Downloaded From https://tknovels.com.ng [10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: *_INAYAH_* _(Riba Biyu)_ _Mamuhgee_ Document queen meenali 1 _*please masu daukamun Sunayen books da Labarai suna sauyawa suyi nasu lamarin ina ganinku dan Allah ku daina ba kyau, kuma masu copying nagani allah ya kyauta ngd duk cikin Qaunace allah yaqaro kauna🥰*_ _BismillahirRahmanirRaheem_ Tasowa tayi ahankali tana takowa zuwa tsakar gidansu datake jiyo maganar mahaifiyarta da yayyunta maza tareda kishiyar mahaifiyartata suna magana duk a jujjuye sbd hankalinsa daya tashi lokaci daya cikin mummanan yanayi da tashin hankalin mugun labarin dayazo musu yanzu yanzun. Ita kanta hankalinta baa kwance yakeba dama can sbd halinda take ciki na jinyar mijinta dake kwance asibiti Yana jinyar accident dasukai kwana biyu dasuka wuce a hanyarsa ta dawowa daga gurin daurin auren qaninsa dasuke uwa daya uba daya, Kaman a fizge kunnuwanta suka jiyo mata abinda babban yayanta Umar ke fada saidai Sam takasa fahimtar abinda yafada din zahirance Dan haka tana buqatan jinsa da kyau, Ta qaraso jikin kofar ta yaye labule ta fito tana kallonsu daya bayan daya fararen idanuwanta dasuka jima da shigewa ciki ciki sbd damuwar datake ciki kwanakin, Suma ita suke kallo Kaman yanda take binsu da kallo kowannensu fuskarsa cike dauke da alhini dakuma tausayinta Dan kuwa Rashin miji a irin shekarunta abin tausayi Ga Kuma 'da da ciki dake jikinta. Kallon mahaifiyarta tayi taga yanda tayi qasa da Kai cikin yanayi na hawayen dasuke Neman saukar mata takasa kallon Yar Tata Dan haka ta kalli kishiyar mahaifiyarta kai tsaye tace" Inna Menene duk kukai wani iri haka? Lafiya kuwa? Wani abin yakuma faruwa ne? Maida kallonta tayi kan yayyunta dake tsaye suna kallonta tace" Yaya Umar,Yaya kabiru? Lafiya duk kukai shiru haka? Jikin Abban Abdul ya tashi ne? Ajiyar zuciya Yaya kabirun ya sauke tareda gyara tsayuwarsa ya kalleta da Dan alhininsa irin na maza masu taurin zuciya Kai tsaye yace" Khadija bayan barowarki asibiti yanzu Allah yayiwa Salisu cikawa........ Bai qarasa ba ta waiwayo gefensa tana kallonsa cikeda zallan mamaki da faduwar gaba muryarta na gwamutsuwa tace" Yanzu fa na Barosa Yana barci, Wanka fa kawai zanyi nakoma asibitin shine zaace ya rasu???? Yanzu yanzu fa? Da sauri innar ta riqota cikin tausayawa tace" Hadiza karkiyiwa ubangijin haka, Tawakkali zakiyi tunda kinsan dai baa wasan mutuwa... Idonta na sauya zuwa ja da hawayen dake kokarin cikowa saidai taurin zuciyarta ya hanasu fitowa ta katse innar da cewa" Inna bacci nabarosa yanayi fa, Yaji sauki sosai yau, Rasuwa fa akace, Mutuwa fa kenan, ya tafi ba dawowa har abada, Ta Yaya zanyi....... Cikin Dan daga murya Yaya kabirun yace" Ke Khadija Menene hakan? Rasuwa fa akace Miki salisun yayi, Ki nutsu ki fahimci ita rasuwa babu ruwanta da yanzu yanzun dakike fada, Kiyi gaggawar bude hankalinki ki fahimci abinda yafaru dake, Salisu ya rasu bazai taba tashiba...... Bakinsa take kalla kanta na juyawa Zuciyarta na harbawa da mugun qarfi Kaman zata faso kirjinta, Mamarta ta kalla idanuwanta na qafewa taga alamar gskiyar zancensa akan fuskan mamar, Ta waiwaya ta kalli Yaya kabiru Shima hakan tagani. Wani busasshen yawu ta hadiye wanda har yankan maqoshinta yake Ta juya kai tsaye Takoma dakin mama ta dauki doguwar hijabinta data cire bayan shigowarta gidan ta zira ko waya da kudin adaidaita Bata daukaba ta fito ta zira slippers din mamarta daya Da nata takalmun daya batareda ta luraba ta nufi kofa tana jefa ka kawai dan bata cikin hayyacin kallon gaban nata asibitin take buqatan isa kawai. Inna ce tayi saurin janyo nata hijabin tabi bayanta tana Kiran sunanta, Mamarta kuwa kallon Yaya Umar tayi tana cewa" Bisu kabasu kudin adaidata ban Saka ran kowannensu ya daukaba. Juyawa yayi ya bisu A titi yayi saurin taddasu ya ciro 1000 ya miqawa Inna Yana cewa" Ga kudin adaidata Inna Ki lura da ita Inna kartaje asibiti tayita wainnan maganganun Tawakkali akeyi kifada mata Inna. Da sauri innar ta qarasa gurin hadizar daketa zuba sauri tana tafiya ta riqota ta riqe hannunta gam tana kokarin Kiran sunanta saiga adaidata gabansu ba Bata lokaci suka fada ciki innarce tafada masa asibitin da zasu Khadijan kuwa Banda rawa babu abinda qafafunta da hannuwanta keyi. Isarsu asibitin ko Gama tsayuwa baiyiba Khadija ta sauka tareda wucewa da sauri ta nufi hanyar Emergency ward da har lokacin Salisu anan yake., Tun daga nesa Yan uwan Salisu din maza da mata suka hangota tana tahowa a gigice ko ganin gabanta batayi Hankalinsu yakuma tashi da tsananin tausayinta dan haka da yawansu suka qara fashewa da sabon kukan Rashin Dan uwansu. Tana qarasowa da kallo tabisu daya baya daya taga yanda mahaifiyar salisun ke rusa kuka take taji Rabin jikinta na neman mutuwa ta qarasa dakin tashige da gudu ta nufi gadonsa da gawarsa kawai ta tadda a rufe da zanin gadon data zo masa dashi yau da safen. Tsawonsa ta kalla tareda hannuwansa da aka miqar, Kasa gasgatawa tayi Saida takai hannu ta yaye zanin tayi arba da kyakkawar fuskarsa ta asalin fulanin Yola.... Mummanan bugawa zuciyarta tayi ba tsammani idonta yarufe tana kokarin zubewa Inna tayi saurin tarota tana Kiran sunanta Amma Sam batajinta sai neman somewa takeyi. Da sauri hajiyarsu salisun ta qaraso tana cewa" Ku koma gida da ita karta shiga wani Mummanan halin ga juna biyu a jikinta. Qwacewa takeson yi Dan Bata tunanin zata bar gawar salisun ta tafi koina Amma batada qarfin motsawa bare magana Dan bakinta take ya manne Kaman an Saka mata glue. Tana kallon gawar mijinta Salisu aka jata aka fice da ita har waje aka kuma sakata napep tareda Inna da qanwar salisun suka nufi can gidan iyayen salisun. Suna isa ko tsakar gidan Bata qarasa shigaba ta yanke jiki ta fadi jini nabin qafafunta. Hankali tashe sukai kanta tareda ciccibarta zuwa dakin hajiyarsu salisun Inna na Kiran sunanta hankali tashe. Jini sosai take zubarwa Wanda ya tabbar musu da cikin zubewa ne yayi babu tantama Dan haka basuyi wani yunqurin maidata asibiti ba haka Inna da dattijuwar gidan qanwar mahaifinsu suka taimaka mata gurin ganin jinin yagama zuba ta Dan gyara. Kururuwar koke koken da gidan ya dauka ne ya tabbatar musu da isowar gawar Salisu gida Tana jin hakan ta rintse idonta cikin tsananin azaba sauran abin dake cikin nata ya qarasa zubowa sai alokacin wani irin gunjin kuka Mai tafe da radadin zuciya ya kufce mata. Inna dake kanta ta qara matsowa tana dafata cikin tausayawa jin irin girman kukan datake, Kuka takeyi sosai zuciyarta na radadin Rashin mijinta uban 'danta dakuma wannan cikin daya qwallafa ransa akansa, Ashe tareda cikin zasu bar duniya Rana daya shiyasa Allah ya saka masa tsananin kaunar cikin abokin tafiyarsa ne kenan. Bata damu da yanayin datake ciki ba Haka ta dafa ta miqe tsaye tareda qarasawa tsakiyar bayin dakin hajiyar ta wanke jikinta daqyar sbd tsananin rawar da hannuwanta da qafafunta keyi. Fitowa tayi Kai tsaye ta karba zanin da inna ke miqo mata ta daura wani irin tsananin jiri da ciwon mara Mai tsananin gaske Yana nukurkusarta Amma taqi yarda tazauna Kai tsaye ta fito tsakar gidan sanyeda hijabinta tanajin yanda tako ina gidan ke amsa amon kukan Yan uwan Salisu. Gawarsa dake shimfide a dakin da zaai masa wanka ta nufa ta zube gabansa tafara rero wani irin gunjin kuka tana Kiran sunansa. Duk yanda akaso janyeta kasawa akai sbd kuka takeyi sosai zuciyarta na tsananin qunar Rashin mijinta datake tsananin so da kauna yau gashi ya tafi yabarta cikin duniyar da kowa babu abinda yasani sai kansa, Ina zata da 'danta Abdul Wanda tasan babu Wanda zai daki kirji a cikin danginta Kona salisun ya tallafi rayuwarsu. Lokacinda za ai masa wanka da sirita aka samu aka janyeta daga dakin musamman da itama wani irin gagarumin zazzabi ya rufeta lokaci daya dakuma sabon jinin daya Kuma balle mata sai alokacinma kowa ya San da Bari tayi. Baa kaita asibiti ba a dakinta dake gidan aka kwantar da ita kasancewar a gidan suke zaune tareda iyayen salisun tunda dagasu har iyayen ba masu hali ban Dan hakan nema sukeda daki daya tal da Dan qaramin palo da bandaki acikin palon, Tana daki ana fama da ita har aka tafi da gawar makwancinsa, Iya fatu aka kirawo makociyarsu Mai karban haihuwa ita tazo ta duba hadizan ta tabbar musu da cikin yagama zubewa Nan aka shiga wani jimamin aka fara kulawa da hadizan. Sbd yanayin jikinta dakuma zaman gaisuwar da ake gidan yasa dole Inna ta zauna tareda ita tadawo da kwana gidan tunda maman hadizan bazatazo ta zauna ba. Sosai take fama da jinyar kanta bayan kwana biyu da rasuwar sbd takasa daina kukan mutuwar Salisu, Salisu mijine ma gari Kuma uba nagari hakama 'da na gari gun iyayensa. Cikin kwana biyu duk tabi ta yamutse da tsananin damuwa dakuma ciwo dake damunta na tsananin ciwon mara na barin datai. Angama zaman gaisuwar har anyi sati biyu babu wani Abu daya sauya daga gareta saima sabon ciwon damuwa daya kamata Sam takasa fita daga halin damuwar Rashin mijinta, Inna na tareda ita har lokacin Kuma dai ita zata zauna da itan har tsawon watannin dazata Gama takabarta kafin sukoma gida tare. Abdul Yana gurin mama dama tun tana zaman jinyar abbansa asibitin kafin rasuwar tasa Dan haka kullum a daki suke wuni daga ita sai Inna, Abincinta Wanda yake kicin dinsu tun Wanda salisun ya siya shi Inna ke dafa musu yana qarewa babu Wanda yakawo musu wani saidai aka ringa Basu daga cikin gidan Idan an dafa, Wanda ake basun baya wani isarsu itada innar dan haka so da yawa innar Idan taci na safe yafe mata na ranar take ita taci, Itakuma Idan anbasu na daren saitace ta koshi saita barwa innar taci. Tun daga Nan yanayin yafara kulle musu Da innar dai taga daga ita har hadizan sunfara dogayen wuyan yunwa Kamar Yan gudun hijira dole taje gida ta sanarwa mamar hadizan sukai shawara akaiwa Umar da kabiru magana akan su taimakawa hadizan da abinci shine suka Dan fara taimakawar duk bayan kwana biyu suna Bata dubu daddaya ko dari Biyar Biyar. Tun suna Bata tana samun na siyan abinci da Kamar su sabulun wanki hardai Suma ana Jan lokaci suka daina sbd Suma da nauyin nasu iyalan akansu dan haka suka koma Yar gidan jiya. Watan salisun uku da satittika da rasuwa gabaki daya rayuwarta ta juya mata upside down sbd hajiyarsa itama ta kanta takeyi Dan dama shine kawai Mai tausayi da tallafa mata acikin yayanta shiyasa itama bazata iya daukan nauyin hadizarba Dan haka kowa tasa ta fisshesa akeyi a gidan. Hadizar ta rame ta hargitse ta sauya kamanni sosai bayan dogon wuya da dogon hanci sai ido dasuka fito kaman me Neman allura a duhu haka Takoma dama ita Inna sun saba da talaucinsu Dan haka masifar quncin Rashin ba wani damunta tayiba Kaman dai yanda tausayin rayuwar hadizan tafi damunta sbd tasan wani sabon gararin ne zata tadda gida koda tagama zaman takabar sunkoma. Ta bangare daya tunda tayi barin cikinta lokacin rasuwar Salisu har yanzu takasa ganewa lafiyaarta sbd ciwon mararta yi yakeyi Yana tasan mata, Wani lokacin idan yatasar mata Kaman zata rasa ranta haka take fama dashi Amma Bata taba zuwa asibiti ba Dan babu hali, Ko innar dasuke tare Bata sanarwaba Dan karta daga mata hankali bayan daga ita har mamarta tada hankali kawai zasuyi basuda wata mafitar. Cikin wani irin tsanani da matsuwar Rashi da tarin damuwa tagama zaman takabarta suka fara Shirin tattarawarta komawarta gidansu. Hajiyar Salisu tayi sabon kukan mutuwarsa lokacinda hadizan zata tafi, Tanajin inama tanada halin cigaba da kulawa da matar salisunta da 'dansa data riqesu Amma batada Wannan halin, Ko Abdul dinma tana tsananin kaunarsa saidai bazata iya riqonsaba shiyasa batamayi maganar karbarsaba, Da mahaifinsu salisun Shima Yana raye tasan bazai taba barin hadiza da Abdul din su tafi ba. Ita kanta hadizan ta San cewa Rashin halin ne yasa hajiyar batai yunkurin cewa a bar mata abdul ba Dan tunda salisun ya rasu itama yanzu abincinta neman gagarta yake Gwara tabarwa hadizar 'danta tasan duk tsanani zata nema ta kula dashi. ##MAMUH# #ZAFAFABIYAR# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS 4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: *_INAYAH_* _Mamuhgee_ *_Arewabooks@Mamuhgee_* 2 Dawowarta gidansu dole dakin Inna ta tare tareda innar tunda babu wani extra daki dazata zauna a gidan bayan  nan, Duka duka dakuna biyu ne gidan sai bandaki dake tsakar gida, Daki daya na mama daya na innar, Ko acan dah da mahaifinsu na raye zagayen dakuna yake, Ita Kuma Idan Yana kwana dakin mama saita kwana a dakin Inna, Idan a dakin Inna zai kwana saita kwana a dakin mama Ahaka ta girma harya rasu itama akai mata aure. Dawowarta gida wata sabuwar rayuwar zullumin kullum tashiga acikinta, Daga Inna har mama babu Mai wata qwaqwarar sana'a, Mamace ke Saida lallen hausa Inna Kuma tana saida su kanwa da borkono To tundama ta tafi taya hadizan zaman takaba sana'ar ta tafi sbd jarin ba wani Mai yawa bane dakuma hardashi suka hada duk suka cinye a can gurin zaman tunda sun shiga tsanani, Dan haka sana'ar innace kawai yanzu take Dan taimakawa ta wani bangaren Amma kam suna cikin gararin yanayi sbd Suma dama can salisun ne yake dauke da nauyin nasu tunda nasu yayan basa taimakonsu kansu da matayensu da yayansu kawai suka sani. Ita Inna Bata taba haihuwaba shiyasa tun take riqon hadiza tun tana yarinya gashi Kuma hadizar ce kawai mace acikin yayan mama dukansu mazane su uku, Malam Nafi'u Wanda Allah yayi rasuwa watannin baya, Sai Kabiru da Umar dasu kuma ayanzu kownanensu yakeda mata daddaya da yara kusan Biyar biyar, Sai ita autarsu Khadija wadda Rashin tsayayyan manemi yasa batai auren wuriba sai data dan girma a gida sosai takai kusan shekara ashirin da takwas  kafin tasamu salisunta dasuke tsananin so da kaunar juna sukai aure ya dauke nauyin tallafawa su Inna daidai gwargwadonsa. Daga Yaya Umar har Yaya kabiru babu Wanda  ya dauke lalaurar kula dasu mama, Saidai idan an kwana biyu su samu Kamar dubu daddaya su Basu ko 500 Wanda sukam suke ganin kokarinsu a hakan suyita saka musu albarka duk da innar tasan basa kyautawa suna kallo Salisu ke ciyar dasu bayan Shima ba wani karfin yake dashiba kawai zuciyar alkhairi yafisu. Yya Kabiru koyarwa yakeyi a secondary school din gwamnati dake kusa da anguwar dayake da iyalinsa Kusan shekara goma kenan Yana aikin koyarwar Amma babu wani cigaba kullum Yana Nan a yanda yake. Yaya Umar kuwa sanaa kowacce yi yakeyi baida tsayayya guda daya Amma dai yafi yin ta dillancin harkar Saida filaye da gidaje Dan Yana samu sosai acikinta shiyasa yafi yya Kabiru rufin asiri, Qarshema dai fadawa yayi siyasa sbd uban gidansa dayasashi fitowa Dan samun kudin jam'iyyar da zasu fito ta karkashinta tunda sunsan dai ba ci zasuyiba Amma sunsan jam'iyyar zata Basu kudi sosai Dan haka gadan gadan yafada siyasa baji ba gani, Yaya kabiru daya fahimci akwai samu sosai a harkar take ya marawa Umar din Baya Dan Shima ya samma masa Idan ta 'bulle. Itakam hadiza ganin zaman baida wata mafita Ga Abdul ya isa sakawa makaranta tuni Sbd abbansa koda ya rasu yanada burin sakasa makaranta alokacin, Yanzu komai ya juye musu Kuma tanada burin bawa Abdul din ilimi Dan ya anfana rayuwarsa, Gasu Inna da mama kullum cikin dubaru ake Yau aci kwadon kwaki, Gobe aci kwadon qanzo, sai ankwana hudu ko Biyar Daqyar ake hada cinikin da zaai musu tuwon gari da miya. Dole hadiza ta tashi ta Saida katifarta da ita kadai ta dawo da ita sai tarkacen kayan kitchen ta kwashesu takai kasuwar Yan kayan hannu ta saida ta tattaro kan kudin taraba biyu ta siyo musu abinci da kayan abincin tadawo gida. Sana'ar kosan safe dakuma awarar Rana tafara da sauran kudin yafara juyuwa. Kasancewar ita Inna da sauran karfinta sai tana taya hadizar aikin sana'ar musamman awarar datafi wuyar sha'ani. Cikin ikon Allah lokaci qanqani saigashi sana'ar ta samu karbuwa sosai duk da farko taci tsananin wuyar wuta da Rashin jamaa masu siya tunda baa saniba, Babu ranarda Bata konewa shiyasa kusan koina tagama kokkonewa hannuwa da qafafu Har fuska ma wani lokacin idan Mai yayi watsi. Ba laifi yanzu basa neman komai a gurin kowa Wanda dai zasuci saidai Dan abinda baa rasaba. Inna ma tuni dole suke komai tare sbd aikin yanawa hadizan yawa ga koko dasuke hadawa dashi yanzu da safe, Da Rana ma yanzu ba awarar kawai sukeba harda dankalin hausa da wainar rogo. Dole dai yanzu innace take aikin kosai da kokon safe ita Kuma tana awarar da sauransu da Rana sbd dukkaninsu aikin yayi mutsu tsananin wuya musamman tunda aikin wuta ne, Mama ba cikakkiyar lafiyayyaceba shiyasa Basu taba barin ta shiga sana'ar ba, Tunda mahaifinsu ya rasu haka take yau lafiya gobe ciwo, Hawan jini da ciwon sugar ke tsananin damunta Dan haka lallabawa kawai takeyi tana rayuwar. Ahaka hadiza ta samu ta sanya Abdul a makarantar gwamnati yafara zuwa Kullum ita ke rakasa da qafa tadawo Idan antashi haka take komawa ta dawo dashi sbd akwai Dan nisa sosai. Hutun farko na makarantar tabi taqarasa hargitsewa sbd yanda kullum saita kaisa ta daukosa ga lattin fara sanaarta datakeyi Idan taje daukosa, Dole Inna ce take fara yimata kafin ta dawo daukosa ganin mutane sun fara janyewa ansamu wata Yar baqin cikin ta fara sana'ar a makwaftansu. Ganin Inna ma wahalar duniya tafara sakota gaba sbd ayyukan sun mata yawa ko baccin arziki bata samu sosai dole mama ta ringa karba tanayi sbd Suma su ringa samun sassaauci tunda Allah yasa yanzu da aikin suka dogara kacokam. Tsawon lokaci rayuwar tana yanda take garesu ba wani dogon sauyi saima ciwo daya kwantar da mama Dan haka suka sake zagewa da Sanaa ga Inna itama karfinta yayi qasa, Ga Abdul yanzu karatun nasa yafara nisa tunda Yana aji biyu yanzu. Ita kanta lafiyarta wani lokacin qaranci take mata sbd ciwon mararta har lokacin Yana taso mata akai akai gashi wani babban ikon Allah dayake kamata shine tunda tayi Bari lokacin rasuwar Salisu har yau Bata taba yin wani al'adar ba, Tayiwa Inna maganar innar tace mata wasu matan na hakan musamman Idan suntaba samun matsala ta Bari Dan haka ko jinin Al'adar zai koma ya ringa zuwa daidai sai tayi wani auren kilan. Da Wannan zancen ta tattara maganar Rashin zuwan Al'adar ta watsar tafara neman wata sana'ar sbd wannan din ta daina tafiya sosai sbd kusan anguwar ganin ana samu duk sun fara sana'ar shiyasa yanzu ba mutane sosai. Ganin wata sana'ar taki samuwane Duk Wanda tafara Bata karbuwa gashi jarin nata tafiya gurin hidimar gidan yasa dole tafara zuwa aiki wani gida acan GRA da mama Indo qanwar Inna ta Samar mata. Fara aikinta sai rayuwa kuwa ta sauya musu Dan yanzu da albashin suke komai. Bata wani jimaba da fara aikin saigashi hajiyar suka tattara suka bar qasar itada 'yayanta dole tadawo zaman gida ba wani aikin. Jin bazata iya zaman ba aikin komaiba yasa takuma zuwa tasamu mama inda dake shirye shiryen tafiya Lagos itama aikin Sanaa tace takuma samar mata wani aikin. "Babu wani gidan aiki Idan ba Lagos Zaki shirya ki bini ba kya ringa musu aike daga can kokuma abaki Aron kudi ki bar musu Idan munje can kya ringa biyana da kudin aikinki??" Haka mama indo ta sanar mata Dan haka batada wani sauran zabi bayan amincewarta sbd suna cikin tsananin halin nema gskia. Ko data sanar dasu Inna farko sunso hanawa Amma ganin yanda mama Indo tai musu bayanin aikine kawai a wani babban restaurant na masu kudi da aka bude Kuma sunada masauki Mai kyau da restaurant din suka tanadarwa ma'aikatansu a tsaftace cikin kwanciyar hankali. Hakan yasa suka amince tareda bawa mama Indon Amanar kula da hadizar duk da ba yarinya bace. Kudi sosai hadiza ta karba gurin mama Indo ta siyawa su mama abinci Mai Dan yawa tareda dinkawa Abdul uniforms har kala biyu da sabbin takarman zuwa makaranta da slippers harma da sababbin litattafai. Sauran kudin taje takuma siyo musu sabulan wanka da omon wanki dasu lalle da kanwar dazasu ringa saidawa daga zaune cikin gida ta damqawa Inna sauran kudaden a hannunta. Daga Yaya Umar har Yaya kabiru babu Wanda yayi yunqurin hanata tafiya sbd su yanzu siyasar gabansu ta ishesu shi Yaya kabiru harda tattara  aikinsa yayi ya ajiye sbd ganin sun fara samu ba laifi. _LAGOS_ Da farko tafara Shan wuyar rayuwar garin data aikin dasukeyi sbd wani sabon hotel ne da aka bude aka daukesu aikin Dan haka wainda basajin turanci bangaren restaurant aka ajesu gurin harkar abinci., Farko ganin baa bacci kwana akeyi aiki yasa tafarajin zuciyarta tayi sanyi da rayuwar, Amma ana Bata albashin farko taga irin yawan kudin sai kawai ta tattara kyuya da damuwar komai ta watsar ta zage da aiki gadan gadan. Kasancewarta mai tsananin kokarin aiki da Amana da ladabi yasa cikin wainda aka daukesu tare watansu biyu aka qara mata matsayi tareda dauketa daga kitchen aka maida bangaren tsafta, Ma'ana bangaren masu Kai abinci dakunan manyan Idan sunyi odar abinci Dan haka kusan yanzu hutawa takeyi sosai sai anyi odar abinci taje takai. Gidan dasuke cikin kudinsu na albashi ake Dan tsakura duk wata ana biyan haya Dan haka hankalinta ya kwanta sosai gashi ahakan duk wata take turawa su Inna Yan canji ta hanyar Mai pos din kusada gidan nasu data baro. Kwanciyar hankali da hutu da Kuma nutsuwar datake samu yasa tafara sauyawa sosai sbd abinci Mai kyau na hotel din sukeci, Nama da kayan Dadi kala kala haka suke ci dan haka tafara sauyawa sosai, Mama indo dai ita a bangaren abinci take har lokacin Kuma babu ranar sauyata daga gurin sbd yanda ta iya wata irin lallausan sakwara da Amala,Eba,semo duka dai kalolin swallow babu Wanda mama Indo Bata qwareba shiyasa saka barta agurin Kuma itama ahakan ba qananun kudi take samuba sbd yanda suke tsananin son aikinta. Hutu da nutsuwar da kwanciyar hankalin data samu tareda abinci mai kyau yasa tafara sauyawa jikinta yafara budewa da wata irin kiba, Hasken fatarta daya jima da dafewa saigashi yafara washewa Yana dawowa, Da farko tayi mamakin hakan Amma ganin rayuwar nutsuwar datake yasa Bata damuba saima Jin dadin hakan datai sbd tasan inshallah yanzu zata iya samun miji tayi aure tunda tayi kyan gani. Ba laifi cikin qanqanin lokaci tasan mutane dakuma Yan tsirarrakun areas da streets sbd tana fita Yar siyayyarta Yanzu har maganin gargajiya take siya daga nan ta aikawa mama da koyaushe take fama da jiki duk da ana cemata taji sauki din saidai yanayin muryar maman yasa ta fahimci suna fadane kawai Dan kwantar mata da hankali. Hakama Abdul tana Dan yimasa siyayya idan zatai Aiken ta aika musu. Tana gab da cike shekara a sabuwar rayuwarta ta Lagos ta fahimci wani babban alamari Mai tsananin ban tsoro da firgitarwa a tareda ita. Bata tabbatarba Dan haka ta saka lokacin zuwa wani qaramin asibiti dake kusada anguwar dasuke, Ana albashi da kwana biyu ta kwasa ta nufi asibiti a dubata sbd tabbas Idan tanaji Kuma tana fahimtar daidai motsin ciki takeji a cikinta Wanda girman daya fara yasa ta dauka kibar datayi ce Kuma hakan Wainda take taredasu suke fada tayi qiba tayi tumbi. To me take Shirin ji ne? Tsakanin kwanaki Biyar zuwa yanzu take Jin motsin sosai da juyi Wanda ta tabbarda cikin haihuwane kawai yake Wannan motsin. #MAMUH# #LOVE# #ROMANCE# #ZAFAFABIYAR#[10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: *_INAYAH_* _Mamuhgee_ *_Arewabooks@Mamuhgee_* 3 InnalillahiWainna ilayhirrajiun" Shine abinda zuciyarta tafada lokacinda take zaune cikin jerin layin ganin likita data buga sammakon zuwa. Gyara zamanta tayi a karo na Bata lissafi sbd gabaki daya takasa nutsuwa ta aje jikinta guri daya, A tsananin matse take datasan asalin Menene ajikinta, Shin wani ciwon ne yasameta? kokuwa wata lalurarce Wannan da batasan da itaba? Itadai a yanzu koma menene gata agaban dakin ganin likita Allah yasa taji abinda zuciyarta zata iya dauka sbd koma wane irin ciwone atareda ita Bata tunanin Mai saukine sbd girman motsin datake ji. Dago Kai tayi ta Dan bude manyan fararen idanuwanta dasukai jajir da tsantsar damuwa da fargabar fake gamutse cikin ranta da kanta Ta kalla inyamurar data fito daga ganin likitar wadda daga ita mutum biyune ya rage layin yazo kanta. Bin bayan wadda ta shiga tayi harta shige kafin ta dauke kanta tana sunkuyar da kanta gefe tareda rufe idanuwanta tana sake Jin motsin da akeyi acikin cikin nata. Haka ta muskuta tana cigaba da zaman jira zuciyarta na cigaba da cika ta koina da damuwa da fargabar abinda zaije yadawo har tsawon mintuna ashirin kafin aka kirata ta miqe tareda gyara zaman qaramar Jakarta dake rataye kafadarta ta nufi kofar dakin ganin likitan tashige tana kokarin samarwa kanta nutsuwa sbd tayiwa likita bayanin yanayinta a matse. Dr Adebayo A Aziz tagani rubuce a gaban farar Lab coat din dake jikinsa Ta qaraso ta zauna jiki a sanyaye sbd taso tasamu likita Mai Jin hausa koda Yar kadan ce sbd tasamu ya fahimci zancenta dakyau hakama itama ta fahimci abinda zai sanar da ita da kyau. Tanajin dan pidgin dinta data koya a zaman garin Lagos din saidai bazai isheta suyi magana da kyauba Dan haka sai kawai jikinta yakuma sanyi ta gyara zamanta ahankali tana dagowa ta kallesa lokacinda ya bude Baki Yana kallonta Kai tsaye yace" Yes, what's the problem madam? Dan rage kallonta akansa tayi cikin sanyin jiki ta bude Baki tana Kai hannu kan cikinta da yayi tauri cikin kwanakin ta nuna masa tana harhada turancin da qyar cikin gwamutsawa tace" Something is moving inside my here" ta qarasa fada tana nuna masa cikinta da hannuwanta biyu. Is moving very very much, But no pains, No fever, No anything only the movement inside here. Idanuwansa ya Dan zuba mata tareda sakin murmushin bayanin nata. Ya kalli cikin dakyau Yana cewa ta janye hannunta ya gani. You said no any pains or fever? Gyada Kai tayi tana kallon fuskarsa. Rubuce rubuce yayi cikin file dinta kafin ya aje ya miqe tsaye. Gadon dake dakin ya nuna mata Yana cewa tahau ta janye rigarta ya duba cikin. Ajiye Jakarta tayi gefe tareda moqewa ta nufi gadon tahau zuciyarta na cigaba da tsalle cikin rudani da fargaba. Tana janye rigarta tun kafin yakai hannunsa kan cikin idanuwansa suka tabbatar masa da cikine a jikinta Kuma tabbas inshallah zai Kai wata Biyar zuwa shida haka. Hannu yakai yafara Danna cikin da Dan qarfi Yana examining nata aikuwa saiga cikin Yana sake motsawa. Kallonta yayi Yana zare Safar hannunsa yace" Madam ciki wata nawa??? Kallonsa tayi da sauri tana kokarin Jan rigarta ta rufe cikin ta tashi zaune tana Kuma kallonsa Kaman Bata gama fahimtar abinda yafadaba tace" Eh?? Komawa yayi ya zauna gurin daya tashi Yana kallonta bayan itama tadawo ta zauna yace" Madma ciki naka wata nawa?? Girgiza Kai tayi tana kokarin Hana kanta shiga firgici sbd zancen nasa buga kirjinta yake. Ganin halinda take ciki take ya fahimci batasan da cikinba kokuma cikin Bata shirya daukarsaba kokuma ma batada tabbacin na waye acikin mazan datake taredasu dan haka rubuce rubucensa yayi yagama ya kalleta tareda miqa mata takarda yace" Madam you are pregnant, I mean kanada ciki zai Kai like 5mnth Take this kaje kayi scanning ka kawo. Wata takardar yakuma miqa mata yace" And this one,test ne go lab zasu dauka blood naka ayi test na ciki da shauransu, then you'll come back on Monday and bring the results to me. Hannuwanta dake tsananin rawa takai ta karba takardun tareda miqewa tsaye ta fice zuciyarta na wani irin azabar bugawa da nauyin gaske. Kasa barin asibitin tayi Kai tsaye ta nufi bangaren da ake scanning ta biya ta shiga akayo mata cikin mintuna qalilan saigata da result din ciki a hannu. Rufewa idanuwanta sukai da wani irin tsananin duhu, da daddafawa ta samu wata kujerar plastic dake hanyar fita asibitin ta securities ta zube zaune hannuwanta da qafafunta sosai suka dauki wata Mummanan rawa zuciyarta na qafewa da zallar tashin hankalin da Bata taba shigaba ko alokacin mutuwar Salisu. Takardar dake damqe hannunta ta Kuma dagowa ta kalla kafin takuma budewa hannuwanta na rawa tafara bin rubutun dake ciki daki daki da idanuwanta dake mata zallar yajin radadin Neman hawaye Amma Sam babu alamar zuwansu. Daya bayan daya take bin kalmomin tana karantawa da 'Dan ilimin bokon datake dashi na iya secondary. Hawaye ne taji suna ciko idanuwanta take data Gama duba takardar, Ko ba Dan ta karanta ba Wannan takardar da abinda ke cikinta ya tabbatar mata da zancen likitan sbd Zak irinta wannan bayanin ne na ciki ajikin takardar dasukai scanning tareda Salisu wancan lokacin cikin Abdul., Kenan da gaske ta tabbata cikine ajikinta? Tayaya? A Ina ya fito tunda tasani Kuma Allahn da yayita shine mafi sanin Bata taba aikata komaiba a duniya da wani da namijin bayan salisunta. Dama Ace shekarar data gabata ne da saitace cikintane da Salisu ya barta dashi Bai bare ba.... InnalillahiWainna ilayhirrajiun,, Ni hadiza wane irin Mummanan haline Wannan nashiga Wanda bansan meyake faruwaba. Sai alokacin tafashe da wani irin Mummanan kukan mawuyacin halin datake ciki Ga cikin sai sake motsawa yakeyi alamar Yana cikin cikakkiyar koshin lafiyarsa data sanyashi kwanci tsawon shekara biyu sai yanzu daya samu tashi. Kukan fitar hankali tayi tsawon lokacinda Bata saniba agurin har Saida taji idanuwanta da fuskarta sun kumbura kafin ta iya miqewa ta kama hanyar komawa gida. Isarta gida Bata Bari kowa ya gantaba ta shige daki ta aje Jakarta ta fito tayi alwala Takoma dakin sallah kawai tayi ta fara rokon Allah mafita tana hawaye Ahaka ta Gama ta miqe Takoma ta kwanta Bata Kuma fitowaba sai washer gari. Gurin aikima datazo nokewa kawai taketa faman yi tana kame kame sbd ganin Kamar kowa zai fahimci cikin jikinta Dan haka duk tabi tayita Jin kanta a muzance. Tana tashi aiki Bata koma gidaba Kai tsaye gurin wani gurin scanning din daban ta nufa takuma yi, Shima result daya tasamu na akwai ciki. Wani gurin takuma zuwa Shima duk daya, Haka tayita yawon guraren scanning ana Bata result daya Ta tattara tadawo gida hankalinta zuwa lokacin yagama barin jikinta, Tashin hankali da tsananin tsoro takeji yanzu sbd ta tabbata takuma shaidar kanta Idan har Wannan cikin na haihuwane bana aljanuba to wlh cikin Salisu ne ajikinta Wanda yabarta dashi tunda tasan Bata taba ko tunanin 'da namiji ba bayan rasuwar salisunta. A daren kwana tayi wani irin kuka da quncin zuciya mai nauyin gaske. Tayaya zata fuskanci duniya da ciki a jikinta? Cikin da bai tashi fitowa ya bayyana kansaba sai data baro gaban iyayenta tazo Lagos, To tace me akan cikin? Zaa yarda da itane? Cikin qanqanin lokaci damuwa da kunci  sukaiwa rayuwarta mugun baibayi, Sam tarasa walwala da kwanciyar hankali da nutsuwarta, Kullum cikin zullumi da tashin hankali take tashi takuma wuni acikinsa sbd ciki dai yanzu gadan gadan fitowa yakeyi Yana girma ahankali Kaman yanda kowanne lafiyayyan cikin keyi. Lokaci na Ja tadain shiga mutune Sam yanzu Takoma tamkar mujiya sbd yanda cikin yagama fitowa kowa ya ganta Kai tsaye zai shaida cikine a jikinta, Hankalin mama Indo yayi Mummanan tashi da girman mamakin ganin Wannan alamari, Tashin farko Bata yardaba da anata gulmar cikin Hadizar sai data tinkareta ta ganarwa idonta ta tabbatar musamman yanda hadizar takasa hada ido da ita sai hawayen baiqin ciki takeyi. Babu kalar diban albarka da Rashin mutuncin da mama Indo batai mata tareda gori da zagi kala kala karshe ma haka ta tara mata jamaa agabansu tai mata Mummanan wulaqanci har Wanda baima Gama sanin halinda take cikiba yasani, Take gurin aikin dama gidansu aka fara zundenta, Masu zaginta da masu tausayinta dama wainda suke ganin ba komai bane Dan tayi cikin, Haka aka ringa yi da ita tun tana daurewa zuciyarta harta fara gazawa sbd babu inda take Jin Dadi ko sassaunci alamarin duniya yataru yayi duhu, Babbar fargabarta da tashin hankalinta Kar mama inda ta sanarwa su mama da Inna halinda take ciki Dan haka duk tabi ta daga hankalinta wata sabuwar damuwar da tashin hankali yakuma shigarta. Ahankali Ahankali lokaci yakuma tafiya Amma a rayuwar hadiza kullum da'da zurfafa take cikin tashin hankali da damuwa da qunci take sbd rayuwa tayi mata tsanani sosai sbd ciki kam ya tsufa sosai kowanne lokaci zata iya haihuwa, Kullum adduarta Allah yasa ta Haifa abunda yake cikin yazo ba rai ta huta ta tattara Takoma gida sbd bazata iya zuwa gaban iyayenta da Wannan cikin ko abinda zata haifa barema yayyunta data San basuda imanin karbanta da abinda zataje dashi, barinma yanzu dasuke siyasa bazasu yarda da abinda zai taba qimarsu dasuke tunanin sunada ita a manyansu. Wani sabon tashin hankalin ta shiga Rana tsaka da gurin aikin suka sallameta bataredama sun jira watan yaqare anbata albashintaba. Lokacinda taringa roqar Manager tana basa hakurin yabarta zata iya aikinta koda cikin Amma ya rufe ido ya sallameta tareda Bata awanni akan ta tattara tabar gidan kamfani tunda gurin aikinne suke Basu gurin zaman Dan haka Kai tsaye gida Takoma bayan tagama ganin tonan asiri da tozarci iri iri daga gurin abokan aikinta da jamaar hotel din. Kuka zuwa Wannan lokacin ya 'dauke mata zuciyarta bayan radadi da tsananin qunci babu abinda take Mata Dan haka ta tattara kayanta da duka abubuwanta ta fito Kai tsaye ta nufi inda zata shiga motar dazata kaita tashar da zata siya ticket din motar komawa Adamawa. Tunda tashiga mota zuciyarta tai Mata nauyinda Bata ko iya kuka sbd dole dai Takoma gida ta fuskanci Wannan sabuwar qaddarar data zo Mata. Har motarsu tayi wuni guda a Tasha tana zaune guri daya sallah kawai ke tada ita har dare yayi suna tashar Basu tashiba sai tsakiyar dare motocinsu suka tashi aka dauki hanya. A hanya asuba tai musu,Rana tayi musu,yamma tayi sunata Dukan hanya har wani daren yakuma yi suka kwana ahanya sai ana gabanin asuba suka iso cikin garin Adamawa kowa ya sauka. Lokacin har anfara Kiran sallar asuba a masallatai da dama Dan haka dole da yawansu suka tsaya anan tashar sukai sallar asuba ciki harda ita sbd batasan abinda zata tadda a gidan ba gwara tayi sallar ta nema sassauci daga ubangiji dayake jarabtarta da Wannan rayuwar. Qarfe 5:24 mashin ya sauketa bakin kofar gidansu datai mamakin ganinsa bude lokacin ta sauka daga kan mashin din tana miqa masa kudin data fidda daga jaka tun a hanya sbd daga ta saka ya miqa masa ta shige gida batareda ta tsaya jamaar anguwa  sun gantaba. babu kowa tsit anguwar sbd garin da Bai Gama haske ba ta kinkimi qatuwar Jakarta da akwatinta harma da wasu ledojin ta nufi cikin gidan zuciyarta na tsananta bugu duk da tayi imanin da iyayenta bazasuyi Mata zargin Zina ba tunda sune suke tarbiyanceta Kuma sunsan halinta da abinda zata iya dama wanda bazata iyaba koda kuwa inda yafi Lagos taje. Ganin Sabon mashin fil a soron gidan yasata kallon kofar