Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 2
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels KARSHEN MADIGO ( Part 1 ) .. .. Vio Sani Hamza Funtua .. .. Ofishin Dakta Sa’ad ya dau shirun dole tamkar ba mutane a cikin shi, idan da ace za’a ajiye zomo a cikin ofishin bana tunanin zai iya jiyo sautin numfashin mutane biyun dake a ciki. Wasu lokuta, shiru zaifi yawan surutu koda maganar nada ma’ana, amma a wannan lokacin, kunnuwan RUMASA’U a tsunke suke da son jin sakamakon awon da akayi mata. “Dakta Sa’ad, bana jin zan iya jure kallon ka ba tare da kana magana ba. tsawan shekaru ashirin ke nan rabon da Namiji ya burge ni bare na dau mintuna uku ina kallon shi. Zan so ka sanar dani sakamakon awon da kayi min”—Rumasa’u ta fad’a bayan gajiya da tayi akan shirun dakta Sa’ad. Dakta Sa’ad ya gyara zaman gilashin dake a kan karan hancin shi. Duk macen da take zaune a wannan ofishin kuma taji kalaman da Rumasa’u tace akan daktan lallai ba abinda zai hana ta wanke Rumasa’u da mari. Duk inda Namiji yakai a koluluwar had’a sinadaren da mace zata so namiji to Dakta Sa’ad ya had’a su. Daktan ya kara kallon takardar dake hannun shi tare da sake maimaita karanta abinda ke ciki—kusan a karo na hudu. Ya yi gyaran murya mai kamar tari wanda yasa shi bude robar ruwan Swan ya sha. “Kiyi hakuri Rumasa’u, lokuta da dama likitoci kan kasa fitowa kai tsaye su fadiwa mara lafiya cutar dake damun shi musamman idan cutar tayi tsauri sosai, ba komai ke san hakan ba sai don gudun kada su jefa kansu a halin da yafi na cutar illatarwa.” “Dakta tsaya kaji”—Rumasa’u ta dakatar da daktan don sam ita ba wannan bane a gabanta. Ta ci gaba da cewa, “Kana tsoron ko bayan ka fadi min zan ruga a guje in bude tagar ofishin ka in fad’a kasa? Duk da nasan ofishin naka nada tsawan hawa uku? Ko kuwa zan koma gida in sha guba ko in harbe kaina da bindiga? Ko kuma in tsaya a tsakiyar titi mota tazo tabi ta kaina?” Rumasa’u ta d’an tsahirta kamar tana jiran likitan ya bata amsa, sai dai koda ya ce zai bata amsa bazama ta tsaya sauraron shi har sai ta dire da zancen ta, wannan tsayarwa ma tana son hutawa ne. “Ni ba yarinya bace ba a yanzu, shekaru goma sha biyar da suka wuce idan ka yi min irin wannan maganar shine zan yi shiru inbi abinda kake so. Lokacin ko wace mace tana da ikon Mallaka a kaina. Likita kasan kuwa mata nawa suka rasa rayukan su a wannan lokacin?” Daktan Sa’ad ya girgiza kai alamar a’a, Rumasa’u ta ci gaba da cewa, “Idan ban manta ba, mata uku ne suka rasa ransu, kawai a kokarin su na ganin sun mallake ni. Dan haka Dakta, kai tsaye nike so ka sanar dani sakamakon awon da kai min” Dakta sa’ad ya jinjina takardar da sakamakon ke ciki, ya mikawa Rumasa’u, ta karba tana nazarin rubutun dake a ciki. Zuwa wani dan lokaci ta d’ago kai cikin sanyin jiki ta kalli daktan. “Ni ba likita bace, abubuwan dana gane a ciki kadan ne wad’an da koda na hada su basu banin wata ma’ana ba, ko zaka iya fassara min abinda ake nufi? “Rumasa’u. a yanzu haka kina d’auke da cutar STDs kamar HIV wanda kinsan babu wani tabbataccen magani