Reading Abban Sojoji Takun Karshe 2&3 complete by Boss Bature Chapter 111 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zakuna haka sojojin suka tunkari motar shi,hankali tashe ya juya tare da kallon hayaam dake manne ajikinshi tana bacci ta aza kanta asaman kafaɗarshi,jikinta na sanye da dogon hijabi har ƙasa ta sanya niƙab a fuskarta,kamar wata Malamar Addini,
  da ƙarfi ya ambaci sunanta"Hayaam!!Hayaam!!"har cikin kanta ta dinga jin kiran nashi,daƙyar ta iya buɗe baki tare da cewa"wai menene"?
   "Mun ƙaraso gidan fa,dan Allah ki tashi kiyi ma waɗannan dakarun bayani,nifa a tsorace nake dasu,". 
  guntun tsoki taja ta janye jikinta daga nashi,sannan tace"haba sofwan bafa yau ka fara zuwa gidan nan ba,menene abun tsoro aciki,sai kace ba namiji ba,"
   wani irin kallo yayi mata tare da cewa"ba yau na fara zuwa gidan ba,amma ae ko lokacin da na ta6a zuwa ɗaukarki a iya bakin babban gate ɗin nan nake tsaya......'
Bai ƙarasa maganar ba,saboda bugun glass ɗin motar daya ji anyi daga waje,muryar wani basamudan soja ce ta karaɗe kunnansu da cewa"Oya wind down ur glass,"
  A hanzarce Sofwan ya sauke glass ɗin motar,yana ta faman mazurai kamar wani mara gaskiya,
   tambayarsu yashiga yi"Su wanene ku!kuma wurin wa kuka zo,?
   Murya na rawa sofwan yashiga nuna hayaam yana cewa"am..yalla6ai..itace zatayi jawabi,bani ba,"
   girgiza kai hayaam tayi tare da kai hannu ta ɗauko purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,cikin sauri ta ciro wayarta tare da ruƙe ta a hannunta,nan fa tashiga tunanin wa zata kira acikinsu don yayi masu magana subarsu su shiga,
  "Madam ke muke jira,bama son 6ata lokaci and remove dat thing u covered ur face with" muryar sojan ce ta sake katse ta,yana nuna nikab din da yatsansa.
  Tuni taji zufa ta soma karto mata a fuskarta da sauri tasa hannu ta cire nikab din,contact ɗinta tashiga tare da dialing numbar Kanal Yousof,cikin rashin sa'a wayar tashiga ringing amma ba'a ɗaga ba almost 3 times,cikin sauri ta kuma lalubo numbar Junaid,har ta gama ringing junaid bai ɗaga kiran ba,da alama shima baya kusa da wayar tashi,
  Hankalin Hayaam ba ƙaramin tashi yayi ba,dama su biyu kawai take da numbarsu a wayarta gashi duk sunƙi ɗaga kiran,
    ganin zata 6ata masu lokaci yasa sojoji bashi umarnin yaja motar shi yabar wurin,
     Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,ba ƙaramin 6acin rai tashiga ba,amma babu yarda zatayi dolenta su koma,
  Sofwan na ƙoƙarin tashin motar su bar wurin,sai ga motar Sgr ta kunno kai daga cikin babban gate ɗin gidan,
Zuba ma motar ido sukayi gaba ɗayansu musamman hayaam da take jin cewa sauƙi yazo mata,don tasan kowanene zai bada Umarnin abarsu su shiga ciki ne,
"Sir I think something is wrong here," Amstrong ne yayi mashi magana,
Don haka sgr ya bashi command ɗin ya tsayar da motar tasu don jin meke wakana,
A daidai saitin motarsu Hayaam Amstrong ya dakatar da tasu motar,sannan a hankali a wani irin slow glass ɗin motar suka soma saukewa atare,
Waro ido waje hayaam tayi nan take zuciyarta tayi wani irin bugun bazata,ba don komai ba sai don ganin mutumin da tajima bata sashi a idonta ba,wato abun harinta,
A hakimce yake zaune a back seat ɗin motar,ba ƙaramin kyau yayi ba yayi wani fresh dashi,musamman wankan daya ɗauka,Red shirt ce ajikinshi,tare da black trouser,