cikin gidan zuciyarta na neman karaya sbd fahimtar tabbas kodai Yaya kabiru kokuma Yaya Umar ne acikin gidan. Siririyar shaqurarriyar sallama ta saki lokacinda ta shigo tsakiyar gidan daukeda kayanta kamar sabuwar bokanyar datayo gudun hijira. ##MAMUH# #LOVE# #ROMANCE# ##INAYA A MAJEED ABBI# [10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: *_INAYAH_* _Mamuhgee_ *_Arewabooks@Mamuhgee_* 4 Inna ce dake kokarin fitowa bandaki riqeda mama ta amsa sallamar Kai tsaye batareda ta Gama tantance waye me sallamar sbd hankalinta gaba daya dake kan Mama data riqo wadda ko tsayuwa Bata iya yi Dan jikinta matuqar sosai yayi tsanani a kwanakin. Sai data fito tsakar gidan da kyau ta dago tana sake amsa sallamar da hadizar takuma tana kallon mahaifiyarta data sauya kamanni gabaki daya sbd tsanani da azabar ciwo. Hawayene suka ciko idanuwanta da sukai zurfin Rama da irin kukan rayuwar datake ciki ta dago qafafuwanta dasukai Mata sanyi da nauyi ta tunkarosu tana Dan kasa kallon cikin idanuwansu da suka zuba Mata dukkaninsu. Inna da qafafunta suka kusa sakewa sbd tsananin mamaki da faduwar gaba A 'dan rude muryarta na gwamutsuwa tace" Hadiza kece Wannan a tsaye??? Jin hakan yasa mama da Bata gane kowa sosai ta Dan sake riqe hannun innar tana bude idanuwanta ko zata sake ganinta da kyau Sai idanuwanta suka sauka kan tsohon cikin gaban hadizar Ta Dan motsa kadan tana bude Baki cikin sanyin ciwo tace" Lami? Kasa amsawa Inna tayi sbd idanuwanta data kasa daukewa kan tsohon cikin Hadizar. Lami? Wace hadizar Kika ambata? Hadizata ce tadawo? Itace Wannan a tsaye? wani busasshen yawu Inna ta hadiye tareda sake riqo mamar da kyau sbd hannuwanta dataji suna sanyi da daukar rawar tashin hankali mugun ganin datai safiyar fari. Dakyar ta qarasa da maman kofar dakinta tana kokarin kwantarwa kan shimfidar datai Mata a wajen Maman ta Dan janye tana waiwayowa ta kalli hadiza da har lokacin take tsaye a inda take cikin mutuwar jiki da qamewar zuciya. Hadiza? Hadiza kece agurin tsaye? Sai alokacin ta daqo qafafunta ta janyo jiki ta qaraso gaban mamar ta zube tareda fashewa da wani irin kuka dukkanin zuciyarta na Mata wani irin radadin qunci da damuwa da baqin ciki. Kukanta ya tabbatarwa da maman tabbas hadiza ce kuma cikine ajikinta ta samo ta dawo dashi. Cikin rawar murya ta firgici Inna tace" Hadiza cikine ajikinki? Ba musu ba Jan dogon yanayi ta dago jajayen idanuwanta ta kasa kallon innar ta bude Baki murya a shaqe tace" Eh. Hadiza Ina nufin ciki fa na haihuwa? Kuma amsawa tayi da "eh.. Hadiza daga Lagos fa kikaxo da Wannan cikin., Aure kikai acan bamu saniba? Girgiza kai tayi ahankali tareda cewa" Aa inna,Amma wallahi tallahi...... Zubewar innace da sautin salatin Yaya Umar Mai qarfine yasa maganarta yankewa hankali tashe ta dago tana kallonsa idanuwanta jajir. Inna gurin mama ta nufa tana Kiran sunanta, Aishatu? Aishatu? Aishatu Dan Allah karki kashe kanki sbd wannan mugun abun kunyar da hadiza tadauko, Innalillahi Aishatu Dan Allah karki tafi ki barni banida kowa, Malam ya tafi ya barmu ke kadai Kika rage karki tafi ki barni. Kuka Inna ta fashe dashi tana Kiran sunan inna data jima da somewa. Sabon tashin hankali hadiza tasamu kanta aciki Da sauri tayi kan maman itama tana kiran sunanta cikin mummunan mawuyacin hali sbd ita kanta tanaji batada lafiya. Wani Mummanan Marin Rashin Imani da baqin ciki Umar ya sauke Mata lokaci daya Yana kallonta a qazance ransa a matuqar bace yace" Karki kuskura ki tabata, Shekara kusan biyu kena bakya gida Bakizo musu da kudin dakikaje nemaba sai tsohon cikin banza¿ Gashinan Zaki kasheta lokaci daya da baqin ciki, Tashi na daina ganinki wlh kafin na illataki daga ke har abin banzan da kike dauke dashi. Yanda yayi maganar a tsananin fushi da bacin Rai har Yana sake yowa Kanta yasata Jan jiki tayi can gefe tana wani irin kukan zuci Mara sauti. Kwasar mamar sukayi sukai cikin daki da ita sai firfita Inna ke Mata tana kuka Wanda yake na firgici da tsoron halinda Aishatun zata shiga dakuma zallar baqin cikin al'amarin da hadizar take tafe dashi. Duk dubarunsu da ruwa dasuka ringa shafa Mata Bai saka ta farfafo saima qarasa rikicewa sosai da jikin yayi gabaki daya. Hankalinsu duka yatashi Dan haka dole Yaya Umar din ya fidda waya yakira Yaya kabiru, Shima rabon zaai gabansa ne yasashi zuwa gidan tunda asuba sbd ruwan da aka kwana ana zubawa yasashi tunanin gininsa da akeyi acikin gidan da baa kammalaba Wanda yasa ai masa daki daya da bandaki amarya yakeson yi to anan zai kawota ya gwamutsa cikinsu innar. Koda Yaya kabirun ya iso tuni innar tayi nisa Amma basuyi yunqurin kaita asibiti ba saima wani sabon tashin hankalin daya barke tsakaninsu sbd ganin hadiza ce silar koma meya samu mamar. Kabiru buga rantsuwa yayi akan wallahi saita bar gidan da cikin, Bazasu taba barinta ta zaunaba a gidan baqin cikin rainon ciki da goyon shege ya kashesu mama hakama bazasu yarda ta Bata musu sunan dasukai gwagwarmayar samarwa kansuba lokacinda take Lagos tana zubarda mutuncinta da qimartaba. Yaya Umar dinma bayan kabirun yabi akan Takoma inda tafito da cikin. Rokonsu takeyi tana wani irin kukan tausayi da tsananin quncin datake ciki akan su yarda da ita Bata taba aikata Zina ba Amma Sam babu Wanda ya saurareta saima qara harzuqa dasukeyi da tsananin fushi da bacin rai,Yaya Umar Dukan mutuwa yakeson yi Mata Amma Inna dake kuka sosai ta Hana ta riqesa tana bayyanarda nata fishin itama. Riqonsu tadawo yi akan su fito da mama akaita asibiti Nan ne Umar yabi takan qafafuwanta ynaa neman tattakawa a fusace yace" Uban waye Zaki fadawa akai mama asibiti? Lokacinda kike zubarda mutuncinki kinyi tunanin halinda zata shiga Idan taganki da wanna abun. Kukanta qafewa yayi alokacin sbd a yanzu mahaifiyarta kawai takeson yiwa bayanin gaskiyarta, Mahaifiyarta dake cikin mawuyacin hali takeson tabbatarwa Bata lalaceba Kaman ynada suke tunani. Gurin Inna ta rarrafa tana roqonta akan subarta taga mama Dan Allah., Wallahi tallahi Inna ban taba aikata abinda kuke tunaniba, Inna ku yarda Dani Dan Allah, Wlh Inna cikina kwanci yayi sai yanzu yatashi, Inna wlh cikin Salisu ne,Dan Allah inna ke ki yarda Dani.......kuka ta fashe dashi Mai tsananin ciwo tana sauke kanta sbd babu sassauci ko alamar yarda da ita atareda kowa. Tashin hankalin data samu kanta dawowarta bata dauka zata tadda hakanba. Duk wani sauki da rahama Bata samu daga yayyunta har innar ba qarshema haka ciwo ya tasar Mata Wanda tabbatar naqudace Amma tashin hankali yakasa barinta tanema guri ta nutsu ko haihuwarce zatazo. Irin wulaqanci da tozarcin da yayunta sukai Mata bazai taba barin tasamu sassaucin nauyin zuciyarta ba har abada, Sunkuma tabbatar Mata da wallahi bazata taba rainon cikinba a gidan bare haihuwarsa, Idanma ta haifesa koko zasusa abasa yasha ya mutu su sun huta itama ta huta da renon 'dan da babu uba hakama shi kansa Dan ya huta da girma a duniya yatashi cikin gori da wulaqanci. Masiface da tozarci Wanda ya haddasawa maqota sanin abinda tadawo dashi daga Lagos din suka ringa zuba Mata cikin fushi da bacin Rai, Da yawa wasu sunshigo da sunan duba Inna Dan su tabbatarwa da idonsu cikin shege tayo daga zuwa Lagos.... Bata taba kukan Rashin mahaifintaba da Rashin Salisu kamar ayau datai wunin tsananin baqin ciki da danasanin tafiyarta Lagos sbd da agaban iyayenta cikin ya farfado da babu Wanda zaiyi Mata Wannan yankan qaunar. Idanuwanta sunyi wani irin kumburi da Bata iya gani sosai. Daddafawa tayi bayan tasamu dare yayi su Yaya Umar sunbar gidan ta shigo dakin da mahaifiyarta take ta zube gabanta Daqyar sbd tsananin azabar naquda. Hawaye ne suka gangaro Mata takai hanunta dake rawa ahankali ta dafa na mahaifiyarta tareda rintse ido wasu hawayen na tsananta Mata gudu. Kuka takeson yi ganin yanda mahaifiyarta ke numfashi ahankali alamar samun sauki saidai bazata kukanba Dan naqudarta tagama zuwa kusa,ta gyara zamanta da qyar tana hada wani irin zufan gaske tako Ina jikinta azababbiyar azaba takeji Dan haka ta damqe hannun mahaifiyarta da qarfi tana sake wani irin gurnanin Nishi tana Kiran sunayen Allah a azabance. Inna na dakinta kwance zazzabi Mai tsananin gske ya kwantar da ita da wannan babbar masifar data kunno musu Kai Dan haka batasan meyake faruwa da hadizan ba. Naquda Mai tsananin wuya da azaba takeyi gadan gadan Tagama jiqewa sharkaf da zufa hakama mama tuni tafara bude idanuwanta cikin tsananin ciwo, Tanajin 'yarta na nakuda Kuma Mai wuya da azaba Amma babu abinda zata iya yimata hakama babu Wanda zai taimaka Mata... Hawaye da 'dacin tausayin 'yartane ya gangaro gefen idonta ta Dan motsa hanunta dana hadizan yake Kai ta kama hannun hadizar ahankali idanuwanta na zubowa da wasu hawayen masu zafin gaske. Hadiza taji mamar Amma bazata iya magana ba ko juyowa takalleta saima wani wahalllen Nishin datake fitarwa tana fidda Rai ga rayuwa,. Jin take da zata mutu agurin wannan naqudar data godewa Allah ta huta da Wannan rayuwar da babu komai acikinta sai qunci da damuwa. Wani qaqqarfan Nishi ne yafara zuwar Mata Idanuwanta sukai jajir gumin na sake jiqota tako Ina... Cikin dauriya da azaba tafara Addua sbd sanin adduar mace Mai naquda karbabbiyace inshallah. "Ya Allah kaine masanin gaskiyata nida abinda zan Haifa, Ya Allah ka albarki rayuwarsa ko rayuwarta Idan mace ce, Allah ka tallafi rayuwar abinda zan Haifa ka datar dashi kyakkawar rayuwar kwanciyar hankali da nutsuwa. Mahaifiyarta da 'danta Abdul take kokarin yiwa Addua Amma Ina mamar kawai tasamu damar rokarwa Allah sauki jariri ya kunno Kai Kuma adaidai lokacin mama Allah yabata ikon riqe hannunta kyau Dan sassauta Mata radadin datake ciki na kutsowar 'da ya fito ta jikinka. Gabaki daya jaririn ya fado tareda sake lafiyayyan kukan jarirai ba kakkautawa. Wani irin numfashi take saukewa da a wahalce tana Kai hannu inda jaririn yake ta dauko ta Dora jikinta. Daqyar ta bude idonta dakyau ta Dan daga kafar jaririn taga 'ya mace ce Take wasu hawayen suka gangaro Mata masu dumi, Duk da hakan ta godewa Allah daya Bata abinda ta haifar Amma taso namijine sbd zaifi samun qwarin zuciyar fuskantar zunde da qalubalan maganar da zaa ringa binsa dasu na Kalmar 'da Mara uba. Kukan jaririyar ne ya karade gida tako Ina A gigice Inna ta taso ta fado dakin tana Kiran sunan hadiza. Da mamaki da tausayi take kallon hadizar tana cewa" Hadiza ke kadai Kika haihu acikin wannan halin? Komawa tayi da hanzari ta dauko sabuwar Reza a dakinta tazo ta yanke cibin jaririyar tana kallon fuskar Yar da fitilar hannunta. Bata iya cewa komaiba sbd batasan Mai zata fada ba, Rayuwarsu cikin Rana daya Allah ya juya musu akalarta inda yaso dan haka take fatar Allah yabasu ikon cinye Wannan jarabawar. Ruwan zafi ta Dora acikin tsakar dare tazo ta karba karba Yar ta wanke tas Ta juyewa hadizar sauran ruwan itama ta lallaba taje tayo wanka tadawo. Sauran tafasasshen ruwan hadiza ta karba Tasha sosai sbd babu abinci babu komai. Komawa sukayi suka zauna jigum jigum babu Mai cewa qala. Hadizar zaune take bakin shimfidar mama Idanuwanta dake kumbure ta zubawa jaririyar tana kallo duk da acikin duhune Bata ganin komai. Hannu mahaifiyarta taji akan kafadarta Ta juyo ahankali idanuwanta na Mata nauyi da radadi ta kalla maman cikin duhu ta bude Baki jikinta matuqar sanyaye muryarta a shaqe tace" Mama 'ya mace ce na Haifa. Wani sanyayyan numfashin da Baya fita sosai maman tasaki tareda janye hannunta kan hadizar ta bude Baki daqyar cikin yanayi na majinyaci Mai tsananin Jin jiki ta Kira sunan Hadizar. ##MAMUH# #ZAFAFABIYAR# #LOVE# #ROMANCE# #INAYA A MAJEED# #AYSHATOUH# [10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: *_INAYAH_* _Mamuhgee_ *_Arewabooks@Mamuhgee_* 5 Daqyar ta iya furta "Hadiza Allah zai zama gatanki, Allah zai raya Miki 'yarki cikin Aminci inshallah. Allah ya Raya zuriarki ya sanyawa zuriarki albarka kinji¿ Hakama halima ki kula da ita tamkar uwar data dauki cikinki ta haifeki sbd dagani harku har abada bamuda abinda zamu saka Mata dashi akan halacci da kaunarta garemu, Batada kowa saiku ku sauke nauyin uwa mahaifiya akanta kinji hadiza. kasa kuka tayi sbd yanda zuciyarta taso tsayawa cak daga bugawa da sanyin kalaman mahaifiyarta, Tunda mutuwa ta dauki mijinta Bata taba samun kyakkawar kalamiba daya taba zuciyarta sai yau da mahaifiyarta ta furta matasu adaidai lokacinda duniya da kowa ya juya Mata baya ana gudunta akan abinda daya sameta. Cikin rawar murya dake son bayyanarda kukan dake kokarin yiwa kansa iso tace" Mama kin yarda da bazan taba aikata abinda ake zargina dashiba??? Mamar Bata iya mgna ba saidai gyara kanta tayi ahankali tana rufe Idanuwanta dake lumshewa da kansu... Kalmar shahada take kokarin furtawa a kakkarye Hadizar naji ta tabbatarwa da kanta rasuwa mamar zatayi Cikin sanyi da qarfin zuciya ta Bata sauran Kalmar shahadar Cikin saa maman ta karba ta qarasa daqyar sbd Rai dayazo gangar fita. Wata masifar a rayuwa fin karfin wata masifar take, Idanuwanta da zuciyarta ne suka bushe Mata alokaci daya Saidai wani irin gagarumin nauyi daya tokale zuciyarta ya tsaya a maqoshinta. Hannnunta na cikin na mahaifiyarta ta cika, Rintse idanuwanta tayi ahankali tana Jin nauyin Kirjin nata na tsananta Ta miqe tsaye ahankali tareda aje jaririyarta a gefe ta matsa gurin inna dake qudundune gefe tana Nishin azababben zazzabi takai hannu ta tada ita tareda Kiran sunanta ahankali cikin sanyi tace" Inna ki tashi Allah ya karbi ran mama... Wani mugun yunquri Inna tayi tana tashi zaune idanuwanta a waje ta kalli inda mamar take tana qara hasken fitilarta tace" Aishatu ta rasu kikace hadiza? Yanzu nabarta akwance fa tana numfashi. Miqewa tsaye tayi ta nufi maman hankali tashe tana cewa" Ya akai kikasan ta rasu ne tunda ba ganewa zakiyiba. Gaban gawar maman ta tsaya tana Kiran sunanta muryarta na rawa cikin firgici. Data tabbatarda Aishatun ta rasu ficewa tayi daga dakin ta zauna tsakar gida tana rusa wani irin kuka Mai rauni. Tun tanada shekara goma Sha uku Malam ya aurota daga qauyensu kasancewarta marainiya itada qanwarta Indo yazo ya kawosu Mama lokacin itama batafi shekara goma Sha biyarba ya hadasu suka zauna lafiya harya aurar da Indo itama. Lafiya kalau sukai rayuwa da mama tamkar yaya da qanwa haka suka zauna harsukai wayo mamar ta hayayyafa su kabiru har manyanci da tsufa yakamasu suna zaune lafiya, Basu qara kaunar juna na mutunta junaba saida malam ya rasu ya barsu Ita Inna Batada kowa sai mama da 'yayan mamar da itace tayi renon kowannensu harya girma. Yau aishatu ta tafi tabarta da tsananin kewa da kadaici adaidai lokacinda 'yayanta suke tsaka da rikicin da zai rabasu har abada Idan ba Allah ne ya kawo dauki ba. Koda aka fito sallar asuba tuni su Yaya Umar da malam kabiru suka iso sbd Inna ta buga musu da 'yar qaramar wayarsu da hadiza ta siya musu tun kafin zuwanta Lagos wadda da ita take waya dasu. Hadiza na zaune gefe cikin dakin da jaririyarta a dunqule suka shigo babu Wanda ya kalla inda take sukaiwa gawar mahaifiyarsu Addua suka fice Dan fara shirye shiryen jana'izarta da sauransu. Jaririyarta data Kira da sunan AYSHATUH daidai bayan rasuwar mahaifiyarta sai baccinta takeyi sanyeda kayan sanyi farare tas data zakulo daga kayanta data Bari Nan gida tun kafin tafiyarta, Kayan tun na Abdul ne Dan haka sun Mata yawa sosai amma tunda babu wani kayan haka ta Sanya Mata su. Jamaar anguwa da koina sunji labarin rasuwar Mama Dan haka mutane sukaita shigowa cikeda alhini. Tana dakin itadai Bata fitoba da jaririyarta sbd mutane zasu iya zunde duk da rasuwar da akai mata tasani Dan haka ta kame kanta a daki Bata fitoba har akaiwa mamar wanka da sitira ta matso tayi Mata Addua aka Dauketa aka tafi da ita. Duk yanda taso kuka takasa zuciyarta ta bushe ta kafe da tsagwaron qunci da baqin ciki. Saida Yan gaisuwa suka rage tana daki tafito taje tayi wanka da tafasasshen ruwan da Inna ta Dora Mata tana gurin wankan jaririyarta tayita kuka Nan take Yan zaman gaisuwar suka fara yi da ita. Haka tafito bandaki Takoma daki Bata Kuma fitowaba, Wankanba itace tayiwa jaririyar da kanta sbd inna na cikin Yan gaisuwa. Har dare Bata fitoba tana daki Saidai taci abinci data fidda kudi tabawa innar aka siyo musu sukaci da daddare. Washe gari take anguwa da jamaa suka dauka cewar haihuwar cikin shegen datai shine ya kashe mama da baqin ciki Dan haka Take masifar gidan takuma tashi da daddare harta kwanta su malam kabiru suka shiga shida Yaya Umar sukace wlh saita bar gidan da 'yarta bazata rena 'yar datai sanadin mutuwar mahaifiyarsuba adakin mahaifiyar tasu. Tunda mama ta rasu zuciyarta ta kafe Dan haka ta tashi ta hau tattara kayanta. Kallonta Inna tayi tana cewa "Ina Zaki ki barni hadiza? Wasu siraren hawayen tsananin tausayin Inna ne suka gangaro Mata. Inna abar tausayice tako Ina sbd barinta tamkar watsar da itane ga duniya Dan kuwa su Yaya Umar Basu tallafi mahaifiyarsu data kawosu duniyaba tanada Rai tayaya zasu iya tallafar rayuwar Inna da batada kowa batada komai... To Amma ya zatai tunda ankoreta ita kanta, Kuma ita kanta zataso tafiyar sbd yanda ake zundenta da qyamatarta da yarta tareda jifanta da alkaba'i daban daban akan itace tayi sanadin mutuwar mahaifiyarta. Tana kuka ta tattara kayanta tabar gidan cikeda baqin ciki da quncin Rashin ganinta Abdul daya koma hannun hajiyarsu Salisu sbd jinyar da mama keyi Inna Batada lokacin kulawa dashi. Inna kam itama kukanta daukewa yayi bayan tafiyar hadizar da sunaji suna gani su malam Umar ana gaman zaman gaisuwa ya Roshe dakin mama ya hade da wanda yafara ginawa cikin gidan ya fake da sunan zai kawowa Inna abokiyar zamane sbd kadaici. Barin Hadiza gida ya rusa rayuwar Inna da ita kanta hadizar wadda batasan Ina ta nufaba. ALLAH YA ZAMA GATAN MARAYA A DUK INDA YAKE..AMIN ************** _March 2002_ _7:26am_ Kokarin saka Mata pink safa a qananun qafafunta yakeyi Yana dan sake waiwayawa yana kallon wajen dakin nasu dan duba yanayin garin dakeda hadari sosai Wanda tun bayan sallar asuba yaketa haduwa. Ganin yanda duk tabi ta lafe masa tamkar Mara lfy yasashi dagowa ya kalli kyakkawar qaramar fuskarta dake kallonsa da idanuwanta dako yaushe zai kaita makarantar raino sai tayi wannna qyuyar wadda tun batai wayo hakaba takeda ita. Batasan kowaba bayan mahaifin nata da a duniya batada kowa bayanshi Kuma Bata yarda da kowa sai shi din  sai uwar renonta yagana wadda take kira da Ummey. Cikin idanuwanta dasuka Dan Yi Kaman zatai hawaye ya kalla ya saki ajiyar zuciya ahankali Yana janyota jikinsa cikin lallausan muryarsa me zallan nutsuwa ya furta _"INAYA.._ Hawayene suka fara gangaro Mata ta girgiza kai ahankali cikin Rashin budewar harshenta sosai tace" _ABBI..._ cikin kulawa ya hanata fadar abinda yasan rigimace kawai zatayi sbd batason zuwa Kuma ya saba da hakan tunda yafara kaita kullum saitai masa wannna rigimar. Share Mata hawayenta yayi tareda miqewa tsaye ya dauki Yar jakar takardar dayake saka Mata robar ruwan pure daya dayake juye Mata a empty robar Coke sai fanke da kosan matar kofar gidansu daake soyawa na siyarwa. Daukarta yayi ya riqe jakar a dayan hannunsa suka fito ya janyo kofar dakin tareda Sanya padlock dinsa ya rufe kofar dakin nasa ya juya ya nufi hanyar kofar ficewa. Dukkanin jamaar gidan hayar dasuke gidan kusan kowa yafito Yana hada hadarsa a qatoton tsakar. Da damarsu dasukaci karo da fitowarsa da mugun kallo suka bisa Wasu Kuma dai tabe Baki sukai suka dauke Kai Suma. Maman habiba ce dai da Bata gajiya da cusa kai tana ganinsa ta taso tana washe baki da cewa" Aa su INAYAN Abbinta ce anfito zaa tafi makaranta? Zo mu gaisa kinji? Hannu ta miqa Dan karbanta Inayar ta sake maqalewa Mahaifinta tana lafewa tareda rintse ido batamason kallon maman habiba din. Yar dariya tasake tana cewa "Inaya haryanzu dai qyuya ko? To adawo lfy. Amin kawai ya iya bude bakinsa ya furta ahankali kafin ya ra6a maman habiban ya wuce tana bin bayansa da kallo. Mijintane ya qaraso ta bayanta Yana kallon Wanda takebin da kallo yace" Zuwaira bazaki daina shiga sha'anin Wannan Mai shegen girman kan da miskilanciba ko? Sam Dan iskan yaro a naqushe cikin talauci Amma baya ganin girman kowa Baya daraja kowa a duniyarsa babu abinda yasani sai wannan aljanar 'yar tasa Mai kama da   'yar Rake, Kullum Yana tafe Yana kame kansa Kaman dan kwalisar daya sauko daga jirgi., Ke Kuma sai naci da shishigi kike masa akan yabaki renon Yar tasa kina samun 'yan kudin da yagana ke samu gurinsa. Juyowa tayi tana fuskantar mijin nata tace" Baban habiba laifine Dan na nace masa akan yaban renon Nima naringa samun Yan qananun canjin da yagana ke samu? Inace Idan nasamu kudin Kai zan rufawa asiri na ringa Dan samun ciyar da yarana tunda Kai zuciyarka ta jima da mutuwa bazaka iya fita kayi ko aikin wahalar dashi yakeyi Dan ya kula da 'yarsa kasamoba... Cikin masifa Yana jefanta da mugun kallo yace" Idan zuciyata mutuwa tayi ke taki konewa tayi ko? Sbd Naga alamar son abin duniyarki Neman yake ya rufe Miki ido yaro Dan qarami Wanda kikai qani dashi Zaki zauna Yana wulaqantaki tunda ko kallonki bantaba ganin yayiba duk wannna shishigin da kike masa akan 'yarsa dako qafarta baya barin ta taka tsakar gidan Nan Kamar akansa aka fara haihuwa mu duka 'yayanmu ba 'Yaya bane sai tasa 'yar ce kawai 'ya, Yasan Yana tsananin jinta kamar ransa ubanwa yace ya rabu da uwarta? Cikin takaici maman habiba tace "Ina ruwanka da Idan sakin uwarta yayi idanma mutuwa tayi,meye naka? Bbn habiba ka fita fa idona na rufe kabarni nasamu nacusa kaina a gurin nasa nasamu abinda nakeso. Inaya dai inshallah sai ka ganni Ina renonta Ina laifin dari Biyar duk sati?wlh zanyi kokari nasamu tunda Kai din ba nemowa kakeyiba sai shegen gulma da sa ido. Qaramin tsaki ta sake tana juyawa ta wucewarta tabarsa tsaye Yana binta da hararar mugun rainin datai masa Bata kunyar fada masa magana kowace iri tunda taga ita ke nomowa ta ciyar dashi. Suna fitowa gida Kai tsaye hanyar titi ya nufa Bai Kuma sauketaba har lokacin sbd karta Bata qafafunta da takarminta da daudar hanya tunda lokacin damuna ne. Barema koba lokacin damuna bane baya ajeta koyaushe daukarta yakeyi daga cikin gida har inda yake kaita, Bai cika barin ta fitoba tayi tafiyaba koyaushe daukar 'yarsa yakeyi shiyasa tayi wani irin mugun sabo da abbin nata Bata yarda da kowa saishi Bata iya zama da kowa sai shi, Wani irin qawa zucin Mahaifinta Allah ya dasa Mata acikin ranta sbd tunda tafara wayo shine halitta mafi soyuwa a zuciya da idanuwanta, Yagana farkoma data fara wayo qin yarda takeyi yabarta gurinta yaje gurin nema sai ahankali tadan fara sabawa da ita Amma harya dawo daukanta Bata sakewa duk da qananun shekarunta tasan Mahaifinta ta yanda ko sallamarsa taji daga nesa tana gane shine. Wata qaramar private school ya nufa da ita Kai tsaye dake anguwar. Yana Isa dayake maigadin makarantar ya sanshi sosai sbd yanda kullum yake zuwa kawo 'yarsa tun tana jinjira har tayi shekaru hudu yanzu. Da sakewar fuskar ya miqe tsaye Yana cewa" *_Haji ABDUL-MAJEED_* baban Inaya sannu da qarasowa, Inayar ya kalla yana dariya yace" Inayar Abbi sauko to na kaiki gurin yagana. Kallon Abbin nata tayi tana sake riqesa idanuwanta na kokarin cikowa da hawaye Kaman yanda tasaba kullum aka kawota. Wata boyayyar ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta cikin kulawa tareda zareta daga jikinsa ya miqawa yagana data iso gurinsu tana Kiran sunanta cikin kulawa da kauna. A natse da kamilalliyar murya yace" Barka da safiya yagana, Mun tashi lfy? Lfy kalau Baban Inaya, Ya Inaya?antashi lfy? Alhmdlh" ya furta a taqaice Yana maida kallonsa kan inayar datake kallonsa ya sakar Mata wani taqaitaccen murmushin da duk duniya ita kadaice yakewa murmushi da tattausan lafazi ya furta "INAYA" Karkiyi kuka zandawo da wuri inshallah kinji?? Gyada Kai tayi ahankali tana cewa" Abbi... Kallon yagana yayi yana ciro 500 ya miqa Mata tareda jakar inayar Yana cewa" Ku shige zan koma daga Nan. Juyawa sukai yaganar tayi ciki da ita tana Mata wasa. 200 yaciro ya miqawa Jamilu Mai gadin Shima kafin ya juya ya wuce yanajin yanda yake jero godiya Yana adduar Allah ya Raya musu Inaya. ##MAMUH# #ZAFAFABIYAR #AYSHATOUH INAYA# #A MAJEED# #LOVE/ROMANCE# [10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: *_Mamuhgee 6_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Yagana aiki takeyi a qaramar private school din dake kusa da anguwar tasu amatsayin nanny Mai kula da yara Amma gidansu na haya 'daya da ABDULMAJEED din da yarsa Inayah, Tun 'yarsa na jaririya shi kadai ke dawainiya da lalurar kulawa da ita sai yaganar wadda Rana daya suka tare gidan hayar itama tazo tareda mijinta da kusan yake kwance ba lafiyayyeba, Da farko sbd babu yanda zaiyi ne yasa ya amince yaganar datai masa tayin taimaka masa da rainon 'yar tasa da Kai tsaye ya sanar Mata da ya rabu da mahaifiyarta. Yagana itace tayi rainon Inaya hartai wayo ta girma tasan Mahaifinta har takewa yaganar qyuya akansa shiyasa daga baya Takoma gurin Mahaifinta gabaki daya saidai idan zai fita takaita gurin yaganar Amma daya dawo yake zuwa ya taho da ita Da haka harsuka koma rayuwarsu su kadai, a dakinsa yake Mata wanka cikin qatuwar robar wankanta daya siyo Zata tsaya aciki kokuma ta zauna aciki yayi Mata wankanta tas ya shiryata. Rayuwarsa da 'yarsa wata irin rayuwace dasuke abarsu su kadai dagashi sai ita sai yagana data Dan shigo ciki, Duk duniyarsa babu wani buri ko abinda yake gabansa bayan 'yarsa INAYA dayake iyayin komai dabai sabawa shariah ba Dan inganta rayuwarta da Bata wadatacciyar tarbiya da nutsuwar rayuwa, Bayan INAYA babu wani Abu dayake so da kauna a duniyarsa, Ita kadaice abinda yakeda, Ita kadaice Nutsuwarsa da abinda yake kalla yaji qwarin gwiwar cigaba da yaqi da gwagwarmaya Dan inganta rayuwarsu musamman ganin yanda takeda tsananin qawa zucinsa kasancewarsa Mahaifinta Kuma mahaifiyarta. Kafin tayi wayon datake dashi yanzu yasha wata irin gwagwarmayar wahalalliyar rayuwa Dan samarda abinda zai rainar masa ita., Karatun jamia yake alokacin hakama bayada aikin komai face kalolin aikin wahalar daya ringa yi Yana samarda abubuwan da kowane baby zai buqata. Cikin wani irin tsananin hali yasamu ya kammala karatunsa yayi service yafara zuwa yan ayyukan da zasu ringa taimaka masa Dan lalurarsa data 'yarsa. Sana'ar gadin wani gida yafarayi tsawon watanni kafin Mai gidan yabar qasar Dole ya nema wata aikin. Daqyar yakuma samun aikin security a wata private hospital. Da Wannan aikin yake rayuwa kafin raga baya yasamu aikin wankin mota yana hadawa dashi. Shekarar inaya uku yafara tunanin aure badan Jin dadinsaba ko Dan yanajin buqatar hakan Kawai dai zaiyi auren ne Dan ya samarwa 'yarsa kwanciyar hankalin samun mutum ataredasu ko zata sake tayi rayuwa Kamar kowanne yaro, Amma badan wai ya Samar Mata uwaba, Har abada shine uba Kuma uwar INAYArsa, Har abada babu mace data Isa ta zamto uwa ga INAYA, Shine uwa Kuma uba Ita kanta Inayah duk da qarancin shekarunta tariga ta Dan San halayen Mahaifinta Dan haka ta daina ambatar sunan mahaifiya tuni sbd Hani da yayi mata da hakan aduk lokacinda bakinta ya furta Mama. Alokacinda yayi neman auren farko ga 'yar Mai Basu sallah a masallacin anguwar da farko lafiya kalau yafara zuwa fira bawai danma yasan Mai zaiyita fadaba sbd shi miskilin mutum ne shiyasa Bai cika shiga mutaneba, Iyakacinsa da 'yan anguwar da mutanen gidan hayarsu gaisuwa Itama gaisuwar sbd sanin mahimmancinta a addini ne. Da yawa mutanen anguwar da mutanen gidansu na haya kallon me girman Kai da Rashin mutunta mutane suke masa saidai Kuma basa iya fada gaban idanuwansa sbd kwarjinsa da kamewar mutuncin kansa duk da kasancewarsa qaramin matashi. ABDULMAJEED ABBI kamar yanda yarsa ke kiransa kusan hakan kowa ya sansa, Wani irin baudadden mutum ne da babu Wanda yake iya gane inda ya dosa, Meye ne acikin ransa?, Meye abinda yake tunani?, Waye shi? Sam babu Wanda yace yataba ganin koda murmushinsa bare dariyarsa sbd Bayan 'yarsa babu Wanda ya taba yiwa koda murmushin bare dariyar Dan haka kusan kowa baya masa dogon shishigi ciki kuwa harda yan saka idon anguwa da munafukan anguwa kowa ya kama kansa dashi Zagi dai ne Idan anzauna dattijawan anguwa da Basu San su kama girmansuba sai sunyi saka idon kullum cikin zaginsa sukeyi sunayi dashi a fakaice Idan yawuce ta gabansu yayi musu sallama ya gaishesu haka zasu ringa washe Baki suna amsawa suna yabonsa da yabon 'yarsa Daya wuce zasu fara zundensa. Aurensa da Hafsat yar liman ya lalace ne bayanda aka zuga mahaifin nata da cewar ana zargin zafin zuciyarsa da baqar zuciya kamar kuturu ya ringa azabtarda matarsa da duka da yunwa da wahala da baqin talauci ta gudu ta barsa da jinjirar 'ya bayan ta haihu, Wasu Kuma suka ringa fadar bada aure ya Haifa yarsaba Dan haka hafsatu renon 'yar gaba da fatiha kawai zata tayi. Wannan zugar ta lalata maganar aurensa da Hafsat wadda take tsananin sonsa Kuma shi kansa har cikin ransa ya yaba da nutsuwarta yayi shaawar auranta ta zauna da Inayah. Bayan an hana masa auren hafsa bai cire raiba sbd yanzu sosai yakeda shaawar samarwa Inayah Mai zama da ita Dan haka tunanin yin auren yashigesa sosai bawai Dan har lokacin tunaninsa ya sauya akan Mata bane dakuma Wai Jin Yana son aure ko mace ba, Sam Mata bayada shaawarsu ko kadan, Baya Kuma Jin tunaninsa da tsananin yanayinsu zai sauya a zuciyarsa har abada. Fatima yakuma nema aure a bayan layinsu bayan ya Dan kwana biyu Yana zuwa fira gunta daganan ya aika Mijin Yagana da Daman shine kawai yake tsananin ganin girmansa da mutuncinsa ya nema masa aurenta. Kamar yanda tafaru farko hakance takuma faruwa Har anbasa auren daga baya aka fasa sbd wasu maganganun da aka Kuma kaiwa mahaifanta itama. Cikin qanqanin lokaci Saida ya nema aure so hudu ana hanasa daga Nan Mata suka Kuma ficewa a Ransa kwata kwata Musamman sbd yanda aka dauki hanyar aibata masa 'ya sai hakan yakuma tsananta qamewar zuciyarsa akan Mata da mutane, Bai Kuma shaawar neman kowace macen ba, Yacire maganar aure daga ransa kwata kwata har abada bayajin zai Kuma kallon kowace mace da sunan wani abu face sunansu na mace. Daga Wannan lokacin burinsa ya sauyu ya karkata ga ilmantar da 'yarsa yakuma dage ba dare ba Rana da Neman aiki da mafita dama Kuma karatu dayakeson qarawa sbd babban burinsane Dana mahaifinsa tun Yana raye. Aikin wahalarsa dayakeyi ya matuqar tsananta Dan kuwa bayan security na asibiti da aikin wankin mota yanzu harda sana'ar 'dan acaba yanayi Idan yasamu abokin aikinsa na gurin aikin security ya basa Aron mashin dinsa yayi. Rayuwa Mai tsanani da wahalar gaske yake gudanarwa, Baya samun cin abincin dazai kosar da cikinsa, Duk Rana da dukan ruwan dayake Sha na fafatawar ayyukan wahalar dayake duk na inganta rayuwar Inayah ne, Ita yake siyawa Yar sitirar sakawa sbd ko sitirar arziki basudashi, Abincinta da Shanta sune yake iya kokarin samarwa, So da dama haka yake wuni da yunwa  saidai yasha ruwa da Dan biredi haka ya kwanta amma Inayah baya taba Bari ta nema abinci ko abin buqata ta rasa. Ahaka yake gudanar da rayuwarsa acikin wani irin tsananin hali. Yagana tana samun aiki a private school ta primary ya dage yayo wahalarsa yasamu ya saka Inaya duk da kusan shekarunta sunyi qanqanci Amma haka ya sakata sbd a gida yagana ta dena zama aikin take zuwa Shima gashi yanzu ya sake dagewa da ayyukan wahala iri iri da yawon Neman aiki Dan haka kullum yake kaita makarantar idan yadawo da wuri ya biya ya daukota Idan baidawoba anan take zama tareda yagana har sai antada Yan primary kowa ya tafi sai sudawo gida ta zauna gurin yagana harya dawo, Yana dawowa yake tsayawa gurin yagana ya dauketa su shige Bata qara fitowa dakinsu sai washe gari Idan zaije sallah wani lokacin yakan kaita gurin yagana yaje yadawo Wani lokacin Kuma rufeta yake a dakin yaje yadawo sbd itama Kaman tayi gadon mahaifin nata miskilace ta gaske batason zuwa koina tafison ta zauna gurin Abbin nata. Musamman sun saba rayuwarsu daga ita sai shi. ***** Wani tsautsayi daya samesu shine dakinsu daya fara zubar ruwa ta sama Idan ana ruwa yasa tunda damunar ta tsayu sosai yadaina baccin dare, Zaune yake kwana yayi gadin Inayah tayi bacci sbd gudin yanayi na tsautsayi ko zai riskesu, Da safe kafin su fita zai kwashe ruwan daya taru a dakin ya goge musu ya gyare dakin dako ledar qasa babu sai Rabin dakin ne kawai keda Leda Shima gurin katifar Inayah sbd kada sanyi ya kamata. Sauyin aiki akai masa daga security na asibiti zuwa na wani super market. Ranar farko daya fara aiki a super market din yahadu da wani class mate dinsa a gurin. Da farko Nuradden ya bayyanarda mamakinsa sosai ganin A MAJEED a matsayin security sbd sanin tsananin ilimi da kyakkawar takardun da MAJEED din yake dasu Dan haka Bai wani boyeba ya bayyanarda mamakinsa tareda yimasa tayin wani aikin wanda yafi Wannan. Da farko MAJEED yaso kaucewa tayin Amma Nuradden din ya dage tareda tabbar masa ba daga garesa bane taimakon dagaske maikatan ake nema. Amincewa yayi washe gari ya Isa makekiyar maaikatar kasuwancin mahaifin Nuradden din cikin saa yasamu aikin cashier na daya daga cikin manyan malls dinsu sbd sunason fara jarabta aikinsa kafin su basa wani aikin daya kamata shima sbd Nuradden yayita zuzuta musu ilimi da MAJEED din yakedashi Dan hkaa ahankali cikin yardar Allah yafara aikinsa na cashier a gurin. ******** Tunda yasamu aikin cashier a taqon mall din rayuwar tafara yi masa sauki shida yarsa harma da yagana da mijin yaganar sbd shi din mutum ne Mai alkhairi musamman ga mutanenda suke tsananin kaunar Inayah, Duk Mai kaunar Inayah to tabbas matsayinsa a cikin ransa Mai girma ne, Yanda yake tsananin kaunar 'yarsa Jin yake komai zai iyayiwa duk namijin daya aurawa ita duk ranarda ya cutatar masa da ita, Wasu lokutan har fargabar yanda zai fara fuskantar bayar da ita aure zuwa wani gurin yake Dan haka alqawarine Mai girma acikin ransa na zai wadatar da ita da ilimin Mai zurfi sbd rayuwa a gidan wani tayi Mata sauki. Majeed sam Bai damu da abun hannunsaba duk lokacinda yasamu 'yan kudade baya qyashi haka zai kashewa Inaya sauran Kuma ya bawa su yaganah Suma tunda ba laifi suna cikin yanayin rayuwa suma, Basu taba haihuwaba itada mijinta wanda yake zaune baya iya fita nema sbd yanayin Rashin lafiya dayake ciki na sugar gashi anyanke duka qafafun nasa biyu duk sbd lalurar a keke yake rayuwa, Dan haka shigowar Inaya da Abbin nata rayuwarsu ba qaramin taimakawa rayuwarsu yakeyiba Hakannema yasa duk yanda ake gulmar da zindensa babu ruwansu basa shiga