na warkewa din-din-din. Sannan kina da cutar BMI a hausance cutar nauyin jiki wanda illar cutar zata bayyana nan da wani karamin lokaci. Haka zalika, sakamakon awon ya nuna kina dauke da cutar sankarar mahaifa da ciwon daji, ma’ana Cancer. Sai dai babbar matsalar shine, kwakwalwarki ta fara tabuwa sakamakon Mad’igon da kika dau shekaru kina yi.” Dakta Sa’ad yayi shiru ba tare da ya kara cewa komai ba, ya sunkuyar da kanshi kasa, hawayen takaici da tausayin Rumasa’u suka gangaro mashi. Cikin murya mai rawa-rawa Rumasa’u ta ce da shi “Dakta kukan me kake yi?” A hankali ya d’aga kai ya kalle ta, “Dole nai maki kuka Rumasa’u, ina takaicin yadda mace yar shekaru ashirin da biyar kamar ki rayuwarta zata kare a haka” Rumasa’u tai murmushi, “Dakta ke nan, na sosu kwarai da jin irin cutukan da nike dauke da su, wanda duka na same su ne a sanadin rayuwar da nayi a baya. Na kuma gode kwarai dakta.” Ta mike tsaye da alamar zata tafi, dakta Sa’ad ya mike shima bayan ya share hawayen dake a fuskar shi. “Duk lokacin da kike bukatar wani taimako, kada ki manta, ina nan zan kuma taimaka maki.” Rumasa’u ta kara yin murmushi a karo na biyu, “Na gode dakta, bazan kuma taba mancewa da irin taimakon da kai min ba. Inaga ya kamata ka huta hakanan, dan ba lallai bane ba ka sake gani na.” “Me yasa?” Har Rumasa’u ta juya, kamar ta tuno da wani abu kuma sai ta dawo, ta nemi waje a kusa da likitan ta zauna, ta ciro Bindiga kirar “AK47” daga cikin jakarta. Dakta Sa’ad na ganin bindiga a hannun ta hankalin shi ya tashi, ya ja baya nesa da ita, yana tambayarta, “Rumasa’u ina kika samo bindiga? Ki mayar da ita cikin jakar ki, meke damun ki?” A karo na uku Rumasa’u tai murmushi, ta mike tsaye tana kallon dakta Sa’ad, ta sake sanya hannu a cikin jakar ta ta ciro wani karfe da ake kira “Silencer” da turanci wanda ake sawa a karshen bindiga don kada tai kara idan an harbata. Ta sanya ma bindigar, cikin yanayin rashin tausayi ta saita Dakta Sa’ad. Hankalin Dakta sa’ad ya dugunzuma, ya fad’i kasa yana tuba da rokon Rumasa’u kada ta harbe shi. “Rumasa’u me kike nufin yi? Kada ki manta na taimake ki a rayuwar ki, ina kallonki a matsayin ‘yata. Dukkan abubuwan da suka faru a baya wallahi ba nufina bane, biya na ake, wanda idan banyi ba kashe ni zasu yi.” “Shi yasa yanzu zan kaika inda babu wanda zai saka har kayi, inda babu wanda zai kara kashe ka. Lokacin ka ya kare Dakta, zan fara kawo KARSHEN MADIGO ta kanka.” Dakta Sa’ad na magiya Rumasa’u ta danna kunamar bindigar, harsashi ya fita ba tare da yin kara ba ya sauka a kan Dakta, take kwakwalwar shi tai fitar burgu daga saman kanshi tare da harsashin suka tsaya cak a jikin bango. Jini ya bata kan teburin da kujeru. Rumasa’u ta mayar da bindigar ta a cikin jaka, ta fita daga ofishin.KARSHEN MADIGO ( Part 2 ) .. .. .. Sadaukarwa ga Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya... .. © Sani Hamza Funtua .. INDA AKA TSAYA:- Dakta Sa’ad na magiya Rumasa’u ta danna kunamar bindigar, harsashi ya fita ba tare da yin kara ba ya sauka a kan Dakta, take kwakwalwar shi tai fitar burgu