƙunna tare da fashewa da kuka,ta dafe kanta da hannunta saboda raɗaɗin da yake yi mata,gaba ɗaya rayuwarta ta shiga ƙunci taji ta tsani kanta,kamar ta kashe kanta haka ta dinga ji a lokacin,

ta jima abakin fanfon kafin ta koma cikin ɗakinta,a lokacin triplets ɗinta suna kwance sae sharar bacci sukeyi,komawa tayi daga gefen gadon ta zauna tare da ɗan russinawa dai dai saitin fuskokinsu tana kallonsu,yadda suke sharar baccin su zai tabbatar maka da cewar suna cikin kwanciyar hankali,tasa su gaba tayi tana faman shessheƙar kuka muryarta na rawa ta dinga cewa"Na cuci kaina!Kuma nacuci rayuwar ƴa'ƴana,Haƙƙin mahaifina kadae bazai ƙyale ni ba,na bijire mashi na ƙuntata mashi duk don saboda in auri sayyadi,haƙiƙa na tafka babban kuskuren da bazan ta6a gyarashi ba,Ni duk a zato na kowane mutun daya iya jan ayar kur'ani ya fassarata kuma yayi wa'azi abainar jama'a,mutumin kirki ne bai aikata zunubi tsarkakakke ne shi,ashe ba haka bane,ko acikin malaman akwai nagari akwai kuma na banza,wanda suke amfani da iliminsu na addini don su cutar da mutane,Mommy saida ta gargaɗe ni akan hakan amma na bijire mata saboda na makance akan soyayyar sayyadi,Ni ban tsaya nayi bincike akan rayuwarshi ba,kawai natashi na aure shi,kuma na ƙuntata ma mahaifina duk don saboda shi,na kuma ƙuntatama Mijina mai sona da gaskiya,wlh na cuci rayuwata....!kaicona.......'

Sosai abu ke shassheƙar kukan,sautin kukan da takeyi ne ya farkar da Sehrish sai faman mutsustsuka idanunta takeyi da hannayenta,hannu abu takai tare da ɗauko ta,ta zaunar da ita asaman cinyoyinta,shafa fuskarta tayi tare da cewa"Rishina kin farka?kina jin yunwa ne"?
  A hankali ta ware kyawawan idanuwanta akan fuskar mahaifiyarsu,koda taga hawaye na zuba a idanun oumman tasu,sae ta sanya tafin hannunta tana share mata su tana cewa"oum ki daina,banasho,nima inyi kuka,'tayi maganar da hausarta ta ƴan koyon magana,hada ta6e la66anta zatayi kuka,
Hakan da tayi yasa abu ta fashe da dariyar karfin hali tana kallonta,kwantar da kanta tayi asaman ƙirjinta tana shafa sumar kanta tace"na tambayeki kina jin yunwa baki faɗa mun ba,'
Cikin shagwa6a tace"inaji,amma tare dashu usana da johad anci.  '
  Abu tace"shikenan,bari mu jira su farka daga baccin sai in dafa maku ko indomie ce kuci,bayan kun gama ci sai inyi maku wanka,in shafa maku mai in canza maku kaya sannan in kaiku gidan maman sadeeq ku tayata fira,kina son zuwa ko?
  Inasho,ta bata amsa,
Suna cikin yin fira da ita sai ga sayyadi ya faɗo cikin ɗakin nata,tana ganinshi gabanta ya faɗi rass don yanzu yafi yi mata kama da ibliss,
  Yadda ya nufo ta a fusace yasa tayi saurin sauke sehrish daga jikinta ta miƙe tsaye tana kallonshi fuskarta da alamun tsoro,