sbd sukam majeed kusan shine rufin asirinsu yanzu Suma qarshe aka ringa binsu da zagin makwadaita Dan sungansa kalar 'yayan masu arziki dama Kuma a wani bangaren da yawansu suna masa kallon Wanda yafito daga zuriar masu hannu da shuni Kuma duk iya gulma da bin diddiqi ankasa sanin asalinsa dakuma inda yafito. ***Ahankali Lokaci yaja sosai har INAYA ta kammala nursery tashiga primary hartayi nisa tana primary 4. Har lokacin a mall yake aiki saidai ba laifi yasamu qarin girma sosai harya zama assistant manager, Alhmdlh komai Yana tafiyar musu a daidai dan kuwa babu kalar Jin dadin da Inayah Bata samu gurin mahaifinta sai Wanda baa rasaba daidai gwargwadonsa. Yanason tashi yabar gidan ya kama haya wani gurin sbd 'yarsa datake girma gashi gidan gidan tarone mutane iri daban daban amma Kuma sbd rayuwar kadaici da zata iya wargaza Mata walwalarta data fara samu sakamon girma data fara shiyasa Bai tashiba gidan har lokacin Amma zuwa lokacin yanada halin sauyawa din tunda sunfara samun rufin asiri. Inaya na gaf da kammala primary 4 yasamu hayar wani gidan acan hanyar gurin aikin nasa Dan haka yafara musu shirye shiryen tashi duk da ba wani kayan suke dashiba bayan katifar baccin Inayah sabuwa Mai dakan mutum daya, Sai qaton bargon dayake shimfidawa qasa ya kwanta sai jakar kayansu da 'yan abubuwan amfanin cin abinci. yasamu su yagana da maganar tashin nasa dakuma tayin dayakeda niyar yimusu ko Allah zaisa su amince. A zaune ya samu malam Aminu Mijin yaganar a kofar dakinsu kan tabarma Yana Dan sauraron radio dayake dare yayi Dan har qarfe tara takusa bugawa. Inayah batai bacciba sbd assignment datake dashi dazai koya Mata Kaman yanda yasaba yimata tishin karatunta na bokon Dana addini kowanne dare kafin tayi bacci Dan haka tareda ita yaqaraso shimfidar malam Aminun Yana riqeda hannunta jikinta sanyeda doguwar rigar bacci Mai kauri da har qasa sai qaramar hular sanyi akanta, Hatta qafafunta suna sanye cikin safa Mara nauyi sbd Sam baya Wasa da duk abinda zai taba masa lafiyarta shiyasa ko Yaya yaji Alamar sanyi to baya Wasa ko bacci zatai saida socks. A natse Kaman yanda yake koda yaushe ya zauna gefen tabarmar Yana bude Baki cikin kamilalliyar muryarsa Mai nutsuwa yace" Barka da dare Malam, Yaya lafiyar jikin? Allah yaqaro afuwa da nisan kwana. Sosai cikin kulawa malam din ya amsa Yana kallon Inayah data zauna gefen mahaifin nata yace" Inayah yau bakiyi bacci da wuriba Kika biyo Abbin naki cikin sanyin Nan. Ahankali ta kallesa tana sake Dan guntun murmushinta da qaramar muryarta tace" Ina wuni malam? Sake Yar dariyar kulawa da shaawar nutsuwarta data abbinta yayi Yana amsawa kafin yace" Ki shiga ciki gurin ummen taki yagana tana sallah ne. Sake riqe hannun abbinta tayi tana sauke Kai Dan Saida Abbin ya Dan kalleta da fararen idanuwansa yayi Mata alamar taje din tukuna ta miqe ta nufi kofar dakin da sallamarta a Baki ta shige. Cikin nutsuwa yayiwa malam din tayin zama dasu a sabon gidan hayar daya kama Mai daukeda dakuna uku zuwa., Baya boye boye shi mutum ne Mai magana kai tsaye Dan haka Kai tsaye ya sanarwa da malam din sbd yanda Inayah tayi sabo fa yagana dakuma yanda INAYArsa zata cigaba da walwalarta cikin mutane Idan taga Basu kadaineba a gidan. Da farko malam shiru yayi Yana nazarin al'amarin sbd Kai tsaye suje su qarawa Abdulmajeed din nauyi Kaman Bai kamata ba tunda Shima yanzunema ya 'dan damu walwala ta abin yi. Amma Kuma ata wani fannin kaman yanda Abdulmajeed din yafada rayuwar Inayah kam Idan babu mutane zata iya rasa walwalarta Duk da idan tana ganin Mahaifinta Bata buqatan kowa Amma ai shi mutum rahama ne, Kuma itama yaganarsa Yana so tasamu mutanenda koba ransa zasu dauka amanartaba tunda Suma ba kowane dasuba Kaman su Abdulmajeed din. Abdulmajeed yabarsu akan suyi shawara kafin lokacin tashin nasu yayi ahaka akabar zancen Idan yayi shawara da yagana. Bayan komawarsu daki tace zatai fitsari dayake yanzu tafara girma dole badan yasoba yake barinta zuwa bandakin gidan Amma qaidane Bata Idan so nawa zata shiga bandakin saiya wanke Mata shi dasu Izal germicide harma dasu Dettol kafin tashiga Kuma harta Gama tafito Yana tsaye bakin bandaki Yana gadinta. Idan Kuma baya gidane to yagana ma ta saba itace zatai Wannan aikin haka zata wanke takuma tsaya harsai inayan ta fito. Su hand sanitizers kuwa baya Bari suna qarewa yake siyowa sbd ita din, Data fito toilet din kokuma tafito filin gidan tayi wani abin yake tsaftace Mata hannaye dasu sbd shi wani irin mutum ne Mai tsananin tsaftar gaske shiyasa a wani fannin mutanen gidan da anguwar dama Yan gurin aikinsa ke ganin kamar yana qyamar mutane. Yanzu dinma datace zata bandakin kayan wanke bandakin ya dauka tareda fitila mai tsananin haske ya fice yaje ya wankesa tas tashiga Yana tsaye ta fito ya wanke Mata qafafunta da hannayenta suka koma dakin. Da kanta ta Kuma gyara shimfidar lafiyayyar katifarta tayi Addua ta kwanta ya gyara mata rufarta kafin ya miqe ya dauko jakar takardunsa na karatun masters dayakeson farawa da yardar ubangiji Idan su yagana su amince zasu zauna dashi da Inayah sbd zaifi nutsuwar karatun idan yasan yarsa yanzu tana tareda mutane nagari zai ringa zuwa makaranta hankali kwance yadawo yaje aiki. ##MAMUH# #ZAFAFABIYAR# #AYSHATOUH INAYAH# #LOVE/ROMANCE#[10/13, 4:51 PM] +234 703 121 9749: *_Mamuhgee 7_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Washe gari asubar fari yatada ita suka nufi bandaki tun kafin sauran jamaar gidan su firfito, Fara wanke bandakin yayi tas bayan ya tsayar da ita gefen wajen bayin inda ruwan bazai taba taba. Yana cikin wankewar jamaar gidan Yan son banza suka fara fitowa da duhun asubar sbd su samu sauran tsaftar Albarkacin Inayah. Baban habiba ne agaba da qatuwar butarsa ya nufi bayin yaja ya tsaya daga gefe sbd sanin daga Inayah har Abbin nata basa rabar mutane., Yana tsayuwa oga Abdul Ganiyu ya iso da nasa qatoton cikin riqeda bokiti ya tsaya shima. Fitowa Majeed yayi daga bayin da fitilarsa Mai tsananin haske ya kallesu Dan yasaba ganinsu kowacce asuba sune manyan Yan jiran banza a gidan sauran Basu qarasoba tukana. Inayah ya kalla tareda kamo hannunta ya dan janyo daga jikin bangon datake tsaye ya miqa Mata fitilar tareda qatuwar butarsa ta roba shikuma ya daukar Mata bucket din ruwa suka shiga ya ajiye Mata ya fito. Tsayawa yayi bakin kofar daga nesa kadan Sai alokacin ya Dan kalli su bbn habiban a natse ba sauti sosai ya musu barka da asuba. Baki washe suka karba suna masa sannu da kokari na wanke bayin. Suna tsaye a gurin Daya bayan daya jamaar gidan masu son amfani da bayi lokacinda yakeda tsaftarsa suka firfito sukazo suka bi layi sbd gari na Gama wayewa kowa yafara kaida kawo cikin mintuna ashirin bayin gidan zai masifar rikicewa a lalatasa gabaki daya sai Mai hakurin qazantane kawai zai iya Shiga Shiyasa da yawansu Allah Allah sikeyi siga Majeed yadawo gidan zaiyi amfani da bayin kokuma 'yarsa zatayi shiga Take zasu fara shirin Yana fitowa su Shiga sbd tsafta. Hankali kwance a natse tayo wankanta da sabulunta na Dettol da soso Mai taushi tayo alwala ta fito saida ya rakata har daki ta shige kafin yadawo ya shiga yafito yayi alwala ya fice zuwa masallaci da har an tada sallah. Sam babu mutum daya a gidan daya yarda dashi akan 'yarsa datake 'ya mace, Bama gidan ba kawai ko makaranta koyaushe cikin nanatawa yaganah kular masa da ita yake, shiyasa qafarsa qafarta duk inda zasu sai idan yaje gun aikine tana gurin yaganah wadda itama take taka tsan tsan da Inayan ganin Mahaifinta yanda Sam baya sake ko Wasa da al'amarinta tako Ina. Vaseline na Dettol dake ajiye akan qaramin tebir da kayan shafarsu da wasu daga cikin litattafan abbinta dake Kai ta dauka tareda komawa ta zauna bakin katifarta ta fara shafawa a natse ga sauran baccin dakecin idonta Amma dayake tafara sabawa da tashin asuba tunda tayi wayo abbin ke tada da asuba kullum shine saukinta, Sama sama tagama shafa Vaseline din Bai wani shafu ba sbd tasaba abbinta ke Mata makomai yanzu ne dai take su wanka da shafa Mai da kanta tareda saka Kaya duk da hakan haryanzu wasu lokutan shine yake saka Mata wasu kayan Idan takasa sanyawa daidai. Qaramin body mist dinsu ta shafa kafin ta Sanya vest da qaramin zaninta na atampa ta saka hijab tayi sallah tana gamawa tun kafin Abbin yadawo Takoma ta kwanta sbd bacci takeji sosai Kuma Yana shigowa karatun zai sakata suyi dan haka da wuri ta koma baccin. Acan masallaci ana Gama sallar yayi adhkar da adduoinsa ya fito sbd da wuri yake dawowa Idan yafita sallah idan har yasan a daki yabarta ita kadai. Kallonta yayi Kai tsaye Yana shigowa yaga harta koma bacci Dan haka ya kyaleta ya dauki nasa kayan wankan ya wuce gurin wanka. Saida yakuma wanke bayin kafin ya shiga yayo wankan ya fito yadawo daki ya shirya fes cikin blue polo shirt  da baqin wando. Qaramin gas dinsu daya siya kwanakin ya janyo ya fito dashi kofar dakin ya kunna ya Dora ruwan zafi. Dakin ya dawo ya dauki Yan canjinsa dake aje kan table din dakin ya fita. Raba mutane ya ringa Yi Yana wucewa sbd kusan kowa yatashi gidan anata hada Hada, Masu sana'a nata hidima da kokarin hada sana'arsu akan lokaci, Masu fita aiki da hidimar yau da kullum Suma sai kaida kawon Shirin fitar sukeyi, Masu zaman banzan gidan qalilan ne Daga 'yan Mata biyu masu zaman kansu suna kawo mazan dasuka ga dama sai dattijuwa iya kande dake sana'ar zaune wato saka ido da kayan Mata saikuma baban habiba da shima baya fita nema ko sana'ar komai sai ta saka idon shima Amma bayan su duka  jamaar gidan suna fita nema da sanaa. Shagon kofar gidan ya Isa ya tsaya daga gefe sbd mutanen dake ciki su rage. Mintuna uku ya dauka a gurin kafin suka Dan rage ya qarasa yayiwa Mai shagon sallama a natse. Cikin washe Baki hafizu Mai shago ya amsa sallamar Yana cewa" Barka da safiya Baban Inayah Ina kwana?antashi lfy? Ya Inayah? A taqaice ya amsa da kalmar "Lafiya kalau alhmdlh" Dari Biyar ya miqa masa yace" Bread daya zakaban da Kwai biyu. Cikin sauri kuwa ya hada masa abinda yace din a Leda ya miqo masa tareda sauran canjin Yana cewa" Mu wuni lfy baban Inayah. Amin nagode Mal hafizu. Ciki yadawo ya fara juye ruwan zafin a cup babba ya maida sauran ruwan ya dafa Mata indomie da dafaffen qwai ya juye a qaramar kularta ta makaranta ya saka Mata a basket tareda cika Mata robar ruwanta mahadin kular ya jefa Mata biscuit din digestive daya ya ajiye gefe sai alokacin ya tada ita ta fita bakin kofar dakin nasu tayi brush ta wanke fuska sukaje tayo fitsari tadawo tayi Shirin makaranta suka Sha tea kafin suka fito tana biye dashi Kamar cingum yanda wasu ke kiranta akan baban nata. Gurinsu yagana suka nufa Dan gaisawa dasu kafin ya wuce Dan haryanzu baya Bari yagana ta wuce masa da ita kullum safiya saiya kaita yake wucewa aikinsa saidai suk hade can. Cikin yanayi suka samu su yaganar sbd jikin malam din daya tashi jikin dare da zazzabi ya kwana Mai qarfi. Cikin kulawa yai masa ya jiki kafin ya ciro dubu daya ya miqa Mata yace" Yaganah ki kokarta asamo adaidaita saiki kaisa asibitin Zan Kai INAYAH makaranta daga can Zan biya gurin aikin saina bada uzurinda Zan sameku asibitin muga abinda Allah zaiyi. Karba tayi cikeda godia jikinta duk a mace da yanayin malam din sbd ko magana bayason yi Kai kawai yake gyadawa Majeed din alamar godiya. Fita sukayi Yana riqeda hannun Inayar suka nufi makaranta Saida suka qarasa bakin kofar makarantar ta juyo tana kallonsa fuska a Dan shagwabe ta bude madaidaicin bakinta tace" Abbi Idan kaje asibiti taredasu Umma yaganah waye zaizo ya tafi Dani Idan an tashi? Na tafi na da kaina abbi Zan iya. Fararen idanuwansa ya saukar Mata a  'dan bude yace" Koba yau ba duk ranar Dana samu kin fita kinbi hanya da kanki zakisan Hukuncin dazan dauka akanki, Kina kina? Gyada Kai tayi tareda sake cewa" To Abbi na zaunane nayita jira har kazo? Umma yagana Bata makaranta Idan antashi zanji tsoro aka barni, Kazo da wuri kaji Abbi??? Gyara Mata zaman hijabinta yayi Yana gyada Kai cikeda kulawa yace" Kidai jirani kinji abinda na fada, Wuce karkiyi latti, Allah ya bada saa. Amin Abbi. Juyawa tayi ta shige ciki shikuma ya juya ya tara mashin ya hau ya nufi gurin aiki Kai tsaye. Bai wani jimaba gurin aikin ya bayyanarwa da manager uzurinsa ya fito ya kama hanyar asibiti sbd Yagana ta sanar masa suna Isa anbasu gado. Koda ya Isa asibitin jikin malam din yaqara tsanani sosai Kamar Kar a iso dan haka ya karba takardun magani da abubuwan da aka rubutan. Ba wasu kudaden ne dashiba shima Amma haka ya tafi gurin siyan maganin Dan yaji ko nawane kudin. Ana Gama duba takardar a pharmacy aka miqo masa kudin a rubuce. Dubu talatin harda shida da wata dari  takwas akai yagani rubuce. Ajiyar zuciya tareda numfashi ya sauke a hankali tareda kallon Mai shagon a hankali ya furta" Nagode" ya juya ya wuce yabar gurin. Bayada ko dubu goma a halin yanzu Dan kuwa duka duka dubu shida ce a account dinsa Kuma koshi kansa baya tabata Dan na siyayyar Inayah ne na abincin zuwa makaranta daya kusa qarewa. Kallo takardar ya Kuma yi tareda sake lumshe fararen idanuwansa cikin tsananin tausayin malam din da yaganah. A iya fahimta da Dan sanin da yayi musu yasan basuda kowa sai junansu, Yasan dai Yan asalin jahar borno ne suna cikin Wainda sukayo gudun hijira tunda dadewa dangi da sauran Yan uwa duk sun mutu wasu Kuma Suma sun fada wata duniyar suna ganin garari. Fuskarsa ya shafa ahankali kafin ya juya ya nufa titi Dan hawa mashin yakoma gurin aikinsa ya gwada rokon manager albashinsa na Wannan watan idan zai samu yanzu koba komai saura sati daya watan ya qare. Kokarin tare mashin yake Yar qaramar wayarsa ta Itel ta ringa vibrating sbd ya kashe qararta bayaso. Ciro wayar yayi daga aljihu yaga sunan yaganah ya dauka Yana cewa" Assalamualaikum" cikin nutsuwar muryarsa Kamar kodayaushe. Wata sanyayyar ajiyar zuciya Mai zafi tareda mutuwar jiki yaganan ta sauke kafin tace" Abdulmajeed kadawo kawai malam yariga ya tafi lokaci yayi... Wani irin kuka Mai sanyi ta fashe dashi tareda kashe wayar sbd sai alokacin kukan ya zo Mata. Innalillahi wainna ilayhirrajiun" ya furta Yana maida wayar aljihu ya tsallaka titin yakoma cikin asibitin Yana jinjina Kai cikin jimamin mutuwar. Kuka sosai Yaganah keyi daqyar ya iya furta Mata kalmomin ban hakuri da tawakkali dazai iya furtawa shima. Basuda wani jamaa dagashi har ita yaganar har malam din Dan haka babu maganar tsayawa Jan lokacin jana'iza Asibiti na Gama nasu aikin suka Basu gawar suka dawo gida da ita. Sosai jamaar gidan Dana anguwa suka nuna alhininsu akai masa sitira aka kaisa. Bai samu zuwa maqabarta ba sbd gabaki daya hankalinsa daya rabu biyu Yana kan Inayah da aka tadasu makaranta lokacin Dan haka makarantar ya wuce Kai tsaye ya daukota suka dawo gidan yabarta gurin yagana yabi sauran Wainda zasu maqabartar suka wuce. Babu wani zaman karban gaisuwa dasukai saidai Wanda yazo yaje har kofar dakin yagana yayi Mata gaisuwa ya wuce sun daiyi Mata tasu karar sun zauna ranar daya rasun daga ranar saidai masu zuwa jefi jefi har akai sati biyu. Tunda akai rasuwar babu ranarda Inayah Bata fashin makaranta zai kaita da kansa ya wuce aiki Idan lokacin tashi yayi zai Baro gurin aikinsa ya rakota gida kafin ya koma. Wani sabon Nauyin ne yakuma hawa kansa na Yaganah sbd kallok uwa dayake Mata gakuma tausayin halinda take ciki din na Rashin miji,Dan uwa,abokin fira,abokin rayuwa Wanda suke tare tun kuruciya gashi ko tashin hankalin daya sakosu gudun hijira Bai rabasuba sai yanzu da Mai gaba daya tazo wato mutuwa. Sbd matsayin Yaganah agun Inayah yasa Dole ya dauki nauyinta ya ratayawa kansa Dan haka yanzu komai nasu tareda ita yake siya sbd ko aikin ta daina zuwa Dole sbd takaba, Ta wani bangaren Kuma mutuwar ta tabata sosai Dan komai ya fice Mata arai Daqyar Inayah ke samu tana dan sakata magana wasu lokutan. Rasuwar tasa Dole yakoma ya saki gidan daya kama ya karba kudinsa kafin Yaganah ta Gama zaman takaba zai nema musu wani Mai Yar damar Inshallah. Dan haka kudin saiya tattara ya hada ya siya musu abinci isasshe da siyayyar makarantar Inayah suka shiga jss 1. Watan malam din shida cif da rasuwa sukabar gidan suka koma sabon qaramin gidan daya kama din Wanda yamafi na farkon kusa da gurin aikin nasa, Dakuna biyu ne a gidan da qaramin toilet harda broken tiles dinsa. Daki daya ya dauka Dayan Kuma haka Dole dai yaganah da Inayah suka zauna daki daya Amma wasu kayan nata na dakin baban nata sbd sabo. Katifar Inayah ta farko ya dauka sai ya siya musu wata Yar katifar Mai Dan girma tareda zanin gado da pillow sbd sanin Inayah da bacci da pillow. Labulai ma ba laifi ya Samar musu iya daidai nasu sai kayan aikin abinci da kusan duk nasun ne na da. Ahaka cikin Dan rufin asirinsu suka fara gudanar da rayuwarsu a sabon guri cikin nutsuwa. Bayan tarewarsu anguwar Basu wani dauki dogon lokaci sosaiba Yan anguwar Suma suka gane halayensa na Rashin shiga mutane da kamewar Kai dan haka suke mutuntasa duk da zamansa matashi ba wani babba ba. Kwarjinsa hadi da Kamun kansa da Rashin shigewa al'amuran jamaa musamman wainda Basu shafesaba yasa duk inda ya zauna ake mutuntasa sbd shi kamilin mutum girmamasa akeyi Koda baida wasu manyan shekaru. Islamiyar dake cikin anguwar ya sakata tareda sauya Mata makarantar bokonma sbd waccan din tayi nisa Dan haka gabaki daya yanzu komai nasu ya Dan sauya, Yagana ke girkin abinci da tsaftace koina na gidan ta sakewarta Takoma tamkar yanda take a da dinta, Sosai take kulawa da Inayah tamkar jikarta data Haifa uwarta, Shi kansa Baban Inayar yana cikin kulawar yaganan Dan kuwa abincinsa  baa Wasa dashi, Musamman data fahimci shi Mai tsananin tsaftar gaske ne sai baa Wasa da qazanta a gidan ko kadan. Yan anguwama ganin irin kauna da kulawa Mai girma dake tsananinsu yasa suke daukar yaganar a matsayin mahaifiyarsa. ##MAMUH# *_For More pages ku garzaya arewabooks_* #LOVE/ROMANCE# #INAYAH#AYSHATOUH# #ZAFAFA BIYAR _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [10/13, 4:51 PM] +234 703 121 9749: *_Mamuhgee 8_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Farkon zaman yaganah dasu duk wata Yana fidda kudin Albashinta na zama da kulawa da Inayah, Lokacinda ya fara Bata kudin sosai ta nuna masa Rashin Jin dadinta sbd sune suka taimaketa bawai itace take taimakonsu ba, Kai tsaye ta nuna masa Karya Kuma nuna mata kudi da sunan biyanta akan zaman datake da Inayah harma dashi.. Ganin ta nuna Rashin Jin dadin hakan sosai yasa Bai Kuma tinanin Bata dinba Amma Kuma bayajin ya nutsu da Rashin Bata Wannan haqqin nata Dan haka cikin dabara ya jata banki ya bude Mata account batareda ya sanar da ita asalin dalilin hakan ba,duk wata Yana Sanya Mata 3k a account sbd shi mutum ne da bayason haqqin kowa akansa, Bayason Alfarmar mutane sbd Rashin yarda da kowa musamman akan sha'anin da duk ya shafi Inayah duk da yaganah ta musamman ce a rayuwarsu yanzu, Tsananin qauna da shaquwar dake tsakaninta da Inayah yasa tasamu matsayi Mai girma a idonsa harma da wani bangare mai girma na zuciyarsa. Haryanzu dasuke rayuwa da Umma yaganah shine maiyiwa Inayah wasu abubuwan Kaman koyaushe Idan zata Sanya Kaya tafi zuwa gurinsa ya zabar Mata Wanda zata saka, Shine suke Cin abinci tare kaman yanda tasaba hakama bacci a dakinsa Saida Umma Yaganah tayi da gaske kafin suka samu ta daina kwana gurinsa sbd wani irin Sabone datayi da hakan tun tana jinjira tareda Mahaifinta take bacci harta Wannan girman shiyasa takasa sabawa da rayuwa ba gurinsaba. Shi kansa duk dare ya ringa haske haske fitilar wayarsa Yana leqowa dayaji motsi sbd duk inda yake bayajin cikakkiyar nutsuwa Koda rana Koda dare Idan baya ganinsa guri daya da ita, Allah ya sanyosa cikin irin iyayenda sukeda wata irin taka tsantsan akan tarbiya da safety na rayuwar 'yayansu, Sam Sam bayada yarda ko nutsuwa akan komai indai gameda 'yarsa ne Cikinma ahakan yasamu nutsuwa sosai dakuma yarda matuqar sosai da Umma yaganah. Umma yaganah tun Bata iya rayuwar Majeed dinba harta iya ta karance komai nasa musamman tsaftarsa dake wahalar da ita farko Amma daga baya ta saba shiyasa yanzu take tsananin Jin dadin rayuwarta dasu hankali kwance su ci Mai kyau da lafiya su Sha Mai kyau da lafiya. Kullum safiyar fari yana dawowa masallaci yake ficewa morning jogging (gudun safe), Koda yake dawowa Inayah tagama Shirin makaranta zai rakata makarantar yadawo yayi wanka wata ran ya tsaya yaci abinci kafin yafita wataran baya tsayawa sbd kaucewa lattin Isa gurin aiki, Baida wani Abu dake gabansa bayan jajirwa tuquru akan aikinsa sai kulawa da gidansa, Bayada aboki ko daya a yanzu, Baya doguwar mu'amala da kowa data wuce ta aiki saita gaisawa da Yan gajerun abubuwan da baa rasaba na mu'amalantar mutanen. ** Ansamu cigaba ta bangarora da dama na rayuwarsu Wanda ciki ya hada da sauyawar gidan dasuke ciki zuwa mai kyau da yalwa da tsari sbd yanzu Inayah nada nata dakin, Shima Abbin yasake zama magidancinsa sbd yazama baban matashiyar budurwa ga Kuma tarin aiki da masters dinsa dayake kammalawa takardun kawai suka rage masa Kuma da yardar Allah Yana karba zasu bar Nan sbd komai nasu yagama kammala. Daga Boko Inayah Umma yaganah ce ke zuwa su dawo tare yanzu sbd shi aikinsa baya barinsa dawowa ya rakota gida shiyasa umman ke zuwa yanzu, Inayar tayita fushi tana nuna batason ana zuwa dawowa da ita Amma Abbin yaqi daina rakata hakama yaqi Bari Umma yaganah ta daina zuwa dawowa da ita duk da ta girma sosai suna kiris da shiga SS 2 Qawayenta har dariya suke Mata suna kiranta da 'yar Abbi da Umma yaganah, Wasunsu Kuma burgesu abin yake sbd ganin yanda da girmanta ma Mahaifinta Bai daina ji da itaba ko Dan batada qanne ne wata kila, Gashi baya Bata kudi ko kadan duk abinda takeso ko buqata shine yake siya Mata Amma baya Bata Kuma baya Bari ana Bata. Lokacinda period yafara zuwar Mata yazo Mata a yanayi Mai zuwa da ciwon Mara Dan haka hankalinsa yayi matuqar tashi musamman wata na biyu da abin zai sake zuwa saiyafi na farkon sbd na farkon Bata wani wahalaba gashi umma yagana ma Bata tsaya fada masa ko meneneba kawai dai ya dauka zazzabine tayi ta Kuma warke, Amma Wannan watan dayaga yanda take zuba amai tana kukan ciwon Mara hankalinsa tashi yayi damuwa sosai kan fuskarsa. Asibiti ya dauketa suka kaita sai acan likita ke masa bayanin menene ciwon, Da farko Bai Gama ganewaba sai daga baya Umma yaganah tasake masa budadden bayani akan jinin haila ne Inayar tafara. Tsit yayi Yana kallon kofa da fararen idanuwansa zuciyarsa na Dan yin nauyi sbd wani matakin girman ne Inayah takuma hawa yanzu tarbiyarta da kula da ita zaifi hatsari., Shi gabaki dayama Banda Umma yaganah tai masa bayani baiwani San yayane Mata ke wannan al'amarin, Sam bayada sani ko kadan akan Mata da yanda suke su irin wannna din duk kuwa da yanada ilimin addininsa daidai gwargwadonsa Amma Sam baida sani anan, a ilimance a al'adance a rayuwance ma Dan haka Koda suka dawo gida gurin aiki yakoma dazai dawo yazo Mata dasu pads daga gurin aikinsa, Dazai siya dinma Dole cikin ma'aikatansu Mata wata ta zabar masu masu kyan ya siya yazo dasu yabawa Umma yaganah, Su panties Bai siyaba sbd yasan koyaushe cikin siya Mata undies sababbi yake sbd kiyayewa da tsaftarta. Tun daga Wannan lokacin duk wata haka ake fama da ita har aka samu ta saba ta iya danne ciwonta idan lokacin period din yayi tadawo ma bamai sanin lokaci yyai tayi ta gamawarta sabanin farkon da duk wata Abbin yasan lokacinda takeyi sbd yanayinta da wuyar datake Sha. ******** Shekara daya da Gama masters dinsa komai nasu yagama sauyawa tako Ina, shekaru sun qaru sun fara zama manyanci, Arziki ya fara zaunuwa ta hannu ta banki, Hakama rayuwa ta sake budewa tako wane fannin sbd tuni yabar mall a asalin kamfanin yake aiki kuma a babban matsayi yafara zama sbd qualification dinsa da zurfin Aiki da iliminsa dayakeda. Da farko sosai Yaso samun matsala sbd Yan hassadar zuwansa da finsu matsayi da yayi Hakan ya haifar masa da matsala sosai har yaji yafara gajiya da gurin aikin musamman sbd bayason Al'amarin damuwa da tashin hankali. Ta wani bangaren yanata samun invitation na offern aiki daga guraren dayayita neman aiki dasu tun wancan lokacin Yanzu sai babban matsayi Mai kyau suke masa tayi Amma dai sbd halacci ya zabi ya zauna Nan din Amma al'amarin Yana neman gagara. A gida sbd lokaci girma sosai dayazo masa yasa yanzu akwai qarin ganin girman juna sosai fiyeda da tsakaninsa da Umma yaganah sbd yanzu yafara wuce matsayin matashi Dan haka ganin girman tsakaninsu yafara qaruwa Amma dai ita sakewa har lokacin akwaita sosai tsakaninsu Bata sauyaba. Inayah kuwa haryanzu shaquwarta da abbinta saima abinda ya qaru sbd yanzu ma kusan itace ke gyara bagarensa duk da sunada Mai aiki dake zuwa tayi aiki Takoma gida sbd Abbin dayace Umma yaganah tasa asamo sbd Inayah karatu take bayason tana tsayawa aiki, Hakama itama Umma yaganar yakamata ta huta a rayuwa yanzu tunda an bautu iya bautuwa yanzu hutu yazo ahuta tunda Allah yakawo damar. Daga Umma yaganah sai Inayah ne kawai suka San abinda yakeso dakuma abinda yafi buqata Dan haka acikin akwai Mai aikin gidan har lokacin Umma ce kawai ke girkin dayake ci hakama Inayah ce yanzu ta karbar Mata gyaran palonsa zuwa dakinsa duk da dama can bedroom dinsa ne kawai Umma yaganah bata shiga Inayah ce kawai Mai shiga shima Idan bayanan datai girma yanzu. Yanzu yanada arzikin siyan mota Amma har lokacin Bai siyaba sbd yanke shawarar komawa Lagos a reshensu na aiki dake can sbd Nan din fitinar tafara yawa yadda abubuwan aikin nan din sun fara rushewa Dan kuwa maha'intar kamfanin sun fidda zalamarsu a fili take komai yafara rushewa. Yana ganin hakan ya rubuta takardar aje aiki yafara aikawa Nuradden dake Lagos ta email. Da farko hankalin Nuradden yatashi da barin aikin na A Majeed sbd sun riga dama suna kokarin rasa reshensu na can Idan A Majeed yabar aiki zasuyi Rashin babban gifted Dan haka da wuri ya sanar fa mahaifinsa dake Singapore halinda ake ciki. ***Kwana biyu Yana hutawa sosai a gida cikin iyalinsa hankali kwance musamman daya kasance dama baya wani yawo sosai daga aiki sai gida sai wasu guraren qalilan sai Kuma makarantar Inayah da har lokacin Yana zuwa kaita. Ganin Abbinta gida kwana biyu kuwa Inayah sai takejin Dadi sosai sbd Dana aikinsa Yana riqesa sosai Lokacin Kuma yake gida itama Kuma makarantar yamma Dan gaka yawanci sai dare suke samun lokacin zama dashi. Satinsa biyu a gida Yana hutu ana ukun ya shirya zuwa wani aikin da akeson daukarsa saiga sakon Amb Ibrahim Dikko mahaifin Nuradden daga Singapore. Sabuwar offer ce na aiki dasu a Singapore. Kai tsaye farko dakatar da offer din yayi sbd bayajin zai iya barin qasar yaje wata qasar aiki yabarsu Inayah anan su kadai Dan haka Kai tsaye bayan kwana biyu yayi rejecting offer din. Wancan aikin ya karba harya fara Amma Nuradden suka kasa barinsa sunata bibiyarsa. Sake sabon nazari yayi akan aikin sai kawai ya amince bayan an amince masa da zuwa dawu Inayah Amma Lagos zasu zauna tsawon lokaci kafin. Lokaci qanqani suka dauka kafin suka tattara suka koma Lagos gabaki daya acan suka dasa sabuwar rayuwa. Da farko sunsha wahalar rayuwar garin kafin suka saba saidai kam makaranta da Dole da qarfin hali Umma yagana ce aka koyawa mota Kuma Allah yasa ta iya tunda ba wani manyata tayiba dan haka ya siya musu mota itace take kaita tana daukota, Koda minti daya Bata taba Bari tayi lattin Isa makarantar daukan Inayah ba sbd maimaicin dokar hakan daga gurin mahaifinta. Aiki yamasa yawa sosai yanzu dan haka sosai baya wani zama, Haha tafiye tafiyen garuruwa harma da 'yan wasu qasashen daya fara sbd aikin nasa shiyasa yanzu Dole tarbiyar Inayah tadawo hannun Umma yaganah gaba daya saidai koyaushe cikin Kira da maimaita akula yake nanata musu. Inayah na kammala secondary school bada jimawaba ya tattarasu suka koma Singapore sbd hankalinsa daya rabu biyu. Rayuwarsu a Hougang Singapore wata sabuwar wayayyar rayuwace ta hutu da Jin Dadi sbd arziki daya zaunawa Abbin. Watansu tara a Hougang suka dawo cikin asalin Singapore Singapore, Bayan aikin kamfani wani karatu yasake jonawa cikin shekara biyu ya kammala tareda samun wani babban aiki a Australia suka bar Singapore. Bayan barowarsa Nigeria ko shekara hudu Bai gama rufawaba kamfanin gabaki ya rushe akai gwanjonsa Wanda shine tashin farko ya siye kamfanin da malls malls din na can Nigeria harma Dana Singapore ya damqawa Nuradden da mahaifinsa Wanda manyanci yasa shima yace abawa Nuradden din yaci gaba da kularwa da A Majeed din dasu tunda yanzu komai ya zama mallakinsa ne Amma hallacinsa yasa yabar kamfanin a hannunsu suci gaba da kulawa. Sun sallami dukkanin ma'aikatan dasuke zargi da ha'incin Daya kaisu ga rushewa suka rasa komai aka Kuma zuba sabbin ma'aikata bayan ansake gyara companies din da malls malls dinsu. *_BAYAN WASU SHEKARU....._* #MAMUH# #ZAFAFABIYAR# #A.A MAJEED# #INAYAH# #AYSHATOUH# #RIBABIYU# *_Dan samun cigaban labarin follow me @Mamuhgee at arewabooks_* *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107*_Mamuhgee 9_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* _A.A MAJEED's_ _659 Melrose victoria mosmon,_ _SYDNEY,AUSTRALIA._ A hankali ta qarasa zare navy blue turkian doguwar rigar dake jikinta ta jefar kan brown Chiara Andreatti sofa dake babban bedroom din nata. Kyakkawar fuskarta datai ja ta Dan kalla ta cikin mirror tana Dan yamutsa fuska kafin takai hannunta akan fuskar ta shafa gefen damarta da wani Dan qaramin pimple ya fito mata qwaya daya tal daya hanata fita koina tun shekaran jiya. Ajiyar zuciya ta sauke tareda zare fararen undies dake jikinta ta nufi toilet dasu a hannu tana shige ta jefa cikin laundry ball dake gurin ta nufi inda brushes dinta suke ta dauka daya tareda diban Toothpaste tafara brush tana kallon fuskarta jikin mirror tana sake Jin damuwar kurjin fuskar tata, Tana gamawa  jacuzzi ta nufi ta shige tareda sakarwa kanta ruwan dumi tana Dan lumshe ido sbd damuwarta ta Dan saketa. Mintuna qalilan ta dauka tana wankan kafin ta fito daure da brown towel kanta ma daure da brown towel din qarami fatar jikin qyalli takeyi tana bayyanarda tsananin hutu,Jin Dadi da tsadaddiyar kular datake samu ta hanyar amfani da skin products masu tsananin kyau da tsada. Kai tsaye gaban madubin dakinta ta nufa ta zauna tareda kunna hand dryer tafara busar da gashin kanta data kunce bobmarley braids (kitso/kalban Bob Marley) jiya da yamma. Doguwar malaysian riga ta saka har qasa Mara nauyi ash kala ta zira Burberry slippers ta fito daga bedroom din nata hannunta riqeda wayarta tana kokarin saka Kira. Qamshin turarenta na Versace(Bright crystal) ne yafara bayyanarda fitowarta daga bedroom dinta zuwa babban yalwataccen palon gidan dake. Zubbi Mai aikinsu tun a Singapore Yar Amana wadda Alhaji Nuradden Aminin Abbi ya Aiko musu daga Nigeria itace ta dago daga kunna qatuwar Humidifier dake palon bayan tagama gyare koina na gidan ta tsaftace ta kalli hanyar da Inayah ta fito tana kallon kyakkawar fuskarta ta saki dan gajeran murmushi tana cewa" Good morning Inayah. Kallonta Inayah tayi da fararen idanuwanta tana amsawa Kai tsaye da cewa" Morning zubbi. Hanyar bedroom din Umma yaganah ta kalla tana cewa" Umma yaganah ta tashi? Yes ma" zubbi tafada tana qarasowa Dan shiryawa Inayah breakfast dinta kan dining ta nufi babban Australian kitchen dinsu ta shige. Kai tsaye ta murda kofar dakin ta shige tana qaramar sallama da cewa" Umma yaganah yauma bazan fita koinaba fuskana ta sake kumbura da ja... Zaune umman take kan wata tattausar sofa kalar ash na komai dakin dayake ash Mai haske, Farin glass ne a idonta tana karanta wani Arabic hisnul Muslim Jikinta sanyeda doguwar rigar plain cotton Swiss Mai tsada light pink. Dagowa tayi tana kallon Inayah cikin kulawa da tsananin bayyananniyar kaunar Inayah data Dade da shiga jininta ta ajiye littafin gefe kan table tareda maida hankalinta kan Inayan gaba daya tace" Yau kam saikin fita Inayah, Meyesa kike Wasa da karatunki ne yanzu? So kike abbinki ya dawo yasan kwana biyu bakya zuwa makaranta? Karatun likitanci fa kikeyi karki manta, Ahakan zakiyi wani abin arziki kullum cikin shiriritar Gayu ya hanaki Wannan da wancan? Akan pimples bazakice kindaina fitaba sai kin warke Dan haka Ki Gama breakfast kije kiyi Shirin zuwa makaranta. Zama Inayah tayi gefen umman tareda yamutsa fuska tana kokarin yin magana umman ta katseta tana cewa" Abbinki kinfi kowa sanin fadan bacin ran dazai nuna Idan yasan kina skipping ranakun zuwa school, Banason bacin ransa akan Rashin dalilinki. Kai Umma yaganah Abbi fa idan yaji abinda ya hanani zuwa bazaiyi fada ba. Inayah please Mana, Ki daure ki cire Rashin son makaranta a ranki bayan kinsan Abbinki yanada riqaqqen raayi akan son karatunki. Bari sai Akira likita tazo ta sake duba fuskar taki,ok? Gyada Kai tayi tareda miqewa tana kokarin barin dakin tace" Good morning,ban gaishekiba Dana shigo. Wani qayataccen murmushi Umma yaganah ta sake tana kallon fatar wuyan Inayar dake bayyane tana sheqi sbd yanayin rigarta cikin Yar dariya tace" Barkanki da safiya kema Inayah Majeed. waiwayowa tayi ta kalli Umman tana Yar murmushi sbd friends dinta ne masu Kiranta Kai tsaye hakan Amma ko umman sau tari hakan take kiranta itama. Dining ta nufa ta zauna hankali kwance Tasha black tea da toasted bread biyu da kwai ta tashi tabar gurin ta nufi dakinta tana sake Danna Kiran Mahaifinta dataketa Kira tun dazu takasa samunsa sai yanzu Kiran yashiga. ***Zaune yake a palon madaidaicin duplex dinsa dake Singapore tareda CM Nuradden Aminin huldodinsa suna meeting akan aikin da zaaiwa sabon kamfaninsa da aka bude reshensa a portharcourt Nigeria. Kan couch Mai zaman mutum biyu yake zaune sanyeda sky blue English kaftans masu tsananin taushi da tsadar dake bayyane. Wayarsa dake gefensa ajiye ya waiwaya a natse ya kalla ganin hasken data kawo alamar shigowar Kira ko saqo., Fararen idanuwansa yafara Dan juyowa ya kalla CM Nuradden dasu Ahankali cikin nutsuwa yace" One minute. Hannunsa yakai ya dauki wayar kai tsaye tareda kaiwa kunnensa cikin nutsuwar murya da Allah yayi masa Mai tattareda kamewa saidai kasancewar 'yarsa ce tilo datafi masa kowa da komai daya mallaka a duniya ahakan muryar tasa a bayyane take da kauna da kulawa Kai tsaye ya furta" Yes,INAYAH. wata ajiyar zuciya ta sake tana zama bakin gadon dakinta cikin tsananin kauna da kewan mahaifin nata tace" Good morning Abbi. Ahankali ya dago fararen idanuwansa ya kalli agogon _Patek Philippe_ dake