daga saman kanshi tare da harsashin suka tsaya cak a jikin bango. Jini ya bata kan teburin da kujeru. Rumasa’u ta mayar da bindigar ta a cikin jaka, ta fita daga ofishin. . CI GABA Cikin nutsuwa taci gaba da tafiya bayan ta fito daga ofishin, har ta fita daga cikin asibitin babu wani wanda ya maida hankalin shi akan ta kowa na harkokin gaban shi. Kai tsaye ta isa harabar inda ake ajiye motoci ta shiga motar ta kirar Highlander. “Na fi son na rinka shiga motar da zan rinka ganin tsakiyar rufin sauran motoci, yadda nike a haka, so nike kullum in ganni a gidan sama mai badawa ba wanda ke mika hannu ba”—Rumasa’u take fadin haka wata rana da suke hira ita da kawarta Zainab. Tunda Rumasa’u ta tashi bata da wata kawa data wuce Zainab, tare sukai wasan kasa har zuwa girman su. Iyayen Zainab sun rasu a had’arin mota wanda hakan yasa mahaifin Rumasa’u Alhaji Baffajo rike Zainab a gidan shi tamkar yar da ya haifa. Mahaifiyar Rumasa’u ta rasu lokacin Rumasa’u nada shekaru Goma sha biyar—wannan ma labari ne mai zuwa nan gaba. A hankali take tafiya a kan titin da zai sadata da gidanta dake a unguwar G.R.A, babu alamar nadama a tare da ita akan kashe Dakta da tayi,. Sai dai hawaye da ke gangarowadaga idanuwan nata cikin kwanciyar hankali. “Ina da cutuka kusan hudu a jiki na, nan da wani karamin lokacin zai iya rasa rayuwata don duka cutukan da nike dauke dasu ba masu magani bane. Ya zama dole a gare ni na dau fansar watsar min rayuwa da akai, ba zan taba mutuwa ni kad’ai ba”. Hakan take sakawa a cikin zuciyar tata. Har ta isa gida tana zubar da wannan hawayen wanda bata san ko yaushe zasu tsaya ba, ta dai san cewa hannuwanta bazasu taimaka wajen tsayar da zubar su ba. A gaban katafaren gidan ta mai hawa biyu ta tsaya, tayi oda mai gadi ya bude kantamemen gate d’in. ta shigar da motar tare da ajiyeta a harabar da aka ware don ajiye motoci. Bayan ta kashe motar, ta kuma cire dukkan abubuwan da zata shiga cikin gida dasu. Ta fito ta rufe kofar motar kana ta yunkura don shiga cikin gida. “Yar Halak kinki ambato”, wata murya ta fad’a. Rumasa’u ta juya don ganin mai wannan muryar, har matar ta karasa inda Rumasa’u take Rumasa’un bata gane ta ba. Matar wacce zan iya cewa ta dau kira irin ta mawakiyar nan “Cellidion” wajen Shaf, kyau kuwa wannan ba’a magana don tsatson larabawa ce. Yanayin salon tafiyar ta kadai zai tabbatar maka da cewa wannan matar bata saba tafiya da kafafuwanta ba, adon tayi kuwa ya isa ya fad’i maka cewa lallai don ance maka itace d’iyar Ambasadan kasar United Emirate a Nigeria bazakai musu ba. Matar mai kimanin shekaru talatin da biyar ta tsaya gaban Rumasa’u, ta mika mata hannu, Rumasa’u ta mika nata hannun don suyi musabaha, sai dai Matar ba hakan take nufi ba, domin tana jin hannun Rumasa’u a cikin nata tayi saurin sunbatar hannun Rumasa’un. “Na fara yarda daga zancen mutane akan ki yake Rumasa’u” “Ko me mutane ke cewa akai na?” Rumasa’au ta tambaya ba tare da ta nuna alamar mamakin ganin matar ba duk da cewa wannan ne karo na farko da suka hadu. Matar tayi murmushi, har yanzu hannun Rumasa’u