Reading FURAR DANKO PART2 COMPLETE BY BILLYN ABDUL Chapter 24 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Nima da nake anan ɗin yana damuna, shiyyasa nake jin da inada dama zanje Nigeria a tsakanin nan gaskiya. Ga batun mutumin nan, nasan hatsabibine bana wasa ba, zai iya bin hanyoyi da yawa dan ganin ya cuta mana.”
         Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, sai kuma ta saki murmushi da shafa fuskarsa, wasa ta cigaba da yi da gashin ƙasunbarsa a hankali. “Humm ni dai ka kwantar da hankalinka. Na farko dai batun wata Umma ma ka ajiyesa gefe ita ta jama kanta damuwa da ita baida wani amfani. Na biyu mune ya kamata mu kwantarma da Abba hankali shi da Ammah dan suna damuwa ne saboda abinda duk ya faru a kammu akayisa. Sulaiman kuwa shi ba komai bane a yanzu takansa ma yakeyi. Amma kamar yanda ka faɗa kam zai iya yin komai da ga sanda ya farga ruwa ya ƙare masa. Dan haka komai yana buƙatar ayisa cikin gaggawa a yanzu gaskiya”.
        “Kema kinzo da shawara kam. Sai dai kin san kamashi a yanzu kai tsaye bazai yiwu ba duk da muna da hujjoji”.
     “Eh hakane, muna buƙatar gaɓa. Ma'ana a kamashi cikin wani laifi dumu-dumu irin wanda baida mafitar nan. Wannan shine zai sa a cigaba da zaƙulo laifukansa na ɓoye. Shiyyasa ka daure ka barni na koma Nigeria. Aikin nan yana buƙatar fuska da fuska ne fa”.
            A take fuskarsa ta tsuke, babu alamar zai ce komai. Kansa ta ɗaga da ga kafaɗarta tana mai zuba masa idanu. “Wai kai ance maka zan gudu ne. Ina fa gama abinda nakeyi zan dawo ALLAH kuwa. In dai gudu ne kasa a ranka ka ƙaremin nawa yanzu babu sauran wajen ɓuya. Idan ma nace zan barka ai Uncle Yousuf da Daddy sai sunyi farfesuna koma su tauneni ɗanya. Kasan irin matsayin da kake da shi kuwa yanzu a gidan mu. Ai ko Ummita dana sani a baya-bayan nan defender ɗinka ce ta gani kasheni.”
        Kallonta kawai yake shi dai, kafin ya samu damar cewa wani abu kira ya shigo masa waya. Ita ta miƙe zuwa mirror ta ɗakko. Gannin Daddynta ne ta ɗaga tana kaiwa kunne.
    “My Son!”.
Daddy ya faɗa daga can. Cikin ɓata fuska tamkar tana gabansa ta ce, “ALLAH ya soni nima ina da Ammah da Uncle You da Abba da Mommy, ga Baba Garko”.
        Sosai Daddy ke dariya. Ya ce, “Oh oh irin wannan gori haka Mawaddat. To ai ALLAH yasa ma Baba Garkon nawa ne ɗan sammiki nayi. Kinga sai ki ƙarata da iyayenki nima ki barmin nawa da kuma yaro na”.
     Dariya tayi itama da faɗin, “Ai nafa bar maka Daddy ku ƙarata.”
   “To shike nan ƴar albarka. Ki faɗawa mijin naki gamu nan tafe in sha ALLAH. Ina fatan dai yana gidan?”.
         “Lah Daddy wai nan zaku zo? Dama kana London”. Ta ƙare maganar cikin shagwaɓa. Murmushi Daddy yayi da ga can har tana iya jin sautinsa. “A'a yau dai zamu shigo, ina Manchester.”
     “To Daddy ALLAH ya kawoku lafiya, mizan dafa muku?”.
      “Basai kin dafa komai ba ƴar Daddynta. Muda bazamu jimaba ma. Bye bye sai munzo”. Ya yanke wayar kafin tace wani abu. Bata damu ba ta zauna kusa da Smart da ke kallonta tana murmushi. “Mr A dama Daddy zasu zo shine baka sanar min ba?”.
          Murmushi kawai yay mata baice komai ba. Itama sai ta dungure masa kai tana miƙewa. Fita tai a ɗakin zuwa kitchen ta barsa shi da ɗansa.....