launin rigar ya ƙara fito da wannan hasken fatar nashi sosai fari sol kamar ka ta6a jini ya zuba,sumar kan nan kuwa tana ɗaure abayanshi,yayin da idanunshi ke lumshe tamkar mai jin bacci,
Cikin sauri sojan ya ƙarasa inda yake tare da buga ƙafa ya sara mashi sannan yace"Sir,wasu baƙin fuska ne ke son shiga cikin gidan,kuma basu da shaidar da zamu iya barinsu su shiga cikin gidan,shiyasa muka dakatar dasu,
kusan 5 mins bai buɗe bakin shi ba,babu alamar cewa zaiyi magana ma,kowa yayi tsit yana jiran jin ta bakin shi,kai har sai da sojan ya fidda rai da zaiyi magana sannan Calmly yace"What about asking their details?
Sojan yace"ban tambaye su wannan ba,amma bari naje na tambaye su,"
juyawa yayi tare da ɗan matsawa kusa da motar Sofwan yace"yana buƙatar bayani a wurinku,ku gabatar da kanku don yasan su wanene ku,"
jin shiru hayaam bata ce komai ba yasa sofwan juyawa zaiyi mata magana,sakin baki yayi yana kallon ikon Allah,gaba ɗaya hankalinta ya tafi kan Sgr,ba ƙaramin tafiya da imaninta yayi ba,
Nan take yaji wani irin kishi ya rufe shi,acikin ranshi yace"haba no wonder,sai yanzu na gane dalilin dayasa hayaam ta haukace mun akan wannan Namijin,mutum kullum ƙara kyau yake yi,kamar shi yayi kanshi don kyau,muddin irin wannan na yawo agari tofa bazamu ta6a yin kasuwa ba,"
"Don't waste our time"! muryar sojan ce ta katse mashi tunanin nashi,
Cikin sauri yace"Hayaam!magana fa ake maki,kiyi masu bayanin alaƙarki da mutanen gidan,"
Ajiyar zuciya hayaam tasaki,sannan anatse ta soma magana"ka sanar dashi cewa ƙanwar matar yayansu ce hayaam,"
Juyawa sojan yayi tare da komawa wurin motarsu Sgr yace"yalla6ai tace ita ƙanwar matar yayanku ce kuma sunanta Hayaam,"
a hankali sgr ya ɗan buɗe idanun shi,
Hakan yasa Hayaam dake hangen shi ta soma washe baki,ba don komai ba sai don ita atunainta sgr ya gane jawabin da Sojan yayi mashi,
Cike da ƙasaita yace"sam wannan bayanin bai kwantamin araina ba!infact,I don't know any person wit dat name hayaam or what...,ban ta6a jin sunan ba,Sergeant!!a sallamesu su koma,nd add more security!!"
Yana ƙarasa maganar tashi,glass ɗin motar ya ɗaga sama sannan a hankali Amstrong ya tashi motar,anatse yake driving ɗinshi har suka bar wurin gaba ɗaya,
dariya ce ƙumshe abakin sofwan amma ya gaza fitar da ita saboda tsoran 6acin ran hayaam,sam yaƙi yarda su haɗa ido da ita,saboda tsoran karta huce akanshi,
Kamar ta aza hannu akai ta fasa ihu haka taji,zuciyarta har wani boiling take tana burning saboda tsantsar 6acin rai da baƙin ciki,ashe duk haukan nata ma abanxa ne Sgr baisanta ba,baisan wacece ita ba duk zuwan da takeyi gidan a lokacin baya,
daƙyar sofwan ya daure ya cije tare da ce mata"mu juya ko"?
A tsiwace tace"bansani ba!!mtswww" ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki,
Can kuma tace"babu inda zanje wlh,kota tsiya kota arziƙi wlh saina shiga cikin gidan koda kuwa zamu kwana anan ne,don bazanyi tafiyar banza ba,"
Cikin sanyin murya sofwan yace"Hayam ki bi komai a hankali!su fa waɗannan mutanen da kika gani ba kamar sofwan ɗin da kika raina bane,muddin kikace zakiyi masu rashin kunya wlh dukan tsiya zaki sha,kakkarya ƙasusuwan jikinki zasu yi,kuma kada kiyi tunanin cewa zakiyi masu kwarkwasa ko kija hankalinsu da kyanki,don wlh babu ruwansu da mace,su ba mayin mata bane irina,so u ave to be very careful,"