na a hannunta, ta murza hannun tare da jin laushin fatar ta, cikin yanayin annashuwa taja iska da siririn hancinta kamar mai son jin wani kamshi dake fitowa daga nesa, ta ajiye numfashin kana cikin lumshe idanu ta kalli Rumasa’u. “Baki sanni ba ko Rumasa’u” “Nasha haduwa da ire iren ki dama wadan da suka fiki, baki alamar hakan ba?” “Kwarai na gani, rashin nuna damuwarki na rashin sani na, ya tabbatar min da cewa zaki zamo masoyiya ta hakika” Ba tare da cewa komai ba, Rumasa’u ta juya tare da nufar cikin gidan, Matar ta bi bayan ta. Suka shiga cikin kantamemen gidan ba tare da shamaki ba. Duk inda ake neman cikar tsari na falo to wannan ya wuce shi, ba sai na tsaya kamanta yadda tsarin falon yake ba, amma ku dauka kamar yadda matar gwamna zata tsara falonta to haka wannan falon ma yake a tsare. Kai tsaye Rumasa’u ta wuce inda Friza take, ta bude ta ciro kalolin lemuka har guda biyu, a gefe guda kuma akwai gwandon kofuna, ta ciri guda biyu ta koma inda Matar take tsaye. Suka zauna a saman kujera d’aya, Rumasa’u ta zuba masu lemun suka sha cikin annashuwa. “Sunana Nurul Huda, ni ce babbar ‘ya a wajen Ambasadan kasar United Emirate a nan kasar taku.” “Ni kin san sunana, kinga basai na yi bayanin kaina ba” “Haka ne wannan, amma fa gaskiya kina da kyau” Rumasa’u ta kalli kanta ta jinjina kai tare da yarda da cewar tabbas tana da kyau, badan NurulHuda balarabiya bace da babu mahad’i a tsakanin su, duk abinda Nuru take dashi Rumasa’u ma nada shi. Bayan sun gama shan lemun, Nuru ta bude jakarta ta ciro bandir din kudi ‘yan dubu dubu har bandir goma, milyan d’aya ke nan. Ta ajiye a saman cinyar Rumasa’u. Rumasa’au ta dauki bandir d’aya ta rinka jujjuya shi. “Waya turo ki wajena?” “Manajar ki ce, Hajiya Babba” Rumasa’u ta jinjina kai. “Kema fa kina da kyau Nuru, babu macen da zata kalleki bata lashe baki ba, dubi zubin kirjinki, na dad’e banga mace irin ki ba” Nuru ta d’an yi murmushi tare da jin dadin wannan wasawar da akai mata, hakan ya bata kwarin guiwar kara matsawa daf da Rumasa’u, ta rike hannuwanta tana wasa da yatsun ta. “Kina da laushin fata, ga yatsunki abin kauna. Babu wata rana da zanyi farin cikinta irin wannan, wannan ne karo na farko da zan fara wannan harkar” Rumasa’u ta nuna alamar mamakinta a fili, ta kara da tambaya, “Da gaske kike Nuru?” “Wallahi kau” “Amma mace kamar ki, me yasa kika zabi wannan harkar?” “Kawai na Tsani Maza” Rumasa’u ta jinjina kai, kashi hamsin daga matan dake Mad’igo kusan amsar su ke nan “Na tsani Maza”, babu wacce zata tsani namiji face sai wacce sha’awarta ta karkata ga yar uwarta mace. A cikin Zuciyar Rumasa’u tace “Yau kuma zaki tsani Mata” Kamar yadda saurayi da budurwa yan nanaye, ko miji da mata suke fara tadowa junan su sha’awa, haka ta kasance a tsakanin Rumasa’u da Nuru. Sun dau lokaci a cikin falon suna shafar junan su da yiwa juna “Kiss”, shaukin hakan ne yasa Nuru ta fara fita daga hayyacin ta, ganin hakan yasa Rumnasa’u ta d’aga Nuru cif kamar ta dauki bebi ta wuce da ita cikin uwar d’aki. A wannan yammacin sun farantawa junan su rai. Misalin karfe