      ★Tarba ta mutuntawa Daddy da Uncle Yousuf suka samu, shi Daddy wannan shine zuwansa na farko, Uncle Yousuf kam ɗan gida ne. Sun ci abinci a tare cikin farin ciki. AA na nane da Daddy dan akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakaninsu. Kasancewar ba wani jimawa akai da rabuwa ba bai manta kakan nasa ba. Bayan sunci sun sha sukai zaman abinda ya tarasu. Tsakanin Lulu da Daddy sun ɗan ƙara tattaunawa akan abinda ya faru tsakaninsa da Sulaiman da Mahaifiyarta. Yanzun ma sai da tai hawaye. Ashe babban kuka na gaba, dan lokacin da suka fara kallon abinda ke cikin camara ba Lulu ba hatta Smart da Uncle Yousuf sai da sukai hawaye. Daddy kam ƙasa kawai yay da kansa yana mai jin kewar matar tasa. Kuka sosai Lulu keyi na fitar hankali da ganin mahaifiyarta. Smart na son lallashinta yarasa yanda zai yi ga surukai. Dole ya hakura ya zuba mata ido sai tissue da yake faman miƙa mata na share hawaye, sai Daddy ne ya sakata a jikinsa ta gefe yana lallashinta. Yau jinta take kamar gata ga mahaifiyarta. Ashe dai haka suke tsananin kama, dan duk wanda ya ganta yasan mamanta yasan itace ta haifi abinta. Suna kama matuƙa tamkar tayi kaki ta ajiye ne. Ƙuruciya kawai Lulun zata fita. Ganin waɗan nan tsiyataku na Alh. Sulaiman ya sa Lulu cewa tanada shawara. Su duka idanu suka zuba mata alamar saurare. Zamanta ta gyara cikin dasashiyyar muryarta da kuka ya ɗasar ta ce,.........✍️