daure a hannunsu ya maida idanuwanta ya dan kalli CM Nuradden yasan Inayah zataci lokacin magana dashi sosai Dan Kuma CM flight zaibi yakoma Nigeria zuwa 11 dan haka Kai tsaye cikin nutsuwa da kulawa yace" Morning Inayah, Kintashi lfy? Lfy kalau, Abbi haryanzu kana Singapore? Yaya aiki? When are you coming back? Cikin nutsuwa ya amsa ta da cewa" Inayah Ina magana da CM yanzu, Anjima I will you back,ok? Ki kula,Ki gaida Umma yaganah. Ok Abbi sai anjima. I miss you. Kashe wayar yayi tareda ajewa gefensa kafin ya dago ya kalli CM dake jiransa dan harya fara shiga yanayi na  damuwa sbd sanin wayar Inayah ga mahaifin nata sai tasa a rasa meetings masu mahimmanci dazasu kawo manyan dukiya da dama Dan ansaba Indai akan Inayah ne AA MAJEED nada raunin duba al'amura da dama masu mahimmanci Kuma hakn wani al'amarine da kusan duk wnada yake hulda ko mu'amala dashi yasani, 'yarsa Inayah itace Rauninsa da kowa yakasa sani duniya akansa sai Aminin nasa Cm Nuradden sai Kuma Umma yaganah sbd sune sukeda cikakkiyar shaidar yanda 'yarsa take a Ransa fiyeda duk abinda yakeda, Hakama 'yarsa Inayar itace qarfin Rayuwarsa, Duk Wannan arzikin da dukiya Mai yawan daya Tara basukai masa mahimmancin farin cikin yarsa na wuni daya ba, Inayah da kanta tasan itace hasken rayuwar Mahaifinta kaman yanda itama kowa yasanta yasan Mahaifinta shine abinda Bata iya hada girma da tsananin kaunarsa da komai, Shine Abbinta,shine mahaifi Uba Kuma mahaifi UWA. Numfashi CM ya sauke ya sauke yana kallon A MAJEED din sbd ya dauka zaman jiran yagama wayar ya samesa ne saigashi Allah yasa yau A MAJEED din ya taqaita. A MAJEED ya fahimci zullumin da CM ya shiga dan haka ya taqaita wayar Cikin nutsuwa ya dauki takardun da zai saka hannu akai yafara signing Yana cewa" Sauran takardun na AIA sa hannun Inayah zaa saka a takardun Amma ba yanzuba saita kammala karatunta tukuna so agama aikin kawai kafin lokacin. Alright Inshallah. Sai 10 suka rabu da CM bayan daya daga cikin ma'aikatansu yakaisa airport ya wuce. 11:30 shima yabi jirgi tareda secretary dinsa suka bar Singapore zuwa Australia. ****Badan tasoba haka tayi Shirin makaranta ta fice daga gidan zuwa school bayan tayi waya da qawarta da itama duk sunne ba wani son karatun sukeba sunfi ganewa Gayu da rayuwa kawai irin ta 'yayan gata masu abin duniya. Duk da Bata wani son karatun sosai bashi yasaka Bata maida hankali ga karatunba idan taje, Wuyarta dama dai taje din sbd idan taje sosai take maida hankali ga karatun Kuma Allah ya taimaketa tanada qwaqwalwar daukan karatun sosai Dan ahakan Bata taba failing ba Koyaushe tana samun grades masu kyau, Kawai dai Allah Bai saka Mata wani son karatun bane Abinda Allah yasaka Mata so shine Tanada shaawar yin aure kawai sbd ta daina zuwa makaranta tayi rayuwarta yanda taga dama daga shopping sai zuwa beauty parlor dasu spa sai yawan qasashen dataga dama., Ko yanzu kusan rayuwarta hakanne, Batada wani aikin bayan yawon shoppings da zuwa su spa day guraren gyaran jiki sbd Bata hada gyaran jikinta da komaiba Wanda kusan hakanne yasa koyaushe fatarta da jikinta koina yake sheqin hutu da lafiya cikakkiya da zallar gyara na musamman, Yawon qasashene Bata wani Yi sbd duk qasashen datake zuwa tareda Abbin take zuwa kokuma zuwa umrah ko Hajj tareda Umma yaganah Dan haka Bata wani samu tana yawon yanda takeso sbd haryanzu dasuka samu sauyin rayuwa mai tsananin nisa Abbinta baya barinta tana yawo yanda takeso duk da kuwa ba wani zama yakeyiba Amma dokarsa na aiki a gidan duk inda yake kuwa. Hakan yasa takeson aure fiyeda karatu musamman ma auren irin na wayayye irinta dazai barta tayi rayuwar datakeso ta Rashin takura da damuwa kawai suyita soyayya suna shaqatawa sbd love na cikin abubuwan datake yiwa kanta shaawar samun kanta aciki hakanne ma yasa bayan abbinta da yaganah to Babu Wanda takeso sama da saurayinta Zaid. Soyayyar Zaid tayi wani irin nisa a ranta Kaman yanda shima yake tsananin son Inayan, Kusan yanayin rayuwarsu daya sbd shima iyayensa masu arzikine sosai Amma suna Nigeria Dan asalin portharcourt ne karatu yake a qasar, Kaman yanda take wayayyar Yar gata girman turai hakan yake shima sbd tun Yana yaro shima kusan a qasahen turawan ya tashi tareda iyayensa sai daga baya Suka koma gida sukabarsa Yana karatu. Dan haka da rayuwar Zaid tayi daidai da tata sai soyayyarsu takeda wani irin qarfi da shaquwa. Abbinta yasan raayinta na Rashin maida hankali kan karatu yakuma san aurene takeso fiyeda karatun Amma yaqi nuna Mata ya sanin sbd karta sake samun damar nuna batason karatun, Shikuma raayinsane riqaqqe dakuma buri akan bazatai mata aureba saita Gama karatun. ##MAMUH# #ZAFAFABIYAR# #AA MAJEED# #AYSHATOUH INAYAH# #LOVE #ROMANCE #MARRIAGE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107*_10_* *_Arewabook@Mamuhgee_* Tana isowa gidan tun a compound tasan Abbi yadawo gida sbd ganin sabuwar motarsa da tunda sukazo take a gefe rufe ruf Amma gatanan a fake gefe da alama da ita aka daukosa daga airport. Kofar palonsu ta dosa tana warware nadin qaramin gyalen dake kanta tun daga hanya Tana isa ta bude kofar Kai tsaye ta shige. Bakowa a palon sai Qamshin RoseNight da Sanyin AC daya Gama cike palon Saikuma qatuwar tv dake aiki ba murya sosai. Su zubbi da Salimat tuni suka Gama aikinsu suka nufi bangarensu tunda Mai gidan na gari Dan haka idan ba aiki ba Babu abinda zai Kuma shigowa dasu saikuma idan kiransu akai. Dakinta ta nufa direct ta tube tafada toilet tayi wanka ta fito daureda towel. Kiran Dr ne yashigo wayarta da sauri sauri ta dauka tace Masa" I'm kinda busy I will call you. Aje wayar tayi tareda nufar gaban madubi ta shafa Neutrogena oil dinta ta fesa spray kawai ta koma gurin kayanta ta saka wata chiffon wide neck gown Mara nauyi ta ziro slippers ta fito ko wayarta Bata daukoba. Kai tsaye hanyar palon Abbi ta nufa tana tunanin yanda ya shammaceta Saida yadawo ya fada Mata da ba lallai ta jima gurin aikinba ayau. Da farin ciki bayyane kan kyakkyawar fuskarta tayi knocking kofar harso biyu kafin taji muryarsa daga ciki a natse ya furta" Yes Inayah, You can cm in. Shigowa tayi da sallamar dake bayyanarda farin cikinta na ganinsa ta qaraso har gefensa ta zauna tana cewa" Abbi kana tunawa danima kuwa? You look more than cool and calm. Wani qayataccen murmushi Mara sauti ya sake Yana kallon yanda itama tayi Yar rama ta yanayin aikin data samu kanta aciki da cikakkiyar kulawa yace" Dr INAYAH A MAJEED ko gaisuwa babu tukuna kafin complains su biyo baya. Cikin murnarta tace' Abbinah barka da dawowa Munyi kewarka Kagani har Rama nayi sbd ban saba dadewa hakaba bakanan, Ga stress na aiki. Yar dariya kadan yayi Yana cewa" Duk kokarin Dr Abdul akanki menene da stress acikin aikin? Dr Abdul yana fadamun irin kokarin da kike keep it up okay. Tun yanzu Ina alfahari da 'yata Zata Zama babbar likita wata ran. Taji dadin kalmomin nasa Dan babu abinda yafi komai faranta ranta kaman ta faranta ran mahaifinta harya bayyanarda hakan. Firar familyn CM tafarai Masa tana sanar dashi irin kulawa da kaunar dasuke Mata harma da umma yaganah. Sosai yaji dadin hakan Kuma a gaban nata yakira Cm yayi Masa godia a gajarce na yanda iyalansa suka karbi nasa iyalin da hannu babbiyu. Daganan firar Dr Abdul suka koma wadda kusan duk Rabin firar itace taketa fadar halayen Dr Abdul din dakuma yanda take kulawa da tattalinta. Abbinta saurarenta kawai yakeyi Yana nazarin irin shaquwar data samu da Dr Abdul din lokaci daya, Yana fatan alaqar da tsaya iya ta aiki sbd irin wannan yabo da Inayah ke Masa baya fatan tasake shiga wata soyayyar yanzu Musamman ko Dan yanayin weak heart nata Duk da wani bangaren Dr Abdulsamad ya kwanta Masa sosai a Rai. Sai dare tabaro gurin Abbin Dan abincima acan palonsa sukaci tare sbd shi kansa yariga yashige ne bazai fitoba sai gobe shiyasa shima Bai fito main hall ba cin abincin dare. Tana baro palon Abbin gurin umma taje sukai Saida safe ta wuce daki ta kwanta bayan tayi waya sama sama da Dr Abdul akan daga gobe a Shift din dare zasu sake komawa. Washe gari da safe batada zuwa asibiti Dan haka baccin safe tayi sosai sai 11 ta fito lokacin Abbi baya gida ya fita. Sanye da Riga da skirt na atampa ta fito tana waya da Neesah. Breakfast tayi ita kadai sbd tasan ko umma ta jima da yin nata. Tana gamawa ta nufi dakin umma yaganah acan tayi kwanciyarta tana chatting sama sama saiga su Mimi sun taho gidan dukkaninsu yiwa Abbi barka da zuwa aikuwa take gida ya kaure da hayaniya. Mimi harda tsarabar wasu kayan atampopin tayiwa Inayah aikuwa umma ta gode Mata sosai itama Inayah din tanajin dadin kayan Dan haka ta gode mata. Dakinta suka koma itada Safnah suna firarsu ta matasan 'yan mata, Fira suke akan anty Hafsat da Bata isoba sun biya sun ajeta gidan yayar mijin qanwarta dasuke tsananin mutunci sosai, daga can zaa kawota Nan din. Saida suka gama cin abincin Rana kusan karfe biyu da mintuna kafin Anty Hafsat ta iso gidan. Da farin cikin ganin siyama Inayah tarbota tun daga harabar gidan. Faruk Ismail shine Wanda yakawo anth Hafsat daga gidansu. Kallo daya yayiwa Inayah yaji Tai Masa sbd shima tunda yayo karatu a Malaysia yadawo yakasa ganin macen datai Masa gashi dama iyeyensa sun takurasa akan aure. Ganin dayayiwa Inayah da yanayin gidan nasu yasa Kai tsaye ya 'dan fahimci wayayyu ne jama'ar gidan, Da alama sun danyi nasu yawon bude Ido wata qasar. Inayah gabaki daya batama wani lura dashiba sbd hankalinta dake anty Hafsat da Siyama tana murmushi dukkanin kyanta na Kuma bayyana. Anty Hafsat ce ta juyo ta kallesa tana cewa" Ok faruk nagode sosai Ka Isa gida lafiya. Gyada Kai kawai yayi tareda tada motarsa yabar harabar gidan ya fice Yana ayyanawa aransa shikam yaga matar aure irin class dinsa dayakeso. Inayah kam Anata bangaren ko kula batai dashiba Dan a daukarta driver nema yakawo antyn. A gidan suka wuni Anata fira da hayaniya sai yamma da Abbin yadawo aka kaisu palonsa suka gaisa a matuqar mutunce da girmamawa. Sai dare suka tafi bayan Abbi yayi musu kyautar kudi na Musamman ga Yara. Inayah Jin tayi kaman kada su tafi sbd yanzu da qarfi da yaji tafara sabo da rayuwar hayaniya Dan duk Wanda zai Yi rayuwa a Lagos dolensa ya koya daukan hayaniya duk da sukam anguwarsu batada abinda ya hadata da hayaniyar ko hayaniyar ma Kai securities basa Bari magana suke maka sbd gudun shiga haqqin wasu. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[10/14, 11:00 AM] +234 806 831 3988: *_Mamuhgee 11_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Washe gari ba wani dogon walwala ta tashi Saima guraren 9 ta tashi Dan tun asuba tayi sallarta, Zare dukkanin kayanta tayi ta jefa kan kujera ta wuce toilet tashige tana kokarin daura towel jikinta. Sosai ta jima tana wankan sbd tasaba Bata lokaci gurin kyalekyalen wankan, Sai bayan mintuna ta fito daure da milk towel kanta Kuma nade da wani towel din mara girma. Natsatsen Qamshin shower gel dinta na AESOP Mai sanyin Dadi ne ke tashi ajikinta ta kalla Inda qaramin bedside agogonta yake ta kalli time taga goma yakusa Dan haka Kai tsaye ta nufi gaban mirror tagara shiryawa. Moisturizer kadan ta shafa na LA PRAIRIE sai oil na Neutrogena da kome Zata shafa saita shafasa takejin skin dinta daidai. Dama kafin ta fito daga wanka zubbi tagama gyara mata dakin ta kunna humidifier dasu fresheners masu sanyin qamshi ta fice da kayan data cire zuwa laundry. Elira kaftan dress ta saka dark brown da scarf sai Cassandra wedge sandal ta fito gabaki daya qamshinta na JO MALONE sea salt yana gauraya iskar hanyar datake biyowa. Kai tsaye dakin umma yaganah ta nufa tasan lokacin umman bacci takeyi sbd a qaidarta haryanzu data fara tsufa Bata daina saka hannu akan aikin abincin A MAJEED matuqar yana gari tariga ta saba Matuqar baka ganta kitchen ba A MAJEED baya gari Dan hakan Bata komawa bacci bayan asuba saita tabbatarda abincin breakfast yagama kammaluwa a dining saita koma ta kwanta sai 12 take tashi tayi wanka ta Kuma leqawa kitchen din sakawa zubbi hannu a abincin ranar. Kaman yanda tasani bacci umman keyi Dan hakan fitowa tayi dakin Kai tsaye ta nufi hanyar dakin cin abincinsu tana shiga abbin na shigowa ta dago ta kallesa da fararen idanuwanta dasukaji tsadaddiyar fenty beauty mascara da eyeliner Qamshinsa daya doke nata ta shaqa tareda dakatawa daga zaunawan da zatai cikin nutsuwa da girmamawa tareda tsananin kauna irin ta 'da da mahaifi tace" Good morning Abbi, Barka da fitowa. Saida ya kalleta cikin nutsuwa ya ja kujera ahankali ya zauna yana sake kallonta ganin yanayinta na sanyi jiki har lokacin Basarwa yayi sbd karta samu damar fara Masa hawaye agurin yace" Morning, Kin tashi lfy? Ya umma yaganah? Tana bacci ne? Zama tayi tana cewa" Eh Takoma bacci. Itace ta zuba Masa breakfast din kafin tazuba nata Takoma ta zauna tafara ci. A natse yakecin brown past din da aka hada da soyayyan dankali da hanta sbd Sarai umma yagana tasan Baya wani cin kayan fulawa sosai yafison abinci Mai suna abinci bawai wani jagwalgwalon gayuba. Satar kallonsa Inayah keyi tanason magana akan roqonsa maganarsu ta jiyan amma tana shakkar hukunci ko dokar ta qara tsanani akan iya ta jiyan. Kasa daurewa tayi ta aje fork din hannunta tareda dagowa ta kallesa a marairaice tace" Abbi.... Tissue ya dauka tareda goge bakinsa kafin ya dago ya kalleta da dukkanin fararen idanuwanta ya zuba mata yana jiran abinda takeso fada. Ganin yanda ya zuba mata idanuwansa yasata sauke Kai tana qaqalo hawaye cikin idanuwanta ta dago ta kallesa hawayen na gangarowa kan kumatunta tace" Abbi Dan Allah kayi hkr bazan sake tsallake zuwa school ba I promise Amma Dan Allah kada ka hanani fita ko zuwa wani gurin. Hawayenta dake gangarowa ya kalla tareda Dan sake wani gajeran murmushi dayayi Masa zuwan bazata sbd ganin qarfi da yaji wai 'yarsa daya Rena da hannunsa keson yimasa dabara, Duka duka Inayah nawa take? Yaushe tayi girman da wayon datake ganin Zata iya Masa wani sisina da hawayenta tunda tasan bayaso.. Ita Bata tashi da mahaifiyaba bare ace takoya ko tagani agurinta Amma wai hartasan taringa Masa hawayen kirsa Dan yaringa barinta tana yanda takeso. Sake fadada murmushinsa yayi kadan yana Kuma kallon hawayen nata datake tsiyaya da gaske Wanda badan yagama saninsu a yanzuba da tuni zuciyarsa zatayi 'daci da ganinsu Amma yanzu mamaki yake sosai ta yanda take iya hakan. Numfashi ya sauke ahankali tareda zaran tissue dake kan dining din ya miqa mata yana cewa" Ya Isa idan kingama tashi muje nine zan aje school din yau kafin na wuce office. Share hawayen tayi da tissue din daya Bata tana jin Dadi cikin ranta na yanda kwata kwata Abbinta baya juran hawayenta. Miqewa tayi tabiyo bayansa tareda daukan LV hanbag dinta tafito tana duba wayarta dake ringing da sunan Zaid akai. Bata wani dauki wayarba ta jefa jaka sbd tanason samu ta lallaba abbinta yabarta taringa zuwa duk Inda ta saba zuwanta itadai tanaso gskia. Cikin black BMW 7 series suka fita shine da kansa yake tuqa motar tana gaba zaune, gabaki daya Qamshin tsadaddun turarukansu yagama sauya numfashin motar Amma dayake motar tasace shine Wanda yafi shigarta sai nasa ya take natan sbd tuni akwai qamshinsa acikin motar. har bakin makaranta ya ajiyeta batareda ya tankawa uban magiya ra rokon datake masaba, Saida yayi parking ya juyo ya kalleta fuska a Dan sake cikeda kulawarsa da taushin murya yace" Inayah.¿ Dagowa tayi ta kallesa tana kokarin qirqiro wasu hawayen dasuke son qin zuwa, Ahankali tace" Naam Abbi. Wannan kukan na karya dagayau gabaki daya na sokesa Shima, Meye amfanin hawaye Dan ki dagawa mahaifinki hankali? Akwai wani Wanda yake Baki shawaran yin hakan ne sbd kawai kisa mahaifinki yamiki abinda kikeso? Girgiza Mai tayi tana kallonsa da rauni tace" No Abbi. No Inayah fadamun gaskia sbd nasan banbawa 'yata tarbiyar hakanba, Meye amfanin hawaye kawai sbd dagawa iyaye hankali, Wannan ne last time dazan Kuma ganin wannan hawayen ok? Gyada Kai tayi tareda maida hawayen dama Kuma fama taketayi akan suzo din basu zoba sbd Allah yasani batada wani dalilin kuka a rayuwarta sbd alhmdllh Allah ya wadatar da mahaifinta abinda duk take buqata a rayuwa, Mahaifiya kawai ta rasa wadda koda ganganci ko subutar Baki Bata taba ambatar ko sunan uwa agaban abbin harma da bayansa sbd tsananin fushi da bacin ran dayake nunawa sosai wadda kusan itama sai hakan ya samu shiga zuciyarta na fushi dajin bacin rai aduk lokacinda ta tuno da dole tanada uwa kodai tabarta da mahaifinta lokacin dayake cikin zafin talaucinsa kokuma ta tafi tabarsu sbd bazata iya hakuri da wani hali daga murdaddun halayensaba Dan kuwa tasani abbin nata murdadden mutum ne itada umma yagana ne kawai suke iya Zama da abinsu sbd sunsan komai dayakeso da Wanda bayaso. Bata saba batawa Abbinta raiba ko tayi Bata iya hakurin dacin ransa akanta Dan haka ta kallesa tareda dafa hannunsa ahankali a marairaice tace" Abbi kayi hkr nadaina daga yau. Gyada mata Kai yayi tareda dafa kanta cikin kulawa yace" Shikenan kije karkiyi latti, Ki kula. Murmushi tasake tana cewa" Ok bye Abbi Allah yabada sa'an aiki. Fita motar tayi tana daga Masa hannu daya kafin ta juya ta wuce. Neesah dake jiran isowarta taqaraso suka nufi ciki suna maganar Abbinta daya soke zuwanta spas kwata kwata. Saida suka shige ya juya yabar gurin sai alokacin ya dauki wayarsa dake ajiye ya kunna ya nufi hanyar office. Yau daga makaranta gida ta wuto direct basu tsaya yawon dasuka sababa na gurare Itama Neesah yau dole gida ta wuce Amma badan sunso hakanba sai Dan bata iya take umarni Abbinta dakuma Bata Masa rai. Kwana biyu haka suka daina yawo suka maida hankali kan karatu musamman dama sunyi nisa sosai. Kwana biyun ita kanta umma yagana Saida taringa jinjinawa sabon umarnin na A MAJEED sbd a duniya shi kadaine yakai yakuma Isa yakeda ikon Hana Inayah yawo, Sam batason Zama gida itada Neesah Dan hakan yanzu kwanakin duk sunbi sun wani sukurkurce sbd daga makaranta sai gida. Shi kansa abbin yana lure da duk wani motsinsu sbd 'yarsa, Bai taba tunanin rabata da Neesah ba sbd bincikensa tun farko dayasa ana bimasa akan Neesah batada wata gurbatacciyar tarbiya Gata ne kawai itama da 'yanci yayi mata yawa da iyayenta suka bata Dan hakan bayan yawon shoppings dasu beauty spa sai yawon dai guraren dasuke zuwa tareda friends Amma sosai batama alaqa da harkar data shafi na banza shiyasa baiyi yunqurin rabata da 'yarsaba yabarsu suna rayuwarsu tunda dama dole Inayah zatai rayuwarta da friends. Ahakan suka dauki tsawon lokaci har suka samu 2 weeks break a lokacinne Zaid yafara takura mata sosai akan maganar aurensu. Kai tsaye yafito yake matsar da ita akan sosai yake buqatan aure sbd shi buqatarsa tafara zuwa na Neman mace. Da farko fada sukayi sosai ta nuna Masa ya rabu da friends dinsa da basu dauka sex abakin komaiba sbd yanayin rayuwar turai dasuke dakuma kusan dukkaninsu tashin turai dinne. Shawararta ya dauka ya daina biyewasu zacks kwana biyu sbd dama sune suke tada Masa da shaawar hakan, Da yawa yan matansu a gida suke kaisu suna wasu abubuwan gabansa gashi dama babban gidane suke zaune su ukun kowa da babban bedroom dinsa da fadeden bathroom aciki harma da closet room. Su ukun friends ne tare suke kusan tun yarinta, Zacks bama musulmi bane black American ne, Sai Sufian shikuma kusanma 'dan uwansa ne sbd fmly friends ne ahalinsu. Tare suke lafiyayyar rayuwa a gidan sbd kowannensu yanaji da kudi da gata ba laifi, Yan mata kuwa kusan kullum cikin sauyawa sukeyi babu ranarda mace Bata kwana gidan Idan zacks Bai kawoba Sufian zai kawo Dan hakan yau da gobe suka ringa saka Zaid cikin yanayi na damuwa gashi yanzu tsakani da Allah yakan ji shaawar mace lokuta da dama. Kwana biyu yafara kasa daurewa shine yafara takurawa Inayah maganar aurensu. Yauma kusan fadan sukayi akan maganar cikin yanayi na takaicinsu zacks tace Masa" Baby nafada maka Abbi bama zai kalleniba naje da maganar Kuma shikenan nice zanje na rokesa akan ayi aure yanzu? Kana tunani kuwa? Please ba Abbi ba Nima banajin na shiryawa auren yanzu idan har sbd wannan maganar kakeson auren yanzu...bazan iyaba please baby mubar maganar Nan banason jinta tana damuna ma. Shima ransa Dan baci yayi Dan haka Bai Kuma tayar mata da maganarba saiya koma kiran dad dinsa yana matsa Masa sosai akan maganar auren Dan hakan dole dad din nasa ya nema A MAJEED da maganar idan da hali suna son ayi auren yanzu. ##MAMUH# #INAYAH# #RIBA BIYU# #LOVE/ROMANCE# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [10/14, 2:23 PM] +234 806 831 3988: *_Mamuhgee 12_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Dad din zaid yasan Sarai waye A MAJEED Dan hakan Bai tsaya nemansa a wayaba sbd sanin babu abinda zai gane a wayar tunda A MAJEED din ba wai son auren yanzu yakeba yakuma sanar dasu hakan batareda ya fada dalilinsaba saidai Kuma kusan duk Wanda yasansa yasan dalilin nasa ba boyayye bane duba da yanda yake Da zurfi da ilimin boko sosai daya Gama ratsasa sunsan babu yanda mutum irinsa zai aurar da yarsa qwalli daya dazata gadi tarin dukiya da companies dinsa batareda tasamu ilimin itama Mai zurfiba Amma ya suka iya tunda sunaso dole haka ya tattara ya tsaro tafiya ya taso zuwa qasar. Shi dad din tun farko bakin rai bakin fama yakeson auren tsakanin 'yayan nasu sbd burinsa nason qulla alaqa Mai qarfi da A MAJEED, Babu wani Mai son abun duniya da kudi daba zaiso shi ko 'dansa su auri 'yar A MAJEED qwaya daya tal ba wadda zai iya bada duk tarin himilin dukiyarsa akantaba Dan haka ba dauki bare wasa shi kam so yake ayi auren kota yaya Dan Inayah idan tana hannun 'dansu tamkar suna riqene da mukullin dukiyar A MAJEED da Baya tabuwa bare juyiwa ga kowa,Dan banzan naira da dollar sungama zauna Masa tako Ina,sun girmesa Sbd har lokacin baiyi shekarunsuba badan yanada zuqeqiyar budurwar 'yaba ai yanada sauran lokaci a cikin matasa Amma dai koma menene yaro da kudi abokin manya dama abokanan huldarsa manyan ne na gaske. Zuwan dadyn Zaid Sydney yasa damuwar da Inayah tafara shiga ya dan fara raguwa sbd gabaki daya kwata kwata yanzu itada Zaid din kullum cikin hayaniya suke, Bazata iya daukan fada bare rabuwa da Zaid ba Ayanzu din tafison Dad din nasa yayiwa abbin mgn idan ya amince ayi auren Dan gskia tana tsananin son Zaid dinta koma menene ayi auren zatai maganin wannan iskancin da yayi mata daga baya. Yau daga makaranta Saida su biya ta siyo wasu abubuwan wankanta dasu undies da Bata rabo da siya akai akai, Sai yamma suka dawo Shima tun acan take waya da abbin akai akai tanaji idan yadawo gida sbd kada ya rigasu komawa yaga sunyi yammacin dawowa. Da motan Neesah suka dawo sbd yauma Abbinta ne ya ajeta makarantar Dan dama haryanzu data girma dinnan idan yana gari yawanci shine yake ajeta school saidai driver yaje ya daukota kokuma su dawo a motar Neesah. Neesah Bata shigoba ta wuce Dan hakan itama Kai tsaye tana shigowa bakowa a palo dakinta ta nufa. Ajiye kayan hannunta tayi tana ajiye numfashin 'yar gajiya da yunwa datake ji Dan haka tubewa tahi ta fada toilet tayo wanka tafito ta sanya Abayar sallarta tana idarwa tayi adhkar ta miqe ta sanya ash riga da wandon Burberry masu kauri saidai qananun size ne Dan sun zauna daidai jikinta,basu matsetaba hakama basuyi mata yawaba daidai jikinta. Sponge resort Slippers ta zuro ta fito tana qamshinta hankali kwance. Dakin umma yagana take kokarin zuwa saiga umman ta fito. Cikin shagwabe fuska ta rungumo hannun umman suna juyawa zuwa dakin cin abinci tana cewa" Umma yaganah yunwa nakeji sosai. Murmushi umman tayi tareda Dan janye jikinta daga Inayar tana cewa" Haryanzu kin kasa iya fara gaisuwa kafin komai ko Inayah? Sake kwantar da kanta tayi kafadar umman tana cewa" Umma yaganah kullum fa Ina gaisheki kafin nafita idan nadawoma inayi ranarda na manta ba sai ayi hakuri Amin uzuriba for God sake,Kuma ma fa na........ Qamshin Turaren Abbinta yasata shanye abinda Zata fada din suka kalla hanyar palonsa atareda umma yaganah aikuwa shi dinne tafe cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Sanye yake da fararen Adidas riga da wando masu kauri hular dake hadeda rigar itace rufe akansa Qafafunsa kuma black santoni slippers ne. Gabaki daya Abbinta idan yayi shiga tamkar matashi yake komawa musamman irin wainnan shigar da yakeyi idan zaiyi geamin(exercise/motsa jiki) ko idan zai kwanta ranarda yakejin sanyi kenan, Yawan geamin dinsa yasa kullum yake sake Zama tamkar wani sabon matashin da yanzune yake lokacinsa sudaima sun rasa gane irin kyan jiki da kyan siffarsa daya hanasa manyanta sosai. Umma yaganah ce tafara bude Baki tana kallonsa tace" ABDULMAJEED barka da fitowa. Cikin yar girmamawa ya Dan kalleta kadan tareda dauke idonsa akanta yana cewa" Mun wuni lfy umma yaganah? Wata jarabawa kokuma ace lalura datake kansa tsawon shekaru shine Baya kallon mata kallon daya wuce daya zuwa biyu, Sam ya dade da rufe shafin mace ata kowanne fani na rayuwarsa bayan 'yarsa, Duk huldar aiki dazata hadasa da mata Baya wani maida hankali sosai akansu Wanda Kuma kusan ba kowane ya fahimci hakanba tunda dama shi ba mutum ne Mai sakewa mutuneba shiyasa baa wani ganewa saidai umma yaganah da Inayah dasuka Sansa ciki da Bai sune sukasan babu macen dayakewa kallon daya wuce biyu zuwa uku, Umman ma haryanzu idan yayi mata kallo daya zuwa biyu koda suna magana ne Baya qarawa shiyasa da yawa idan kana Masa bayani saika dauka hankalinsa Baya kanka and yafi maida hankali kan wani abun daban ko waya haka Amma Kuma ahakan yafi fahimtar bayanin da ake masa. Wainda suka 'dan Sansa da kadan daga halayensa idan suna magana dashi sukaga Baya wani abun daban ya tsaya yana saurarensu to kuwa sun San tabbas Bayada niyar saurarensu ne,idan kanason Kama mutuncin kanka saika dakata kabar maganar Dan ba lokacinta zaiyiba. Zama sukayi dukkaninsu a dining Inayah ta zubawa kowa abincin kafin Takoma ta zauna itama bayan ta zuba nata, White rice ce da chicken vegetables with scrambled eggs. Suna fara cin abincin Inayah ta kalli abbin dayakecin abincin a natse kunnuwansa na sauraren sautin yanayin cin abincinta take ya fahimci akwai maganar datakeson yi. "Abbi" ta furta sunan ahankali cikin kulawa da bayyanarda 'yar shagwaban data taso acikinta. Kallonta umma yaganah tayi cikin kulawa ya katseta da cewa" Ba yanzu ba Inayah, Bakiga Abbinki yanacin abinciba? Surutu lokacin cin abinci baida amfanin kinmatane? Marairaice fuska tayi cikin son fadar abinda yaketa nuqurqusanta Kuma tasan Idan ba fada Masa tayiba Dad din Zaid yayi Masa zuwan Kai tsaye da bazata ransa zai baci akan da sanin ta akazo maganar, Bazata iya daukan fushi ko bacin ran abbintaba akanta Dan haka Kai tsaye takuma kallonsa bayan tayiwa umma yaganah fuskar riqon tabarta tayi magana. Abbi Dad din Zaid Yana gari yazo fa.... Ahankali ya qarasa hadiye sauran abincin dayake bakinsa ya dauki ruwa mara sanyi sosai dake gabansa cikin glass cup yasha ya ajiye sauran ya dauki tissue Saida ya goge bakinsa ya dago da manyan idanuwansa ya kalleta hankali kwance yace" Yes,Uhum? Dad din Zaid Yana gari zan Masa wani Abun ne? Gurina yazo ne? Abbi dama gurinka ne zaizo kuyi magana,karyazo ne baka saniba ranka ya baci Abbi shine nafada maka Kuma banice nace suzoba Abb... Umma yaganah ya kalla Kai tsaye da tambayar "Kinsan da hakan ne umma yaganah? Ta sanar dake Zata basu Daman zuwa neman aurenta? Ajiyar zuciya umman ta sauke cikin sanyin jiki sbd Inayah dai Bata gane kwaba, Kallonsa take cikin sanyin jiki tace" Ta sanarmun da mahaifin nasa zaizo Amma na kaina na Kira Zaid din nace su dakatar da zuwan sbd Jan magana daya koyaushe baida amfani tunda dai anbasu auren Inayar Yin auren ne dai tunda anfada musu ba yanzuba na rasa naci irin na 'yaran yanzu tunda ba cewa akai a gaban zaa fasaba... Jin shirunsa Yana saurarensu yasa dukkaninsu suka Sha jikinsu sbd sanin hakan abinda yake nufi, Dukkaninsu sun fahimci bacin ransa akan hakan shiyasa suka sake yin wani tsamo tsamo. Cikowa idanuwan Inayah sukai da hawaye batareda ta saniba cikin sanyin murya da sigar ban hakuri ta taso tadawo gefensa tareda Dafa hannunsa ahankali tana cewa" Abbi Banice nace suzoba wlh, Nayiwa Zaid din maganar kada dad din yazo Amma baijiba, Abbi wlh bani bace... Batareda ya kalletaba yace "It's okay saiyaxo Ina jiransa. Miqewa yayi tareda kallon umma kadan yace" Mu kwana lfy umma yaganah. Allah ya tashemu lfy" tafada itama tana bin bayansa da kallo ranta babu Dadi da yanayin, Babbar matsalar basa wani gane bacin rai ko fushinsa bare kasan halinda kake ciki shiyasa koyaushe irin wannan kuskuren yafaru sun ringa Kara kaina kenan gurin samun sanin yanda ransa ya dauki Al'amari. Bayan barinsa gurin Kallon umma yaganah Inayah tayi da raunannun idanuwanta zatai magana umma ta tareta da cewa" Inayah meyasa kikai maganar Nan? Maimakon ki dakatar dasu Zaid din shine Zaki Kuma kawo maganar gaban mahaifinki bayan kinsan bayason maimaicin zance, Anyita maimaita zancen Nan Kuma kinfi kowa sanin mahaifinki magana daya yakeyi akanki meyasa bazakiyi respecting hakanba? Yanzu gashinan zakiwa kanki Dan kuwa Abbin zai iya Hana auren gabaki daya yace su hakura suje su nema wata su aura idan sunaga bazasu iya jiranba Kinga kuwa wa garin ya waya. Batada abin fada sbd jikinta daya Gama mutuwa da yanayin mahaifinta daya qi barin su gane yanda ya karbi zancen. Cikin sanyi ta dauki orange juice din dake gabanta ta Sha sosai ta aje cup din sbd bazata iya cin abincinba Kuma. Miqewa tayi tareda yiwa umma yaganah Saida safe ta wuce dakinta itama. Itama umman kammalawa tayi ta miqe tabar dakin ta dauki sauran abincin datasan zai moru takai fridge ta jera kafin ta wuce nata dakin zubbi tazo ta tattara gurin ta gyare Takoma dakinta itama. Bayan isarta daki ta Gama duk abinda zatayi ta hau makeken gadonta ta kwanta tareda daukan wayarta ta saka Kiran Zaid. Daukan wayar yayi tun kafin yayi wata magana tace" Zaid please ka dakatar da zuwan dad gurin Abbi banason cigaba da Bata ransa akan maganar wani auren yanzu, Nidai gskia mu haqura abari sai lokacinda Abbina yace koma yaushe ne zamu jira I don't want to stress him with unnecessary abubuwa kaman hakan tunda yace ajira kawai ajira Dad dinka yakoma please... Inayah are you out of your mind or what?"" yafada cikin Dan daga murya. Kinajin kanki da abinda kike fada kuwa? Dad ya taso all the fuckin way from Nigeria yazo kice yakoma sbd kada a dama Abbinki? Are you for real?Kinajin kanki kuwa? Zaid please karmu batawa juna Rai abanza mubar maganar auren Nan yanzu sai gaba.... Datse wayar yayi ya kashe gabaki daya ya jefar gefensa Dan zuciyarsa tafara baci sosai da yanda koyaushe Abbinta shine gaba shine yafi kowa mutunci,yanaji kaman mahaifinsa take kokarin ciwo mutunci Dan haka cigaba da wayarsu yanzu zai iya hadasu fada sosai shiyasa ya kashe din. Inayah ma wayar tabi da kallo cikeda mamaki da Dan takaici, Ita Zaid yake kashewa waya yau? Wai kodai bayan matsalarsa ta buqatan aure yanada wata matsalar ne da ita Bata saniba Dan kuwa wlh bazata dauka wannan wulaqancin tun yanzuba tana magana ya kashe mata waya. ##MAMUH# #A MAJEED/AYSHATOUH INAYAH/LOVE/ROMANCE/MARRIAGE #RIBA BIYU *_FOR MORE PAGES KUYI FOLLOWING DINA A AREWABOOKS@Mamuhgee_* _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107 [10/14, 2:23 PM] +234 806 831 3988: *_Mamuhgee 13_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Da 'dacin Rai duka suka kwana a daren , Inayah Kuma harda matsuwa tayi garin ya waye ta nemesa taji dalilinsa na kashe mata waya sbd ko Abbinta baya kashe mata waya shi dayafi kowane namiji daraja agurinta da rayuwarta. Duk yanda Abbi yakai ga bacin rai baya taba Bari agane Dan haka da safen koda ya fito kyakkyawar  fuskarsa na ayanda take koyaushe ba damuwa. Black Armani's ne ajikinsa sosai yayi fresh acikin black kala din, Cikin sanyi ta kallesa tanason shagwabe Masa Amma tunanin Tayi Masa laifi daren na jiya yasa ta Dan nutsu duk da hakan cikin marairaicewa tace" Good morning Abbi" tana qarasowa gurinsa itama shirye cikin milk sleeves riga da skirt na Balenciaga. Morning Inayah" ya amsa Yana kallon yanda idanuwanta sukai zuru zuru sbd daren jiyan da Bata samu bacciba. Dining suka zauna bayan ya gaisa da umma yaganah yasake kallon Inayah din da itama taketa qara wani kalar tausayi ganin take ya nuna ya lura da yanayinta na rashin baccin da Bata samuba Kuma tasan dole zai nuna damuwarsa akan hakan shiyasa take sake yin kalar tausayi. Black tea Ginger tea Mai zafi aka fara zuba Masa ya dauka yafara Sha ahankali tareda Dan sake kallon fuskar Inayah din ya dauke fuska Kai tsaye ya bude Baki cikin nutsuwa yace" Inayah¿ A marairaice tace" Yes Abbi¿ Kallonta yayi bayan ya aje cup din hannunsa fuska a Dan matse yace" Next abinda zakiyi na soke alaqarki da kowanne namiji sai bayan kin Gama karatu kwata kwata shine kici gaba da saka damuwar soyayya aranki harya hanaki bacci irin haka, Umma yaganah ya kalla cikin jaddada zancensa yace" Yaushe tasan wani soyayya hakane? Ki ringa Mata fada sosai idan ba hakanba zan tattara mubar qasar gabaki daya mu koma Nigeria ko Zata maida hankali a karatun can. Hawaye takeson yi Amma tunowa da ya Hana yasata maida hawayen cikin sanyi tace" Abbi Dan Allah kayi hkr, Ba tunanin komaine yasa banyi bacciba inada test ne yau so I had to study all night... Waiwayowa yai ya watsa Mata manyan idanuwansa ahankali Yana sake mamaki da jinjinawa sauyin sabbin halayenda Inayah ke dauka, Yaushe Kuma ta iya harda yimasa qarya? Sauke Kai tayi qasa tana Dan sosa wuyanta gabanta na faduwar kada yagane qaryarta saidai Batasan ta makaroba. Qarasa Shan tea dinsa yayi Bai wani Abinci sosai ba ya kammala ya miqe Yana cewa" Muje zan ajeki school. Satar kallon umma yaganah tayi tana neman qaryar dazata Kuma shimfidawa yatafi yabarta ta tafi school din da kanta Dan dole tana buqatan biyawa gurin Zaid suyi magana. Rasa abin fada tayi dole badan tasoba ta miqe suka bar gurin umma nai musu adduar dawowa lfy. Shi kadaine ya amsa Banda ita data shiga tunanin abinyi Dan yanzu tasan kila Abbin zai qara Mata tsananin fita akan na dah. Yau bashine yake tuqa motarba driver dinsa ne yake jansu. Har suka Isa makarantar kame kamen basa hakuri takeyi Amma Bai wani bi takan zancen nataba saima zancen karatun dayayi Mata daban. Suna Isa aka sauketa suka wuce sai alokacin yabi bayanta da kallo, yanajin tausayin 'yarsa fiyeda komai, Hakama Baya iya hakurin damuwarta, Ya rasa waye yake gurbata Masa tunani da tarbiyar 'ya akan ire iren hakan, Kwata kwata haryanzu bayajin sha'awar kowace