biyar suka kimtsa tare da yin wanka da canja kaya, a tare suka shiga cikin kitchen suka had’a abinda zasu ci, suka koma kan dinning, kowa na ba dayan a baki. Soyayya ta rana d’aya ta kullu a tsakanin su. Anyi yarjejeniya akan cewa Nuru zata kwana Uku ne a wannan gidan akan farashin Milyan d’aya. A kaf cikin sashen kasar da muke, babu wata mace wacce take da babbar nasaba da sura irin Rumasa’u, hakan yasa tafi kowace mace tsada a harkar. Mata daga kasashen waje, wasu larabawa, wasu turawa, wasu indiyawa wasu yan cana, duk sukan shigo kasar don dai su yi soyayya da Rumasa’u. Hakan ya biyo bayan sihiri da kafin da Hajiya Babba, manajar Rumasa’un tai mata, duk macen data had’a idanu da Rumasa’u to ko nawa Rumasa’un ta tambayar ba jayayya zata biya. Misalin karfe tara na dare, soyayya ta kara tashi a tsakanin Rumasa’u da Nuru, bayan sun dau kusan awa d’aya suna abu daya, Rumasa’u ta gaji, ta sauka daga saman gadon ta shiga toilet tayi wanka. Bayan ta gama ta tsaya gaban madubin dake a cikin kewayen ta kalli kanta da irin kirar da take da shi. Cikin nutsuwa ta karasa gaban madubu, ta sa hannu daga sama ta ja madubin a gaban ta, madubin ya baro da jikin bango, wanda ya bada wata yar karamar kofa, Rumasa’u ta sa hannun ta a cikin kofar ta ciro wata bindigar daban da wacce ta kashe Dakta Sa’ad da ita. Ta maida madubin ta jingina shi da bango kamar babu yadda za’ai ya rabu da bangon. Ta sanya doguwar riga kana ta fita daga kewayen. Zaune a saman gado ta iske Nuru, Nuru tayi saurin mikewa tsaye ganin bindiga a hannun Rumasa’u, ta fara yin rawar jiki tana ja da baya har ta kai karshen bango. “Rumasa’u me nene hakan? Ya na ganki rike da bindiga? Ko kudin dana baki sun maki kadan ne? Just Tell me how much you want” “Bana bukatar kudin ki Nuru, wad’an nan ma da kika bani sun ishe ni, ina so ne kawai na hutar dake daga bayar da kudin ki. Sannan tunda wannan ne karo ne na farko da kika fara, nan gaba bazaki yi da kowa ba, ko ba komai, zan hana faruwar shigar wasu wannan harkar ta sanadin ki.” “Rumasa’u don Allah kiyi hakuri, kada ki kashe ni, ina da abubuwan da nike so inyi da rayuwata” “Nima haka Nuru, ina da buri da yawa, sai dai nan da yan kwanki ko shekaru zan mutu. Kinga in dai na rage irinku a duniya na ci riba. Sai mun had’u a kiyama” Tana rufe bakinta ta danna kunamar bindigar, karar bidigar ya amsa amo a cikin d’akin. Take Nuru ta zube kasa matatta. Rumasa’u ta dauki wayar ta dake kan gado ta lalubo wata lamba. “Ma’aikaci. Ga aiki na samar maka, kazo gidana, amma kuzo da salataf mai yawa, sannan ko alamar jini bana son gani. Zan ajiye maku kudi a saman gado, in kun gama sai ka kira ni.” Ta maida wayar ta aje, ta bude durowar kayanta ta ciro kaya kala biyar ta sanya a cikin karamar jakar tafiya, ta ajiye masu Ma’aikaci dubu dari uku, ta saka sauran dari bakwan a cikin jakar ta fita daga dakin.KARSHEN MADIGO KASHI NA UKU Sadaukarwa ga Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya... © Sani Hamza Funtua INDA AKA TSAYA Ta maida wayar ta aje, ta bude durowar kayanta ta ciro kaya kala biyar ta