_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣8️⃣




.......“In dai muna son kama mutumin nan ya zama mai ƙarfin da bashi da mafita dolene sai mun haɗa hannu da Baba Garko, inba hakaba ko yazo hannu zai zama a banza ne, kai koda an kaisa kotu ne zai iya kuɓuta ma fa, idan ma an tsallake nan alƙali ya yanke masa hukunci to abokan huɗɗarsa zasu iya cireshi saboda yana huɗɗa ne da manya-manyan shegu na duniya bawai na Nigeria kawai ba. Duk da dai abu ɗaya dana sani ga manyan dilas na waɗan nan kayan a duk sanda sukaga zata kwaɓe musu ko zaka ci amanarsu zasu iya kashe juna. Ma'ana kamar yanda sukeyi akan duk wanda ya so bijire musu, shima ya koyo wannan ɗabi'ar ne a hannun turawan nan. Dan haka dolene zamuyi amfani da matakai uku na salon yaƙin kuma duk masu kamanceceniya da juna. Matakin farko shine Baba Garko, sai kuma kama duk wanda suke zagaye da Sulaiman ɗaya bayan ɗaya, hakan zaisa mu ruɗa masa hanjin ciki da jigata masa rayuwa mu sabautashi a tsaye. Hikimar saka Baba Garko anan itace yanada ƙarfi, sannan a fannin safarar miyagun kwayoyi shi maƙiyinsu ne, zai iya yin komai akan duk wanda hukuma ta cafke ta yanda bazasu taɓa kuɓuta ba. Mataki na biyu zamu ƙullama Sulaiman talala tsakaninsa da abokan huɗɗarsa musamman turawan nan na ƙasar Mexico. Kunsan duk wani shege akan harkar waɗan nan kayan yana ƙasar Mexico, saboda wannan matsalar na zagaye da rayuwarsu fiye da kowa a duniya, kuma nanne Sulaiman yafi safarar kayansa. Na uku dolene mu ɓoye kammu mu duka ta yanda idan muka kunnamasa wuta Daddy zai fara hara har zuwa wani mataki, saboda shi kaɗai yasan yana da camara ɗin nan, mu kuma zamuyi amfani da wannan fusatar tashi ne muyita fidda laifinsa waje ta yanda wasan zai zame masa gaba kura baya sayaki...”
        Su duka babu wanda murmushi bai bayyana a kan fuskarsa ba, domin gamsuwa da shawaranta ɗari bisa ɗari. Albarka Daddy ya dinga saka mata, yayinda Uncle Yousuf ke tayashi. Smart dai na murmushi da binta da kallo ƙasa-ƙasa. Dan ya sake tabbatar da lallai matar tasa ƙwaruwace a lauyanci ashe tasan mutakeyi. Daddy ne yace, “Ni yanzu gaskiya bawani sanin kowa da kowa na cikin kasuwancin nayi ba, inma komai zai mana wahala sai dai wannan”.
      “Shima bazai mana wahala ba Daddy, karka manta lungu da saƙo na sani, nasan manya da yara masu wannan business ɗin, kuma duk da haka zan nemo Nadiya itama, duk da bana jin zata bamu haɗin kai ta ciki sauƙi saboda abinda nai maita a last rabuwarmu, amma zan ƙoƙarta naga na ta dawo gareni saboda nasanta zata iya komai akan kuɗi, dan wannan ita ido ce a garemu tamkar google. A yanzu haka zan iya bada list na wanda wasan zai fara a kansu”.
         Anan ma duk sun gamsu da zancenta, a take kuma ta zana musu sunaye da adireshin wajajen da take sayen kayayyakin, tun daga hannun ƙananan ƙwari har zuwa manya-manyan dila data sani a dalilin abokan huɗɗar nata. Ba kuma wai a wajen Kano kawai suke ba, a faɗin Nigeria gaba ɗaya harma da kasashen ƙetare dake maƙwaftaka da Najeriyar. Sosai Daddy yasha mamakin ganin waɗanda ta zano ɗin, har ma da Uncle Yousuf. Shi dai Smart ba kowa ya sani ba sai ɗaidaiku irin su Hon Nakowa suma dan sun kasance sanannun ƴan siyasa ne. Sai dai ganin sunan MM Atik Kumo ya sashi kallonta. Ta fahimci mi yake nufi, dan haka ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Shima Dila ne ai, ko'a ranar daka ɗakkoni a gidan nan tare da tsoffin nan gidansa ne, sannan shine ya sayar mana da kayan”.
       “Shi wannan ɗin da nake gani simi-simi?”.
     Lulu ta ce, “Humm bakaga komaiba ma, wasu ma dan ban san yanda zan misaltasu bane ku gane saboda sunan banza na sansu da shi, wasu kuma haɗuwar club ne kawai”.
   Babu wanda ya sake iya magana dan sun san a zancen Lulun kam babu tantama...