ya ƙarasa maganar fuskarshi ɗauke da dariya,don yau ba ƙaramin nishaɗi yasamu a wurin Sgr ba,ba ƙaramin burge shi yayi ba yanayin acting ɗinsa babu wasa aciki,Namijin ne dae na gaske,
Tsuke fuska hayaam tayi,harara ta watsa mashi tare da jan dogon tsoki batare da tace komai ba,
tunani tashiga yi akan yadda za'ae su shiga cikin gidan,nan take zuciyarta ta bata shawarar ta kira Aunty babba ta sanar mata,tana ƙoƙarin kiran nata sai ga Motar Haroon ta shararo da gudun gaske cikin layin,
tunkan ya ƙaraso wurinsu ya rage gudun motar tashi,sai da yazo dai dai bakin gate ɗin gidan sannan yayi parking ɗin motar tare da sauke glass ɗinta,da alama yasha ya bugu har takai mashi karo,saboda yarda idanunshi ke ta faman rurrufewa sunyi luhu luhu dasu,
dakyar ya iya tsayar da idanunshi akan Motar sofwan,nan take suka hango mashi kyakkyawar fuskar hayaam,ɗaga murya yayi tare da kwala ma sojojin kira,cikin sauri suka tunkari motar tashi tare da sara mashi,
Yatsina fuska yayi ya kallesu a wulaƙance yace"Meke faruwa anan ne?su wanene acikin motar can"?
ɗaya daga cikinsu ne yace "Yalla6ai,ba mu san ko su wanene ba,mun hana su shiga ciki ne saboda basu da shaidar da zamu iya barinsu shiga cikin......'
Tunkan ya ƙarasa maganar haroon ya katse shi da cewa"Saboda gidan na ubanku ne!wai ma uban wanene ya kafa wannan dokar ta hana mutane shiga cikin gidan nan ne!"?ni banga amfanin takurawa mutane ba,idan tsaro ne ba Allah ke tsarewa ba mtswwww,
Shiru sojojin sukayi suna sauraron faɗan nashi kamar ubansu,hayaam kuwa tunda taji yana zazzaga masifa yasata ɗagowa tana kallonsu,ganin yarda yake banbamin bala'e akan an hanasu shiga yasa ta soma sakin murmushin jin daɗi,
Sofwan kuwa jinjina kai yayi tare da cewa"ikon Allah,kowanene wancan jarababben da yake ta faman tada jijiyoyin wuya,da alama ba ƙaramin hatsabibi bane,'
Cikin lallashi sojojin suka haɗa baki wurin cewa"Sorry sir!Allah ya huci zuciyarka!"
Hura hanci haroon ya shiga yi kafin daga bisani yace"Ban amince abarsu su shiga da motar da suka zo da ita ba!shi namijin yaja motar ya koma gidan ubansa,ita kuma budurwar kuce mata tashigo daga cikin motata na sauke ta cikin gidan,idan har bata amince ba to su tattara su koma inda suka fito,".
"An gama yalla6ai,"atare suka amsa mashi,sannan suka juya tare da tunkarar motar sofwan,tun kafin su ƙaraso hayaam ta buɗe motar jiki na rawa ta fito saboda taji duk bayaninshi acikin kunnanta,
Hankali tashe sofwan yace"Hayaam ni kuma awani matsayi kika ajiye ni ne"?
Batare da ta waigo ta kalleshi ba tace"Zan kiraka a waya,in nasamu lokaci,ta bude back door ta dau jakanta"
Jiki asanyaye Sofwan yaja motar,yayin da zuciyarshi ke cike da 6acin ran abunda tayi mashi,yasha wahalar kawota,amma ko godiya babu balle yayi tunanin sake samun wani abu awurinta,tuni yaji hawaye sun cika mashi idanunshi,tabbas hayam ta cuce shi sosai ba ƙaramar wahala yasha akanta ba,duk don ya mallake ta amma gashi nan ya tashi a tutar babu!dashi da Zero basu da bambanci ƙwara ma zero yana da amfani wurin yin lissafi,