sanya a cikin karamar jakar tafiya, ta ajiye masu Ma’aikaci dubu dari uku, ta saka sauran dari bakwan a cikin jakar ta fita daga dakin. CI GABA... Wani yanayi da Rumasa’u ke shi kullum shine nutsuwa, ko da ace gwamna ne ta kashe bazaka taba ganin alamar damuwa ko tsoro a tare da ita, sai ma dai yanayin fara’a da takewa fuskarta ado dashi. Bayan ta fito daga cikin gidan ta karasa inda motarta take, ta shiga mai gadi ya tashi da saurin shi ya bude mata “gate”, ta tsaya kusa da mai gadin ta sauke gilashin kofar da take. “Ranki ya dade har zaki fita ne?” mai gadin ya tambaya cikin girmamawa da alamar wasa. Rumasa’u tai murmushi kana ta amsa mashi da cewa, “Zan fita Baban Hafsat. Ina su Hafsat d’in suke ne? Tunda na shigo banji koda kukanta ba” Mai gadin ya nuna jin dadin shi yadda Rumasa’u ta dauko zancen iyalan shi. “Ai yau tana gidan kakarta, a can zata kwana” “Hafsa ko rigima.” “Sha’anin yara ke nan, Muna nan muna jira muga ‘ya’yanki wata rana” Wannan maganar ta soki kahon zuciyar Rumasa’u, ta kalli mai gadi ta jinjina kai kawai tana murmushi, amma tunani yayi awon gaba da ita a lokaci d’aya. Bayan ta nisa ta sake kallon mai gadin cikin nutsuwa. “Baban Hafsa kana ganin ina da sauran lokacin da zanyi aure har in haifi ‘ya’ya?” “kwarai ma kuwa Ranki ya dade, ai tunda nike a rayuwa ban taba ganin mace mai farin jini da son mutane kamar ki ba. Yanayin yadda naga mata na zarya, matan ma masu kud’i, wasu jinin sarauta, wasu attajirai, wasu ma daga kasashen waje suke zuwa wajen ki. Hajiya ai rayuwarki sai dai muce Allah yasa kifi haka.” Rumasa’u ta girgiza kai kawai, ta tsahirta kana ta ce, “Kasan abinda ke kawo su wajena kuwa?” Mai gadi yad’an dau karamin lokaci yana so ya gano amsar wannan tambayar, ganin kada ya bata lokaci yaja hirar ta katse yayi saurin cewa, “Hajiya, ai a nawa tunanin, kina d’aya daga cikin manyan mutane a kasar nan, duk da ban san a ko wane fanni bane amma nasan ke oga ce. Kina kuma kula da marasa karfi da marayu, dole ne a rinka zuwa daga kasashe wajen bada tallafi...” Rumasa’u ta katse shi da cewa, “Ba haka bane ba, Ni matar Mata ce” Mai gadi ya d’an nuna alamar rashin fahimtar wannan maganar ta Rumasa’u. itama ta lura da wannan yanayin, hakan yasa bata bari ya ce wani abu ba ta ci gaba da magana. “Kada ka damu, nan gaba kdan zaka fahimci abinda nike nufi. Baban Hafsa, akwai Motar da wannan matar tazo da ita d’azu, ka canja lamba da kuma fenti, ga makullinta na mallaka maka ita.” Ta mikawa Mai gadi makullin motar ya sa hannu ya karba, ya durkusa har kasa yana godiya da Allah yashi albarka. Rumasa’u ta amsa da ‘Amin’ ta ja motarta ta fita daga cikin gidan. Mai gadi ya tsashi jiki na rawa ya kulle gate d’in. ya rinka jujjuya makullin motar, da gudun shi ya karasa inda motar take. Motar kirar Lexus ce mai ruwan toka. “Ban taba haduwa da macen dake da kirki kamar Rumasa’u ba, duk da cewa bazata girme ni ba, amma ko na girmeta baifi na bata shekara daya ko biyu ba. Tunda na fara yi mata aikin gadi, ban taba siyan abinci ko sutura ba daga ni har iyalina ita ke yi mana. Kai wani lokaci