       A ranar su Daddy suka koma Manchester, dan washe gari suke son tafiya Nigeria su duka biyun, a Abuja kuma zasu sauka domin wucewa da su Twins, dan har Daddy ya nema musu transper zuwa Kano, duk da dai sun so bijirewa ya nuna musu basu isa ba. Har Mommy sai da ta kirashi akan hakan ya nuna mata babu ruwanta, ƴaƴansa ne, yanda yaso haka zai tafi da rayuwarsu. Dama dai da amincewarsa suke aiki a Abujar yanzu kuma yace su dawo gida suyi a gabansa. Jin ya buɗe mata wuta dole ta kama kanta, dan Daddy nada haƙuri, idan aka ƙuresa kuma akwai hayaƙi.
     Tunda su Daddy suka wuce Lulu ta maida Camara ɗin nan abar kallo, sai da Smart ya ga kukan nata yayi yawa ya kwace ya ɓoye, duk roƙon datai masa akan ya bata ƙi yayi. Da ga ƙarshe ma ya ɗauketa suka fita. Wannan ɗan yawon da sukayi ne ya rage mata raɗaɗi da damuwar da take a ciki sosai. Dan basu dawo gidan ba sai da dare ya tsala kasancewar su daren da rana duk babu ruwansu bai hanasu hidimar gabansu. Washe gari ya kwasheta suka sake fita, sune har wajen gyaran jiki da wajen wasan yara aka kai AA duk da shi ba fahimtar komai yake ba. Wannan ɗan busy ɗin ya saka mata nutsuwa ta cire komai a ranta, sai sake duƙufa yima mahaifiyarki addu'a kuma.
      Ahmad yay kiran Smart akan pharmacy da jami'an tsaro dana hukumar NDLEA sukaima dirar mikiya. Inda babu wani shan wahala aka gano na mahaifin aunty Khadijah ne dai, ta kai ma har an kamashi shi da yaran pharmacy ɗin gaba ɗaya. Duk da wasu sun rantse su basu san ana wannan baƙin kasuwancin ba. Sai dai ba'a sauraresu ba an ce sai abinda bincike ya tabbatar... Sosai Smart da Lulu suka tausayama Aunty Khadijah, dan Ahmad yace ana faɗa mata yanke jiki tai ta faɗi a asibiti, yanzu hakama tana can, bama ita kawai ba, zuri'ar gidansu gaba ɗaya suna cikin tashin hankalin al'amarin, dan abunne da babu wanda ya taɓa kawowa a ransa.....

*_NIGERIA_*

   Tako ina komai a hargitse yake. Musamman ma a fanin iyalan Alhaji Sadi Dikkon da aka wayi gari da labaran kamashi, tare da yima babban pharmacy ɗin da sai yau mutane da yawa suka san nashi ne tsirara. Inda aka dinga nuna miyagun kwayoyin dake danƙare a cikin pharmacy ɗin da yanda ake kasuwancinsu a tsawon lokaci batare da hukumomi sun fargaba balle jama'ar gari da basu taɓa kawoma ransu ba. Gaba ɗaya Kano a rikice take da kace nace, saboda Alhaji Sadi babban mutum ne da ke a cikin jerin ƴan kasuwar da ake ji da su a Kanon dama ƙasar ta wani fannin. Sannan sam a fuska bazaka taɓa kawoma kanka zai iya aikata irin wannan ƙazamin kasuwancin ba.
         