Nuna ta yayi da hannunshi yana huci yace"Abu!uban me ya kaiki yin la6e aɗakin can!angaya maki banganki bane?duk wani motsin ki acikin gidan nan,acikin kunne na nake jinshi,basai da na faɗa maki cewa kada ki tsananta bincike akaina ba!
  duk da tsoranshi da take ji hakan bai hanata tanka mashi ba,
"Saboda baka da gaskiya shiyasa ka hana inyi bincike akanka!yau naga komai da idanuna ashe kai ba sayyadi bane!baƙin shaiɗan ne wanda ke 6oye mugayen halayansa!wlh nayi danasanin auranka sayyadi yafi sau aƙirga,banta6a sanin cewa kai dabba bane sae yau!wlh sai ka sake ni don bazan iya cigaba da zama da fasiƙin mutun irinka ba......'
  Tunkan ta ƙarasa maganar sayyad ya fashe da dariya hada dafe cikinshi,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,shiru tayi tana kallonshi,
  Sai da ya gama tiƙar dariyarshi sannan ya sassauta muryarshi tamkar zai lallashe ta yace"My wife,yau da bakinki kike jifana da waɗannan munanan kalaman?nifa ne sayyadin nan naki da kika kwallafa rai akai,ban wani canza ba,'tundaga kan yadda yake yi mata magana ta gane cewa ba karamin gogaggen ɗan bariki ba ne,ya kware wurin iya sarrafa harshe dama da irin kalaman nan nashi ya yaudareta tun farko,in yazo zance ya tsareta da idanunshi yana yi mata nasiha,
  daƙyar ta iya haɗiye miyan dake bakinta,cikin sanyin murya tace"Kaji tsoran Allah!meyasa kayi amfani da ilmin da kake dashi na addini wurin cutar da rayuwata?saboda kasan cewa inason malamin addini mahaddacin al'qur'ani shiyasa ka biyomin ta wannan sigar don ka yaudare ni,laifin me nayi maka da har na cancanci hakan a wurinka"?
  shu'umin murmushin nan nashi ya saki kafin yace"Ae malaman ma suna muka tara!abu kinyi kuskuren yadda da cewar kowane malamin addini mutumin kirki ne,wasu malam ne nagaske wasu kuma suna yin amfani da maluntar tasu da wata manufa don su Cimma burinsu kamar ni kenan!saboda kawai kin ganni malami ina yin shigar mutunci in yi wa'azi in janyo aya in fassara gani kuma mahaddacin kur'ani sai akace maki ni mutumin kirki ne?An rubuta a goshi na ne?me yasa kuke yin believing da abunda idanuwanku suka gwada maku ne?duk wani ɗan adam da kika sani aduniyar nan bai da tabbas!duk yadda kikaso ki gane mutun na gari kona banza abun zaiyi matuƙar wuya agare ki,saboda akwai masu fuska biyu,zaki ga mutumin banza yana aikata abunda yaga dama agaban kowa baijin kunyar kowa zai aikata zina zaiyi sata,zai zalunci wani zai sha giya,zai yi kaza yayi kaza,kinga shi wannan ya bayyana asalin suffarshi,wani kuwa zaki ganshi babban malami ne mahaddacin al'qur'ani wanda ya saba wa'azi agaban dubban jama'a yana faɗakar dasu cewa suji tsoran Allah kar suyi kaza idan sukayi kaza zasu shiga wuta idan sukayi kaza kuma zasu shiga Aljanna,idan kika bincika kuma wannan malamin ɗabi'unsa da halayansa iri ɗaya ne dana wannan mutumin dana fara kwatanta maki!amma shi bai bayyana suffarshi ta asali ba,yazo da sigar maluntaka don ya cimma wata manufa tashi ta hanyar yin amfani da ilmin addinin da yake dashi,wani kuma zaki ga malamin ne nagaske akwai ilmin addinin Akanshi amma baki ta6a ganewa, kamar dae Abusufyan yaron kirki,abusufyan tun yana da shekara sha wani abu aduniya ya haddace al'qur'ani mai girma tare da manya manyan littattafai na addini,amma ya ɗabi'unsa da halayansa suke?babu mai iya gane cewa yana da ilmin addini akanshi indae ba anyi mu'amala dashi ba,saboda irin rayuwar daya taso yanayi,abota da mata da kuma rashin kunya baijin kunyar furta kalami abakinsa ko gaban wanene 6arota kawai yake yi,kowa zaiyi tunanin cewa shi jahilin addini ne ashe ba haka bane,yasan me yakeyi kuma yana da kyakkyawar zuciya ba kamar sayyadi ba,
*dawa zamu yadda aduniyar nan?lalube kawai mukeyi acikin duhu,musamman zamanin nan da muke ciki,Zaiyi wuya ka gane mutun na gari dana banza,shiyasa da yawa mata muke shan wahala wurin neman miji na gari da zamuyi rayuwa dashi,tunda bamu da tabbas akansu Mazan!haka matan ma bamu da tabbas mu kanmu,da mazan da matan wahala kowa ke sha wurin neman righteous life partners,A ƙarshe nidae shawarar da zan ba mutun shine ya dage da addu'a kawai,sannan ya gyara rayuwarshi in ma akwai wani kuskuren da yake aikatawa ko min ƙankantarshi,saboda da yawa wasu abubuwan wlh mu muke ja ma kanmu batare da mun sani ba,muyi ta ganin ba dai dai ba arayuwarmu,dole sai mun gyara sannan zamu ga dai dai mu kanmu,Allah yasa mu dace,Amin.