irin mace bare marmarin ajiyeta shiyasa yake tsananin mamakin yanda Inayah ta qwallafa Rai a soyayya da son aure tunda ba ganin tayiba a gidansu ana soyayyar, hasalima shi soyayyarce sam baisan yama akeyintaba bare harka Gama macewa akan wani kaje kana Hana kanka bacci a wofi. Motar Abbin na barin makarantar ta fito zuwa coffee shop din dake makarantar ta samu Neesah dake can ta zauna tareda fidda wayarta batareda ta iya wata doguwar maganar da Neesarba tafara saka Kiran zaid. Kasa samunsa tayi dole qarshe tabar Masa sakon murya da cewa idan ya kunna waya yakirata Kuma ya tabbata Dad baije gurin Abbinta ba sbd zasu iya yiwa kansa Abbin ya dakatar da soyayyarsu sai gaba din. Bayan Gama tura Masa sakon muryan aje wayar tayi gabanta zuciyarta ba wani Dadi ta Dan yamutsa fuska tareda Kiran sunan waiter a tushe tace" 2 Cappuccino's please. Kallonta Neesah tayi tana cewa" Kodai zamu samesa ne? Bazai tsaya sauraren wannan ba namafi zatan Dad din nasa ya riga Abbi Isa office dinsa jiransa. Kasa cewa komai tayi Saida aka kawo Mata cappuccino din ta fara Sha ahankali kafin tace" Banajin komai sai bacin ran mahaifina, Zuwan dadyn Zaid zai fusata Abbi Kuma na fadawa Zaid kada yaje Amma Yana banza da zancen yakuma Dan akan Abbina bana daukan wannan so gwarama ya daina wannan saurin. Bari naji Inda yake saimu samesa" cewar Neesah tana fidda wayarta daga qaramar Louis Vuitton handbag dinta. Kinason Abbi ya daina kulani kwata kwata yayi fushi danine? Kinsan halinda mahaifina zai shiga kuwa idan yaji naje gidan namiji Gskia bazan iyaba, Bari anjima idan Bai kiraba na sake kiransa. Maida wayar Neesah tayi tana cewa" Amma dai bafa lallai yazoba Sai sungama magana da Abbin hakan Kuma shine qarshen Bata komai. A qasan maqoshi ta furta" Allah ma yasa Abbi ya gaji da wannan zaryan ya amince musu ayi auren yanzu sbd Gaskia Ina son Zaid dina sosai,I can't live without him, duk wannan fadan danake na qarfin haline Ina tsananin sonsa gaskia. ******** _AAM's BUILDINGs_ Zaune Yake kan sofa dake makeken office dinsa hankali kwance ya jingina bayansa kadan yana sauraren Former Ambi Mukhtar Asheer mahaifin Zaid. Gabaki daya idanuwansa dake Dan rikata wanda duk ya zubawa sbd kwarjini su ya zubawa Ambi din Yana kallonsa Yana saurare. Da gaskiyarsa ta hakika yake sake tsaro jawabansa Dan shawo kan A MAJEED din ya amince da auren 'yayan nasu a yanzu sbd kaucewa barna tunda yaran sun matsa sunason ayi. Amma abinda Bai saniba gameda A MAJEED shine wannan zuba Masa idon da yayi baida niyar daukan zancen ne. Qaramin numfashi ya sauke a natse kafin ya Dan dauke kallonsa daga Ambin ya dauki wayarsa dake gefensa ya ajiye gabansa cikin nutsuwa yakuma nagowa ya kallesa yace" Kaman yanda nafada last time dakuma farkon zuwanku neman auren maganar dai tana Nan a hakan, Hakuri zaa cigaba dayi inshallah babu wani abinda zai faru ko biyowa Baya dangane da wata barna ko makamancin hakan... Inayah dai tunda nace nabawa Zaid aurenta bazan fasaba kokuma sauyawa matuqar ba itace tace ta fasa Dinba kokuma wani dalilin dazai iya hanawar Kuma ba'a fatan hakan, Dan haka Ambi Ina sake baka hakuri kuci gaba da hakuri inshallah lokacin ya kusa sbd tana gab da kammala karatun tunda duka duka shekara dayane ya rage Mata inshallah... Amma tunda Kai kana hango wata barna da Zata iya biyo bayan rashin auren da wuri To inaga na dakatarda haduwarsu kawai su tsaya iya waya zuwa sbd kiyayewa sai a sanarda shi Zaid din Inayah Kuma zan fada Mata Daga yanzu haduwarsu iya wayane ya dakata da zuwa gurinta for now, Allah yayi Mana jagora duka. Sake da Baki Ambi yake kallon A MAJEED din Yana sauraron bayanansa dake fitowa suna zuwa Kai tsaye, Yasani yakuma ji wainda suka San A MAJEED din suna fadar Kai tsaye yake magana Baya wani kwana kwana ko lanqwasa Musamman zancen daya shafa 'yarsa dayake ganin baida abinda yafita. Jin shiru yasa Ambi ya rufe bakinsa tareda sauke numfashi Yana yaqen dole yace" Shikenan ba komai zamu cigaba da jiran tunda Shima akwai nasa programs din dazai kammala zuwa next year din sai abin yazo musu duk a natse ma, Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi. Amin" ya furta Yana kallon ruwa da aka kawowa Ambi din Bai Sha ba yace" Me zaa kawo maka? Any drink, coffee or something? No,no,no I don't think i need anything Thank you, Ruwan ma is okay. Daukan ruwan yayi yasha kadan tareda ajiyewa suka Dan fada wata firar daban wadda Bata shafi iyalansuba ta business industries ahakan har ya Dan ja lokaci sosai sai lokacin tashinsa suka fito tare ya maidasa har masaukinsa kafin ya wuce gida da driver dinsa. Da daddare zaid yazo masaukin dadynsa Dan jin yanda aka Kai qarshe Dan Shikam ma wlh yanzu yafara gundura da qaidan abbin Inayah Lokacinda dadyn Zaid ke yiwa Zaid bayanin komai Shima sai alokacin yake bayyana zallar bacin ransa da yanda A MAJEED din yaketa ja musu Rai akan 'yarsa saikace itace 'yar datafi kowa gata a duniya, Saikace shine kadai Mai arzikin dayake da 'ya. Cikin damuwa Zaid yace" Dad inason Inayah sosai Amma gskia bazan iya wannan hakurin ba, Is either ta dagawa babanta hankali akaina kokuma na barta sai ranarda Abbin nata ya tashi aurar da ita Amma gskia zan nema wata yanzu. Cikin takaici dadynsa yake kallon bakinsa dake magana yace" Bakada hankali ko? Kasan me ake nufi da auren connection kuwa? Duk da connecting naku akaiba kune kuka hadu da juna da kanku Amma wannan auren shine yanzu kowa keson ace 'yayansa sunyi wato auren arziki da samun connections. Duk tarin arzikinsa da uban dukiyar daya tara 'yarsa 'daya, Hakama Bayada Mata bare asaka ran zai Kuma haihuwar wasu 'yayan, Duka wannan arzikin da dukiyar 'yarsa yake tarawa Dan haka duk Wanda zai aureta shine Mai babban rabo tunda 'yar tasa mace ce wani abun dole saidai mijinta, Ahakan kake maganar ka nema wata ka bar Inayah din? Ka kuwa San waye A MAJEED da abin daya mallaka? Ka kuwa San tarin arzikin dayakedasu a Nigeria ma kawai? To idan kanka ya daina lissafi Bari na maka budaddiyar wasika, Idan ka rabu da Inayah wlh ka tabbatada wadda zaka kawo mahaifinta yafi A MAJEED Jan wuya, Dama ba sonta kakeba dakaketa ikirarin bazaka iya rayuwa babu ta ba,zaka mutu idan baka sametaba, Nonsense, Uban me kakesha da duk kabi ka dagawa mutane hankali akan son auren yanzu? Duk ma abinda kake biyewa su Sufian suna baka kanasha da kabi duk da rikice da Neman mace gwara ka daina Sha sbd Ni Future dinka tsayayya nake hango maka, Duk tarin nawa arzikin danakeda kaima kakesa nafison ka hada Dana uban matarka koina yazama kanada connections dinsa da tarin arziki So idan ma ki fita hankalinka better cm back to your damn senses Neman Mata ko buqatan mace bashine naka ba yanzu. Duk abinda dad din yafada Masa yasan hakan ne Amma dai gaskia shi yanzu mace yake buqata matuqa, Kuma kaman dai yanda dad yafada akan abinda yake ikirari kan son dayakewa Inayah gaskia ne haryanzu tsananin son Inayah na Nan daram a ransa saidai Shima tasa buqatar Gaskia ce Kuma tabbas wasu abubuwan sukesha taredasu Sufian. Dan haka zai sama Inayah suyi magana dole ita kadaice Zata iya saka Abbinta yabarsu suyi aure yanzu. Koda yakoma gida Bai kirata ranarba sai washe gari da safe. Tana ganin kiransa lokacin tana taredasu Abbi da umma kan dining Dan haka tsulum ta miqe tareda cewa ta koshi tabar dining din. Umma ce kawai tabi bayanta da kallo Shikuwa abincinsa yake cigaba daci hankali kwance bawai Kuma Dan Bai fahimta komaiba. Fada sosai tayi Masa a wayar Shima farko fadan yayi Mata kafin ya sauko Yana rarrashinta. Kashe wayarta tayi itama tareda jefarwa tana cewa" Saina Rama Nima kaji yanda naji. Bai sake kiraba kaman ita yanda tayita yi daya kashe Mata wayar Sai abin yamata ciwo itama ta sharesa badan tasoba. Sanin Inayah nayi Masa tsananin so yasa ya daga mata hankali kwana biyu da rashin Kira kafin Kuma daga baya qarshe Bai Ankara ba yafara mata yar barazanar auren wata kafin tagama nata karatun saiyayi ta biyu da ita. #MAMUH# #RIBA BIYU/MARRIAGE #A MAJEED/AYSHATOUH INAYAH/LOVE/ROMANCE *_FOR MORE PAGES KUYI FOLLOWING DINA A AREWABOOKS@Mamuhgee_* _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* _BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_ _4 BOOKS  4500_ _3 BOOKS : 3500_ _2 BOOKS : 2500_ _1 BOOK: 1500_ YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾 ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 SEKU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902 IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇 09134848107*_14_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Farko Inayah tayi mamaki sosai da maganganun Zaid din sbd Bata dauka Yana fada da gaske bane kawai dai yanason daga Mata hankaline sai kawai Bata dauki zancen da wani mahimmanciba tadaiyi mamakin Inda yasamu guts na iya fada Mata hakan. Shima Zaid din ganin ta watsar da maganar yasan Bata dauka maganan bane Dan haka ya tattara Shima ya watsar Yafara Dan kula tsohuwar budurwarsa data maqale tanason su dawo tare dama friend din Sufian ce. Tunda dad din yazo yasamu Abbi sukai magana da yanda sukai da me ake ciki babu abinda Abbi ya sanar masu daga ita har umma yaganah, Maganar dakatar da zuwan Zaid ma shine da kansa ya kirasa ya sanar Masa Dan haka Inayah Bata saniba Shikuwa Zaid din tuni hakan yasa ya sake watsar da zancen Inayah yanzu yakama Amal suka bude shafin soyayya duk da ba wani jinta yakeba Inayah ce kawai a ransa har koda yaushe. Illar Abokai masu aikita barna Dana Amal yasa tuni yafara samun cikakkiyar nutsuwar samun mace atareda Amal dan haka yanzu yasamu nutsuwa sosai hankali kwance yake jin dadinsa da Amal. Ahankali jin Dadi da samun cikakkiyar macen data iya biya Masa buqatarsa yasa ya daina kiran Inayah gabaki daya idanma ta Kira komai basayi yanzu sai hayaniyar fada sbd haryanzu fushi yakeyi akan yanda ta zabi hakura dashi har sai bayan shekara. Itama haushi takeji na yanda ya daina zuwa gurinta kwata kwata wayarma Neman gagarsu takeyi. Tun tana jin haushi hankalinta haryazo ya tashi sosai tafara shiga damuwa. Umma yaganah ma saida tashiga damuwar yanda Inayar kwana biyu ta daga hankalinta akan matsalarta da Zaid,ta kirasa da kanta Dan taji menene matsalar suketa fada yanzu koda yaushe Amma Bai dagaba Kuma daga baya Bai biyo kiranba Dan haka itama tasan da wuya idan ba babbar matsala bace gashi basuda ikon fadawa Abbi kokuma tambayarsa. Ahakan har sukai exams suka kammala suka samu qaramin break na sati biyu sbd daga wannan sai final exams Dinsu. Karatu takeyi sosai kaman zata rasa Zaid takeji idan Bata maida hankali sosai tayi karatun taci exams ta wuce gurinba, Har wata irin Rama ta ringa yi sbd tsananin karatu da Kuma matsalarta da Zaid sbd yanzu kam sosai tasan suna gab da rabuwa tunda sukanyi sati ma basuyi wayaba, Ta bangare daya Abbinta ya maida hankali sosai Shima akanta sbd ganin tayi karatu sosai duk da yasan kanta na ja sosai akan karatu Amma dai wannan kaman wani burinsa ne akan yarsa. Ta bangare daya Shima ramarta da damuwarta tafara sakashi damuwa Sam Baya buqatan abinda zai sakata muguwar damuwa irin hakan, Dan haka da kansa ya janye maganar Hana zuwan Zaid yabasa damar zuwa akai akai gurinta yanzu tunda ana gab da Gama karatun. Sosai Inayah taji dadin ganin Zaid ranarda yazo Dan dama sbd dokar abbin yasa ya janye kansa daga gareta dakuma Amal data Gama kamesa tako Ina yanzu. Ranar da farin ciki ta wuni Wanda yabawa Abbinta mamaki duk da yanzu bayajin Zaid din da yarsa sbd yana lure da kaman ya sauya sabon halaye, barinsa yayi kawai yaga yanda Al'amarin zai kasance. Yanzu hankalin Inayah ya kwanta tunda Zaid yadawo Mata yanda suke farko Amma har lokacin Batasan da wata Amal a rayuwarsa ba, Shima yanzu sosai yake jin Inayar tunda sun kusa dai cika sharuddan mahaifinta suyi auren Dan haka saiya fara tsananin kiyaye alaqarsa da Amal sbd koda tsautsayi bayason Inayah tasan da Amal bare mahaifinta dazai iya hadawa harshi hai dad dinsa yayi dealing Dinsu idan suka tarwatsa rayuwar 'yarsa. *****Maganar aure dole Abbinta ya aminta da ita aka tsaida lokacin auren wata biyar masu zuwa Wanda sukai daidai da kammala karatunta da wata daya kenan, Dan haka tuni aka fara shirye shiryen Auren ta bangaren mata kenan suda sukeda hidimar yi ta shagalin biki. Inayah tunda aka tsaida lokacin auren ta Zaid daga ita har Zaid din suke cikin wani irin tsananin farin ciki, Iyayensama kaman zasu janyo lokacin sukeje musamman dad dinsa, Umma yaganah ma kam fadar farin cikin datake kwana dashi tana tashi dashi bazai yiyuba, Babban burinta a dah shine ganin ranarda MAJEED zaiyi aure ya ajiye mace da sunan matarsa kafin Auren Inayah yazo daga baya saigashi na Inayah dinne a gaba duk da hakan tana farin ciki, Bare tunda auren Inayah Yana hanya Inshallah Shima nasa Yana hanya din. A Nigeria Abbinta keson sukoma ayi auren acan kafin sudawo daga baya, Aikuwa Murna kan Murna agurin Umma yaganah sbd tanason zuwa Nigeria dama sbd sada zumunta da jama'ar arziki da aka zazzauna tare acan baya. Neesah da Inayah duk da irin yanda suka maida hankali sosai akan karatun yanzu hakan Bai hanasu tsananin Shirin gaske ba akan yawon shoppings da gyaran jiki duk da Abbin baisan tana zuwaba tunda ya hanata zuwa spa's. Amal kuwa daga hankalinta tayi akan auren Zaid Dan haka tafara kokarin tona asirin alaqarta da Zaid gurin Inayah Amma tana shakka sosai na mahaifin Inayah sbd ita batama da kowa qasar karatu kawai takeyi da watsewarta Dan haka take shakkar taba Inayah,Amma badan mahaifin Inayar ba da tuni ta yaga Mata rigar mutunci tasa anyi Mata kaca kaca da ita. ****Saura wata daya sufara exams Neesah ta aje Inayah gida da mota ta nufo hanyar gidansu taci Karo da motar Zaid a gabanta tareda Amal zaune gaban motar suna wani irin tuqi a hankali. Sake kallon motar tayi da kyau ta tabbarda motar Zaid ce Kuma da mace aciki. Bata kawo tunanin komaiba tayi over taking dinsa ta wuce motarsa tana Masa horn alamar gaisuwa. Bai lura da motartaba sbd hankalinsa na kan Amal dake Masa wani shegen Wasa Yana dariya. Amal din taga Neesah Dan haka take sake Matsoda fuskarta tayi kissing bakinsa tana lasar kumatunsa. Wani shegen burki Neesah taja tana neman gefen hanya ta saukar da motarta sbd kokarin kufce Mata datake. Kutttt....."tafada cikeda mamaki da faduwar gaba sbd kasa yarda da abinda tagani, Zaid?da wata macen Kuma? Har suna irin haka? Anya kuwa Zaid ne? Zaid din Inayah da babu wata bayan Inayah agunsa. "Oh my God, this is unbelievable" tafada zufa na Dan karyo Mata na tashin hankali, "I can't tell this to Inayah, Bazata yardaba,Nima nakasa yarda da abinda nagani gskia. Sosai takejin firgici da tsoron abinda tagani din, Tun baayi aurenba Zaid ya iya cin amanan Inayah duk yanda take tsananin sonsa da kaunarsa, Tabawa rayuwar aure datakeson yi Amana da yarda da burirrika Tun yanzu hakan yafara faruwa to me Zata tadda idan taje gidan nasa? Inayah nada tsananin zafin kishi na gaske ga zuciyarta nada rauni wlh bazata iya daukan hakan ba, She is too weak to take this, Tayaya Zata iya daukan wannan? Daqyar Neesah ta iya tattara kanta ta tada motar ta nufi hanyar gida jikinta amace Dan Jin take Kamar itace akewa wannan cin amanar tunda aminiyarta akewa, Ta yanke shawarar bazata fadawa kowaba Amma Zata saka Ido sosai tasan Gaskiar Zaid din tun kafin ayi auren. Tun daga ranar Neesah tasaka ido sosai akan Zaid da Amal saigashi kuwa dai ta tabbatar da wata irin qazamar soyayya sukeyi Mai zurfi., Hankalinta ya tashi sosai saidai Kuma batason fadawa Inayah sbd ga karatu Mai nauyi agabansu ga tsoron halinda Zata shiga, Gashi Abbi ma ba abun wasaba bare ta fada Masa. Haka tanaji tana kallo Zaid nata yaudarar mata Inayah. Ana cikin hakan suka fara exams dole ta tattarasa ta watsar suka maida hankali akan karatunsu. Suna cikin exams Dr farhat taci gaba da Taya umma yaganah shirye shiryen biki da tafiyarsu Nigeria wadda zasuyi bayan Gama exams din Inayah. Ta dayan bangaren Zaid yakasa rabuwa da Amal duk da kwata kwata ko Rabin matsayi Inayah aransa Bata kaiba Amma sbd mumunar jarabta yakasa rabuwa da ita. ****Ranarda su Inayah suka kammala jarabawa kwana sukayi farin ciki itada Abbinta da umma yaganah. Kwana biyu tsakani suka wuce umrah, Sati biyu acan suka dawo aka fara shirye shiryen zuwansu Nigeria sbd Saura sati uku bikin. Koda suka dawo dayake tareda Neesah da Abbin da umma sukeje, Tanata kiran Zaid Bata samu gashi baisan sun isoba, Batada karyar dazataiwa Abbi ta fita ranar Dan haka tace itace Zata Kai Neesah gida. Kai tsaye yace umma yaganah ce Zata kaita gida sbd yiwa iyayenta godia. Bata damuba tace bakomai sbd tasan umma bazata hanata biyawa gidan Zaid dinba. Sai yamma suka fito shiye take cikin riga da wando na Nike black da sneakers farare ta saka face mask da hular rigar kayan sbd batason kowa ya ganeta lokacinda Zata shiga gidan Zaid Dan kada afadawa Abbinta da Kaman duk motsinta Yana sane dashi. Da farko umma yaganah qin yarda tayi abiya din suka ringa rokonta, Musamman Neesah datakeson abiya din ko Allah zaisa yau kowa yasan mummunan rayuwar dayakeyi tun baayi aurenba Allah yaraba Inayah da rayuwar damuwa. Cikin saa kuwa suna Isa motar Zaid na gida Dan haka Kai tsaye suka shiga itada Neesah Banda umma data zauna a mota. Door bell suka ringa dannawa babu Wanda yazo ya bude Dan haka Inayah datasan password din kofar ta saka kawai ta bude suka shiga. Da gudunta ta nufa kofar dakinsa tana Kiran sunansa. Bakin kofar dakin ta tsaya batareda tashigaba sbd sanin Bai kamata tafara Kiran sunansa ahankali cikin shagwaba da soyayya. Yana kitchen tareda Amal suna cin pizza dasukai order yagama ci yaje gidansu Inayah sbd yasan sun jima da isowa yanzu. Neesah ce ta ringa Jin dariyarsu ta nufa kofar ta leqa ahankali aikuwa tagansu suna cin pizza kowanne babu wani kayan kirki jikinsu sai wasanni sukeyi hannuwansa na cikin fingilalliyar rigar baccin jikinta dake nuni da tun safe suna daki suna Abu daya. Da sauri Neesah ta Isa kofar bedroom dinsa da Inayah take ta kamo hannunta tana cewa" Yana kitchen. Ha yar kitchen din suka nufa Inayah na Kiran sunansa da cewa" Baby, Baby where are you? Bab....... Cak ta tsaya kafin ta qarasa kitchen din ganin abinda takasa ganewa. Da gudu ta qaraso cikin gurin tana kallon yanda yake kokarin ture Amal daga jikinsa hankali tashe Yana cewa" Baby? Me kikeyi anan? Abbinki yasan kinzo kuwa? Bakya tsoron yasan kin zo? Amal ya kalla da sauri Yana cewa" Inayah ba abinda kike tunani bane ki..... Tsayawa gabansa Neesah tayi Rai abace tace" Karma kayi wahalar bayanin komai, Ni nasan wannan qazamar rayuwar da kakeyi bada sanin kowaba tuntuni yanzu Kuma Inayah tagani da idonta. Jan hannun Inayah tayi suka juya suka fice. Har mota Inayah kasa cewa komai tayi sbd cak kanta da tunaninta ya tsaya. Umma yaganah sai tambayar abinda yafaru takeyi sunqi cewa komai sai ajiyar zuciya da Inayah ke jerowa cikin fita hayyaci. Suna tsayuwa kofar gidansu Neesah Sai alokacin Inayah ta juyo ta kalli Neesah murya a sarke tace" Neesah Zaid nagani da mace right? Numfashi Neesah tasake tareda kallon umma data gwalo Ido ta gyada Kai. Wait wait wait, Ina nufin mace Naga zaid da ita cikin yanayi na aikata wani Abu fa? Kai tsaye tace" Yes Inayah zai kika gani Kuma ba qarya idonki yamikiba, Gskia ne,Kuma ba tun yanzu bane sun jima atare, Zaid ba yanda kikasansaba yake yanzu. Numfashinta taji Yana Neman hardewa Dan haka da sauri umma da itama tashiga shock ta fincike Mata mask din hancinta tana Kiran sunanta. ##MAMUH# #INAYAH #MAJEEDs LOVE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_15_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Cikin damuwa umma yaganah tace" Ga irinta Nan ai Nima Dana biyewa roqonku aka biyo din Kuma wlh sbd MAJEED yasan zaku biyo din yasa yace nice zan maida Neesan gida gashi nawa zuwanma baiyi amfanin abinda yaso yayi ba, Yanzu Ina amfanin wannan mugun ji da mugun ganin ana zaune kalau buki saura kwanaki, Innalillahi wainnan ilaihrrjiun. ACn motar suka qara umma na Kiran sunan Inayah cikin Dan sauti Mai tashi tace" Karki saka wannan aranki kijawa mahaifinki Inayah tunda zuwan qaddarane koma yayane, Kuma dai Ni nakasa yarda da abinda kuke cewan kungani,Zaid dinne Kuma yake Neman Mata? Kun kuwa tabbata? Idan har bawai kamasu kukayi tirmi da tabaryaba karku zartar da hukunci sbd ana maganar Zina ne anan fa.... Cikin wani irin tsananin fushi da kukan gaske da tunda take arayuwarta Bata taba yinsaba sai yau akan wani namiji Tace" Umma yaganah kiyi shiru kawai sbd bakisan abinda idanuwana suka ganiba, Wallahi tallahi tare yake da wannan dai dana gansu ayau nasan tare suke akwai abinda suke aikatawa, Hannunsa fa acikin rigarta Yana matsa nonuwarta Kuma...... A kidime umman ta katseta da cewa" Innalillahi Inayah banason ji daina fada, Kuma karma nakuma Jin wannan zancen banzan, kema daina fadan wannan maganar a bakinki batada dadin ji kadama koda tsautsayi mubari MAJEED yasan mun biya gidansa da wannan mugun labarin. Da zallar mamaki Neesah ke kallonta tace" Umma yaganah idan Abbi baijiba shiru zaayi Inayah ta aura mazinaci? Kinga Neesah ku Yara ne, Wannan bawai maganace da Kai tsaye zaa fito afada cewa zaid ga abinda yakeyiba sbd akwai maganar manya ta aure acikin lamarin Dan haka komai a sannu zaa bisa, Kuma idan ance arusa auren atake sbd haka shi Wanda Zata samu agaba ansan nasa boyayyan halin? Da yawa akwai mazinata a mazan aure Amma baka taba sani, Itama Dan Allah yayi Zata sanine kafin Auren, Idan anzauna an duba komai a tsare zaa iya samun mafitar komai a natse., Muje na rakaki ciki na gaisa da haj Salma da dadynki idan Yana gidan nazo mu wuce kafin qawarki ta some Mana anan asirinmu yagama tonuwa. Daqyar Inayah ta iya danne halinda take ciki suka shiga su dukansu aka ringa Murna da musu sannu da zuwa. Momyn Neesah murnar ganinsu takeyi sosai itada qanwarta dadyn Neesah din musamman ganin dattijuwa umma yaganah da kanta a gidan Dan kallon mahaifiyar MAJEED suke Mata. Angama gaishe gaishe da firar dawowarsu lafiya dama firar bikin Inayah dake gabansu Kuma yanzu, Sai kame kame umman da Neesah keyi sbd kowannensu har lokacin cikin shock din abinda yafaru suke da Inayah dasuketa Allah Allah agama atafi gida kafin ta ringa rusa musu kuka agurin Dan Zata iya gashi Allah yasa tasamu jarumtar dannewa din kada su momy sugane. Basu wani jimaba suka fito sbd cewar datayi kanta na ciwo su koma gida. Har mota dukkaninsu suka rakosu har momy. Shahada kawai umma yaganah tayi tabari Inayah taja motar suka nufo hanyar gida. Suna fitowa gidansu Neesah hawayen datake riqewa suka fara gangaro Mata zuciyarta na wani irin tafasa. Tunda take rayuwarta Bata taba Jin 'daci da qunci ba irin yau din, Dukkanin rayuwarta quncinta biyu ne zuwa uku, 'Bacin ran mahaifinta, Rashin uwa, Saikuma 'yar damuwar yau da gobe da bazaa rasaba Amma ita ko zafin rashi da talauci Bata saniba tunda koda mahaifinta yayi talauci da gwagwarmayar rayuwa batada wayo Tana qarama Kuma ko a wancan lokacin baitaba barinta ta nema Abu ta rasaba. Sbd tana tuqi yasa umma yaganah batai Mata maganaba Dan tasan tana buqatan kukan ko zataji sassauci shiyasa taja bakinta tayi shiru tana kallo Inayan na wani irin gudu dasu. Zuciyan Inayah wani 'daci da zafi take Mata Mai tsanani, Tayaya Zaid har zai iya taba jikin wata macen ba itaba? Tayaya zaid zai iya hakan? Tsigar jikintane yafara tashi sbd tsananin qyanqyami da baqin cikin abin, Meyasa bazai kasa hakurin sauran kwanakin daya rage aurensuba zaije ya iya hada jiki da wata, Harma ya iya hada shimfida da ita, Kuka sosai takeyi har suka Isa gidan, Parking din motar ma a juye tayisa ta fito tayi ciki da gudu tana share hawayenta Dan batasaniba ko Abbinta na gida. Dakinta ta nufa ta zauna kan sofa tana kokarin tsaida hawayenta da hannuwanta dake tawa., Umma yaganah ce tashigo dakin tareda rufe kofar jikinta a mace ta qaraso gurin Inayan ta zauna gefenta tareda diban tissue dake gaban mirror tafara sharewa Inayah hawayen cikin tsananin kulawa da nutsuwa Dan Inayah ta fahimta abinda Zata fada Mata din, "Inayah karki daga hankalinki kishiga tashin hankali akan wannan mugun tsautsayin, Kinga na farko mahaifinki shine babban fargabar yasan kinje gidan saurayi, Na biyu nima nasan ba qaramin qona ransa zanyiba idan yaji na biye Miki nabada damar zuwan gidan nasa, Hakama Kinga abinda kika gani bawai kinada tabbacin ya aikata wani mummunan abin bane duk da ba mutunci ko kamun kan dazaisa yakai mace gidansa harma ki samesu a ayanda Bai kamataba, Dan hakan kiyi hkr karki daga hankalinki da kaina Nima zan fadawa Abbinki idan har ta tabbata Zaid din yagama 'bata rayuwarsa da neme nemen matan banza, Sbd yanzu MAJEED najin wannan zancen kinsan kome zai faru bazai basu aurenba kuma so gwara afara tabbatarwa Kuma ko an tabbatar akwai tsautsayi akwai qaddara kilan sune suka ritsa dashi kawai bawai halinsa bane, Kinga idan yayi alqawarin gyarawa ai shikenan ba komai bane sai muyita adduar Allah yasa ya gane din ya daina. Kasa magana tayi sai kuka datake faman rusawa umman tana share Mata hawaye. Daqyar umma yaganah ta rarrasheta sukabar maganar akan Abbinta bazaijiba tukuna sai sun tabbarda abin bamai gyaruwa bane Dan kuwa Inayah tayi rantsuwar bazata auresaba matuqar tagane takuma tabbatarda Neman matan yake da gaske Kuma Yana kwanciya dasu sbd ta wani fannin ta gado halin mahaifinta sosai da sosai gurin tsananin qyanqyamin gaske shiyasa take ganin bazata iya hada miji da wata macenba. Kashe wayarta tayi sbd yanda Zaid din keta faman Kira Kuma batajin Zata iya daga wayarsa shiyasa ta kashe duk da Bata kashe wayarta duk tsanani sbd Abbinta kada yakira yaji kashe Sam ya hanata kashe waya bayan shi Yana shigowa gida yake kashe wayoyinsa sai Kuma idan zai fita kokuma ya saka silent sbd rashin son damuwa. Da daddare cikin qarfin hali umma yaganah ta sakata fitowa cin abinci suka Dan ringa kamewa sbd kada Abbin yagane. Kallo daya yayiwa Inayah lokacinda take qarasowa gurin cin abincin sanye cikin Riga da wandon Prada farare masu kauri sosai kaman na sanyi da qaramar hula gabaki daya saita fito kaman qaramar baby. Yanayin shigarta da fuskarta datake fresh ba komai da alama wanka tayi Kuma Bata shafa komaiba sai turarenta da qamshinsa ke tashi ahankali. Shine yafi kowa sanin Inayah sbd shine mahaifinta Dan haka fuskarta da yanayin shigarta ya bayyanar Masa da 'yarsa na cikin damuwa... Sake kallon yanayinta yayi yanda take cin abinci jikinta amatuqar sanyaye bakuma wai Dan tana jin yunwa ko dadin abincin ba, Cusawa kawai takeyi. Gun umma yaganah ya 'dan maida kallonsa yaga yanda ita Kuma take Dan hada kokarin share guminta akai akai duk da tsananin sanyin Aircon da babu Inda babusa a cikin gidan... Maida kallonsa yayi a natse kan Inayah da hankalinta Baya kan kowa saina abincin datake ci Shima bawai hankalinta na kan abincin bane. Jin yayi kwata kwata abincin dayake gabansa fita ransa sbd yasan akwai abinda suke boye Masa Dan daga umma yaganah har Inayar babu Wanda Bai San halayensa ciki da wajeba,hakama kallo daya yake musu kowannensu ya gane halinda suke ciki sbd Sam Baya Wasa da kulawa dakuma tarbiyar gidansa Wanda umma yaganah ta jima da Zama cikin ahalinsa Dan haka itama duk da tana matsayin uwa shine Mai lurarda ita lokuta da dama. Ruwan sanyi da aka Dan zubawa lemon ya dauka ahankali yakai bakinsa yasha tareda ajiyewa ya dauki tissue ya goge bakinsa ya miqe yabar dining din. Daga umma yaganah har Inayah babu Wanda yayi Magana daya miqe din sbd hankalinsu Baya Kai Kuma hakan yasake tabbatar Masa da zarginsa akansu na akwai abinda suke boyewa basason ya sanin Dan Bai taba miqewa daga dining batareda dayansu ya ringa maimaita Masa ko ya qoshi da abincinba Dan sun San rashin zamansa yasa Baya wani samun damar cin abinci yanda ya kamata shiyasa daya miqe zasu fara tambayar ya koshi kokuwa ya zauna yaqara ci. Yana barin dining din Umma yaganah ta kalli Inayah cikin qosawa tace" Inayah kinason sakawa Abbinki tunanin akwai wata matsalar ne? Ba nace Miki da kaina zan sanar Masa ba idan aka bada lokaci akasan Gaskiar lamarin¿ Kallon umman tayi tana jin damuwa sosai, Ita sbd batada uwa batama San uwartaba shiyasa Abbinta takejin idan Abu ya sameta Bata sanar masaba kaman zuciyarta Zata buga. Ahankali ta gyada Kai tana cewa" Abbi fa kinsani kwana biyu cikakki bazamuyiba muna wannan boyon zai gano mu. "Nasani shiyasa nakeson kiyi kokarin cire damuwar komai aranki. Bata iya cewa komaiba ta miqe tana daukan tissue tace" Zan kwanta da wuri umma, Goodnight. Daqyar ta iya tattara kanta ta nutsu yanda Abbinta bazai gano kamaiba ta qarasa palonsa cikin sanyi da shagwaba ta nuna Masa bacci takeji Zata kwanta da wuri tai Masa goodnight Shima ta fice. Bai bi bayanta da kalloba sbd Baya buqatan qari fahimta yasan for sure akwai wani abu, Idan irin hakan tafaru bayace musu komai sharesu yake sbd cikin kwana biyu yasan zai Gama sanin meke faruwa. Tana barin palon Abbi taji idanuwanta na cikowa da hawayen rashin sanar dashi damuwarta sbd Abbinta shine maganin kowacce damuwarta Wanda Allah ne ya tsaya musu duka akan hakan. #MAMUH# #LOVE# #MARRIAGE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*16* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Tana Isa bedroom dinta ta kwanta ko kallon Inda wayarta take bataiba. Bata wani qin samun bacci ba, Sosai tayi bacci kaman yanda ta saba saidai tana farkawa damuwar dake dabaibaye cikin ranta ta dawo Mata sabuwa fil harma wani 'dacin maqoshi takeji sbd tsananin damuwa da fargabar abinda zaije yadawo, Tanajin wani irin tsananin bacin Rai da zafin abinda Zaid din yayi Mata da har takejin bazata taba iya mantawaba Amma ta wani bangaren tana cikin tsananin fargaba da tsoron rasashi sbd girman son datake Masa. Tayi lattin sallah Dan haka alwala tafara yowa tazo tayi sallar asuba tukuna tayi adhkar. Tana gamawa ta koma kan gadonta tashige bargo tana son komawa bacci. Rufe idanuwanta tayi tana sake gyara kwanciyarta Amma takasa Jin dadin kwanciyar, Sake juyawa tayi dayan banagren tana Dan yamutsa fuska cikin yanayi na qosawa. Jin duk batajin dadin kwanciyar yasata yaye bargon datake rufe dashi tareda tashi zaune ta kalli wayarta dake kan bedside, takuma dauke Kai tana Dan sake yamutsa fuska. Mintuna biyu ahakan kafin ta qarasa yaye bargon tayi gefe dashi tareda ziro qafafuwanta qasa tana daukar wayarta ta kunna ko duba wayar bataiba daga kunnawan darai ta ajiyeta Nan Inda ta dauka ta miqe tsaye tareda nufar Inda tarin jerin takalmanta suke jere Kaya guda,kusan babu designer shoe brand dinda batada masu zallar tsada. Time ta kalla taga yanzuma 6:30 tayi Dan haka tasan har yanxu dadynta Yana geam, Riga da wandon Nike ta saka black da Triple S Balenciaga sneakers farare ta fito ta nufi gym Dinsu dake gidan Wanda saika ratsa palon daya raba palonsu Dana Abbinta zaka Isa watadaccen gym din Mai girma da tsari. Tana Isa knocking daya tayi ta tura kofar da kusan tafi karfinta sbd qarfin kifar tashiga tana gyara qaramar Vandanar dake kanta. Sanye yake da black Lululemon wears na exercise, Bench press yakeyi da nannauyan qarfe a hannayensa Yana dagawa da dawowa, Shigowarta baisa ya dakataba Kuma Bai waiwayo ya kalli Wanda ta shigoba Dan yasan babu Mai shigowa Nan din kaf idan ba 'yarsaba., Cikin kauna da kulawa ta qaraso gurinsa tana cewa" Good morning Abbi" A natse ya qarasa abinda yakeyi ya ajiye qarfen tareda tashi zaune wasu qananun zufa abinda ya Gama suna gangara kan lafiyayyar fresh fatarsa ya kalleta lokacinda take daukan ruwa tana basa takuma cewa" Abbi ka tashi lfy? Idonta yafara kalla baiga alamar rashin bacci atareda itaba Dan haka Kai tsaye cikin nutsuwa da kulawa yace" Morning Inayah, Lfy kalau alhmdllh, Me zakiyi da gymin yanzu? kinason ki rage keda kike amarya? Ko Kin manta kin daina zumudin auren ne tun yanzu?" ya qarasa cikin yanayi na Wasa da 'yar tasa tilo. 