        Alh. Sulaiman na kwance a gidansa hankali kwance, yana ma tsaka da jin daɗin duniyarsa shi da amaryarsa kira ya shigo masa a waya kusan ƙarfe biyun dare. Rai a ɓace ya ɗaga duk da yaga Hon Nakowa ne a kan layi. Sai dai yana ɗagawar furucin Hon. Nakowa ya sashi zabura yana ture matar tasa gefe da lailayo wata gawurtacciyar ashariya mai kawuna goma sha biyu ya dire. Har neman taune halshensa yake wajen faɗin, “Tayaya hakan ya faru? Shi wane sakaci ne ya kaishi ga haka?”.
         “Babu fa wanda yasan yanda akayi, Garko kaima kasan Alhaji Dikko na cikin mutane masu taka tsantsan matuƙa. Kawai dai akwai abinda ya kamata musani, sannan muna buƙatar zaman meeting na gaggawa dan nasan zuwa safiya zasu iya cewa zasu kamashi”.
      “Wane zaman jira zai tsayayi ayi meeting da shi, a daren nan ya sayi ticket ya bar ƙasar nan kawai, idan kuma ya bari suka kamashi to tabbas zai mutu, dan mutuwarsa tafi rayuwarsa muhimmanci a garemu yanzu. Sauran aikin zamu ƙarasa a rufe zance. Dan haka kai kiran su Baita yanzun nan mu haɗu, dan muna buƙatar ganin shugaban NDLEA da IG ma kansa”.
      Cikin gamsuwa Hon. Nakowa yace “Hakan yayi”.
         Alh. Sulaiman na yanke waya idonsa ya sauka akan amaryarsa data zuba masa ido. Wani irin dafe kai yayi da faɗin, “Oh shiitt” dan harga ALLAH ruɗewa tasa ya manta bashi kaɗai bane a ɗakin ya zauna yana sakin zance har haka. A wani irin fusace ya nufeta, babu zato taji ya mata wata irin tsawa da nunata da yatsa. Har sai da ta zabura.
     “Me kika ji?!!”.
Ya faɗa a gigice. Kanta ta shiga girgiza masa jikinta na rawa. “Banji komai ba wlhy Alhaji. Kwata-kwata banji komai ba”.
           “Idan ma kin jin ki ɗauka baki ji ba, idan kuma kikace zaki nuna kinji kiyi kuka da kanki”. Da ga haka ya wuce fuuu zuwa toilet domin tsarkake jikinsa. Tashin hankali na haƙiƙa ta shiga, dan jikinta har rawa yake yi, zuciyarta kamar zata faso ƙirjinta ta fito. Gaba ɗaya kalaman mijin nata sun ɗimautata, so take tabar ɗakin ko zata samu iska, sai dai babu dama, dan fitar tata zai iya sawa ya zargi wani zataje ta faɗawa. Bata taɓa sanin atsabibancin mijin nasu ya kai haka ba, karo na farko a rayuwarta da taji ashe garama da ALLAH bai bata haihuwa a gidan nan ba..
      Tana a kwancen ya fito, jikinsa duk laima bai damu ba ya saka jallabiya tare da zarar wayarsa da key ɗin mota ya fice. Da kallo kawai ta bishi kamar matacciya, dan ko dogon numfashi bata iyayi saboda tsabar tashin hankalin da take ciki..

        ★A lokacin da su Alh. Sulaiman ke nufar inda zasu haɗu meeting a lokacin jami'an tsaro sukai dirar mikiya gidan Alhaji Dikko dake ƙoƙarin sulalewa ya bar gidan batare da sanin ko iyalinsa ba. Aiko a take sukai ram da shi. Jiniyar motocin jami'an tsaron ne ya fargar da iyalinsa dama ƴan anguwa. Hankalin kowa a tashe, yaran sai kuka suke suna kiran yayunsu a wayoyi, ta hakane Aunty Khadijah da batasan mike faruwa ba tun safe da aka fara tone-tone a pharmacy ɗin mahaifin nata da ita kanta bata taɓa sanin nasa ɗin bane labari ya risketa daga bakin ƙaninta. A wajen ta yanke jiki ta faɗi tana tsaka da duba mara lafiya. Tun a daren Coach da Ahmad suka nufi asibitin cikin tashin hankali. Shine ma ya samu damar kiran Smart suka tattauna bayan aunty Khadijah ta farfaɗo an mata allurar barci mai ƙarfi. Zuwa safiya labari ya ƙara karaɗe ko'ina da ina, yayinda shugaban NDLEA na Kano dama na ƙasa gaba ɗaya suka ƙi ɗaga kiran su Alh. Sulaiman. Hakama IG da CP basu ɗaga musu kira ba. Abinda basu sani ba shine akwai wata ƙullaliya tsakanin gwamna da Alhaji Dikko, yana samun labarin abinda ke faruwa yay kiran CP da shugaban NDLEA na jiha yay musu gargaɗi. Tare da tabbatar musu in suka bari Alhaji Dikko ya ƙuɓuce musu a bakin aikinsu. Sannan Baba Garko ogan Gwamna ne na amana, dan haka yay kiranshi shima akan su IG da shugaban NDLEA na ƙasa. Shi baba Garko dama abune daya tsana a rayuwarsa, yake kuma yaƙi da masu alaƙa da shi, amma sam bai san akwai alaƙa tsakanin ɗansa Sulaiman da Alhaji Sadi Dikko ba sam...
     Matuƙar tashin hankali sun shiga jin an cafke Alhaji Dikko, a take meeting ɗin su ya canja akala zuwa shirya yanda zasu kashe Alhaji Dikkon kawai. Dan sunci alwashin bazasu taɓa barinsa ya tona musu asiri ba. Sai dai dolene suyi komai ta ƙarƙashin ƙasa saboda gujema idon mutane a kansu. Sun nema amintattunsu dake cikin jami'an tsaron, kai tsaye suka basu umarnin kashe Alhaji Dikko ta hanyar guba. Kasancewar suma abokan cin mushen nasu ne sukai na'am da hakan. Dan in dai aiki ya buɗe suma nasu ya buɗe ai........✍️