Haƙiƙa su Sehrish sunga rayuwa fiye da tunanin mai tunani,uƙuba babu irin wadda basu sha ba a hannun mutumin nan,tun kafin su mallaki hankalinsu suke jin wannan sautin abun da mahaifinsu ke aikata shi da manyan alhazawan nan dake kawo mashi ziyara,abun ba ƙaramin tsoratar dasu yake yi ba,duk subi su gigice,babu yadda abu batayi ba akan ya daina shigo mata dasu cikin gidan amma ko ajikinshi,in ma ta takura mashi sai ya kwatseta da cewa ae gidan bana Ubanta bane,da kuɗinshi ya siyi gidan,
Abu har ya fara affecting ɗinsu sehrish daga sunji gurnanin nan sai subi su gigice su firgice suna yi mata kuka suna cewa Oumma dodo,dodo,ta rasa yadda zatayi dasu baiwar Allah,ƙarshe ta dinga kaisu gidan makwabciyarta suna yini acan wani sa'en ma har kwana suke yi agidanta,
Lokacin da Sayyadi ya gane hakan,ba ƙaramin faɗa yayi mata ba akan tadaina kai mashi ƴa'ƴanshi gidan makwabtansu,dama basu shiri da Mijin maman sadeeq,shima malamine sosai amma malamin gaske ba irin sayyadi ba,shiyasa ya tsane shi,saboda ya sanya mashi ido sosai akan lamurran rayuwarshi duk da bai ta6a tarar shi da sunan zaiyi mashi magana ba,babu wanda ke tanka ma wani acikinsu,ƙaryace ta haɗu da gaskiya,kuma a makarantar islamiyya ɗaya suke koyarwa,tun lokacin da sayyadi ke tarayya da abu,sae da ya ta6a kiranta ya gargaɗeta akan ta daina kulashi,su kansu basu san asalinshi ba,kuma basu yadda dashi ba acikin malaman makarantar amma abu taƙi jin maganarshi saboda ta makance akan son shi,maganin marasa jin maganar malamansu kenan da kuma iyayensu kai harma da mazajansu,babu wanda acikinsu bai ja mata kunne ba amma tayi kunnan uwar shaggu dasu ita ga Juliet,yanzu dae ga romeo nan yana ta gasa mata aya a hannu,duk da dae akwai aikin sihiri,Allah ya kara karemu da kariyarsa,Amin

A kwana a tashi babu wuya wurin Allah su Sehrish suka kai shekara 5 a duniya,daga lokacin ne fa sayyadi ya fara sanya masu ido saboda kyawunsu dake fusgarshi,nan fa ya fara saƙa wani abu aranshi,