ma har yan uwana dake kauye sukan rika zuwa tana yi masu sha tara ta arziki. Allah ya kara nisan kwana dai uwar gijiyata”—mai gadi yaci gaba da jero addu’o’i tare da sawa Rumasa’u albarka. Karfe goma da rabi agogon motar Rumasa’u ya nuna, hankalinta na kan titin amma zuciyarta ta tafi tunanin abin yi a gaba, tunda ta baro gidan take tariyo maganganun mai gadi, musamman maganar shi akan suna nan suna jiran suga ‘yayanta. Tun da take a rayuwarta tsawan shekaru talatin a yanzu, sau daya bata taba zaunawa tai nazarin wai samun d’a ba. Kafin mace ta haihu saita sadu da namiji, ita kuma abinda bazata taba yi ba ke nan, ta tsani Maza. Karar shigowar waya ya karade cikin motar, hakan ne ya dawo da Rumasa’u cikin hayyacinta. Tayi mamakin jin karar wayar don ta manta da cewa ta taho da ita, wayar Nuru Huda ce. Rumasa’u ta duba fuskar wayar tare da karanta sunan mai kiran, “HAJIYA BABBA”— sunan mai kiran. Har wayar ta karaci kukanta bata amsa ba, a karo na biyu kiran ya kara shigowa nan ma har ya tsinke bata dauka ba. Bayan kamar minti daya sai karar alamar shigowar sako ya daki kunnuwan Rumasa’u. Da farko dai kamar bazata duba sakon ba, daga bisani ta dauki wayar tare da bude sakon. “Nuru ko dai har kun shiga duniyar kurame ne sai aiki da jiki? Ina son ganin ki yanzu don Ambasada ya kirani yace wai ya kiraki baki dauka ba.” Rumasa’u ta fita daga akwatin sakon, ta duba cikin lambobin da suka kira wayar amma ba’a dauka ba, sunan “My Dad” ya bayyana kasa dana Hajiya Babba. Da sauri Rumasa’u taja birki tare da sauka daga saman titin, ta danna kan lambar Ambasada ta tura mashi sako kamar haka. “Ka hanzarta zuwa gidan Hajiya Babba don d’aukar gawar ‘yarka.” Tana gama rubuta sakon ta rufe wayar tare da cillar da ita nesa da titin. Da sauri kuma ta dauki wayarta ta lalubo lambar Ma’aikaci, bayan wayar ta shiga ya dauka. “Ma’aikaci, ga canjin shawara. Har kun nad’eta da salataf ne? Ma’aikaci ya amsa mata da “Har mun gama yanzu muke shirin fita, an kuma tsaftace ko ina ba alamar koda takun sawaye” “To ku hanyarta warwareta. Sannan na baku mintuna ashirin kacal kusan yadda zakuyi ku saka gawar a cikin gidan Hajiya Babba, musamman a cikin boot din motar ta. Hakan zata yiyu?” “Kwarai ma kuwa Hajiya, ai ko bamu iyawa, aljanu zasu iya. Ki bamu mintuna goma kawai” Dan wannan ta kashe wayar, ta maida kallonta ga motocin dake zuwa da komawa, ta fara nazari akan rayuwarta kwatancin wadan nan motoci. Wata rana dole man dake jikinta zai kare, zata daina amfani. Kafin zuwan wannan ranar, sai ta tsayar da numfashin sama da mutum hamsin koma fiye, hakan ne kawai zai kwantar mata da hankali. “Dole in kasance a gidan Hajiya Babba, don kada zargi ya biyo baya, ba wai burina a kaita kotu da hukuncin daurin rai da rai ba. A’a, ina son Mutuwarta ta zamo a hannuna. Wannan ne kadai zai sa in shafe HAJIYA MAI DALA a doron kasa. Ko Hajiya Mai Dala tana ina yanzu? Koma dai tana ina, labarin kama Hajiya babba zaisa dole ta dawo kasar—don an kama Abokiyar hamayyarta.” An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta

Chapter 1 of 2