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣9️⃣



.......Kowa da abinda ya damesa. Duk da abinda ke faruwa a jihar ta Kano ya girgiza Abba hankalinsa a rabe yake gida biyu a dalilin halin da Ummah ke ciki. Duk da ma dai malaman da aka kawo a wannan karon su sunyi jarumtar tsayawa, sai dai daga kallo ɗaya da sukai mata sukace ta koma cikin ɗaki kawai. Sun tattauna da Abba akan dolene asan mushurikin da yay mata wannan aiki. Cikin nuna rashin amincewa Abba yace shi babu ruwansa. Babu inda zaije neman wani akan aikin da bai aiketa yi ba. Babu irin lallashin da ba'ai masa ba yace babu gudu babu ja da baya. Da ga ƙarshe dole ƴaƴanta ne suka nufi wajen Hajiya Naqiba da ke gida, dan asibiti sun sallamesu kamar yanda suka buƙata akaje akai mata ɗorin gida. Sun sami Hajiya Naqiba a yanayin daya tada musu hankali, dan ƙafarta tai wani irin mahaukacin kumburin da har tafi gangar jikinta girma. Kuka take sosai da ihu na azabar zogi da raɗaɗin da ƙafar kemata. An kira mai ɗori ya tabbatar musu ta sake gocewa, ma'ana dai ɗori baiyi ba. Ya kuma tabbatar musu da shi gaskiya bai san yaya zai yi ba, sai dai su nema wani kuma ya gwada sa'arsa. Daga haka yay tafiyarsa ma shikam. To shine fa ƴaƴan Umma suka samu ana shawarar neman wani mai ɗorin dan an tabbatar musu na gargajiyar dai yafi kar su maidata asibiti. Ga mijinta ya nuna kamar ma abin bai damesa ba duk da irin kiran sunansa da take famanyi shi da ɗanta Maheer. Shi Maheer ɗin da farko ya zauna, da ga baya yay ficewarsa acewarsa shi gaskiya ihun da take ya ishesa, yana fita suka haɗe da abokansa sukai tafiyarsu wajen ƙwalewarsu da kayan shaye-shaye. Dole yaran Umma suka dawo gida jiki a sanyaye. Sun sake iske tashin hankali Umma dake wani irin nishi a ɗaki amma kowa ya kasa shiga ya dubata, Ammah ce ma ta nuna zatai ƙarfin hali Abba ya tabbatar mata idan ta shiga sai ya ɓata mata rai, dole ta kama kanta cikin damuwa. Suma ɗin dai babu wanda yay yinƙurin shigar saboda tsoro....
     Har yamma babu wanda yasan halin da Ummah ke ciki, sai yayanta Jibirin ne ma yay ƙarfin halin bada shawarar a sake kiran malaman nan koda taimakon da zasu musu. Kowa ya bada goyon bayan hakan. Dan haka akai kiransu. Babu jimawa suka iso kasancewar akwai sanayayya tsakaninsu da Jibirin ɗin. Addu'oi sukayi da ƙarfin halin cusa kai a ɗakin, sai gasu suna rige-rigen dawowa a guje. Har yaran gidan dake tsakar gida na tayasu da afkawa ɗakunan iyayensu. Sun tabbatar da gaskiya bazasu iya ba, wannan mummunar halitta ganinta ai tashin hankaline ma. Sun tabbatar da shawararsu kawai ya kamata a bi aje a nemo mutumin da yay musu wannan aiki zaifi sauƙi fa. Wannan al'amari ya sake tayarma da kowa hankali. Dole ƴan uwanta suka tattaru neman mafita su da ƴaƴanta. Dan Abba dai da gaske ya juya musu baya.....