Shu'umin murmushi haroon ya saki lokacin da hayaam ta ƙaraso jikin motar tashi,hannu tasa tare da buɗe gaban motar tashiga ta zauna tare da rufe motar,sannan ta mayar da idonta akan haroon daya zuba mata ido ko kyaftawa baiyi,
ita kanta saida tasha jinin jikinta da ganin irin zubin shi,cikin sanyin murya tace"Sannu ko,"
ɗan ta6e la66ansa yayi tare da cewa"Yawwa,amma naga baƙuwar fuska ina buƙatar ƙarin haske,"
Cike da kwarkwasa tace"Sunana Hayaaam,ni ƙanwar Aunty laila ce da kuma Aunty Amani,"
murmushin gefen fuska haroon yasaki kafin yace"Wow,no wonder that's why naga kamanceceniyar ki da Aunty laila,ashe ke ƙanwarsu ce,amma fa am really sorry game da abunda ya faru,securities ɗin gidan nan basu son ciwon kansu ba,in ba haka ba taya zasu ga mace kamila irinki sanye cikin dogon hijab kuma su hanaki shiga?
Sunnar dakai Hayaam tayi tana faman sakin shu'umin murmushi,aranta tace"dalilin dayasa na sanya dogon hijabi kenan saboda nasan cewa kowa zaiyi tunanin ni mutuniyar kirki ce,hmmmmm basu san cewa da fuska biyu nazo masu ba,"
(Rashin sani yafi dare duhu!hayaam batasan da wa take magana ba,"
"Kada na cika ki da surutu,bari nashiga dake cikin gidan,"
Ya faɗi tare da jan motar da gudun gaske ya shige cikin babban gate din gidan
(Finally hayaam ta samu nasarar shiga cikin gidan) 