Wani sabon salo ya 6ullo mata dashi,na horon yunwa kwata kwata yadaina kawo masu abinci acikin gidan,yaran suyita fama da yunwa,wani lokacin kamar zasu rasa ransu in suka fara billayi suna kuka,hankalinta yabi ya tashi ta rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi,gashi bata da kuɗi bata da hanyar da zata same su balle tace zata ɗauki nauyin ciyar dasu,kamar maroƙiya haka ta koma bi gida gida na makwabtansu akansu ƴan mata abinci taba yaranta,tun tana samu suna ɗan mata har aka fara tseguminta abayan idonta,tun suna gulmarta a6oye har aka farayi agabanta,ƙarshe ma da zarar su sehrish sun leƙa kopar gida za'a fara gulmarsu ana cewa ga ƴa'ƴan abu almajira nan sun fito,haka zasu koma sunayi mata kuka,saboda tsokanarsu da akeyi,har jan gashin kansu akeyi ayita dungurin goshinsu,gaba daya mutane suka ɗauki karan tsana suka ɗaurama yaran,duk irin kyan dake garesu,kowa ya daina taimakonsu,bakomai yafi ɗaga ma abu hankali ba face yadda mutane suka tsani ƴa'ƴanta,babu damar su fita waje da sunan zasuyi wasa cikin ƴan uwansu yara sai ta gansu sun watso da gudu cikin gidan suna kuka,haka zata haɗasu a ƙirjinta ta rungumesu tana kuka,duk wannan abun dake faruwa sayyadi yana sane saboda shine silar komai dake faruwa dasu,

Gaba ɗaya kowa ya ɗauki karan tsana ya ɗaura masu,mutun biyu ne kaɗae suke tausayin rayuwarsu,Maman sadeeq da kuma Mijinta,kullum cikin tausaya masu sukeyi,a kullum su hosana suka shiga gidan yunwa ta koro su,ita ke zama ta girka masu abinci,har ta kaiga in zatayi girki tare dasu take auna abincin don tasan zasu zo nema ne,ita kaɗae ce take kwantar ma abu da hankali,

A ƙarshe dae da abun ya fara yi mata yawa da kanta ta tunkari sayyadi a ɗakinshi lokacin yana a gida baije aiki ba,tunda ta shigo ɗakin ya ɗaure fuskarshi yana daga kishingiɗe saman gadonshi,
Wuri tasamu daga gefe ta zauna ta gaishe shi daƙyar ya amsa mata ma,yadda kasan auren ƙiyayya sukayi dashi,
"Meyasa kake barin mu da yunwa baka ajiye mana abinci acikin gidan nan yanzu?
ta6e bakinshi yayi tare da cewa"Yaushe rabon da kiban haƙƙina na aure?hakanan zan zauna ina ciyar dake da ƴa'ƴanki ne saboda haihuwata kukayi?
"Allah ya kiyaye in ƙara haɗa shimfiɗa dakai sayyad!rashin sani ne yasa ko lokacin baya nake baka haɗin kai,amma yanzu nagane ko kai wanene.... '
Murmushi ya saki yana kallonta batare da ya ƙara tanka mata ba,
Cigaba da magana tayi"bai kamata laifina ya shafe su ba,su fa ƴa'ƴanka ne jininka ne!meyasa zakayi masu horon yunwa saboda laifin da nina maka?haba sayyad sai kace ba ƴa'ƴanka ba?akan idonka ake wulaƙantasu amma ko ajikinka,narasa gane wannan abun.........'takaici ne yasa ta kasa ƙarasa maganar ta fashe mashi da kuka,cikin shessheƙar kuka taci gaba da cewa"tun da na haifi yaran baka ta6a nuna masu soyayya irin ta mahaifi ba,tun satin farko da suka zo duniya,ko ɗaukarsu bakason yi,me yasa dan Allah?kayan sawar su ma duk sun tsufa sunyi masu kaɗan,amma baka ta6a ɗaukar ko fallan atampha ba wannan kace gashi a ɗinka masu,wai kai wani irin mutun ne!?
Da buɗar bakinshi sai cewa yayi"Dabba!"
Shiru abu tayi tana kallonshi kamar ta rufe shi da duka haka take ji,
  "Ko kin manta munanan kalaman da kika jefe ni dasu ne?da bakinki fa kika kirani da sunan dabba,"
  "Dan Allah to kayi hakuri komai ya wuce,ni so nake kawai ka daina yi mana horon yunwa ko dan saboda yaran nan,koda ace ni ba zaka bani ba,su yara ne basu san komai ba,ba zasu iya jurar yunwa ba,sannan kuma ya kamata ka sanyasu makaranta tunda bakinsu yafara buɗewa sosai suna magana,"ba don taso ba haka ta dinga lallashi akan ya taimaki yaran,
  Sai da ya mula ya sha iska sannan yace"ni bazan iya ɗaukar nauyin karatunsu ba,saboda ni ban fito gidan arziƙi ba kamar Abusufyan,kinsan cewa Ni malamin makaranta ne,makarantar ma ta islamiyya,salary ɗina bai wuci 20k ba,idan har kinason kula da yaranki ki tashi tsaye ki nemi kuɗinki mana,'
  Fuskarta ɗauke da damuwa tace"Meyasa zakayi mun haka sayyad!idan kasan cewa ba zaka iya ɗaukar nauyin su ba,meyasa ka bari na haifesu....   '
  Yunƙurawa yayi tare da miƙewa yabar mata ɗakin yana faman buga tsoki,ta jima zaune jugum aɗakin nashi,kafin ta miƙe ta koma bedroom ɗinta,zirga zirga tashiga yi tana neman mafitar yadda zata samu kuɗi don ta tallafama rayuwarsu,bakowa bane ya faɗo mata aranta ba face Ya haris,tana da tabbacin cewa in yaji halin da take ciki zasu iya taimaka mata duk da tana jin kunyar tunkararsu amman bata da wata mafitar data wuce wnn,addu'a ta shiga yi Allah yasa har yanzu da number shi data sani yake amfani,