     ________★

  Al'amari kamar wasa Dada sai da ta kwanta asibiti na kwana biyu, randa aka sallamonta ta samu surukanta cike da gida sunata harkokin arziƙi akan zaman bakwai. Wannan abu ya sake dugunzuma mata zuciya. Baba Garko ya shigo dubata da daddare ta sanya masa kuka. Kallonta kawai ya tsaya yanayi, bawai baya jin tausayinta bane, ba kuma baya sonta bane. Ya riga ya ɗaura ɗammarar horatane kawai. Dan ko auren nan nashi yayisa ne da gayya danya ƙona mata rai tunda yasan babu abinda ta tsana a duniya irin kishiya. Kuma ya samu nasara. A yanzun ma cikin ɓacin rai yaja tsaki da faɗin, “Ni al'amarinki kam ya fara bani tsoro Hajara. Shin wai baƙin ciki kike da ƙaruwar dana samu ko yayane? An faɗa miki haihuwa kin yanke jiki kin faɗi sumammiya, yanzu kin sakani a gaba kina kuka. Kin ganni nan ni bana son damuwa ina cikin farin ciki a ɓata min shi. Idan kinga zaki sakama ranki dangana ki saka, idan kuma kinga wannan halin da kike neman jefa kanki ne abin burgewa sai ki cigaba. Dan bakin alƙalami dai ya rigada ya bushe. Takardu sun jima da rubutuwa babu wata cleaner ɗin gogesu. In sha ALLAHU nan da wata shekarar ma wasu biyun zata sake zubomin a gidan nan, sai ki shirya sake suma. Na barki lafiya”. Da ga haka yay ficewarsa. Sama da ƙasa numfashin Dada ya ringayi, jininta yay masifar hawan da har idanunta na koma mata dishi-dishi, ALLAH ne ya taimaketa Uncle Muneer ya shigo ya sameta a lokacin, da tabbas zuciyarta zata iya bugawa komai ma ya faru....

      (To Baba Garko ALLAH ya raya ƴan biyu. Koda yake kace nanda baɗi ma wasu kake so. Kaga tsoho da rigima🥱😂😂🤣🚴🚴)

      *_★UK★_*

  Alhmdllh a ɓangaren ango da amarya komai na tafiya dai-dai. Basu da wata damuwa sai cilin ɗinsu sukeyi. Duk abinda kuma ke faruwa a 9ja a cikin kunnensu yake. Dan suna samun information sosai ta hanyar Ahmad da su Daddy da suka koma gida. A yanzu haka tarko na biyu suke shirin ɗanawa. Dan sun gama shirya komai tsaff lokaci kawai suke jira.
         Soyayya suke zubama juna mai tsayawa a rai da zuciya harma da gaɓɓan jiki. Duk da Lulu na dojewa da ɓoye nata sirrin har yanzu ta gagara furtawa a baki sai dai Smart ya gani a aikace. Dan zuwa yanzu kam karatun malamin nata tsaff ta haddacesa tama koma ruɗa masa tunani da salo-salonsa. A ranakun da yake da wasa koda ba'a cikin London bane bata iya zama, binsa take su tafi ga ɗan yaronsu da kowa ya gani sai ya tanka. Dan haka Smart ya dage da tofe abinsa da addu'a itama yana cemata tai masa saboda baki.
     Lulu aja rigima bayan ta kira Baba Garko sun masa barka ita da Smart, ta kuma kira maijego da zuwa yanzu sun ƙulle sun zama ƙawaye dan kawai ta turama Dada haushi. Waya ta ɗaga tai kiran Dada. Bayan su. Gaisa Dada na zaton Lulun ta sakko ne daga fushin da take da ita

Please Login or Register in order to submit comment