*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃


*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*

*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*


*LOCATION KANO*

08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka
Wadrobe balls
Madarar kulleccham
Vaseline kulleccham
Kajiji
Halut
Couscous
Khumrah
Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku

It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.
Snack
Awarah
Farah
Zobo
Samosa
Cup cake etc
Contact me 09063302182or 09012179727.

     _💋BOSS BATURE💋_


*Zuwa ga masu karkasamun littafin duk wanda ya ƙara haɗamun document,ban yafe ba!babu yarda za'ae ni ina cikin rubuta littafi na biyu,wasu kuma sun haɗamun document na book 3 don iyayi da kuma ƙarfin hali,sai ja mun surutu sukeyi nacewa naja littafi har book 3 duk da idan naga dama har book 5 ma sai inyi bani naji zan iya ba😒😏🙄😒, wasu har gardama sukeyi mun nacewa book 3 suke so complt,bayan ni iya book 2 nake cikin rubutawa ma,*



Abban sojoji part 2 ❤


Bayan Haroon yayi parking ɗin motar,hayaam tayi mashi godiya tare da ɗaukar bag ɗinta,ta fito daga cikin motar sannan ta nufi cikin gidan,
  Shu'umin murmushin nan nashi ya saki yabi ta da kallo tare da cewa"Nifa bana abu don Allah,kowani tsautsayin ne da ƙaddara suka kawo ta cikin gidan nan!Allah yasa ta kwanan mana biyu...." ya jinjina kai tare da cewa "tsuntsu daga sama gasasshee!"ya ƙarashe maganar tashi tare da zura hannun shi cikin aljihun jeans ɗin dake a jikinshi,wayar shi ya ciro tare da duba screen ɗin, missed calls aka mashi da wata hidden number,
    shiru yayi yana tunanin taya zai bi kiran saboda kira ne mai mahimmanci a wurin shi gashi dole sai in shi mai 6oyayyiyar numbar ne ya kira ka,
  Yana cikin wannan tunanin sai ga kiran ya sake shigowa,cikin sauri yayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnan yana jiran jin me za'a sanar dashi
  Wata irin muryace ta irin hamshaqan matan nan waɗanda suka ji duniya ta soma magana"Haroon!kana shirin jamin bala'e ko?meyasa ka fiye shiririta ne?ko kamanta plan ɗin mu ne"?
   nan take haroon yashiga en ina murya na rawa yace"ban manta ba,inaso nabi komai a hankali......'bata bari ya ƙarasa maganar ba ta kwatsa mashi tsawa"Ya isa Haka! kasani wlh akanka bazan bari nayi gangancin rasa damar da nake da ita ba!haroon zaka iya rasa ranka muddin kace zaka kawomin wasa acikin lamarina!kai kasan wacece NI!bani da imani,"
  Wata irin zufa ce ta soma gangaro mashi daga cikin sumar kanshi,lokaci guda duk yabi ya rikice yashiga zazzare idanu,
   sautin dariyarta ce ta karaɗe kunnan shi,tsagaitawa tayi da yin dariyar sannan ta sassauto da muryarta wurin cewa"Am sorry fa,na tsorata ka ko?
Nannauyar ajiyar zuciya haroon ya saki tare da cewa"Yanzu me kike so ayi ne,just command me zanyi maki koma menene,"!
   "So nake ka kashe JUNAID!saboda shikaɗai ne hanyar da zanbi wurin ƙuntata masu,banaso junaid ya rayu,muddin yana araye toh farin cikin gidan zai cigaba da wanzuwa ne,ni kuma abunda bana so kenan!,"
     girgiza kai haroon yashiga yi tare da cewa"Kiyi haƙuri wannan ne karo na farko da kika ban umarni na musa maki tunda na fara maki aiki!junaid is innocent  I can't kill him,zan iya kawar maki da duk wanda kikeso acikin gidan nan,Amma banda junaid!banda Abbana,Rafayet kuma yafi ƙarfina banda wata hanyar da zan iya cutar dashi,sai ma in jefa kaina cikin matsala!"
   fashewa da dariya tayi tamkar zata fasa screen ɗin wayar,bayan ta tsagaita da yin dariyar taci gaba da magana"kasan koni wacece,kasan kuma abunda zan iya!idan har bazaka iya kawar mun dasu ba,to ni zan iya kawar dasu ta cikin ruwan sanyi,Haroon u must do what i command you!if not i wll expose ur secrets,kai kasan me zai biyo baya,ko ka kashe junaid ko kuma ni in kashe maka rayuwa gaba ɗaya...!!!!
   Waro ido waje Haroon yayi yana sauraronta,