Da wayar makwabciyarta tayi amfani wurin kiran Haris,cikin sa'a ta shiga,lokacin daya ɗaga kiran taji muryarshi sai ta fashe mashi da kuka,nan fa hankalinshi ya tashi ya shiga tambayarta ko lpy,bata 6oye mashi komai ba,game da halin rayuwar da suke ciki ita da ya'yanta,haris yayi mata al'ƙawarin zai taimaka masu,su bashi lokaci,

Bayan wasu ƴan kwanaki haris yayi mata aiken kuɗi masu yawa,dasu tayi amfani wurin nema masu makarantar boko da kuma islamiyya,wani lokacin har zama takeyi da kanta ta koya masu karatu,sun ɗan samu sauƙi a wannan lokacin kafin sayyadi ya sake ƙunsa masu wani baƙin cikin,ya kwashe mata Sehrish da jahad 6at aka neme su aka rasa,kamar abu zata yi hauka wurin nemansu,ashe zuwa yayi ya saida ma ƙungiyarsu yaran don suyi amfani dasu,shi kuma suka bashi makudan kuɗi,Mijin maman sadeeq ne ya tona mashi asiri a wurinta,saboda yaga lokacin daya gudu da yaran a 6oye ya tafi dasu,ranar kaca kaca sukayi dashi har bugunta sai da yayi saboda shaƙo kwalar rigarshi da tayi tana jifanshi da munanan kalamai,a ƙarshe tace zata haɗa shi da Allah in bai dawo mata da ƴa'ƴanta ba,tun daga ranar ta fara sallar dare tana kai kukanta wurin Allah,duk yadda sayyadi yaso ya juye mata tunani akan ta daina ibadar nan amma abun yaci tura,ko yayi nufin yi mata asiri babu abunda ke yin tasiri ajikinta,