'yar qaramar dariya tayi tana hawa kan leg press machine tafara ahankali tana cewa" Abbi naji banason auren Kuma yanzu Banason tafiya nabar gida, Abbi kullum zanyi missing naka, Gskia Zaid zai ajeni a Inda zanna ganinka. Murmushi kawai yasake ahankali Yana goge qananun zufansa da wata farar towel qarama yace" Zaki Saba ahankali musamman idan kika Zama uwa, And kafin can ma you will be busy with your work bazaki samu lokacin tunanin kewan gidaba. Abbi duk da hakan nasan kullum sainayi kewanka,Dan Allah Abbi kace musu anan zasu ajiyeni. Girgiza Mata Kai yayi Yana murmushin wautarta da har take cewa ta girma yanzu idan Yana Mata fadan wani abun, Haryanzu jinjira ce shi agabansa Dan ko wannan auren Dan kawai ta nace tanaso ne yanzu yasa zaiyi Mata Amma tabbas da saita sake wayo da girma sosai Aqalla saita fara aiki tasan ciwon kanta Dana rayuwama Dan kuwa haryanzu Batasan komai na rayuwaba, Babu abinda tasani daga mahaifinta sai mahaifinta tukuna sauran abubuwan. Tare suka qarasa gymin din suka fito itace mai surutu Yana saurarenta hankali kwance daga shi har ita skin Dinsu glowing kawai suke gasa ta tsantsar hutu da wadata kasancewar shi rigarsa armless sai dogon wando, Itama rigarta qaramin hannu me da ita sai dogon wando. Kowannensu hanyar dakinsa ya nufa, Wanka tafara tubewa tayo ta fito kenan wayarta tahau ringing ta qarasa tana dubawa taga Zaid ne. Wani zafin gaske ne ya taso Mata daga qasan zuciya, Duk lokacinda sunan zaid ya fado ranta Jin take tamkar Zata Kama da wuta sbd tsananin zafin kishi da baqin ciki. Jefar da wayar tayi tareda nufar gaban madubu tafara shiryawarta. Oil ta shafa tareda moisturizer kadan ta fesa su spray da body mist dinta ta nufi closet. Sai after 9 tafito sanye cikin fitted long sleeve gown kalar blue sai qaramar scarf nade akanta. Dakin umma yaganah take kokarin Isa Amma taji kaman muryan Abbinta a dining room Yana waya Dan haka ta juya ta nufi dining din. Shi da umma yaganah ne zaune Dan haka itama ta qaraso tana cewa" Tun yanzu anfara ware ni a gidan Nan. Umma yaganah ce tayi Yar dariyar Jin Dadi ganin Inayar ta sake Dama Allah Allah take MAJEED yafita gidan kafin ya dagosu su samu sugani idan zasu iya kashe zancen iya tsakaninsu. Ita harga Allah babbar damuwarta irin fushi Mai tsanani da MAJEED din zaiyi idan yaji 'yarsa da duk arzikinsa da zamansa busy Bai hanasa tsayawa yana ture komaiba Dan ginarda tarbiyarta tun tana jinjira har zuwa yanzu yaji sunje gidan saurayi tasan wlh ranar ransa qarshen bacin Rai zaije, Hakama Kuma qarin abin bacin ran da baqin cikin yaji Inayar da bakinta tana fadar hannun Zaid acikin riga Yana latsa nonuwan wata,su kansu sun San ranar sai yanda Allah dai yayi dasu daga ita umman har Inayar. Ata wani bangaren tasan Sarai Inayah Zata iya fadar hakan gaban Abbin nata. Dan hakan yanzu ba qaramin farin cikin ganin Inayah ta sakeba tayi har Saida kusan Abbin yagane Amma dai baice komaiba har lokacin. Breakfast sukai suka Gama ya fice zuwa aikinsa. Yana fita Inayah ta tattaro bacin ran da baqin cikin dataketa dawainiyar boyewa cikin ranta kaman zai kasheta. Bata wani tsaya dogon zanceba tacewa umma yaganah Zata gidansu Neesah tadawo Dan tanason Jin komai dalla dalla daga gareta idan ba hakanba zuciyarta tashiga tunani kala kala da zasu iya hallakata. Sanin irin tsananin zafin kishi da Allah yayiwa Inayah yasa umma yaganah barinta zuwa gidansu Neesah din. Tana barin gida batabi ta hanyar da saita bi ta anguwarsu Zaid kafin ta Isa gidansu Neesah ba Dan Bata buqatan ganin gidan ko kadan, Jin take ta tsana gidan da anguwar gabaki daya. Tana Isa gidansu Neesah itama Neesar na kokarin fitowa da motarta Zata gurin Inayah din. Komawa ciki Neesah tayi da tata motar INAYAH taqarasa shigowa da tata motar sukai parking tare suka fito kusan lokaci daya. Kallonta Neesah keyi lokacinda ta fito mota fuskarta duk babu walwala. Cikin kulawa tace" Hey babes, Yaya? Are you okay? Wani kallo Inayah tai Mata tana qarasa Kama hannunta data miqo Mata tana cewa" Nai Miki Kama da wadda take okay? Kina tunanin zan Zama daidai bayan abinda idona ya ganarmin jiyan? Ciki suka qarasa suna magana ahankali sbd rashin walwalar Inayah. Momy na gurin dadyn Neesah Dan hakan Kai tsaye dakin Neesah suka wucewarsu. Zama sukai Inayah na wurgi da handbag dinta da car key dinta ta kalli Neesah dake miqo Mata bowl din Candies tace" are you for real? Me zanyi da candies bayan 'dacin da zuciyata take ciki. Ajiyar zuciya Neesah tayi tana Zama cikin sautin Mai mahimmanci tace" Maganar 'dacin Rai ko baqin ciki bashine abinda yakamata ki fuskantaba, Zaid dai wallahi Neman mata yake, Nasha ganinsa da Amal a yanayi marasa kyan gani, Nayi bibiyarsa Dan tabbatarwa Kuma na tabbatar Dan haka bawai maganar kishi ake ananba Maganace ta ki nutsu kisan wanda Zaki aura da halayensa, Bansan yaushe ya sauya yakoma hakan ba Amma a zahirance ya dade a wannan rayuwar da Amal Dan hakan maganar sauyawarsa lokaci daya zaiyi wuya.... Kasa magana Inayah tayi ta zubawa Neesah idanuwanta dasukai jajir sbd tsananin baqin ciki da zafin zuciya. Cikin takaici da masifa tace" Shine Baki taba fadanba? Da banganiba da kaina ahakan Zaki Bari ayi auren nagama haukacewa a sonsa shikuma Yana can Yana kwanciya da wata macen? Cikin damuwa Neesah tace" Inayah Kona fada ba ganewa zakiyiba sbd idonki ya rufe akan Zaid, Tayaya Kai tsaye zance Miki Zaid is sleeping with another woman? Zaki yarda ne idan nafada? Kalman "sleeping with another woman" shine yafi komai gigita dukkaninta Dan hakan Batasan lokacinda hawayen baqin ciki Mai qarfi suka fara gangaro mataba. Sanyi jikin Neesah yayi ta matso kusada ita cikin tausasa murya tace" Inayah wannan shine Namiji, Duka wannan kadan ne idan baka nutsu kasamu mijin dakakeson more rayuwan aure dashi, Inason aure nima kinsani sosai Amma Kuma bazan iya auren Wanda nakewa so irin hakan dakikewa Zaid ba sbd disappointments na cikin irin wannan son.. Gudu hawayenta suka qara sbd ba itace ta sawa kanta son Zaid ba Allah ne ya jarabceta da irin wannan son datake Masa, Uwa uba ga zafin kishi datakeji Kamar ta hadiye zuciyarta ta mutu. Rarrashinta Neesah tafara yi Amma Sam takasa Jin sassauci Dan hakan ta miqe tareda daukan Jakarta da key dinta tana nufar kofa. Binta Neesah tayi tana cewa" Babes Ina Zaki? Cikin qunci tace" Zanje naji daga bakinsa meyesa zaimun hakan. No Inayah please karki Kuma zuwa gidansa sbd kada komai ya qarasa lalacewa, Qazantar da baka ganiba tsaftane. Bata sauraretaba tayi gaba tana cewa" Idan bazakiba please kibarshi a iya. Bazan iya Bari kije ke kadaiba Kuma ai dole zanbiki, Bani key din I will drive. Miqa Mata key din tayi tareda budewa ta shiga kafin Neesah din tashiga mazaunin driver ta tada motar suka fice daga gidan. Tafiya suke zuwa gidan Amma babu wadda zuciyarta Bata bugawa acikinsu, Neesah tasan tabbas sai sun samu Amal a gidan., INAYAH Kuma fargaba da shakkar samun mace take agidan tareda zaid sbd wannan karon bazata iya daurewaba komai zai iya faruwa Dan kuwa zuciyarta Zata iya bugawa. Kuma ganin Zaid da wata tamkar qarasa buga zuciyarta ne zatai. A slow Neesah ke tafiyar itama tanata adduar Allah yasa kada su tadda Zaid a gidanma gabaki daya bare wata Amal. #MAMUH# #AA MAJEED #AYSHATOUH INAYAH #MARRIAGE #LOVE/ROMANCE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_17_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Suna Isa kofar gidan dake cikin jerin irin tsarin gine ginen turawa da basada gate sai harabar gida. Parking Neesah tayi tana kallon motar Zaid data tabbatar da Yana gidan, Kallon Inayah da idanuwanta sukai jajir tayi duk saitaji ranta yasake dugunzuma itama, Allah yasani tafi kowa sanin irin son da Inayah kewa Zaid tunda itace aminiyarta, Mahaifinta yasan tana son Zaid shiyasa dole shima yake kaunar Zaid Hakan yasa duk suma suke kaunar zaid sbd Inayah na sonsa. Wannan abin dayayiwa Inayah yasa taji duk ya fita ranta, Takuma San tata tsanar Mai saukice akan wadda mahaifin Inayah zai Masa duk ranarda yasan abinda yayiwa 'yarsa. Motar INAYAH ta bude Kai tsaye tareda nufar hanyar kofar gidan Neesah ta fito da sauri tabi bayanta tana cewa" Inayah give him a call atleast yasan da zuwanki, Banason asake samun....... Maganarsu ce ta katse daidai bude kofar da Zaid yayi zai fito Amal na bayansa riqeda hannunsa tana Masa magana Kamar wata karuwa. Ba zato ba tsammani yagansu kofar, Qwace hannunsa yayi da sauri daga na Amal Yana kallon Inayah dake kallonsa cikin Ido da jajayen idanuwanta. Matsowa yayi gabanta zaiyi magana ta girgiza Masa Kai idanuwanta na kasa riqe Mata hawayen dataketa kokarin riqewa. Cikin yanayi na tausasa harshe da damuwa yace" Baby babu wani abinda yake faruwa anan, She's just a friend..... Cikin baqin cikin abinda yafada Amal ta matso gaban Inayah tana kallon kyakkyawar fuskarta datai jajir tace" Banajin fa tana fahimtar abinda kake fada besides inaga ba illa bane idan friends sunje gidan juna hakama ke da qawarki ke kwana gidanku ya damu daya tambaya abinda ke tsakaninku ne...... Wani mahaukacin Mari Inayah ta saukewa Amal sbd baqin cikin abinda take nufin fada akanta da Neesah, Sai alokacin ta juyo ta kalleta cikeda tsana tace" Banajin nayi magana dake bare kiban amsa. Kan Zaid din ta maida kallonta a tsananin qyamace take kallonsa zuciyarta na tafasa da wani irin baqin ciki tace" Me take dashi daka zabi rayuwar shashanci da ita akaina? Tafini kyau ne kokuwa? Ita wacece? Daga Ina ta fito? Ina Zata? Kudi tafimu ne? Cikin Dan daga murya Zaid din ya katseta da cewa" Inayah please duk ba wannan bane, Qaddara ce... Ahankali ta iya bude Baki ta furta" Neesah muje. Juyawa tayi ta wuce tabar gurin ko ganin gabanta batayi sosai. Amal dataga ba'ayi balai da masifar dataso ayiba ta tafi da sauri Tasha gaban Inayah tana cewa" Idan na fahimci maganarki ta qarshe da kyau kina nufin son kudi yasa Zaid da iyayensa suke son aurenki?? Kina tunanin mahaifinki fin nasa mahaifin yayi kome? A wulaqance da zafin kishi da baqin ciki tace" Mahaifina ba abun wasar dazaki iya hadawa da tarkacen haukarki bane so better watch out you bitch.... Da mamaki Zaid ya katseta da cewa" Kece Zaki San abinda zakina fada Inayah sbd Alan haukar kishi ko zafin kanki karki zaga nawa mahaifin.. Murmushin Jin Dadi Amal tayi sbd dama tasan babu Wanda zai dauka zancen banza akan mahaifinsa Musamman Inayah dako Wasa ba'ayi da sunan mahaifinta Dan kuwa Bata dauka ko kadan. Tsoki Mai zafi Inayah tasake batareda tasan ta sakeba zuciyarta na tsananta kuna tace" Ba karuwarka kadaiba ko Kai na haramtawa fadar sunan mahaifina a bakinka bare hadasa da kowa. Juyawa tayi a zafafe tabar gurin tareda nufar mota. Neesah ce ta iya tsayawa qarasa musu da cewa" Zaka iya jawa budurwarka kunnen daina shiga abinda Babu ruwanta. Juyawa tayi itama tabi bayan Inayah dake Jan numfashi cikin mawuyacin hali tamkar Mai Asthma. Da sauri ta tada motar ta nufi hanyar gidansu Inayah din tana adduar kada su sama Abbi a gida. Suna Isa gida umma yaganah na ganinsu tasan ankuma kenan. Dakin umman suka kwantar da ita suna faman kwantar Mata da hankali da kokarin ganin tadawo daidai. Wata irin weak heart gareta da bakomai take iya dauka ba na tashin hankali ko quncin shiyasa tunda take duniya mahaifinta AA MAJEED Bai taba Wasa da duk abinda ya shafi 'yar tasaba, Duk wani gata da walwalar rayuwa ya wadata Yar yasa dashi, Sbd ita yayi gwagwarmaya da Fadi tashin rayuwa ba dare ba Rana Saida Allah yabasa arziki Duk sbd wadatar da 'yartasane gashi lokaci 'daya wani qaton gardin banza zai lalata Masa rayuwar 'ya. Daqyar suka samu ta iya dawowa daidai tayi shiru daga kwance hawayen baqin ciki na gangara daga idonta suna jiqa pillon datake kwance akai. Tunda suka dawo Bata iya fadar kalma ko dayaba sai hawayen baqin cikin datake zubdawa zuciyarta na quntatuwa da rashin Zaid da zatai ta bangare daya Kuma gabaki daya neman fita ranta yakeyi sbd Sam lokaci daya take tsanar duk Wanda ya nuna rashin girmamawa ga mahaifinta. Har Neesah ta wuce gida Inayah taqi cewa komai saidai kukanma ta daina saidai dukkanin fuskarta ta Gama yin ja da kumburar data bayyanarda zallar kukan datasha. Bayan tafiyar Neesah umma yaganah tasata taje tayi wanka da sallah tayi kwanciyarta daki abincima taqi ci tace Bata buqatan komai. Har dare Inayah din Bata fitoba har Abbinta yadawo baisan abinda yake faruwaba dayake latti yadawo gidan Dan hakan yasan sun Riga sunci abincinsu sun kwanta. A cikin daren daqyar Inayah ta iya bacci sbd tsananin ciwon Kai na kuka da damuwar data cikata. Gari na wayewa har 10 Abbin baigantaba Kuma baiga kirantaba Dan hakan Kai tsaye ya daga waya ya Kira wayarta amma yaji akashe. Da Dan mamaki ya kalli wayar tareda ajiyewa ya miqe tsaye Kai Tsaye ya nufi hanyar bedroom dinta. A hanya ya hadu da umma yaganah zubbi na biyeda ita da tray a hannu jere da breakfast zaa kaiwa Inayah din. Da mamaki ya kalli umman Yana sake maida kallonsa kan abincin da zaa kaiwa Inayar harda maganin da tunda safe umma yaganah tasa Dr farhat takawowa Inayah din Dan basuso ya sani. A natse ya bude Baki yace" Meyake faruwa anan? Inayahn batada lafiya ne? Meya sameta? Ajiyar zuciya umman tasake sbd tasan yanzu kam Babu wani sauran boye boye Dan dama ciwon Inayah mahaifin natane yasan yanda yakeyi da ita Tasha magani. Jiki amace tace" Ciwon Kai ne taketa fama dashi Mai Dan tsanani, Dr farhat takawo wannan maganin abata. Manyan fararen idanuwansa ya zubawa umman batareda zallar mamakin dake ransa ya bayyanaba ko kadan sbd qwarewarsa gurin riqe emotions. Kai tsaye dakin ya bude yashiga da nutsatsiyar sallama. Jin muryar Abbinta yasata bude idanuwanta ahankali ta kallesa tanajin wata sabuwar karyewar zuciya da kuka na zuwar Mata. Fuskarta da idanuwanta ya kalla take yasan Bata rintsaba kuka tayi Wanda Bai taba barin tayiba shida yake ubanta, Uban waye yasaka 'yarsa a wannan halin ya furta a zuciyarsa data dauki 'daci da mamaki. Maida kallonsa yayi kan umma data sake shiga kame kamen Inda Zata fara bayani. Gurin Inayar ya qarasa ya tsaya akanta Yana sake kallon yanda fuskarta ta kumbura. Zama yayi bakin gadon tun kafin yace wani Abu ta fashe da kuka tana cewa" Abbi zaid yaci Amanata.... Ahankali yasake ajiyar zuciya sbd yasan zaa Rina ganin yanda Inayah take tsananin sonsa tun farko. Ahankali ya Kai hannu ya zari tissue dake gefen gadon yafara share Mata wahaye Yana sake sakin ajiyar zuciya kafin ya kalleta cikin kulawa da kwantar Mata da hankali yace" Ya Isa haka, Tashi ki wanke fuskarki kizo kici abinci da magani zamuyi maganar daga baya. Bata musawa Abbinta Dan hakan ta miqe tsaye sanyeda Riga da wandon bacci masu santsi ta nufi toilet. Sunanan zaune duka ta fito ta zauna gefen abbin Ta karba abincin tafara da tea Mai zafi da umma yaganah ta dafa Mata da kanta. Tana cikin cin abincin aka Kira wayarsa yamiqe ya fice daga dakin yabarsu. Kallonta umma yaganah tayi tana cewa" Inaga Inayah ki hakura da Zaid tunda dai da alama na Jin nasiha ko magana zaiyiba, Nifa da kaina tun ranarda abin Nan yafaru kullum saina kirasa na Masa nasihu da nuni kan hanya Mai kyau Amma shine Dan baida niyar daidaituwa kullum Ina Masa nasiha yanacan Yana cigaba da aikata alfasharsa, Tsakani da Allah da saninka dai auren mazinaci baida wata riba ko kwanciyar hankali, Tunda baijiba Kuma baida niyar dainawa ki hakura ki cirewa zuciyarki ki dangana Allah yakawo Miki wani mijin Wanda yafisa kyawawan halaye.. Qala Inayah Bata iya cewaba saima danne 'dacin dayake taso Mata takeyi tana jinjina kanta. Duk abinda umma yaganah ta fada akan kunnuwansa Dan hakan take ya dauki hannun abinda yake faruwa. Fasa juyowa yayi ya juya ya komawarsa. Gabaki daya wunin qin Kunna wayarta tayi sbd ko sunan Kiran Zaid Bata qaunar yi akan wayarta, Tabbas tasan yanzu kam Abbinta dole zaisan komai Kuma hakan na nufin aurenta da Zaid ya Gama wargajewa Dan hakan zuciyarta tagama raunana, Wuni tayi tana danne hawaye da baqin ciki. Haka takuma kwana batareda Zaid ya biyota bada hakuri ba hakama koda ta kunna wayarta bataga kiransa ba Dan hakan taqara himmar kokarin fiddasa cikin ranta. Ga Abbinta shima baice musu komaiba sai umma yaganah dayayi magana da ita ta zayyane Masa komai da komawarda Inayah takuma Yi gidansa. Kwana biyu shiru ba Zaid ba wayarsa hakama Abbinta baice Mata komaiba duk saitabi taqarasa shiga wani hali. Ta bangare daya basu daina shirye shiryen tafiya Nigeria ba Dan hakan takejin ko maganar aurenta da Zaid din tana Nan shiyasa wani bangaren takejin kaman zasu shirya komai ya wuce,taqi fidda rai. *_Arewabooks for more pages_* https://arewa-one.vercel.app/chapter?id=634d93b4bf002b318122db87 ##MAMUH# #LOVE/AYSHATOUH INAYAH #ROMANCE/AA MAJEED _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_18_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Washe gari da safe tana zaune dakinta tana waya da Dr farhat kan itama Nigeria zataje saiga zubbi da soqo. Sai data kammala wayar ta kalla zubbin tana cewa" Yes zubbi? Am Mr Zaid ne yazo Yana guestroom Yana buqatan ganinki. Kallon bakin zubbin daya isar da sakon takuma Yi kafin ta Dan jinjina Kai ahankali tace" Ok am coming. Juyawa zubbin tayi ta fice tana cewa" Ok Ma. Zubbi na fita ta rintse idanuwanta tanajin yanayinta na sauyawa zuwa damuwar abinda yakawo Zaid din Kuma. Bude idanuwan tayi tareda miqewa tsaye ta nufi gaban mirror takuma kallon kanta. White Alexandra chiffon top ce ajikinta Mai tsada sai sky blue Levi's ripped jeans, Kanta qaramin farin silky scarf ne a daure, Ko turare Bata buqatan qarawa sbd Qamshin dake tashi jikinta ahankali already Dan haka juyawa kawai tayi ta fice daga dakin ta nufi hanyar palon tana jin gabanta na faduwa kaman yaune ranar farko da Zata fara haduwa da Zaid din. Tun kafin ta Isa take Jin muryarsa qasa qasa Yana waya Dan haka saita dakata Jin abinda yake fada a wayar.. "Nafada Miki karki Kira idan nafita daganan din zan kiraki, Meyesa bakya ganewa ne Amal? Abbinta ne Allah kadai yasan abinda yayiwa dad dina da duk yabi ya rude yasani zuwa Bata hakuri dole, Nafada Miki zan kiraki idan nafita Dan haka banason damuwa, Karki qaramun pressure akan Wanda Abbin Inayah ya dorawa dad shikuma ya Dora mun okay?? Kashe wayar yayi Yana sakin qaramin tsoki Dan Amal dinma gabaki daya tagama fita ransa Dan kuwa tsakanin jiya zuwa yau dad dinsa duk yabi yagama haukace Masa akan abinda yayiwa Inayah, Shi kansa yasan Yana Sonta Amma Kuma bayajin zai Dora soyayyar Tasu akan burika ko ra'ayin iyayensu Wanda ita Kuma gareta da mahaifinta ganin sukeyi komai suke zasu iya samunsa sbd dukiya kokuma wani ikon dasuke gani. Bata taba Jin Zaid yafita ranta kwata kwata ba sai yanzu din dataji irin fassarar daya yiwa mahaifinta da ita, Wani sanyayyan numfashi ta sauke ahankali tareda qarasowa cikin palon batareda ta iya kallon fuskarsaba Dan Zata iya Masa tsana Mai girma. Kan Luxury sofa dake gefe ta zauna tana ajiye wayarta gefenta ta waiwayo ta kallesa Kai tsaye tace" Yes?gani ance kanason ganina? Zuba Mata idanuwa yayi yanajin Sonta na qara Masa yawa Amma Kuma yanda mahaifinta yayi amfani da dama ya rikita nasa mahaifin akanta yasa yaji son nata na komawa fushi Dan haka shima ya Dan kame fuska sosai zaiyi magana ta katsesa da cewa" Please Zaid idan hakuri zaka bani banajin akwai buqatan hakan sbd na Riga na yarda da matar mutum kabarinsa ne so ba buqatan mu..... Inayah kina tunanin ahakan zamuyi auren duk abinda ya hadamu Zaki kwasa ki fadawa mahaifinki shikuma Yana yiwa nawa mahaifin barazana kokuma nuna iko akan wani abin? Kina tunanin abinda kike samu koyaushe da kina gidanku shi Zaki samu a rayuwar aure? Look bazan yarda Kuma bazan dauka ba rashin girmamawa ga iyayena da mahaifinki keyi sbd koba komai nawa iyayen sun girma naki mahaifin ko yayane..... Miqewa tsaye tayi tana kallonsa da mamaki akan fuskarta tace" Zaid Dan Allah katafi bana buqatan ganinka, Kaje kaji da kunyar dayake dawainiya dakai na abinda kamun.... Nace Miki inajin kunyar abinda nayi ne? Kinga alaman kunyar hakan ataredani ne? Sbd me zanji kunya? Sbd Ina tareda wadda tasan damuwana shine zanji kunyarki? Nayi tunanin kece wadda yakamata tafara duba yanayin Dana shiga tun wancan lokacin Amma kika nunan Sam bazaki iya take doka ko sharadin Abbinki ba, You can't do sex before marriage, You can't do this sbd Abbi, You can't do that sbd Abbi, You can't,you can't, you can't,duk sbd Abbinki, Abbinki Annabi ne shi da bazaa..... Wani wawan Marin da batasan yaushe tasamu qarfin yinsaba ta sauke Masa tana Masa kallon zallar tsana Bata iya furta komaiba sai" I hate you Zaid, Na tsaneka sosai, Ban tsaneka sbd kaci Amanata ba sai sbd kalamanka akan mahaifina, Dan haka kaje dakai da wanda yaturoka ban hakuri ku daina wahalarda kanku akan Abbina sbd Abbina nada business daku ne kawai sbd Ni Ayanzu Dana cirewa zuciyata Kai Abbi ko Inda kuke Kuma bazai sake kallaba, So please Mr Zaid can you kindly see your self out..." Taqarasa fada tana nuna Masa hanyar kofa idanuwanta jajir. Wani shegen murmushin takaici da baqin ciki ya sake kafin ya kalli kofar yakuma waiwayo ya kalleta yace" Bakomai bane agurin 'ya Dan ta gada ubanta, Mahaifinki ma ya gagara Zama da mace tayaya kema ake tunanin kiyi aure ki zauna da wani?... Wata irin tsawa Mai qarfi umma yaganah ta sakar Masa tareda Kiran sunansa da qarfi cikin tsananin fushi da bacin rai. Kofa ta nuna Masa tana cewa" Zaka iya ficewa rashin 'da'an ya Isa haka., Juyawa yayi ya nufa kofa yanajin sautin kukan Inayah data sake na tsananin baqin ciki. Wani sanyi da damuwa yaji aransa lokaci daya, Shi mutum ne da Baya Bari idan anmasa saiya rama, Dan hakan ramawace yayi akan rashin da'ar da akaiwa mahaifinsa, Yanzu daya Rama yaji daidai Dan haka zuwa gobe yasan ta sauka zai kirata a waya ya lallabata su shirya Kuma yasan idan ta shirya dashi dole yaganah dama Abbinta su shirya dashi. Wani irin kuka Inayah keyi tun daga qasan zuciyarta takejin zafi da ciwon abinda Zaid din yayi Mata. Janta umma yaganah tayi sukai ciki saidai abinda basu saniba shine MAJEED na gidan yadawo sbd wasu baqinsa dazasu samesa gida yakuma ji duk abinda suke fada. Sam har baqinsa sukazo suka tafi har dare Bai nuna musu yasan abinda yafaruba sai washe gari ya sanarda umma yaganah maganar auren Babu Dan hakan da ita da Inayah din zasu Nigeria hutu sbd Inayah ta sake karta shiga damuwa sosai. Bayanda Abbinta ya sanar da ita da kansa ba maganar aurenta da Zaid tayi kuka sosai sbd Tasan yanzu batada ranar wani auren kuma Dan haka da akace Nigeria zasu Bata wani damuba saima matsuwa datai su tafi ko Zata samu sassaucin tsananin damuwar data shiga. Neesah hankalinta ya tashi Jin tafiyarsu Inayah din Nigeria Dan batada qawa ko daya bare aminiya idanba Inayah ba, Taso binsu Nigeria din Amma momynta tace ba yanzu sbd sunata kokarin ganin tafara aikine yanzu, Itama Inayah sbd Nigeria da zasu koma yasa batai saurin fara aikinba saita dawo tukuna. Cikin kwanaki qalilan aka Gama Shirin tafiyarsu Dan haka Abbi na wucewa Singapore suma suka wuto Nigeria itada Umma yaganah da zubbi. Saukar dare sukai a Murtala Muhammed international airport dake Lagos. CM Nuraddeen da kansa ne yazo daukansu daga airport cikin lafiyayyar Cclass dinsa. Cikin kulawa sosai yake musu barka da sauka tareda gaida umma yaganah cikin girmamawa. Inayah datake amatuqar gajiye ma cikin Dan yanayi na sanyin murya ta gaidasa kafin suka shiga mota suka Kama hanyar gidansu. Orchid Est Ikeja GRA suka iso Lafiyayyan qaton gidansu Wanda suna can abbin ya mallakesa. Akwai Mai aiki daya sai securities dasuka sama a gidan Dan haka CM na ajesu ya wuce gidansa Dan dare yayi sosai. Suna tareda gajiya dan haka basu wani tsaya komaiba kowannensu ya nufi Inda ya tabbatar Nan ne dakinsa sbd yanayin gyaransa. Bedrooms hudu ne a qasa kowanne da toilet na Inayah ne kawai keda closet room na musamman sbd sanin yanda tsarin dakinta na Australia yake. Dakin umma yagana ma babba ne da toilet dinsa aciki Babu abinda babu na Jin Dadi da kwanciyar hankali acikinsa. Dakinsu zubbi Yana daga baya ta hanyar backdoor na kitchen. Shi Abbi hanyar shigowarsama daban take saidai daga palonsa zuwa nasu akwai kofar wadda ta Nan zai ringa shigowa cin abinci a dining room dake babban palon gidan. Babu Wanda yayi yunqurin komai bayan wanka da sallah dakuma bacci dayake cin Inayah Dan Sam acan Bata doguwar tafiya irin wannan. Wanka tayo tafito daga toilet daure da blue towel tana gyara qaramin towel dake daure akanta ta nufi gaban maduba tana goge jikinta ahankali Amma da Dan sauri sbd sallolin dake kanta. Body mist kawai ta shafa tabar gaban madubin ta janyo daya daga jerin akwatinan datazo dasu ta bude ta dauka Riga da wando na bacci masu Dan kauri ta saka tareda jallabiyanta na sallah ta saka. Fitowa tayi tana tafiya Kaman qaramar baby ta qwalawa zubbi Kira. Allah yasa Salimat na kitchen tana musu warming abincin data girka musu tun dazu Itace taji Kiran ta fito tana cewa" Ma, zubbi na daki wanka takeyi. A kasalance Inayah ta kalleta tace, Dama ke zance ta kirawo, Inane gabas?? I mean alkiblah. Nuna Mata tayi tana cewa" Nan Zaki kallah Ma. Gyada Kai kawai tayi tareda juyawa ta koma tana Jan qafa. Sallolin dake kanta tayi duka Tana idarwa Bata tsaya adhzkar sosaiba ta miqe ta cire abayar ta fada dan bubbuga gadon alamar kakkabawa kafin ta fada tashige bargo take bacci Mai qarfi ya dauketa. Dama kusan koina na gidan gyare yake fes daga qamshi sai sanyin AC ke tashi koina. Umma yaganah ce dai data Gama salloli da wanka ta Dan huta kafin tasa suka Kai Mata abinci a dakinta taci Salimat ta tattara gurin kafin takuma brush ta kwanta. Inayah kam Salimat na zuwa dakinta so daya ta dakatar da ita akan kada su sake zuwa tadata su dameta sai gobe Babu abincin da Zata ci a daren. Washe gari qarfe goma na safe ta fito a shirye tsaf cikin Riga da wando marasa nauyi na zaman gida fuskarta fresh sbd isashen baccin data samu Mai nutsuwa. Wayarta ce a hannunta wadda take kashe tun ranarda Zaid yayi Mata Kiran farko bayan rashin mutuncin dayazo yayi Mata har gida. Tun a daki ta zare layin sbd Baida amfani anan. Palon take kalla koina tana Yana tsarin gidan da komai na gidan da yayi Mata daidai da can data baro, Salimat ce datake bin kyakkyawar surarta data Gama bayyana a shape na yanayin kayan jikinta Cikin girmamawa da sakewa tace" Barka da fitowa Ma. Sai alokacin Inayah ta juyo tayi Mata kallon tsaf fuskarta a sake sosai tace" Good morning Ms.....???? Salimat Sharif" salimat ta qarasa Mata. Murmushi Mai kyau Inayah ta sake tana cewa" Salimat ki kirani da Inayah, Just Inayah okay? Yes Ma. Dakin umma yaganah ta nufa tana cewa" Where's zubbi? Ina buqatan Nigerian simcard. Dayake akwai wayar Salimat a kusa ita Inayah din ta karba ta saka numbobin Abbinta ta Kira. Yana tareda abokan aikinsa Amma Yana ganin Kiran Salimat daidai wannan time din yasan Inayah ce Dan haka Kai tsaye ya miqe tsaye tareda daukan wayar ya fice zuwa office dinsa. A natse ya dauka da cewa" Yes,Ms Salimat. Wata qaramar dariya Inayah ta sake ahankali Tana cewa" Abbi kasan nice ba Salimat ba shiyasa ka dauka Kira daya. Murmushi ya sauke Me qaramin sauti kafin yace" Meyasa Zaki kirani da layin? Ba layin Nigeria a wayarmu duka and Abbi Ina buqatan abubuwa da dama kamansu kayan wankana da.... Ok,ok,ya Isa Ya kuke? Kinajin nutsuwa da yanayin gidan? Ina tareda mutane yanzu I will call you back anjima okay? Okay Abbi" ta furta cikin rashin Jin dadin samun lokacinsa. ##MAMUH# #AA MAJEED #INAYAH #LOVE/MARRIAGE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[10/20, 1:31 PM] +234 808 711 8630: *_19_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Breakfast sukayi na Lafiyayyan abincin da rabon umma yaganah dataci sa harta manta, Soyayyar doya da egg sauce dataji Qoda da veggies salimata tayi musu sai chips da plantains da ruwan tea masu Dadi Amma tea kam zubbi ce data San zabin Inayah din akan tea ta dafa. Bataci doyarba sbd Bata wani Saba da itaba chips din kawai taci da sauce sai tea suka koma Palo ta zauna tanajin kadaicin Neesah da batada wayar kiranta. Da Rana gabaki daya familyn gidan CM sukazo gidan Yi musu barka da zuwa Dan haka gidan nasu yake cikeda Baki duk da suma ba wai wani yawane dasuba, Matansa ne biyu haj Raliya da Anty Hafsat sai 'yayansa shida, Biyu maza hudu Mata. Babbar yarsa mace ce kusan sa'ar Inayah saidai tafi Inayah girman jiki sosai ta tsayi data jikin sbd Inayah rayuwar turaice atareda ita tana dieting sosai ba koyaushe takecin abinciba kokuma cin komai tasamu Anyhow Dan hakan ita tana maintaining jikinta sosai sbd kaman yanda tafada so take jikinta yazama abinda zai qara haukatar Mata da mijinda Zata aura, Tanason rayuwa shiyasa takeson Allah yasa ta aura mijinda yafita sanin cikakkiyar rayuwa. Da farko zuwan baqin da hayaniyar da gidan ya dauka yasa taji kanta kaman zai fara ciwo sbd kwata kwata basu wani Saba da ganin baqi irin haka gidansuba musamman da Yara, Ko gidajen friends nata da abokan hulda acan gida dayane take zuwa Mai Yara suma yaran biyu ne Kuma basada hayaniya kaman wainnan. Umma yaganah kuwa Murna da farin ciki Kamar me sbd rayuwarta ta saba da hidimar mutane da hayaniyarsu Amma tunda suka bar qasar Takoma rayuwar kadaici ba mutane a rayuwarsu dagasu saisu sai qaidajjun mutane suma kusan duk turawane, Hakan ne yasa cikeda Murna da farin ciki ta tarba baqin sunata gaggaisawa da firarraki duk duk da ita uwace garesu sai firar ta Zama ta mutunci ce sosai Dan kuwa bakowane yasan ba umma yaganah dince mahaifiyar AA MAJEED ba. Inayah ma dole ta zauna tana Dan yaqen dole acikinsu sbd rashin sabo. Matan Cm din kuwa kowaccensu kokarin jan Inayah take ajikinta sbd basu taba dauka haka Inayah din tasa takeba a fili, Sunsha ganin hotunanta a media sbd mahaifinta da kowa ke mamakin son 'yaya irin nasa dayake fifita 'yarsa akan komai dakeda mahimmanci shiyasama duk Wanda yake hulda da AA MAJEED saiyayi Neman hoton 'yarsa da yake ganin tafi sauran 'yaya, Sundada hotunanta da dama musamman na kammala karatunta dasuka Dan Yi yawo a tsananinsu sbd CM yaje taron kammalawar tasu har can qasar. Haj Raliya da ake kira da Mimi mace ce da kusan komai nata take yinsa akan riba da qaruwa dakuma son yin suna acikin masu arziki, Tunda dadewa takejin inama AA MAJEED nada Mata da duk yanda zatai saitayi sun Zama aminanai na gaske sbd abokanan huldarta duk matan manya ne,matan Naira. Data Gama fahimta daga mijinta tako Ina AA MAJEED baida ra'ayin mace ko kadan yasa tasawa ranta burin ganin A MAJEED din ya aura yarta Safnah, wato babbar 'yar CM din, A MAJEED ya Haifa Safnah sosai tunda kusan tsarar 'yarsace Inayah Amma ita agurinta shekaru ba komai bane idan har zaka sama miji cikakke,tsayayye,hadadde Kuma Wanda ya kafu kaman AA MAJEED. Wannan burin nata yasa suna zuwa gidan taji duk duniya ba Wanda takeso irin Inayah sbd tasan ta hanyar yarsa komai zai iya faruwa. Safnah Batasan burin mahaifiyarta ba sbd har lokacin karatu takeyi Kuma tanada saurayinta dasuka dade tare Dan haka Bata wani San menene yake faruwa Aran mahaifiyartaba. Anty Hafsat ma tana ganin Inayah taji tana kaunarta saidai batai saurin saka wani buri ko qudirin komaiba akan Inayar kaunace ta Gaskia ta shigeta ta 'yarinyar data tashi a hannun ubanta batareda uwaba. Ganin yanda suke nuna kulawa da kaunar Inayah sosai yasa umma yaganah sake Jin Dadi tana Kuma girmama mutuncin iyalan CM din. Safnah ce take Jan Inayah din fira wadda take Dan amsawa sama sama sbd gabaki daya hankalinta yakoma kan rashin layi akwai wayoyin datakeson yi. Wani qaramin lunch party sukai a gidan sbd abinci kala kala da aka dafa tareda snacks dasu Mimin sukazo dasu. Bata saba da yaraba Amma Yar qaramar babyn Anty Hafsat da Bata wuce 3yrs ba Mai suna Siyama tashiga ranta sosai hakan ne ma yasake taimakawa tasake Dan sakewa dasu. Da daddare ma saida sukai dinner kafin driver yazo daukansu suka bar gidan. Umma yaganah saidai taiwa yaran kyautar kudi sbd basuda wata tsarabar badawa duk sai Bataji dadiba sbd ita mutum ce Mai kyauta Musamman yanzu da akazo takanas Dan Yi musu barka da zuwa. Hakan yasa taji tana buqatan siyayyan Yan abubuwa su ajiye ko Dan masu zuwa din. Inayah kam kanta dake Mata ciwon gajiya da hayaniyar da aka wuni anayi ta dafe ahankali ta nufi dakinta tayi wanka da ruwan dumi tareda fitowa ta saka kayan bacci ta kwanta. Bacci ne ya dauketa take sbd tagaji sosai Dan Bata saba hayaniya irin wannanba. Washe gari doma sunyi da Safnah Zata kawo Mata layuka har biyu saidai Kuma dole zasuje ayi Mata register din layin Dan haka suka fita zuwa MTN office har umma yaganah Dan itama tana buqatan layin. Safnah ce tazo da driver din gidansu shine yakaisu akai musu register din bayan sun siya manyan layuka masu special numbers. Suna baro MTN office Inayah taso suyi yawo taga garin Amma umma yaganah tace su koma gida sbd Abbinta baisan da fitarsuba ko yanzu din. Haka suka dawo gida badan Inayah din tasoba. Safnah Bata wuceba anan tasake yimusu wuni sbd Daddynta dayace ta Dan zagaya da INAYAH din tafara sanin gari saigashi baai fitar a sbd Abbinsu dabai saniba. Inayah daqyar taga mintunan da aka dibar Mata sun cika da sauri ta saka layin tareda kunna wayar dama tun acan sun biya kudi an saka Airtime a layukan. Numbern Abbinta akanta take Dan haka Kai tsaye shi tafara Kira. A kowane yanayi 'yarsa tazo Masa Allah na basa ikon ganeta ta hanyoyi da dama sbd sanin dayayi Mata ciki da Bai. Lokacin Kiran ya duba ya auna yaga qarfe Tara da mintuna shida Yakama yanzu a Nigeria Dan haka yasawa ransa Inayah ce Mai Kiran. A natse ya dauki wayar dake gefensa ajiye cikin palonsa Yana kallon wani conference, A hankali cikin nutsuwa da kulawa yace" Hello,Aslm alaikum. W slm, Abbi kana planning yafemu ne? Wani silent murmushi yasake Yana cewa" Yes Mana tunda Inayah ta girma tafara iya zuwa gidan saurayi. Wani qaran shagwaba ta sake tana cewa" Abbi tsautsayi nefa, Kuma banama son tunawa ko kadan sbd Abbi haryanzu fa nakasa daina tuna abinda nagani a gidan, Hannuwan Zaid fa acikin rigar wata Yana taba No..... Buge Mata Baki umma yaganah dake gefenta tayi Yana harararta qasa qasa tace" Bazakiyi hankaliba ko Inayah? Abbin kuwa shiru yayi na wasu sakanni kafin ya Dan gyara murya ahankali Yana cewa" Ya wuce, Daga yanzu karna Kuma Jin kin sake fadan haka da bakinki okay?? Bakisan kinfara girma bane? Likita guda fa ake magana, Dr INAYAH A MAJEED.. Jin dadin sunan daya kirata dashi yasata dariya tana cewa" Yes,ok Sir. Qaramar dariya Mara sauti yasake Yana cewa" Yaya umma yaganah? Ya kukejin yanayin? Are you okay with everything there? Numfashi ta sauke tana cewa" Yes Abbi ba laifi komai yayi munata kewanka kawai, Jiya CM's family sunzo We had a great day with them, They're nice and lovely. So you like them right? Yes Musamman Little Siyama Abbi she's so cute, Dama ace inada qanwa irinta danaji Dadi. Tsit umma yaganah tayi tareda abbin sbd idanba Inayah ba lokuta da dama waye ya Isa yaringa Masa irin maganganun Nan haka? Amma ita tausayima take basa duk lokacinda tayi magana irin hakan, Tunda tafara wayo tun tana qanqanuwarta Bata taba Masa maganar Inda mahaifiyarta takeba sbd sanin yanda ya tsana kalmar, Kwata kwata ta rufe babin tambayar mahaifiyarta kokuma yin maganar ma gabaki daya sbd kaucewa bacin ransa, Ta Riga ta sakawa ranta shine uwarta shine ubanta, Batasan Dadi ko kaunar uwa yanda takeba saidai ta uba Dan hakan Bata taba kafewa aranta Zata iya batawa Abbinta Rai sbd ambatar Inda mahaifiyarta take Dan kuwa koma menene ya rabata da mahaifiyarta tasan bamai Dadi bane sbd yanda mahaifin nata ya tsani koda Wasa a ambata kalmar mahaifiyar Inayah agabansa. Umma yaganah ce Jin yayi shiru tasan kalmar ta sosa ransa Dan hakan tayi saurin saka baki a zancen da cewa" Inayah wai kekam yaushe zakiyi hankali ne? Ina maganar qanwa yanzu a gurinki ai saidai ki bada himma ki nutsu kisamo wani Natsatsen mijin ayi Miki aure ki Haifa 'yayanki irin Siyama din, Abbinki ma Kinga kin Haifa Masa jikoki acikinsu zai darje amaryarsa dal a leda."" Da dariya ta qarasa zancen Itama Inayah dariyar tayi tana kwatanta ranarda Zata Haifa nata 'yayan, Irin qaunar da Abbinta ke mata zatawa nata 'yayan Suma tasan Abbinta zai sosu tunda 'yayan Inayarsa ne. Haka kawai burin ganin hakan shima ya shigeta a fili ta tace" Idan na haihu shikenan Abbi ka Zama grandfather? Dariya yasake ahankali Yana cewa" Inayahn Abbi ma shikenan ta Zama uwa ko? Dariya tasake tana sake cewa" Abbi zanji kunya idan kana fada da kanka fa. Ok ya Isa haka Time to sleep, Umma yaganah taje ta kwanta Inshallah zuwa gobe Zata fara fita asibiti. Ok Tom Allah ya kaimu Saida safe."" Cewar umma yaganah daya fadawa maganar. Amin, goodnight Abbi. Goodnight Inayah. Suna Gama wayar Inayah ta saka numbern Neesah ta Kira. Neesah ma tana ganin numbern Nigeria tasan Inayah ce Dan haka da sauri ta dauka tana cewa" Meyesa kika dauka lokaci kafin ki Kira?? Dariya Inayah tasake tana miqewa daga palon ta nufa dakinta Dan tasan doguwar Hira zasuyi da Aminiyar tata. Aikuwa sabuwar Hira suka dasa Dan tunda suka hadu basu taba tafiya Mai tsayin data rabasu ba irin wannan. Sai dare sosai