  Cigaba da magana tayi"Maganar videon su Twins daka ɗauka,nasan ka goge na wurinka,amma akwai wani a hannuna,zanyi amfani dashi wurin tarwatsa zuciyar mahaifin nan nasu,da kuma masoyina Rafayet!inason ganin tashin hankalin shi sosai...."
  A tsorace haroon yace"Kada ki kuskura ki saki bidiyon nan!in ba haka ba asirina zai tonu ne!kuma kina sane da cewa,muddin asirina ya tonu to ke ma kin gama yawo!!atare zamu fuskanci sakamakon mu,zasu kamo ki ne aduk inda kika 6uya!!"
    ya ƙarasa maganar yana faman sakin huci yayin da idanun shi sukayi jawur saboda tsananin 6acin rai,
   fashewa ta kuma yi da wata irin mahaukaciyar dariya kafin ta tsagaita da yin dariyar tace"Haroon!Iska bata ruƙuwa!domin ni tamkar iskar nake,kada kamanta ina amfani da baƙaƙen aljanu wurin gudanar da aiki na,kuma zanyi amfani dasu ne wurin ganin na tarwatsa dukkan zuri'ar Salahuddeen Hussein!wannan alwashi ne na ɗauka,rai uku masu mahimmanci suka kashe mun,ni kuma rayuka zan ɗauka!don bana yafiya arayuwata!"
  Shiru yayi bai ce komai ba kusan minti biyar, sam baison wani abu ya samu abbanshi shi kaɗae yafi ji sannan yace"Maganar yaran nan fa?su kuma ya zakiyi dasu?
   "Inaso saina fara sanya soyayyarsu acikin zukatan ƴan uwansu sosai,saboda inaso inyi amfani da wannan damar ne wurin ƙuntatawa dukkan wani jin daɗi na zuri'arsu,kamar yarda suka ƙuntata ma tawa zuri'ar,"
    Jinjina kai haroon yayi kafin ya kuma cewa"Yanzu menene plan ɗinki"?
   Wannan karan anatse ta soma magana"plan ɗina shine kawar da junaid,dalilin dayasa nakeson kawar da junaid shine!sihirina bazai ta6a tasiri akan Rafayet ba har sai an samu lagwanshi,kuma ba kowa bane lagwanshi ba fa ce Junaid,da zarar ya rasa junaid zaiyi sakaci da ibadarshi hakan zai bani damar yin aiki akanshi,kuma shi ya kasance Bugun zuciyar family ɗinsu inaso na ɗanɗana masu raɗaɗin rasa mutumin daka kwallafa rai akansa!sannan maganar bidiyon nan zan sake shi a social media kowa ya gani,daga zarar hakan ta faru nasan cewa Martabar family ɗinsu da kuma ƙimar da suke dashi a duniya gaba ɗaya zasu zube,kowa zai tsani zuriyarsu duk wata daraja da suke dashi a idon duniya zata tashi abanza ne!ni kuma hakan nakeso,kafin na saki bidiyon inaso kayi amfani da kuɗin da suka baka wurin barin ƙasar,ka koma malaysia da zama,na shirya maka komai najin daɗin rayuwa acan,giya da mata har saika gaji dasu,"
   shu'umin murmushin nan nashi ya saki aranshi yana ayyana irin rayuwar da zaiyi acan cikin daular da aka shirya mashi,nan take yaji cewa zai iya aikata komai takeso,
  Sam yama manta da waya yake yi saboda tsabar farincikin da ya ziyarce shi,mayar da bayanshi yayi a jikin seat na motar yana cigaba da sakin murmushi,
   "Kana jina kuwa,"muryarta ce ta ratsa kunnan shi,hakan yasa ya dawo daga dogon tunanin daya tafi,
   Sai da ya samu natsuwa sannan yace"Naji duk abunda kika ce,hakan yayi mun sosai,musamman da kika ambaci giya da mata,sai naji wani nishaɗi araina dama irin rayuwar da nakeson yi kenan,amma akwai wata shawara da nakeson baki,in ba damuwa,"
  Tace"ina sauraronka haroon,"
"Ga me da bidiyon tsaraicinsu twins,kada ki sake shi a social media pls,sun riga sun biyani kuɗi kamar yarda na buƙata,shiyasa nakeso ayi masu sassauci,mutun biyu kawai nakeson suga bidiyon nan Abban su da kuma wannan ifiritun sarkin jin kan nan,sannan maganar kashe junaid nasan ban isa na hanaki aikata abunda kika yi niyya ba,amma abunda nakeso ki bar komai a hannuna,ni ko ke babu wanda zai kawar dashi!kiyi amfani da sihirin ki kawai ta cikin ruwan sanyi yarda babu wanda zai zarge ni!!"
     Dariya sosai tayi da alama shawarar Haroon tayi mata,
   Sannan tace"daga yau komai zai fara"!!!
murmushi haroon ya saki tare da cewa"Allah yaba mai rabo sa'a"
  daga haka su kayi sallama ya kashe kiran,kasa fitowa daga cikin motar yayi ba don komai ba sai don kasalar da yaji ta baibaye shi,fuskar junaid kawai yake gani acikin idanun shi,😢