A ƙarshe dae sae gashi a tsakar dare aka dawo mata dasu sun fita hayyacinsu sunyi jaga-jaga dasu,kamar an jefosu haka ta gansu sun faɗo ɗakinta,sae kuka sukeyi ko sutura babu ajikinsu,ga miyau na zalala abakunansu,hankalin abu ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin taƙara sanin wanene sayyadi,kuma ta fara kokwanton cewa Anya ƴa'ƴanshi ne,gaba ɗaya kuɗinta sae da suka ƙare wurin nema masu magani don tunda suka dawo ciwon kai,ciwon ido,ciwon ciki,ciwuka iri-iri haka suka dinga fama dasu,har gadon asibiti aka kwantar dasu sukayi jinya duk ita ke faman ɗawainiya dasu tare da Maman sadeeq,har mijin ta yana zuwa dubasu a asibitin sannan ya taimaka masu da wani abun hadi da addu'oi,amma Sayyadi kuwa ko leƙo asibitin baiyi ba,koda aka sallame su suka dawo gidama basu same shi ba,haka abu taci gaba da shan wahalar rayuwa,ko makarantarma acikin sati bai wuci sau biyu suke zuwa ba,saboda rashin lafiyar da suke ta fama da ita,kuma duk in sukaje makarantar da kuka suke dawowa,saboda yara dake tsokanarsu akan cewa mahaifinsu ɗan mafiya ne mai yankar kawunan mutane,wannan abun ba ƙaramin cutar da rayuwarsu yake yi ba,shiyasa duk suka tsani zuwa makarantar,

Akwai wani lokaci da Sehrish ta fito waje cikin unguwarsu ta miƙi hanya tana tafiya tana kuka abun duniya yayi mata,kwata kwata basu jin daɗin rayuwarsu ta ko'ina a ƙuntace suke,a daidai wannan lokacin Wata danƙareriyar mota tayi parking a gefenta,cikin sauri matashin dake cikin motar ya buɗe ya fito ya tunkareta,sam bata lura da shi ba har sae da ya ruƙo hannunta,a firgice ta juyo tana kallonshi da idanunta waɗanda sukayi jawur saboda kukan da tasha,ga majina duk fuskarta ta 6aci,zuƙunnawa yayi agabanta yana kallonta,gwanin ban tausayi ƴar ƙaramar yarinya ko kallabi babu akanta balle takalma,ga kayan jikinta duk sun 6aci,
Kamar yadda yake kallonta haka itama take kallonshi,ɗan gayu dashi yasha wankan suit ajikinshi,
Cikin sanyin murya yace"Ya sunanki"?
..cikin shessheƙar kuka tace"dan Allah ni ka rabu dani,ka ƙyale ni in tafiyana,'
Abun yaso ya bashi dariya,shafo fuskarta yayi tare da cewa"Faɗamun me yasa kike kuka?idan kika faɗa mun zan taimake ki,'
A ƙule tace"Nidai ka ƙyale ni dan Allah,kawai ka rabu dani,kona faɗa maka babu abunda zaka iyayi mana saboda babu mai sonmu Allah ne kawai ke son mu,'
Tuni yaji hawaye sun cicciko mashi acikin idanunshi,Haris dake zaune cikin mota yana hangensu ta glass ɗin motar ba ƙaramin tausayi yarinyar ta bashi ba,
lallashinta ya shiga yi yana cewa"kiyi haƙuri kinji?bakowa ne baisonku ba,Nima gani kuma ina sonku sosai,ashirye nake dana taimake ku indae kunaso,zan ɗauke ku mu gudu mu bar ƙasar nan,in tafi tare daku can wani wuri mai daɗi kuyi rayuwarku ko baki so?
"dagaske kake"?muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,
ɗaga mata kai yayi alamar eh,tare da cewa"yanzu ki biyoni mu tafi batare da kowa ya ganmu ba,"
Girgiza mashi kai tayi tare da cewa"Su hosana fa?su bazaka tafi tare dasu ba?Oummanmu fa?itama anan zaka barta,
"Kada ki damu suma duk zanzo in ɗaukesu daga baya,"
Maƙe mashi kafaɗa tayi tace"a'a ni bazan bika ba,sae dae inje in kirasu Johad da hosana,mu tafi atare,"
"Shikenan zan jiraki ki kirasu,kada ki faɗa ma kowa babu wanda zai san mun tafi,"
Amsa mashi tayi da toh sannan jiki na rawa ta juya da gudu ta koma gidan,


Please Login or Register in order to submit comment