ta Gama wayoyinta ta miqe ta nufa toilet tayo wanka tazo ta kwanta. Washe gari wuni tayi a daki tana dube dube a waya da laptop sbd asibiti da Zata fara zuwa, Abbinta yafison tafara aiki a asibitin gwamnati kafin taci gaba dayi a asibitin kudi sbd shi qwarewarta yakeso a aiki bawai samun ilimin abuba kawai aiki dashi yafi buqata. Kasancewar Bata Gama hada emails dinta aka fidda ba dama sauran uzurirrika yasa dole a satin Bata fara zuwaba Saida sukai kwana goma Sha biyu da Zuwa Nigeria din tafara fita. ##MAMUH# #A MAJEED/INAYAH #LOVE/MARRIAGE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/20, 1:31 PM] +234 808 711 8630: *_20_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ranarda tafara fita aiki tareda Safnah sukaje sbd driving din Nan Sam batajin Zata iya, Driver ne yakaisu babban Lagos State general hospital. Dr Abdulsamad salees ne likitan da CM yayiwa magana Musamman Dan ya ringa kulawa da aikin Inayah din dakuma guiding nata sbd yanayin asibitin Nan da can Inda tayo karatunta dabam. Dr Abdulsamad kallo daya yayiwa Inayah ya fahimci hankalinta ya 'dan tashi da asibitin sbd yanayin hargitsinta, Shima ba wani jimawa zaiyi a asibitin ba shekara daya zaiyi yakoma Abuja can asibitin dayake aiki, Yanzu watanninsa hudu anan din. Qayataccen murmushi ya sake Mata Yana kallon yanda hankalinta yake Neman sake tashi duk da yasan tasan duk Mai aikin ceton Rai da lafiya Baya kasancewa Mai tsananin qyanqyami sbd aikinsu Bai gadar musu da hakan ba. INAYAH" yakira sunanta cikin kulawa da sakewa fuskarsa daukeda murmushi. Kallonsa tayi da idanuwanta a natse itama ta amsa da" Yes Doctor. Muje afara shigarda isowarki da fara aikinki. Wucewa sukayi a jere Yana sake Jan hankalinta gameda wasu abubuwa da yanayin asibitin. Gyada Masa Kai takeyi tana saurarensa a natse har suka Isa sukai abinda zasuyi suka fito. Safnah Bata tsaya jirantaba sbd dama iya rakiyarce tata Dan haka tareda driver suka koma gida sukabar Inayah din. Har qarfe biyu suna tareda Dr Abdul suna fama da patients, Ba laifi taji dan dadin aiki dashi Dan kuwa sosai ya Bata kulawa da tattali Gashi ya kware sosai akan aikinsa. Sai kusan karfe 3 tadawo gida a matuqar gajiye. Wanka tafara yi tareda wanke jikinta sosai Dan kayan data dawo dasuma daga Palo ta ciresu tabawa zubbi akai laundry dasu. Sallar la'asar da aka Gama tayi Dan tayi azahar acan. Tana idarwa Bata nema abinciba kwantawa tayi tayi baccin awa daya da rabi kafin ta tashi Takoma toilet tayo brush ta wanko fuskarta ta fito tana duba wayarta dake silent. Miscalls din Abbinta ne guda biyu saina Neesah ma kusan hudu saina Mimi mahaifiyar Safnah 'daya. Dakin umma yaganah ta nufa tana Kiran wayar Abbi. Bai dagaba tasan dama zaiyi wuya ya daga waya lokacin Dan haka Bata sake Kiran kowaba ta ajiye wayar tana Zama gefen umma yaganah dake kallonta cikin kulawa tace" Umma yaganah yunwa zai kasheni. Murmushi umman tayi tana cewa" Ahakan Zaki Zama yanda Abbinki keson ki Zama? Bana gane wannan yanzu umma yunwa nakeji sosai fa, Banci komaiba a asibitin Bazan iya Shan koda ruwaba a asibitin Gaskia, Dr Abdul yaso muje restaurant naci abinci Amma bazan iya cin komaiba batareda nazo na cire kayan jikina nayi wankaba. Zubbi ta qwalawa Kira da muryarta Mai sanyi ta gajiya. Zubbin a kusa take dama Dan tana Palo tana gyaran yamma shiyasa taji Kiran tazo. Yes Ma gani. Zubbi ki kawon abinci. Ok. Juyawa tayi ta fice tareda nufar hanyar kitchen. Brown rice da chilled chicken akai su Kuma aka zubo Mata sai ruwa Mara sanyi sosai. Taci abincin sosai ba laifi kafin Tasha ruwa ta bawa zubbi kayan ta maida. Sai alokacin tadawo daidai dan haka takuma daukan wayarta tafara Kiran Neesah. Maganganunsu sukaita Yi tsayin lokaci kafin suka Gama wayar. Bata Kira Mimi ba sai bayan sallar magrib shima sbd ta sake kirantane. Gaisawa sukai a mutunce sai Mimin data ringa tambayarta aiki cikin nuna kulawa. Sosai taji dadin yanda Mimin ta nuna kulawarta harma ta ringa janta hira. Sun jima suna wayar kafin suka Gama bayan ta Bata Safnah sun sake gaisawa itama Tai Mata sannu da gajiyar yau. Sbd tasan Zata fita ko goben yasata kwanciya da wuri bayan tayi sallar ishai. Abbinta ma saidai Tai Masa text ta tura Masa ta kwanta. Washe gari akan lokaci ta shirya ta fito cikin blue skinny jeans da farar laced chiffon top Mai Fadi sosai. Black Prada strap sandals ne a qafarta sai black Prada handbag. Ko data fito driver na jiranta Dan haka tea da cake kawai taci ta fice. A hanya tayi waya da Abbinta harsuka Kai tana waya dashi Saidata Isa office din Dr Abdul ta kashe wayar. Cikeda nutsuwa tayi knocking tareda bude kofar ta shiga da sallama tana kallonsa Yana zaune Yana waya da mahaifiyarsa. Ahankali bude Baki tayi cikin nutsuwa tace" Good morning Dr. Murmushi ya sakar Mata Yana cewa" Morning Dr INAYAH. Murmushi kawai tayi tana nufar gurin Zama ta zauna itama tana duba tata wayar. Tanajin yanda yake waya da mahaifiyarsa cikin nutsuwa da tsananin so da kauna. Yana gamawa basu wani Bata lokaciba suka fita zuwa aikinsu. Yauma kaman jiya sai 3 suka baro asibitin. Yau ko firar Bata samu damar tsayawa Yi da umma ba suna sallar ishai tashige ta kwanta Dan yau din hartafi jiya Shan wahala. Cikin kwanaki kadan tafara sabawa da rayuwar fita aiki kan lokaci da Kuma sabo da shiga jama'a sosai sbd a asibiti Dr Abdul likitan jamaa ne yanada farin Jini da mutunci sosai a idon mutane Musamman patients dinsa, Sam baida qyama ko kasalar aiki Sosai yake sakewa da marasa lafiya ya dubasu yanda Yakamata. Ita kanta zuwa lokacin tayi wani irin sabo dashi hakama itama sbd aiki tareda a qarqashinsa yasa ta koya sabawa da patients tana Dan sake musu haka. Yanayinta da yanayin rayuwarta yasa kusan da yawa asibitin suka santa duk da tana sabuwar zuwa, Yanda take gudanar da rayuwarta yasa kusan duk akasan ba anan tayi zamaba a waje, Gashi batada wasu shekaru masu yawa Amma har ta kammala karatunta hakama ba laifi a iya Yan 'daidaikun dasukasan mahaifinta sunsan ita kadaice 'ya gurin mahaifin nata, Batada wulaqanta mutane Amma tanada Dan wuyar sabo sbd rayuwar gata da shagwabar da ita da mahaifinta yayi Duk da hakan Dr Abdul yana taimakawa sosai gurin koyar da ita yanda zatai hulda da jama'a Musamman patients sbd yanda zatai hulda da jama'a kam Abbinta Bai koyar da itaba sbd ko jama'ar Bata wani shiga sai yanzu da rayuwarta ta Zama ta jamaa cikin lokaci qanqani. Dr Abdulsamad kyakkyawan matashin likita ne Dan asalin Adamawa, Qwararre ne akan aikinsa haka Kuma yasamu nasarori da cigaban rayuwa ta fanni da dama sbd aikinsa. Aikine kawai yakeyi a Lagos din Amma ba anan yake zaune ba tun farko. Baida Mata Kuma Bai taba aureba hakama baida wata tsayayya dayake nema Hasalima Bai taba Jin soyayyar mace sai akan Inayah wadda ganin farko da yayi Mata yakamu da Love at first sight. Ganin yanayin rayuwar Inayar yasa Bai nuna mataba Kuma Bai sanar Mata ba sbd Dan sanin dayayiwa mahaifinta na career dinta yakeson fara tsayar Mata kafin komai Dan hakan shima ya tsaya akanta yaga komai ya tafi daidai. A bangaren gida kuwa da qarfi da yaji su Mimi sun Zama iyayenta sbd wata irin kulawa da kaunar dasuke nuna mata daga Mimi har daddyn harma da anty Hafsat. Tafi Shiri sosai da anty Hafsat akan Mimi sbd ita Mimi uwa ta dauketa anty Hafsat din Kuma tamkar babbar yayarta ta dauketa, Shirinta da anty Hafsat Yana Dan Kona ran Mimi Amma dai idan ta duba kusanci da INAYAH din tasamu da Safnah sai tanajin sanyi sanyi. Cikin yardar Allah Saida sukai wata uku harda kwanaki kafin Abbi ya diro qasar. Tana gurin aiki ya iso Dan haka a kaqe take data dawo gida tagansa. #MAMUH# SORRY SHORT CHAPTER###AMUN UZURI PLEASE. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[10/21, 12:15 PM] +234 808 711 8630: *_21_* *_Arewabook@Mamuhgee_* Tana isowa gidan tun a compound tasan Abbi yadawo gida sbd ganin sabuwar motarsa da tunda sukazo take a gefe rufe ruf Amma gatanan a fake gefe da alama da ita aka daukosa daga airport. Kofar palonsu ta dosa tana warware nadin qaramin gyalen dake kanta tun daga hanya Tana isa ta bude kofar Kai tsaye ta shige. Bakowa a palon sai Qamshin RoseNight da Sanyin AC daya Gama cike palon Saikuma qatuwar tv dake aiki ba murya sosai. Su zubbi da Salimat tuni suka Gama aikinsu suka nufi bangarensu tunda Mai gidan na gari Dan haka idan ba aiki ba Babu abinda zai Kuma shigowa dasu saikuma idan kiransu akai. Dakinta ta nufa direct ta tube tafada toilet tayi wanka ta fito daureda towel. Kiran Dr ne yashigo wayarta da sauri sauri ta dauka tace Masa" I'm kinda busy I will call you. Aje wayar tayi tareda nufar gaban madubi ta shafa Neutrogena oil dinta ta fesa spray kawai ta koma gurin kayanta ta saka wata chiffon wide neck gown Mara nauyi ta ziro slippers ta fito ko wayarta Bata daukoba. Kai tsaye hanyar palon Abbi ta nufa tana tunanin yanda ya shammaceta Saida yadawo ya fada Mata da ba lallai ta jima gurin aikinba ayau. Da farin ciki bayyane kan kyakkyawar fuskarta tayi knocking kofar harso biyu kafin taji muryarsa daga ciki a natse ya furta" Yes Inayah, You can cm in. Shigowa tayi da sallamar dake bayyanarda farin cikinta na ganinsa ta qaraso har gefensa ta zauna tana cewa" Abbi kana tunawa danima kuwa? You look more than cool and calm. Wani qayataccen murmushi Mara sauti ya sake Yana kallon yanda itama tayi Yar rama ta yanayin aikin data samu kanta aciki da cikakkiyar kulawa yace" Dr INAYAH A MAJEED ko gaisuwa babu tukuna kafin complains su biyo baya. Cikin murnarta tace' Abbinah barka da dawowa Munyi kewarka Kagani har Rama nayi sbd ban saba dadewa hakaba bakanan, Ga stress na aiki. Yar dariya kadan yayi Yana cewa" Duk kokarin Dr Abdul akanki menene da stress acikin aikin? Dr Abdul yana fadamun irin kokarin da kike keep it up okay. Tun yanzu Ina alfahari da 'yata Zata Zama babbar likita wata ran. Taji dadin kalmomin nasa Dan babu abinda yafi komai faranta ranta kaman ta faranta ran mahaifinta harya bayyanarda hakan. Firar familyn CM tafarai Masa tana sanar dashi irin kulawa da kaunar dasuke Mata harma da umma yaganah. Sosai yaji dadin hakan Kuma a gaban nata yakira Cm yayi Masa godia a gajarce na yanda iyalansa suka karbi nasa iyalin da hannu babbiyu. Daganan firar Dr Abdul suka koma wadda kusan duk Rabin firar itace taketa fadar halayen Dr Abdul din dakuma yanda take kulawa da tattalinta. Abbinta saurarenta kawai yakeyi Yana nazarin irin shaquwar data samu da Dr Abdul din lokaci daya, Yana fatan alaqar da tsaya iya ta aiki sbd irin wannan yabo da Inayah ke Masa baya fatan tasake shiga wata soyayyar yanzu Musamman ko Dan yanayin weak heart nata Duk da wani bangaren Dr Abdulsamad ya kwanta Masa sosai a Rai. Sai dare tabaro gurin Abbin Dan abincima acan palonsa sukaci tare sbd shi kansa yariga yashige ne bazai fitoba sai gobe shiyasa shima Bai fito main hall ba cin abincin dare. Tana baro palon Abbin gurin umma taje sukai Saida safe ta wuce daki ta kwanta bayan tayi waya sama sama da Dr Abdul akan daga gobe a Shift din dare zasu sake komawa. Washe gari da safe batada zuwa asibiti Dan haka baccin safe tayi sosai sai 11 ta fito lokacin Abbi baya gida ya fita. Sanye da Riga da skirt na atampa ta fito tana waya da Neesah. Breakfast tayi ita kadai sbd tasan ko umma ta jima da yin nata. Tana gamawa ta nufi dakin umma yaganah acan tayi kwanciyarta tana chatting sama sama saiga su Mimi sun taho gidan dukkaninsu yiwa Abbi barka da zuwa aikuwa take gida ya kaure da hayaniya. Mimi harda tsarabar wasu kayan atampopin tayiwa Inayah aikuwa umma ta gode Mata sosai itama Inayah din tanajin dadin kayan Dan haka ta gode mata. Dakinta suka koma itada Safnah suna firarsu ta matasan 'yan mata, Fira suke akan anty Hafsat da Bata isoba sun biya sun ajeta gidan yayar mijin qanwarta dasuke tsananin mutunci sosai, daga can zaa kawota Nan din. Saida suka gama cin abincin Rana kusan karfe biyu da mintuna kafin Anty Hafsat ta iso gidan. Da farin cikin ganin siyama Inayah tarbota tun daga harabar gidan. Faruk Ismail shine Wanda yakawo anth Hafsat daga gidansu. Kallo daya yayiwa Inayah yaji Tai Masa sbd shima tunda yayo karatu a Malaysia yadawo yakasa ganin macen datai Masa gashi dama iyeyensa sun takurasa akan aure. Ganin dayayiwa Inayah da yanayin gidan nasu yasa Kai tsaye ya 'dan fahimci wayayyu ne jama'ar gidan, Da alama sun danyi nasu yawon bude Ido wata qasar. Inayah gabaki daya batama wani lura dashiba sbd hankalinta dake anty Hafsat da Siyama tana murmushi dukkanin kyanta na Kuma bayyana. Anty Hafsat ce ta juyo ta kallesa tana cewa" Ok faruk nagode sosai Ka Isa gida lafiya. Gyada Kai kawai yayi tareda tada motarsa yabar harabar gidan ya fice Yana ayyanawa aransa shikam yaga matar aure irin class dinsa dayakeso. Inayah kam Anata bangaren ko kula batai dashiba Dan a daukarta driver nema yakawo antyn. A gidan suka wuni Anata fira da hayaniya sai yamma da Abbin yadawo aka kaisu palonsa suka gaisa a matuqar mutunce da girmamawa. Sai dare suka tafi bayan Abbi yayi musu kyautar kudi na Musamman ga Yara. Inayah Jin tayi kaman kada su tafi sbd yanzu da qarfi da yaji tafara sabo da rayuwar hayaniya Dan duk Wanda zai Yi rayuwa a Lagos dolensa ya koya daukan hayaniya duk da sukam anguwarsu batada abinda ya hadata da hayaniyar ko hayaniyar ma Kai securities basa Bari magana suke maka sbd gudun shiga haqqin wasu. Suna tafiya itama wanka da sallar ishai kawai tayi ta shirya cikin Riga da wandon Adidas sai qaramar veilhijab da jakar Nike data goyo ta fito tana qamshi Mai sanyi. Umma yaganah ce ta rakota har kofa ta fito tana saka wayarta silent. Abbinta ne da kansa zai kaita Dan haka gaban motar tashiga suka fice ta waiwayo ta kallesa cikin Yar shagwaba tace' Abbi kaman karnaje Allah Yau ban wani hutaba sbd baqi da akai. Murmushi kawai yayi Mata yana cewa" Zaki Saba Inayah. Tura Baki kadan tayi tana lafewa jikin kujera. Suna Isa asibitin Dr Abdul ma na isowa da 'yar qaramar motarsa. Ganin Alhaji MAJEED dinne dakansa yakawo Inayah yasa Dr Abdul qarasowa cikin nutsuwa da tsananin girmamawa ya gaida Abbin Yana cewa" Barka da zuwa Sir. Kallon Abdul din yayi da kyau cikin sake karantar nutsuwarsa ya gyada Kai shima a natse ya amsa da cewa" Thank you Dr, Ya aiki? Ya fama patients da Inayah? Murmushi yayi Yana Dan sake kallon Inayah dake kallonsa fuska asake Ya kasa maida kallonsa sosai akan AA MAJEED din sbd tsananin kwarjini da cika Masa idon da yayi uwa uba ga wata irin nutsuwa da kamewa atare dashi, Shima Adidas dinne a jikinsa black masu hade da hula yayi fresh acikinsu sosai tamkar sabon saurayi Mai tashen samartaka Dan kuwa shi Yama kasa yarda da shine ya Haifa zuqeqiyar budurwar 'ya kaman Inayah. A hankali yace" Lfy kalau alhmdllh Sir. Ok Tom Allah ya taimaka Thank you ko. U're welcome Sir. Jan motar Abbi yayi yabar gurin Suma suka dunguma zuwa ciki. Washe gari qarfe 8 tadawo gida wanka kawai tayi ta shige bargo sai bacci. Bata farkaba sai 1 na Rana shima Kiran Anty Hafsat ne ya tadada. Saidatai wanka tayi sallah taci abinci kafin ta Kira anty Hafsat din wadda tuni takira umma yaganah ta sanar mata 'dan Yar uwarta yaga Inayah din ya rikice musu tun jiya. Umma yaganah Bata wani dauki zancen da mahimmanci ba saidai tace musu ya nema Inayah din da kansa idan sun daidaita ai shikenan haka akeso. Kasancewar Inayah din batada wani saurayi ko daya yasa bata wani damuba tabawa anty Hafsat damar gabatar dashi din. Ranar farko daya fara zuwa gidan Abbinta bayanan yayi tafiya zuwa Kano da CM Dan haka basu wani samu damuwaba ko fargaba daga ita har umma yaganah. Faruk Ismail kyakkyawa ne ba laifi Kuma Dan boko da gayun gaske, Ya waye sbd Yana ganin yayi karatu a Malaysia saidai Kuma daya Gama sanin cikakkiyar waye Inayah da mahaifinta sai ya Dan sassauto daga 'dagawar dayake Yi na shi baa Nigeria yayi karatu ba, Shi karatun kawai yaje yayo yadawo ita kuwa acan taqarasa girma acan tayi karatu. Ranar Ashe Bai yiwa Inayahn kallon tsaf ba sai yau din daya Gama kallonta a natse Yaga irin kyan siffa data fuska dama sanyin halaye so innocent take yaji ya mutu akanta. Cikin sanyi da sakewa irinta wayayyu take komai uwa uba ga shagwaba data Zama kamar halinta sbd tasowarta a shagwaben Dan haka tasaba komai Kai tsaye da gaskiyarta take yinsa. At first Bata tsaya ta karanta Faruk ba sai daga baya daya Gama karantar shikam ya dauki duk wata hanyar mallakar zuciyarta, Tsananin kulawa da kauna Mai girma yake nuna Mata tareda wata irin soyayya. Shikansa yayi mamakin daya iya soyayya lokaci kankani sbd Bai taba soyayyar ba. Halayensa na kulawa da zallar soyayya yasa tuni itama tafada soyayyarsa Mai qarfi taqarasa mantawa da Zaid gabaki daya da babinsa. Soyayya Mai qarfin gaske sukewa junansa cikin watanni kadan Ga Dr Abdul dayake fama da tsananin Sonta Amma haka yabawa kansa hakuri ya danne tunda anriga ansha gabansa. Abbinta Bai damuba sbd tako Ina ya bincika iyaye da familynsu faruk din basuda illa Kuma tunda tagama karatu yanzu baida damuwa da aurenta koba komai auren ne next dama Dan haka yabawa faruk din Daman neman Inayah din. ##MAMUH# #LOVE/ROMANCE #MAJEED/INAYAH/MARRIAGE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/21, 12:15 PM] +234 808 711 8630: *_22_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Lokaci ya tafi sosai dan tuni maganar aurenta da Faruk ta Gama kammaluwa aka saka lokacin biki hankalinta Dana faruk din ya kwanta sbd wata irin soyayya ce sukeyi Mai zurfi da qulafucin juna. Shi kansa Abbin hankalinsa yafi kwantawa sosai da aurenta da Faruk akan can baya da Zaid. Ba maganar komawarsu Australia saidai idan sunje hutu saikuma Abbin da shikam zai ringa zuwa akai akai sbd huldodinsa wasu dasuke can. Daga Nan gidansu har familynsu Anty Hafsat da dangin CM Babu Wanda baya cikin farin ciki da murnar wannan biki sai Mimi wadda baqin cikin datake ciki ya hanata sukuni sbd bazata iya kallo Hafsat tasamu shiga jikin zuriar AA MAJEED ba fiyeda ita Dan kuwa ko yanzu akan wannan auren ba qananan arziki taketa samuba daga AA MAJEED harma da umma yaganah datake Jin Hafsat tagama Mata komai tunda tayi sanadinda Inayarsu tasamu kamilallan miji dayake sonta sosai. Safnah kuwa Bata wani damu da damuwar da Mimin take cikiba sbd tadauka kishi ne irin Wanda Allah ya halitta a zuciyar Mata shine takeyiwa Anty Hafsat na ganin tasamu shiga a Inda itace taso tasamu shigar. Neesah kam Dole da qarfi da yaji tazo Nigeria tareda momy Dan haka Murna a gidan takuma Zama sabuwa. Ta bangaren Dr Abdul son Inayah Bai taba raguwa acikin ransaba saima Jin dayake kaman zuciyarsa bazata iya daukaba ganin Inayah ta aura wani tabarsa, Amma iliminsa na addini Dana bokon daya kedashi Bai barsa ya qullata komaiba saima nesa nesa daya Dan farayi da Inayah sbd zuciyarsa bazata iya cigaba da daukan kishinta Mai tsananin gaske dayake ji Amma Inayah Bata iya nesa dashi sbd yariga yazama tamkar wani babban bangare na rayuwarta a Nigeria, Tayi sabo da shaquwa Mai tsananin gaske dashi da har kaunarsa ta ginu a ranta amatsayin aboki Kuma Dan uwan Dan haka idan yaqi kiranta itace da kanta take kiransa. *****Bikinta Saura sati uku Dr Abdul yabar Lagos yakoma Adamawa Farko hankalin Inayah din yatashi sosai da barinsa Amma hidima da shaanin biki yaqi barinta maida hankali sosai kan tafiyar tasa Sai kawai tabarshi akan idan angama bikin Zatai magana dashi. Anfara gyaran Amarya INAYAH tako Ina, Umma yaganah baji ba gani ta dauko masu gyara daga maiduguri ana gyaran Inayah ta ciki da waje. Anty Hafsat ma ba Zama kusan kullum saitaxo gidan da nata kayan gyaran. Neesah dai kam tana gidan sbd suna sauka Abuja can gidan iyayen momy kwana biyu kawai tayi ta biyo jirgi zuwa Lagos Dan haka duk sauran shirye shiryensu tare suke yinsu Ko Safnah ma kusan kullum gidan take wuni. Umma yaganah taje maiduguri kusan kwananta biyar acan daqyar daqyar ta iya samun wasu daga cikin 'yan uwanta Amma sauran kam duk sun rasu wasu Kuma ba'a San Inda sukeba kaman ita. Wainda ta sama cikin Yan uwan nata bama irin Yan uwan kusa bane Kawun malam mijinta ne da iyalansa ta samu sunkoma kauyensu da aka watse sai wasu daga cikin amininan iyayenta saikuma kishiyar mahaifiyarta da itama ta tsufa sosai. Tayi musu Sha Tara ta arziki tabaro tadawo maiduguri tasake kwana daya tabi jirgi Takoma Lagos. *****A daren da zaa saka amarya lalle saqon wani mugun labarin ya isowa umma yaganah ta hanyar Mimi. Rigimace ta barke a gidansu faruk da iyayensa da shi harma da mahaifin dadynsa.. Wannan wata babbar maganace data girgiza umma da ita kanta Inayah sbd basu taba tsintar wannan mumunar kalmarba sai ranar. AA MAJEED ya Haifa Inayah bada aureba, 'yar gaba da fatiha ce... Tashin hankali Mai girman gaske umma yaganah da Neesah suka Shiga sbd kalmar tayi Muni da yawa. Inayah kuwa zuciyarta ce taji tana harbawa da sauri da qarfi Wani irin zufane masu dumi suka ringa tsatsafo Mata. Dafa kujera tayi ahankali ta zauna tana Jan numfashi da sauri sauri. Ruwa zubbi taje da gudu takawo tabawa Neesah dake Kiran sunanta da Dan qarfi tana cewa" Inayah karki daga hankalinki please Wannan labari ne fa kawai aka kawo. Karban ruwan tayi takai bakinta da Dan sauri ta kwankwada ta miqawa zubbi cup din tana miqewa tsaye tace" Faruk yasan wannan zancen shirme ne, Ina ruwansu data yanda mahaifina ya haifeni, Idanma Ni shigeyarce an haramta auren shegu ne? Tunda Ina tareda mahaifi ai banajin zan karba suna kokuma bin layin shegu.. Umma yaganah ma cikin damuwa da tashin hankalin datake dannewa tace" Menene Kuma na wannan zancen ma Kuma yanzu? Yarinya da ubanta Dan Allah bamason janye janye da wulaqanci, Waye yafara kawo wannan zancen? Wane Mara hankalin ne zai kawo Mana fitina muna shaaninmu cikin Jin Dadi da farin ciki? Kuka sosai anty Hafsat keyi agaban Umma yaganah din sbd batama San Mimi tafara kawo musu zancen basu yardaba sai yanzu datazo da kanta sbd Al'amarin ya tsananta acan familyn Anata rigima da tashin hankali, Mahaifiyar faruk da mahaifiyar dadynsa sunyi rantsuwar bazaai aurenba Dan faruk bazai aura Inayah ba sai mahaifinta ya sanar dasu Gaskiar wannan zancen da aka kawo musu. Dadyn Faruk yasan saidai afasa auren har abada Amma AA MAJEED bazai zauna yiwa kowa bayaniba Dan a aura 'yarsa Kai tsayema za'a samu babbar matsala dashi Dan kuwa suna shegenta Masa 'ya ne Kai tsaye da kalamansu. Shi kansa Alhaji baba kakan faruk din Bai wani goyi bayan faruk da mahaifinsaba sbd ganin kaman harda kwadayin suna da arzikin AA MAJEED sukeson rufe Ido su hada zuria dashi koda da gaske Inayah din 'yar gaban fatiha ce. Dayake maganar a tsakanin mata tafara har lokacin Abbi baisan abinda yake faruwaba dagashi har CM Dan haka su sun Riga sun Gama rabawa jama'arsu katikan daurin aure da invitations na special lunch da zaai bayan daurin auren sbd abokanan huldodinsu Christians da turawan dake Nan tunda su ba daurin aure suke zuwaba. Wasa Wasa saiga zance dai yazama Babba Dan kuwa Dadyn Faruk yasamu CM da zancen har gida sbd bazai iya tunkarar AA MAJEED ba, Ko daya girma MAJEED sosai yanajin kunya da nauyinsa yaje Masa da maganar Dan haka yasamu CM da zancen. Sosai cm ya girgiza da wannan mugun sakon, dan haka baiyi saurin isarda sakonba saiya samu Alhaji baba dasu hajiyar yayi kokarin fahimtar dasu illar abinda zaayi din Dan tamkar tozarcine Kuma wulaqanci ga AA MAJEED da 'yarsa ace zaa tambayesa yanda ya Haifa yarsa. Sam kasa fahimtar juna sukai dasu dashi Dan haka baida wani zabi sai sanarda AA MAJEED halinda ake ciki. Shiru yayi bayan yagama sauraron bayanin CM cikin nutsuwa. Bai bayyanarda bacin Rai ko fushiba saidai kam idanuwansa wannan karon sun bayyanarda tsananin 'dacin daya Kama zuciyarsa. Ba'a taba cin fuska ko cin mutuncin Martabarsaba sai wannan karon, Ko alokacinda yake talakansa baida girma ko qima a idon mutane tunda shi talakane baa ci zarafin mutuncinsa kaman wannan lokacinba. Idanuwansa ya Dan juyo ahankali ya dauki wayarsa dake gefensa ajiye ya Nemo numbern umma yaganah ya saka Kira. Zaune suke gabaki daya gidan yanzu Murna na Neman komawa ciki tunda wannan muguwar magana ta bayyana. Tashin hankalin da Faruk yake cikine ya tabbatarwa dasu Inayah Al'amarin ya girmama, Babban tsoro da fargaba tareda tashin hankalinsu shine idan zancen yaje gaban Abbi yanda zai karbesa. Sbd farin cikin Inayah sunsan zai iya komai hakama sunsan bazai taba bawa Wainda suka shegantata suka alqantata da 'yar gaban fatiha aurentaba, Zancen na zuwa gabansa sunsan maganar bawa su faruk aurenta Kuma ta mutu saidai wani ikon na ubangiji. Hakan yasa Kiran abbin na shigowa wayar umma yaganah duk jikinsu yakuma sanyi sbd sunsan cm na gidan tun dazu suna magana. A natse ta dauka tareda sallama a sanyaye tace'" Naam ABDULMAJEED. Umma kuzo Palo akwai sako. Ina Inayah? Gatanan kwance tana fama da Dan ciwon Kai ne. Kizo harda ita din. Yana fadar hakan ya kashe wayar a natse tareda ajiyewa Yana cigaba da sauraren amininsa CM dake fadar rashin dattakon dasu Alhaji suka nuna akan wannan Al'amarin Magana dai gatanan irinta mata Amma sun biyewa zancen banzan. Shidai Bai iya cewa komaiba sbd zancen yazo Masa ne a bazata, Bai taba tunani ko sanin wani zai iya samun guts na aibata 'yarsaba. Kuma aibatawa mafi muni bafi tozarci Dan kuwa Saida suka kammala komai na ya'da maganar aure ace an fasa. Ta wani bangaren Inayah din yakeji, Tanada rauni sosai Bata iya saka damuwa ka shiga baqin ciki ba sbd sosai take shiga damuwa, Da qarancin shekarunta ace itama wannan shine Karo na biyu ana neman aurenta ana fasawa. Tabbas su Alhaji baba sun tozartasa Tozarta mafi muni. Sallamar umma yaganah ce tasashi Dan rufe Ido ya bude batareda ya juyo ya kallesuba Dan yasan dukansu Babu Wanda yake cikin yanayi Mai kyau sbd daga Inayah din har umma yaganah baisan Wanda yafi wani qulafucin aurenba, Ya rasa meyasa suke tsananin son auren tunda komai lokaci ne dashi. Inayah na ganin yanayin Abbinta tasan maganar fasa aurence zaai Dan haka ta fashe da kuka ahankali tana kwantawa jikin umma yaganah da itama nata idanuwan sukai jajir. Har lokacin Bai waiwayo ya kallesuba saidai cm ne yafara bayani cikin damuwa da rashin Jin Dadi yace" Umma nasan dai kinji bayanin abinda yake faruwa daga bakin Hafsat, Iyayen faruk dai basu amince da auren faruk din da Inayah ba akan wasu dalilansu da Babu amfanin ambatarsu yanzu, Dan haka ayi hakuri maganar auren dai yanzu abarta babuta saidai bamusan abinda Allah zaiyi agaba ba, Faruk idan mijinta ne Inshallah duk wainnan tashin hankalin da maganganun zasu wuce. Inayah ya kalla cikeda tausayi da kulawa yace" Kiyi hakuri kinji Inayah Inshallah Zaki samu mijinda yafi Zaid da Faruk, Wannan fashin auren wata jarabawace da ubangiji ne kadai yasan tanadin da yayi Miki a gaba. Kallonta Abbi yayi da idanuwansa dasuka sauya cikin nutsuwa da Jin zafin abinda akaiwa 'yarsa yace" Karkiyi kuka ki dauka hakan amatsayin wani gwaji daga Allah. Umma yaganah ki kula da ita sosai kada ta saka Al'amarin aranta tajawa kanta damuwa ko wani ciwon. Allah ya zaba Mana abinda yafi Zama Alkhairi. Amin" suka furta CM da umma yaganah Inayah kam kuka takeyi sosai Wanda kusan Bata taba irinsaba. Daqyar ta iya Isa dakin umma ta zube jikin umman Yana Jan numfashi zuciyarta na harbawa da qarfi. Neman yankewa numfashinta keyi da gudu Neesah taje takawo ruwa suka Bata suna Mata firfita duk da sanyin AC daya cika dakin zufa takeyi sosai tana Jan numfashi ga hawaye nabin fuskarta. Hankalin umma yaganah da Neesah harma da Anty Hafsat da Safnah da mimi dake gidan tashi yayi ganin yanda Inayah take cikin yanayin ban tausayi ga hawayen idonta dasuka qi tsayawa. Mimi datai wannan mummunan qullin Saida jikinta yayi sanyi tashiga damuwar tausayin Inayah duk da batai Dan cutatar da Inayah ba tayine Dan lalata Hafsat. Jiki amace suka watse suka koma gida aka bar ssu umman da Inayah suna fama da ita. Abbinta dayasan hakan Zata kasance da ita da wuri ya Kira likita akazo gida aka dubata Harda drip akai Mata qari sbd tashiga tension sosai na Al'amarin. ##MAMUH# #RIBA BIYU# #AYSHATOUH INAYAH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_23_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Da zazzabi ta kwana sosai a daren Dan haka a dakin umma yaganah ma ta kwana sbd tasamu kulawa da ita yanda yakamata Neesah ma kasa kwana tayi daki ita daya ba Inayah tadawo dakin umman suka kwana. Washe gari ba laifi ta tashi da lafiyar jiki saidai rashin ta zuciyata, A sanyaye take gabaki dayanta, Damuwa da 'dacin zuciya harma da baqin ciki sune takeji mamaye da zuciyarta tako Ina, Ga faruk tun jiya sai kiranta yake hankalinsa ya tashi dajin batada lafiya Amma bazata iya daga kiransaba ayanzu Dan kukane kawai zatai tamasa, Sun shirya tareda tsara yanda zasu gudanarda rayuwarsa da tsantsar so da kaunar juna, Daga ita har faruk suna tsananin son juna sbd tako Ina suna ganin sun dace da rayuwarda suke so da burin gudanarwa a rayuwar aure. To menene yasa iyayensa zasu datse musu buri da kaunar junansu? Meyesa zasu aibatata Rana tsaka Dan kawai cin zarafi ga mahaifinta Dan kuwa wannan da gani ba ita sukeson tozartawa da wulaqantawaba sai mahaifinta...sai dai kuma duk abinda zaa tozarta ko cin zarafin mahaifinta fita ranta yake. Tana son faruk kusan ma fiyeda yanda taso Zaid Kuma cire sonsa aranta zaiyi Mata wuya sosai amma Kuma Dole Zata dauki dangana kodan kada acigaba da cin mutuncin Abbinta da maganar yanda ya haifeta, Itadai koma Yaya mahaifinta ya haifeta tunda Bai yar da itaba kokuma ya gudu yabarta kokuma yamayi denying zamansa mahaifinta to tanason abunta ahakan, Idanma bada aure ya haifetaba Bata buqatan sani tunda barna ce to Riga ta afku ba gyara acikinta, Hakama dawo da zancen kokuma tambayarsa akan Gaskiar zancen kaman cin mutuncin mahaifintane zatai bayan Babu ta Inda ya gaza a matsayinsa na uba Wanda ya maye gurbin uwa. Ko danginsu da kakanninta Bata sake tambayaba sbd tsananin dokar daya kafa Mata akan hakan shiyasa Bata sake shaawa ko marmarin tambayaba. Abu daya tasani takuma tabbatar shin, Koma menene ya Raba mahaifinta da mahaifiyarta harma da danginsu ba abune Mai dadiba,tashin hankaline. ****Bayan kwana biyu da fashin auren jama'ar da suka sani sunyita yawo da zancen Wanda har gurin abokan aiki da huldarsa zancen yaje na cewa bada aure ya Haifa yarsaba, Da yawa basu wani damuba sbd harkace data shafesa bawai aikinsaba Haka zalika dukiyarsa da matsayinsa ya hana kowama daga zancen saidai mamaki da la shakka mutane sunyita fada. Inda ma zancen yayi sauki bai wani shiga media ba sbd a Nigeria din ba kowane ya sansaba tunda baa qasar yake zauneba, Manyan mutane abokanan huldodinsa ne kawai suka Sansa sosai sai jama'ar da baa rasaba. AA MAJEED mutum ne da Baya damuwa da Al'amarin kowa sai Wanda ya shafesa, Kuma Sam Baya damuwa da abinda kowa zai fada akansa Dan Bai taba damuwaba sbd yasan iya bayan fage ne bazaa iya zuwa afada a gabansaba sbd iskancinma gurin yinsa ake samu Ko su Alhaji baba duk wannan abin daya faru basu iya zuwa sun fada a gabansa ba sbd kwarjini da cika idon da Allah yayi Masa akan mutane Dan haka shima baiga amfanin nemansuba ko ji daga garesu tunda sun Kai sakon gurin Aminsa CM Kuma ya isar musu da sakonsu ga AA din, Sun dauka zaizo ya rokesu akan janye maganar tunda sunsan Babu abinda bazai iyaba akan farin cikin 'yarsa saigashi sunga sabanin hakan, Abinda basu saniba da akan wani dalilin ne suka soke auren zai iya nemansu a sulhunta Amma Kuma har abada bazai iya bawa Wanda ya sheganta asalin 'yarsa aurenta ba Dan hakan take ya toshe duk wata sauran hanyar dazata ma tunatar da Inayah wannan Al'amarin. Private hospital din da aketa kokarin budewa da sunanta aka sake bada himma sbd ko aikin tafara sosai yanda hankalinta bazai zauna akan damuwar matsalar da aka samuba. Dole ta sakawa kanta dangana da tawakkali sbd ganin Abbinta daya tattara maganarsu faruk ya watsar duk da tasan abin Yana damunsa tunda shi ubane da aka fasa auren yarsa Rana tsaka saidai Kuma bayyanarda damuwar batada wani amfani shiyasa basa gane Inda yanayinsa yake dosa. Umma yaganah ma haka suka hakura suka dauki dangana suka cigaba da adduar Allah yakawo Mata wani mijin yasa hakan shine yafi Zama Alkhairi. Yanzu Bata wani fita asibiti sbd baa kammala tasu asibitin ba gashi Dr Abdul ma Dole yanzu zai dawo yaci gaba da aiki a asibitin tasu idan angama tare. Da labarin lalacewar auren ya samesa baiji dadiba sosai sbd tunanin halinda Inayah Zata shiga Dan haka Saida ya matse ayyukansa yazo Lagos din hankalinsa ya kwanta. Da farko Inayah na ganinsa daya iso gidan nasu Batasan lokacinda ta fashe Masa da kuka ba tana sake maimaita Masa abinda yafaru. Hankalinsa Bai tashi da abinda ya faru dinba kaman yanda hankalinsa yatashi da kukan datakeyi Wanda taketa riqewa da dannewa cikin ranta sbd gudun daga hankalin umma yaganah da Abbinta, Amma tsakani da Allah har cikin ranta tanajin tsananin quncin rashin faruk Wanda gabaki daya yanzu idanma yakira bayan kuka Babu abinda take Masa harya daina kiranta sbd kukanta ba qaramin daga hankalinsa yakeyiba, Kukanta zai iya sakasa bijirewa iyayensa ya dauketa suje suyi aurensu wani gurin Amma Kuma hakan ba qaramar fitina zai tadaba dan kuwa Yana shakkar mahaifin Inayah din sosai tako ina., Bayason ya jawa iyayensa 'daurin da zai taba tsufa da mutuncinsu Amma badan hakanba Babu abinda zai hanasa guduwa da Inayah wani gurin a daura musu aure. Hankalin Dr Abdul ya matuqar dimauta da kukan Inayah wadda yakewa wani irin boyayyan son da yafara fin qarfin qarfinsa, Shi mutum ne Mai tsananin zurfin ciki da iya danne Abu shiyasa son nata yake boye cikin ciki da zuciyarsa Amma irin son dayakejin yanai Mata a yanzu bazai iya barin wani ya auretaba koda zaaita saka ranar auren nata ana warwarewa har sai ranarda ya sameta. Ita kanta tanajin Dr Abdul cikin ranta sosai Amma ba amatsayin masoyiba sai matsayin aboki wanda batada tamkarsa bayan Neesah. A gidan ya qarasa wuninsa Yana rarrashin Inayah shida umma yaganah daketa qara gode Masa kan damuwarsa dayake nunawa sosai akan Inayah din. Yana gidan Abbi yadawo Dan hakama Dole atare dasu yaci abincin dare dukkaninsu a dining. Dr Abdulsamad yasamu shiga sosai agurin Abbi Wanda da farko harsu Inayah din sunyi mamaki sosai tunda sunsan shi mutum ne Mai wuyar sabo da mutane, Bakowa yake yarda yashiga jikinsaba sosai Amma Dr Abdul lokaci qanqani yashiga ran abbin ya kwanta Masa sbd sanin kansa dakuma qaunar Inayah Mai girman gaske daya hanga atareda Dr Abdul din. Ya jima Yana fira agurin abbin kusanma duk akan aikin asibitin ne nasu da ake gab