   ******************
Lokacin da Hayaam ta shiga cikin gidan da sallama abakinta tashiga main palour ɗin,tsayawa tayi da tafiya ganin babu kowa acikin babban falon,takun tafiyar da taji ne yasa ta juyawa ta gefen hagunta tana kallon mai tafiyar,bakowa bace face Sehrish sai faman sauri take yi don ta shiga kitchen,har yanzu shigar ɗazu ce a jikinta,amma ta yafa mayafi ajikinta tayi rolling ɗinshi,
   ta wutsiyar idonta ta hangi mutum hakan yasa ta dakata da yin tafiyar ta ɗan juya don taga wanene,karaf idonta suka haɗu akan na Hayaam,cike da mamaki take kallonta,batasan ko wacece ita ba,amma ganin hasken fatarta yasa tayi tunanin ko ƴar uwarsu Junaid ce,
   tunkararta sehrish tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙarasa inda hayaam take,tunkan sehrish ta ƙaraso zuciyar Hayaam ta shiga bugu,don ta gane cewa itace Ƴar aikin da Aunty laila take bata labarin cewa tana rayuwa acikin gidan,yarinyar da Abbansu ya mayar da ita ɗiyar shi,
   fuska ɗauke da murmushi sehrish tace"Sannu da zuwa,"
   hayaam tace"yawwa,ina mutanen gidan nan?naji shiru ko ba kowa ne"?
  sehrish tace"duk sun fita,amma junaid da Fawan suna acikin bedroom ɗinsu,sai Aunty azmee tana acan cikin kitchen,
   Jinjina kai Hayaam tayi har ta buɗe baki zata kuma cewa wani abu,sai ga Azmee ta fito daga cikin kitchen ɗin,ganin Hayaam yasa ta soma Sakin fara'a kamar gonar auduga,cikin sauri ta tunkaro wurinsu tana cewa"Wata sabon gani!Anya ba idona ne ke nuna min badaidai ba?
  dariya hayaam tayi tare da wuce sehrish ta tunkari wurin Azmeen suka rungume juna,
  ɗago da ita azmee tayi daga jikinta tana cewa"Oh ni Hayaam!ashe dama zan sake ganinki a duniyar nan?gaskiya kun yada zumunci!ina ji tun bikin Amani yaushe rabon ki da gidan nan!
   Sai faman washe baki Hayaam takeyi ba don komai ba sai don sanin cewa Azmee zata kar6eta hannu bibbiyu kuma zata goya mata bayan zama acikin gidan,
     "Kai Aunty azmee,nafa zo bayan bikin Amani kin dai manta ne,gaskiya nayi missing ɗinku sosai,shiyasa ma nace dole nazo naganku,"
  Magana takeyi amma hankalinta na akan Sehrish,dake tsaye tana sauraronsu,
   Azmee tace"mu ma munyi kewarki sosai,amma dai bada wuri zaki koma ba ko?don bazan bari ki tafi batare da kin zauna mana ba,". 
   Anzo wajen da tafiso nan fa tashiga washe baki tana cewa"ae Aunty azmee har sai kun gaji dani,in dae ba ku kuka kore ni ba,amma ni ina nan ba inda zanje,"
  murmushi Azmee tayi tare da cewa"Ae bama wanda zai kore ki hayaam,".
  taƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan sehrish tace"wannan Hayam kenan!ƙanwar matar yayansu ishaq,da kuma Amani wadda tazo ran nan harna gabatar maki da ita"?
  wani irin bugu taji zuciyarta tayi mata ba don komai ba,sai don tuna kalaman Amani da tayi in har wannan takasance ƙanwarta ce,lallaikam akwai matsala,
  da ƙyar sehrish ta ƙaƙalo murmushin yaƙe sannan tace"Allah sarki,ashe kanwarsu ce,naga suna yanayi da Aunty amanin,"
   ta6e baki hayaam tayi jin abunda sehrish tace,
   ruƙo hannunta Azmee tayi tare da cewa"Kada na cika ki da surutu,mu shiga ciki ki huta don nasan ba ƙaramar gajiya kika kwaso ba,"
  atare suka wuce ciki da Azmeee,zuru sehrish tayi ita dai tun da tayi arba da Hayaam taji sam bata kwanta mata arai ba,kama hanyar shiga kitchen ɗin tayi tana cikin tafiya taji muryar junaid ya ambaci sunanta,
   dakatawa tayi da tafiyar sannan ta ɗan juya tana kallon shi,fuskar nan tashi a yamutse alamar daga bacci ya tashi,sai faman sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi yake,
   acikin ranta tace"Shagwa6a66e halan yunwa yake ji ne,"
   ƙarasa saukowa yayi daga saman stairs ɗin kai tsaye wurinta ya nufa,
     Lokacin da ya ƙaraso inda take tsaye muryar shi cike da kasala yace"Reesh har yanzu Abbanmu bai dawo ba"?
ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tamkar zaiyi kuka yace"dama nasani,tunda wannan abokin nashi yazo mai farin gemu,nasan cewa ba zai barshi ya shigo ciki ba,yana can yaja shi sun tafi yawo gidan

Please Login or Register in order to submit comment