da kammalawa, Sai dare yabar gidan yatafi lokacin INAYAH ta jima da yin bacci sbd yanzu Bata wani jimawa take bacci. Neesah Takoma Abuja gurin momy datazo ta jajanta musu suka koma tareda Neesah din Abuja. ******Ahankali Dr Abdul ya Dage sosai gurin mantar da ita faruk dukda da Kamar wuya Amma Kuma dagewar tasa da tsananin kulawarsa akanta yafara cin nasarar hakan Dan yanzu ba laifi tacirewa ranta faruk din ta hakura saima hankalinta data maida sosai akan Dr Abdul din kan aikinsu. Faruk yakoma Malaysia qaro karatu Dan haka yanzu wayar tasu ma kusan kwata kwata sun daina saidai idan sunga juna a social network. ***Lokaci ya 'dan sake ja son da Dr Abdul ke Mata yafara juyewa zuwa wani Al'amarin daban, Yanzu gabaki daya ya sauya akanta yakoma kaman ba Natsatsen Dr Abdul din dakowa ya saniba, Wani irin so Mai zafin gaske yake Mata Wanda harya fara bawa umma yaganah tsoro gashi dai Bai fito yafada Mata Sonta yakeba Amma dai kowa ya kallesa yasan yagama zautiwa a Sonta Dan ko kallonta idan yanayi mantawa yakeyi da kowa. Ita kanta Inayah lokuta da dama tsananin kulawarsa da abubuwan dayake Mata na kauna tsoro da shakka suke Bata Amma har lokacin batajin tana Masa son soyayya saina aboki,yanzuma ya wuce abokinta ya Zama wani bari na rayuwarta. Abbinta ma ya lurada halinda Dr Abdul yake ciki akan Inayah, Baida matsala akan bawa Dr Abdul aurenta Amma Kuma Yana shakkar irin son dayake Mata zai iya cutatar da ita akan kishi kokuma cutatar da duk wanda zai shiga tsakaninsa da ita Dan haka son shima yake sakasa shakku, Ta wani bangaren Kuma tausayinsa yakeji Mai tsanani sbd son mace irin haka kaman ba so bane ciwo ne. Anty Hafsat koda aka fasa auren Inayah da Faruk Bai taba alaqarsuba saima sake shaquwa dasukai Dan haka yanzu tazama antyn Inayah tamkar wata qanwar uwa ko qanwar ubanta Komai na Inayah tasani da ita suke shawara so da dama Hakama Umma yaganah ta zamar musu tamkar uwa a gurinta suke wasu shawarwarin. Anty Hafsat din batai qasa a gwiwa ba takuma hada wani qaninta dasuke uba daya da Inayah. Sadeeq qanin anty Hafsat yayi karatun likita shima anan Lagos yatashi Kuma sosai yakeda abun kansa saidai yayi irin wayewar datai qazanta shima Neman Mata yakeyi sosai Amma Kuma bazaka kallesa kace yanayi dinba Dan kuwa a kamile yake a zahirinsa. Ba laifi ya Dan fara shiga ran Inayah saidai Bata wani zura da yawaba sbd tafara Jin shakkar Al'amarin maza da aure. Shima dagewa yayi da soyayyarsa da kulawarsa harma da alqawuransa yasamu yashiga zuciyar Inayah din. Wannan karonma ba Bata lokaci ya aiko iyayensa da maganar aure. Abbin yaso su saurara Kar ayi rushing din Al'amarin Amma Dr sadeeq din ya dage da iyayensa har abbin ya yarda. Dr Abdulsamad kusan zaucewa yayi da wannan maganar auren Kuma Saida kusan kowa yakusa gane halinda yashiga, Kasa hakuri yayi sbd zuciyarsa bazata iya daukaba yabi ta qarqashin qasa ya lalata auren ta hanyar tona asalin waye Dr Sadeeq Kuma can ma gidansu anty Hafsat akai fitinar ta hada 'dan uwanta da 'yar gaban fatiha tunda ba uwarsu dayaba. Wannan karon har asibiti Inayah ta kwanta ciwo sosai sbd zuciyarta tafara kasa dauka Abubuwan sun fara tabata sosai. Hankalin umma yaganah da mahaifinta ya tashi sosai sbd Saida suka dangana da zuwa Australia taga likita acan tayi jinya Ta huta kanta ya Dan sake kafin suka dawo. Ciwonta ba ita kadai ya taba ba harda Dr Abdul Wanda shima hankalin mahaifiyarsa yafara tashi da wannan mummunan masifar dake tunkarota 'dan ta namiji guda datake alfahari dashi Yana Neman samun tabin qaqwalwa akan son mace. ##MAMUH# #AA MAJEED# #AYSHATOUH INAYAH# #DR ABDUL SALEES/HADIZA _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[10/25, 2:11 PM] +234 913 330 3504: *_24_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Alaqarta da Anty Hafsat Bata taba girgiza ba sbd fashin auren da aka samu akaro na biyu saima tausayin juna dasuke, Su suna ganin qoqarinta da tausayinta akan yanda taketa kokarin hada Alkhairi Amma Alamuran na lalacewa, Itama tausayin Inayah takeji sosai sbd yanda Inayah duk tabi ta sukurkurce akaro na uku da fashin auren. Alqawari tayi bazata qara kawo kowaba ya nema auren Inayah tun basu fara tsanartaba Amma duk mijinta Inayah Zata aura alqawarine ta dauka itace Zata jajirce su tsaya sosai da umma yaganah suyiwa Inayah gyaran gaske da duk wainda sukaiwa kansu hasarar rashin aurenta sai sunyi kukan baqin ciki da Dana sani. Yanzu sosai take tsoron kula mazama kwata kwata basa ranta sunma fice Mata Rai sbd a matsayin da raunin zuciyarta yakai aka Kuma samun matsalar rashin aurenta komai zai iya faruwa da ita Dan haka tayi nesa da duk wata alaqar dazata Kuma jefata soyayya. Abbinta ma sosai yake data da taka tsantsan akan Wanda Zata Kuma samu yaanzu sbd kaucewa hadari da damuwa, Duk aka Kuma samun irin wannan matsalar likita ya fada Masa zuciyarta ba lallai takuma daukan wani mummunan tashin hankalinba. A yanayin weak heart irin na Inayah shi baimasan me zatayi da soyayya ba sbd duk wani disappointment Yana cikin soyayya yake gani. Haka suketa lallabawa da tunanin ta Inda wani manemin auren zai bullo mata., Ita dai umma yaganah fargabarta da babbar damuwarta kada Inayah din itama auren yafita ranta kwata kwata kaman mahaifinta, Shi namijine bazaiyi tsufa a aurenba Nan kusa barema kusan yanzu ne yake cikin shekarun da neman aure agurinsa abune Mai saukin gaske, Ita Kuma yanzu tanada sauran kuruciya ayanzu ne auren ya kamaceta kaman yanda take buri da tsananin kaunar yin auren Dan haka ta ninka roqonta gurin ubangiji Allah yakawo musu abokanan rayuwa masu albarka suyi auren. ***Familyn Dr Abdul hankalinsu yafara tashi akan yanda ya dauko hanyar tabarbarewa akan mace, Duk Wanda yake Dan uwansa yasan INAYAH A MAJEED a rayuwar Dr wata babbar jarabawace, Abin haushi da baqin cikin shine duk yabi ya lalace akanta Amma wai Bata saniba hakama iyayenta suna gani sunyi kaman basu ganiba, Hakan yasa kusan duk wasu Yan uwansa sukaji basa kaunar Inayah din sbd Dan uwansu daya Zama gwanin tausayi baida zance sai nata. Ana cikin hakan Inayah ta hadu da wani yayan abokin Safnah. Mimi da gudu ta ringa Jin Dadi sbd yanzu mijin ta bangarensu ya bullo Dan haka ta zaqe tanata sake cusa zancen Ahmed din gurin Inayah da umma yaganah saidai Inayah Sam hankalinta Bai kwanta takuma sakewa sosai akan soyayyaba Dan har yanzu akwai sauran son faruk maqale acikin ranta. A karon farko da zancen ya Isa kunnen Dr Abdul sanyi jikinsa yayi ya silale ya zaune Yana sauraren Inayah din dake fada Masa da kanta. Bai iya ce Mata komaiba saima kasa kallonta da yayi sbd kada taga yanayinda yake ciki Dan kuwa Zata girgiza da ganin idanuwansa dasukai jajir. Bai iya tsayawa yin aiki ba ranar sulalewa yayi ya koma gida sbd ciwon Kai Mai tsananin gaske daya taso Masa. Itama haka Takoma gida jiki amace sbd yanayin Dr Abdul din daya sakata damuwa. Baiyi bacci ba ranar haka ya kwana Yana juye juyen ciwon Kai Mai tsananin gaske da azaba, Yasani matuqar Mai samu Inayah ba wlh zai iya haukacewa Hauka tuburan ta gaske, INAYAH tazamar Masa jarabawa Kuma qaddara. Hawayene suka gangaro Masa masu zafin gaske ya miqe zaune tareda nade jikinsa waje daya Yana fashewa da kuka Mai tausayin gaske. Washe gari Bai iya fita aikiba sbd ciwo ya kwantar dashi Haka Inayah tazo tareda Dr Emma ya dubasa. Ciwon kansa Mai tsanani ne Dan haka yayi requesting suje asibiti ya dubasa acan Amma yace AA ba buqatan hakan Inshallah maganin ma zaiyi Masa. INAYAH ce tasaka aka kawo maganin daga asibiti yasha ya shige ya kwanta itama Takoma gida jiki duk amace. Kwanansa biyu a kwance kafin ya Dan warware yaci gaba da fita aiki. Babban abinda ya bawa Inayah tsoro itada umma yaganah da Anty Hafsat shine tun ba'aje koinaba akan maganarta da Ahmed Al'amarin ya lalace ta hanyar Kama Ahmed a drugs case. Haka kawai hankalin Inayah yaqara tashi sbd ta tabbatar yanzu kam koma menene yake lalata aurenta daga gareta ne sbd shaidu da komai sun nuna Ahmed gskia mutumin kirkine baya hulda da drugs tako Ina Dan haka akafi tunanin sharri akai Masa. Kan kace me mutane suka fara canfa daga Inayah ne duk Wanda yazo aurenta to masifu kala kala na zuwa garesa. Hankalinta ya tashi sosai da wannan mugun Al'amarin har abin yaso tabata, Abbinta kuwa take yafara Dana sanin dawo dasu Nigeria, Da suna can duk da kila Canfi da wasu abubuwan rashin wayewa basu faruba, A qasar waje da qabilu daban daban anan dinma basu damu da auren Wanda aka Haifa bada aureba sbd idanma hakane shi ai ba laifinsa bane, A taqaicema shi abin tausayi ne Musamman ga Wanda hakan ta kasance dashi Yana musulmi. Amma duk Anbi an hargitsa Masa rayuwa da tunanin 'ya Bayan duk tattalinsa da kulawarsa sun qare akan 'yarsa tilo guda. Fara tunanin maidasu Australia yayi Nan Kuma hankalin umma yaganah yafara tashi sbd har ga Allah tafison zaman Nigeria sbd kana cikin qasarka kafi nutsuwa da kwanciyar hankali idan ba su dasuke Yan boko ba sunfi son rayuwar turai din. Dama shi Abbin yafi kaunar zamansu acan ne sbd nesanta Inayah da irin wainnan maganganun dayasan matuqar suna Nigeria yau da gobe sai Mutane sunfara maganganun dazasu saka Mata wasi wasin asalinsu akanta. Ya zabi barinsu zaman wata qasar ne da nesantata da bude Baki wataran ta tambayesa mahaifiyarta kokuma asalinsu,kokuma labarin yanda mahaifiyarta ta tafi tabarsu. Gashi tun ba'aje koinaba anfara rikita Masa kanta da wainnan fitintinun, Auren data sakawa ranta ta nace gashinan Bata samu 'dan amanar dazai iya aurenta dan Allah ba, Daga Wanda keson aurenta Dan dukiyar mahaifinta sai Mai son wani bangare na jikinta sai masu aibata zuwanta duniya. Dan hakan yanke shawaran maidasu kawai su koma sai Kuma gaba idan Allah yakawo dalilin dawowar. Labarin barinsu Nigeria shine ya fidda asalin ciwon dake damun Dr Abdul akan Inayah Dan kuwa har Saida yayi Dana sanin lalata aurenta da Ahmed tunda wuri., Kusan zaucewa yayi Dan kuwa baimasan lokacinda yakai kansa gurin Abbinta ba Yana kuka da idanuwansa akan yabasa aurenta shi zai aureta sbd Babu Wanda yakaisa sonta. Dama yasan za'ai hakan to Amma shi kam soyayyar Dr Abdul din shakku take sakasa, Son yayi yawa, Bai taba ganin irin hakan ba, Basa Inayah din kaman yanada hadari sosai sbd irin wannan ya wuce so ya zama possession. Amma Kuma ta wani bangaren tausayi Mai zurfi Abdulsamad din yake basa sbd mutum ne Mai nutsuwa da Kamala tareda ilimi sosai Amma sbd soyayya shima duk hakan na Neman gagararsa, He is loosing everything slowly. Ta wani bangaren yasan samun Inayah ce warakar Dr Abdul din haka zalika badan tabin kan son dake Neman yawaba yasan Dr Abdul zai Zama Miji nagari Mai kula da kauna ga Inayah. Dan haka ko yanzu Bai cire ran Dr Abdul din zai kasa kula da Inayah ba, Yana saka ran idan yasamu Inayah din bazai Bari haukarsa ya cutatar da itaba Dan haka yace yabasa dama ya nema Inayah din idan ta amince shikenan, Amma da sharadin zai bisu can qasar zai Samar Masa aiki a one of the best hospitals dake qasar Yaci gaba da aikinsa acan da matarsa. Baiga abinda zai tsaya tunaniba matuqar zaa basa auren Inayah din Dan haka Kai tsaye ya amince, Dan koba komai kusan qaruwarsa ce zuwa wata qasar aiki. A natse abbin ya girgiza Masa Kai Yana cewa" No Kar kayi rushing abubuwan Zaje kayi shawara da iyayenka da mahaifiyarka dakace, Sbd kaman abune da bazaka iya yankewa Kai dayaba Dole kana buqatan iyayenka aciki. Shidai farin cikinsa ya hanama ya tsaya dogon zance ya amsa da cewa" Inshallah zan tafi cikin satin Nan na sanar da ita komai Umman tawa. Allah ya taimaka yasa hakan shine mafi Alkhairi. Amin, thank you sir, Ngd sosai Allah yaqara girma da rufa asiri. Amin. ******Abbi ne da kansa ya sanarda umma yaganah da Inayah buqatan Dr Abdul na abasa damar neman auren Inayah din Kuma yabasa damar Amma sai idan ta amince. Umma yaganah ba Bata lokaci ta bayyanarda farin cikinta sbd ta jima tana yiwa Inayah shaawar auren Dr Abdul din Dan nutsuwarsa da kamalarsa, Gashi kyakkyawa shima da Dan arzikinsa ba laifi. Shi kansa Abbi gskia Dr Abdul din ya kwanta Masa fiyeda duka maneman da Inayah din tayi a baya Amma Kuma yafison tayi zabi akan Dr Abdul din da kanta. Wani iri taji Al'amarin a farko Dan haka batace komaiba. Neesah tafara fadawa a waya Aikuwa Neesah ta ringa tsallen Murna sbd tasan Dr Abdul tako Ina yayi gskia, Ita da harta fara yiwa kanta sha'awar aurensa Amma ganin basa qasa daya yasa bata zurfafawa kantaba dakuma hango tsagwaron son Inayah a idonsa. Safnah ma tsallen murna ta ringa Yi tana cewa" Wlh dama nasan zaai hakan sbd Dr Abdul ya dade da mutuwa akan sonki Naga alama. Anty Hafsat ma a nata bangaren hamdala da godewa Allah tayita yi sbd dukkaninsu sun yaba da mutuncin Dr Abdul dakuma shedar irin son dayake Mata bazai taba gudunta ba Dan duk wani abunda zaa fada. Itadai Inayah tanajin 'yar shakkar Al'amarin sbd girman matsayin Dr Abdul a ranta idan sanadin auren Nan suka rabu tasan Zata shiga mummunan hali fiyeda lokutan baya sbd matsayin Dr Abdul a ranta jinsa take yafi Mata duk wata soyayyar datake abaya, Kaunarsa takeyi sosai cikin ranta tana jinsa tamkar wani jininta, Tasha gwada yimasa kallon wani bangare na rayuwarta sbd mahimmancin mutuncin dasuke da juna. Umma yaganah, Neesah,anty Hafsat da Safnah ne suka taru suka ringa azalzala Mata soyayyarsa da nacin nusar da ita irin yanda yake Sonta. Tun tana jin Al'amarin wani iri sbd Bata taba tunani ko kawo kwatancin soyayya harda aure zai shiga tsakaninta da Dr Abdul dinba har tazo nacinsu da kulawarsa daya soyayyarsa da yanzu yagama bayyanar Mata suka sauya matsayi da kaunarsa cikin ranta zuwa tsaftatacciyar soyayya Mai nutsuwa. ##MAMUH# #RIBA BIYU #AA MAJEED ABBI/AYSHATOUH INAYAH _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/25, 2:11 PM] +234 913 330 3504: *_25_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ganin hankalinta ya kwanta akan auran Dr Abdul din sai kowa yaqara bada himma gurin qarfafa Mata gwiwa da sake kwantar Mata da Al'amarin cikin zuciyarta, Bata sake sakankancewa ta budewa Dr Abdulsamad zuciyarta ba Saida Abbinta ya nuna Mata goyan bayansa akan auren Abdulsamad Dan haka ta budewa Dr Abdul dukkanin zuciyarta ta karba soyayyarsa. Abdulsamad tamkar a mafarki yakejin rayuwarsa yanzu dazai mallaki Inayah amatsayin matarsa halak malak batareda shamakin kowaba., Sosai kowa ke mamakin yanda duk yabi ya kasa sukuni ya rude Yana bayyanarda farin cikinsa koina. Tamkar wani zautacce yakomawa Inayah soyayya yake nuna Mata kamar ba Dr Abdul din data saniba tuntuni. Ita tausayinsama takeji Mai qarfi dayake qarawa soyayyarsa girma cikin ranta sbd Batasan haka yake tsananin sontaba da bazata taba tsayawa kula kowaba da tuni ta amince dashi anyi aurensu. Mahaifiyar Abdulsamad kam sosai take qaunar Inayah sbd yanda 'danta ke tsananin sonta, Da farko hankalinta yaso tashi sbd tunanin Bazaa bawa Abdul dinta auren Inayah ba duba da matsayinsu na wainda sukafi na Abdulsamad din kudi sosai sai gashi anyi halin girma anbasa aurenta Dan haka take kaunar Inayah har ranta duk da iyakacinsu waya haryanzu Allah Bai saka sun hadu a zahiri ba wata kila sai lokacin bikin Auren. ***Ansaka lokacin bikin Wata biyu masu zuwa Dan haka ko wannan karon su umma yaganah da Anty Hafsat da wuri suka fara shirya 'yarsu Inayah tako wane fanni. Gyaranta akeyi sosai Dan kuwa Abbi ya sakar musu kudi suna yanda suke so dasu gurin harkar shirye shiryen bikin. Wannan karon baiyi wani gayyataba sosai sbd kaucewa hayaniya albarka auren akeso ba taronba, CM ne ma dai dayafi A MAJEED din shiga mutane sosai ya dauka nauyin gayyatar ta hanyar aikawa manyan mutanen dasuke taredasu special invitations na auren. Anty Hafsat ta haukace tsima Inayah kawai takeyi tako Ina da abubuwa masu kyau da inganci nasu na manyan mata. Umma yaganah Kuma masu gyaran jiki takuma sakawa aka kawo matasu daga maiduguri harma da 'yan uwanta biyu dasuka zo bikin auren Dan haka tako Ina families din guda uku nasu na A MAJEEDs,da iyalan gidan CM saina dangin ango dasuke Adamwa hidimar biki akeyi gadan gadan ta kowane bangare. Inayah tana cikin wani irin farin ciki Mara misali sbd jikinta da dukkanin imaninta yabata wannan karon Zata auru Inshallah bazaa fasa aurentaba Dan haka taketa Jin farin cikin igiyoyin auren Abdulsamad dintane zasu hau kanta bana kowaba. Shikan oga Dr Abdulsamad fadar irin farin cikin dayake cikima wasane Dan kuwa jin yake Kamar zai take kan jariri dama uwar jaririn ya wuce sbd zumudi da farin ciki. Lafiyayyan lefen aure dangin Abdulsamad din suka kawo ana Saura kwana biyar afara bikin Wanda su umma yaganah sun yaba sosai da irin kokari dakuma uwar dukiyar dasu Abdul din suka kashe. Neesah sai a ranarda aka kawo lefen itama tasamu isowa daga Australia tareda Dr farhat wadda ita ta sauka a gidan Mahaifiyarta dake aure a Lagos din Dan haka tana zuwa suka sake hautsinewa da Murna. Safnah ma tuni tadawo gidan da kwana sai angama biki so gabaki daya gidan dai a kacame yake da jama'ar biki duk da ba wasu masu irin yawa dinnan bane. Inayah gabaki daya ta sauya Takoma tamkar wata jaririyar da aka Haifa acikin watan sbd tsananin kyau da taushi da fatarta tayi, Gyara da rashin fita tareda tsananin hutu da kwanciyar hankalin datake ciki a watannin yasa tayi wani irin zallar fresh sai sheqin fata takeyi. Tunda Dr Abdul yazo yaga irin kyau data qara da sheqin amarci datake tun yanzu yasa yaqarasa rikicewa akanta duk da soyayyarsa Bata shaawa bace Amma tuni kyanta ya qarasa rikita Dan sauran nutsuwar dayake da ita akan Sonta daya zaburesa. Ganin yanda yabi ya rude hakuri na Neman gagararsa yasa Anty Hafsat ta hanasu haduwa sosai tace sai lokacin bikin Dan haka yanzu a waya suke koyaushe ba sakat Kamar wasu hanta sa jini. Abbi kam sosai Al'amarin nasu ke Dan basa mamaki da dariya kawai sbd yanda Inayah tasan ta iya soyayya sosai irin haka Dan shi haryanzu a jaririyar 'yarsa yake kallonta gashi zatai aure takoma qarqashin ikon wani. Yau sosai take amatuqar gajiye sbd saka lalle da akai ayau din can gidan CM Dan haka sosai take amatuqar gajiya Koda suka dawo gida zare tsadadden lace din dake jikinta tayi Mara nauyi ko kadan ta nufi toilet tashige. Gaban mirror ta tsaya tafara goge fuskarta tas da Neutrogena makeup remover wipes. Wanka tayo da ruwan dumi kafin tafito daureda towel tana kallon Neesah ma dake jiran ta fito wankan itama tashiga tayo Dan duk makeup din fuskokinsu damunsu yakeyi sbd basa wani makeup dama can Iyakacinsu Liner da mascara sai lipstick masu tsadan gaske dake zaunawa da kyau abakinsu idan sun saka. Sama sama ta shafa Mai tareda spray dasu khumrahs masu sanyin qamshi da akayo Musamman masu tsada daga maiduguri. Riga da wango tasaka masu kauri sbd sanyi sanyi datake ji. Sallolin dake kanta tafara Yi kafin ta miqe ta fito tana waya da Dr Abdul dinta ta nufi dining tana cewa" Heart yunwa fa nakeji sosai yau banwani ci abinci ba Zaa ramar maka Ni da yunwar biki. Cikin kulawa sa so Mai tsanani ya karyar da murya yana cewa" Ni zasu illata gskia bazan dauka ba, Kyakkyawar amaryar tawa ce zaa Bari da yunwa Gskia bazan yardaba Laifin anty Hafsat ne data hanamu haduwa yanda muka saba kewanki is driving me crazy Gobe da safe zanzo na ganki kafin su Umma su iso sbd itama tana zuwa Zata qarawa anty Hafsat qwarin gwuwar hanamu ganin juna sai ranar Daurin auren. Murmushi tasake Mai kyau tana cewa" Dan Allah kazo goben da wuri Nima nayi kewanka fa sosai. Zama tayi a dining daidai lokacinda Abbi ke isowa dining room din a kasalance ta ajiye wayar sbd bataso Gama waya da Heart dinta ba Amma Kuma girman Abbinta na daban ne akan komai. Kallon abbin tayi Yana sanye da Fararen hoodie graffiti print sweatset. Sanyin qamshinsa ne yake neman danne na Lafiyayyan abincin dake jere kan dining din yayi fresh Kamar ba baban amaryar ba Batasan lokacinda ta sake qaramar dariyaba tana cewa" Abbi barka da fitowa. Da Dan silent murmushi ya kalleta yana amsawa da cewa" Barka Amaryan Dr Abdulsamad. Dariya tasake tana kallonsa tace" Abbi Naga kamanma ka matsu natafi nabar gida, Kullum saikace mun amaryar, Nidai kunya nakeji Gaskia. Wani qayataccen murmushi ya sake daidai lokacinda Neesah da umma yaganah suka iso dining din cin abinci yace" Inayah kinsan kunya dama? Inace you don't know the name kunya, Kin manta a gabana kike zuwa kina kukan soyayya da Kiran sunan zayyan ne sunan koma fahat ne I can't recall And now kinata tsalle da murnan zakiyi aure shine kike fadamun kunya Rashin kunya plus lie ko?? Dariya umma da Neesah sukai umma na saka musu Baki da cewa" Inayah kam ai indai anan cikin gidane Babu Wanda take kunya saidai mutane waje take kunya. Kai umma yaganah please karki sake batan suna gurin Abbi Kinga zaifi kowa kewata fa idan natafi ko Abbi? Abincin data Gama zuba Masa yafara ci yana Dan gyada Mata Kai ahankali. Bayan sun Gama cin abincin bin Abbinta tayi palonsa suka cigaba da maganganunsu na tsakanin uba da 'ya sai kusan after 9 tafito ta nufi daki ta kwanta bayan tasake goge fuskarta da face cleanser. Washe gari shine zaai Mata lalle Kuma tasan heart dinta yace zaizo Dan haka da wuri ta tashi tayi wanka ta shirya cikin Riga da skirt na maroon super exclusive wax da qaramin Marron veil ta fito a sace sbd yaca Mata ya iso Yana palon Abbi. Tana shiga palon Abbin Yana zaune tareda Abbi suna magana cikin nutsuwa. Bude kofar tareda sallamarta a sirance tasaka su waiwayowa kallon kofar atare take zuciyar Abdul yakusa bugawa. Ya salam ya furta a fili batareda yasan ya furta hakan agaban Abbin ba. Qamshintane ya doshi hanyar mamaye palon gabaki daya sbd wasu irin qamshine kala kala na designer turarukanta masu tsada da turarukan khumrahs da akai Mata masu tsananin sanyin qamshi da shiga zuciya. Kallo daya Abbi yayi Mata yaga yanda daga ita har Abdul din suke kallon juna yaji mamakin gaske yana kamasa ta yanda Inayah duk ta lalace har haka baida sani. Ahankali ya dauke Kai daga kallonsu tareda gyara murya yana Kiran sunan Inayah din a natse. Cikin nutsuwa da girmamawa tace" Yes, Good morning Abbi. Qarasowa tayi tareda dauke kallonta daga kan heart din tana Zama kusada Abbinta tasake gaidasa. Amsawa yayi tareda Dan kallonta yace" Hafsat tasan kinzo Nan? Murmushi tayi tana girgiza Kai da cewa" Abbi Bata saniba banaso ta sani please. Da mamaki ya Dan kalleta sbd yasan hakan bai kamataba Musamman yanzu irin yanda yaga suna maitar kallon juna bayason ko kadan shedan ya Shiga zukatansu Koda rungumace suyi kafin aurensu tunda daga yau ne sai gobe jibi zaa daura auren Dan haka ya Dan kame fuska a kame yace" Ok ku gaisa ki koma ciki zanyi magana dashi. Bata fuska take Neman yi ta marairaicewa abbin Amma ganin ba wannan damar yasata kallon Abdul daya Gama mutuwar zaune gurin satar kallonta ta gaishesa a gutsure. Amsawa yayi batareda ya kalleta sosaiba tunda Abbi na gurin Badan sun soba su duka haka ta juya Takoma Inda ta fito. Shima Bai wani gane sauran zantukansa da Abbin ba sama sama ya gane yayi Masa sallama ya wuce. Jiki mace akai Mata zanen kunshin sbd rashin ganawa dakyau da heart dinta. Sai kusan yamma daya kirata yasamu yasaka zuciyarta da ranta ya sake suka Dan zanta a wayar kafin ta aje tashiga wanka sbd anmata dilkan yamma again. Washe gari Koda ta tashi da murnar sauran kwana daya ta tashi hakama da damuwar rabuwa da Abbinta Dan haka ta ringa samun sauyin yanayi aranar, Tayi farin ciki tashiga damuwa ahaka dai yamma tayi duk saitaji tashiga damuwar tunda gobene Zata bar gidan gashi har yamma tayi Babu abinda ya rage a wunin yawuce sai kawai ta fashe musu da kuka. Bata taba tunanin halinda Zata shigana ranarda Zata rabu da mahaifinta sai yau Musamman idan ta tuna da Heart dinta Dan Adamawa ne can zasu tafi da ita bazata sake Zama gurin Abbinta ba Tsorone Mai girma ke Neman cika zuciyarta sbd duk Inda Zata tafi jinta safe cikin nutsuwa da kwanciyar hankali agurin mahaifinta. Tun su anty Hafsat na Mata dariya hardai suka fuskanci da gaske takeyi hankalinta ya tashi matuqa a tsorace take. Umma yaganah ma jikinta duk yayi sanyi Musamman itama datai wata irin sabo da shaquwa da Inayah din tun jarinta. Heart dinta hankalinsa ya tashi da kukan nata sbd kowa yayi yayi taqiyin shiru shiyasa anty Hafsat tafada Masa kozai iya zuwa ya lallashi Inayah din Itama umma yaganah takira Abbi tafada Masa Inayah fa tana nan tana zabga kukan bazata iya zuwa Inda Batasan kowaba ta rabu da mahaifinta. Cewa yayi idan yagama magana da baqinsa dasuka iso Lagos domin daurin auren goben zai iso gidan. Dr Abdulsamad Yana tareda mahaifiyarsa da qannan babansa biyu Mata sai 'yayan yayyun mahaifiyar tasa biyu suma Koda anty Hafsat me Masa wannan bayanin. Kallon umman yayi yace" Umma Bari naje gidan Inayah ce tanata kuka wai bazata iya zuwa garinda batasan kowaba. Murmushi umman tayi cikeda mamakin shirme irin na Inayah Gata ta girma dai Amma gata yasa yarinyar kasa nuna ta girma. Wayarta dake gefenta ta dauka tana cewa" Kaga bara natashi muje tare sbd dama yakamata da muka iso munje gidan an gaisa kafin goben ranar biki muje gidan, Kaga dama abinda yasa nazo da kaina kenan sbd Inayah din tasake tasan muna kaunarta sosai Nice zan karbeta da hannuna Inshallah cikin Amana bazamu Bari tayi kukan baro gidaba. Gaba yayi Yana cewa" Okay umma saikin fito to. Bayan fitarsa tsadadden mayafinta dake ajiye ta dauka tareda LV handbag dinta ta nufi kofa tana cewa" Nafisat zo muje Naga kece a shirye da alama su Asmau akwai sauran gajiya atare dasu kaman wainda sukai tafiyar mota bayan jirgi kuka biyo. Ficewa suke kokarin Yi yayar mahaifin Dr Abdul dake sallah tana idarwa cikin Dan daga murya tace" HADIZAH. cak umman ta tsaya tareda waiwayo tace" Na'am. ###MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[10/26, 8:44 PM] Sweet sis: *_26_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ku jirani a motar Bara na sauya Kaya muje Nima zan gaisa da iyayen na Inayah tunda dai kaman yanda kikace din yakamata muje a gaisa basai gobe bayan daurin aurenba muje. Ok Tom muna jiranki a motar. Juyawa tayi ta fice daga babban dakin ta ratsa palon zuwa babban palon gidan na mijinta Wanda Sam basa Zama anan tunda aikinsa na soja ya maidasa Abuja ita saita koma Adamawa sbd uwar gidantace a Abuja ita Kuma a Lagos to ana Masa transfer zuwa Abuja tabar Lagos Takoma babban gidansa dake adamawa. Tana Isa motar Haj balaraba na isowa Dan haka sai kawai suka shiga suka wuce zuwa gidansu Inayah din. Tafiyar mintuna sukayi suka iso lafiyayyar anguwar ta masu abun duniya. Kai tsaye security ya budewa Abdulsamad din gate Yana daga murya da cewa" Welcome Sir. Yauwa thank you Bosco. Parking yayi tareda kashe motar suka firfito su umman na sake yaba arzikinsu Inayah din Dan kuwa gidan irin tsarin ginin turai ne komai ma kusan yanda Inayah takeso akayisa. Kai tsaye hanyar kofar palon cikin gida ya nufa dasu Sbd su din Bai kamata yabi ta hanyar palon Abbi dasuba. Suna Isa kofa Safnah na fitowa da waya a hannunta tanayi ganinsu yasata katse wayar Dan nuna girmamawa gasu umman Abdul din dasuke manyan Mata sosai. Cikin sakewar fuska da girmamawa tafara musu sannu da zuwa tana gaidasu. Juyawa tayi tai musu jagora zuwa can qurya palonda kowa yake Anata fama da Inayah din. Tsokar Abdulsamad tayi da cewa" Yanzu sbd heart din taka ka tado su umma da magribar fari Dan azo a rarrasheta. Dariya yayi yana cewa" Safnah harda ku kuka sake rudar mun da ita gskia Amma haka kawai baby bazata fara kukan Nan ba. Shi a palo ya zauna Yana amsa waya sukuma su umma palon ciki tayi dasu. Su umma yaganah dasu Mimi na ganinsu cikeda farin ciki da mutuntawa suka tarbesu suna musu sannu da zuwa a waye. Mahaifiyar Abdulsamad hadiza babbar mace ce Mai tattare da Kamala da mutunci sosai Kuma a bayyane ta nuna kaunarta da kulawarta ga Inayah. Drinks da snacks zubbi da Salimat suketa aikin kawo musu Anata sake musu sannu da zuwa. Cikin Jin Dadi da farin cikin yanda aka karbesu hannu bibbiyu da mutuntawa suketa amsawa suna sake yaba gatan da Inayah take dashi Dan duk Wanda is kalla yanayinsa a gidan zaka tabbatarda yanda yake kaunarta tunda kusan duk albarkacinta kowa keci acikinsu adai cikin gidan da rayuwar AA MAJEED. Da 'yar Raha umma yaganah tace" Kuna fama da gajiyar tafiya Rigimar Inayah ta fiddoku, Shima Abdul din dabai daukokuba ai yabari Kun huta shegantaka ne kawai irin na Inayah Zata fara kukan barin gida tun yanzu Ai tabari har zuwa goben idan andaura aure. Yar dariya Haj balaraba tayi tana cewa" Ai Dole zatayi kuka tun yanzu sbd auren nesa na gida Daman sai kaji kaman shikenan katafi. Umma Hadiza kuwa Inayah data fito daga bedroom sanye cikin Riga da skirt na soft embroidery Swiss Mai kyau da tsada navy blue ta zuba Mata Ido gabaki daya tana kallonta. Duk hotunan Inayah da vidcall dasuke ganinta idan Abdulsamad na gida basu bayyanar Mata da kamannin Inayah ba kaman yanzu datake ganinta a gabanta. Da farko zuciyarta harbawa tayi da kyawun fuska Dana jikin Inayah hartana Jin Anya Abdulsamad bazai bartaba akan matarsa Inayah bayan auren To Amma Kuma zuciyarta tarigada ta kamu da kaunar Inayah tun kafin auren sbd son da Abdulsamad ke Mata to yanzuma data ganta saitaji kaunarta Mai nutsuwa da tsafta takuma shigarta. A natse Inayah ta qaraso Inda suke fuskarta duk yayi ja sbd har lokacin hawaye takeyi sosai Musamman ganinsu umma Hadiza sai taji kaman sunzo tafiya da itane gabaki daya zatabar gida. Cikin farin ciki da kulawa tareda murmushi a fuska umma Hadiza ta kamo hannunta ta zaunar da ita a gefenta tana cewa" Zo ki zauna 'yata Inayah kinji, Ki daina kuka sbd inshallah bazamu taba Bari kiyi kewansu umma da Abbinki ba sosai Dan zamuyita tattalinki muma kaman yanda suke Inshallah. Ba kunya Inayah ta dago ta kalli umma Hadiza alamar da gaske kike fada. Da sauri umma da Anty Hafsat suka dungure Mata kan suna cewa" Inayah wai bazakiyi hankaliba ko?? Su umma Hadiza da haj balaraba kuwa dariya suka sake atare harma dasu Neesah Haj balaraba na cewa" Eh Inayah Inshallah bazakiyi kukan shigowa zuriar muba da yardar Allah, Barema wannan ja'irin Abdulsamad duk Wanda ya damar Masa Mata Inayah ai nasan zaburewa zaiyi da rashin arziki kala kala Shima Kinga muna kaunarsa sosai Dan haka bazamu Bari matarsa ta Shiga damuwar dashima zai shigaba. Washe Baki su umma yaganah suka hau Yi suna Jin dadin sirikan da Inayah tasamu masu kaunarta. Murya a sanyaye Inayah ta bude Baki cikin girmamawa ta gaidasu tana Dan sake goge hawayenta. Inayah daina kukan kinji Inshallah Baki rabu da gida ba duk lokacinda kikaso gida zakizo ki gansu Kuma kin manta Anan Abdulsamad din yake aiki ne? Bawani dadewa zakuyi a Adamawanba zaku dawo Lagos mune ma zamu ringa zuwa dubaku basaikunyi wahalar zuwanba. Ahankali Inayah ta saki Dan siririn murmushi tana kallon su Anty Hafsat dake Mata dariya. Da Raha Haj balaraba tasake cewa" Inayah akwai sauran kuruciya kam, Gaki 'yar fari shiyasa aketa shagwaba ko? Nikam ma menene Ma'anar sunan Inayah Dan naji sunan shima na Yan shagwaba. Dariya sukai saidai anty Hafsat ce tace" Ma'anar sunan Inayah shine kyauta daga Allah, Kaman ace kyautar datazo wadda bayan Allah Babu Mai iya baka ita. Dukkaninsu murmushi sukai ana cigaba da Dan sake maganganu cikin Raha da mutuntawa har lokacin sallah yafara wucewa Dole suka tashi Dan gabatar da sallah. A dakin umma yaganah aka Kai su umma Hadizan suyi sallah sai alokacin Inayah tasamu ta Isa Palo gurin Heart dinta. Yana ganinta ya taso a natse tareda miqa hannunsa ahankali ya kamo nata hannun suka Isa kujera suka zauna Yana kallon fuskarta datai ja cikin damuwa da kulawa sosai yace" Baby sosai kikai kuka haka? Oh my God,why baby? Wasu hawayen takuma gangaro Masa tana sake narkar Masa da fuska tace" Heart Dan Allah karmu dade Adamawa da yawa mudawo Lagos da wuri. Numfashi ya sauke Yana goge mata hawayenta da tissue din dake palon cikin kulawa kaman ya janyota ya rungumo yace" Baby ki daina hawaye da damuwa please, Idan Dan zakibar gidane na miki alqawarin bazamu dauki lokaciba zamu dawo okay? Gyada Masa Kai tayi tana tsayar da hawayenta. Lallabata yayi takoma ciki Dan yin sallah shima ya fice zuwa qaramin masallacin dake gefen gidan yayo sallah Yana dawowa yace su umma su fito ya maidasu gida akwai baqinsa dasuka iso daga Adamawa yau Dan daurin aure zai samesu a hotels din dasuka sassauka su gaisa friends dinsane sosai. Yana harabar gidan jikin motarsa Yana jiransu saiga motar Abbi tashigo yadawo shima. Su umma Hadizan ne suka fito tareda su Anty Hafsat da Mimi dasuka rakosu harma da Inayah dake maqale gefen Haj balaraba tana sake rarrashinta cikin kauna da kulawa. Cikin maroon luxury motar Bentley bentayga yadawo gidan Dan haka suna ganin motar duk suka tsaya Dan gaidashi dakuma su umma Hadizan ma su gaisa tunda yariga yadawo. Cikin wani Sky blue tsadaddiyar soft Italian cashmere a jikinsa ya fito Fuskarsa fresh a kamile. Kyakkyawar fuskarsa ya juyo da ita ya kalli Inda suke gabaki dayansu sun tsaya suna jiran fitowarsa daga motar a girmame. Hasken fatarsa da dogon hancin zuwa haiba da kwarjini Mai yawa da Allah yayi Masa yasa dukkaninsu Babu Mai iya Masa kallon quru quru saidai a gaisa kana Dan sauke Kai a mutunce. Inayah ce tabar gefen Haj balaraba ta nufesa tana kallonsa cikin kulawa tace" Abbi barka da dawowa. Wani nutsatsen murmushi ya sakar Mata Yana amsawa Kai tsaye da kallon fuskarta datai ja sbd kuka a natse cikin lafazinsa masu nutsuwa yace" Duk kukan da kikaita yine wannan? Bata fuska tayi zatai magana anty have ta Dan qaraso kadan tana Masa sannu da zuwa cikin girmamawa tace" Sirikan Inayah dinne wato mahaifiyar Abdulsamad sukazo tareda yayar mahaifinsa zasu tafi ko zaku gaisa. Ok ba damuwa" Ya furta tareda qarasa tahowa cikin nutsuwa Inayah din na gefensa kaman Zata maqale Masa. Tunda suka doso su kowa ya sake Dan kame kansa suna rage kallonsu akansa sbd kam badai cika Ido da zallar haiba ba. Umma Hadiza datai Masa kallo daya taga fuskar kaman wadda ta sani Dan haka ita bata dauke idonta akansaba taci gaba da bude idanuwanta dakyau akansa. Dan juyawa kanta yayi kadan sbd toshewar Dan qwaqwalwanta ke Neman Yi gabaki daya da kamannin nasa. Baya wani kallon Mata Musamman su din dayaga ba laifi dattijai ne Dan haka a mutunce ya gaisa dasu ya kalli Abdulsamad dake nuna umma Hadiza yace" Sir wannan itace mahaifiyar tawa. Dan sake fuska Abbin yayi kadan tareda kallon umma Hadizan a natse yace" Barka da zuwa Haj, Ya hanya? Allah ya hutarda gajiya...... Tsit yayi bayan yasamu yakai qarshen gaisuwar a Dan rarrabe. Kallon fuskarta yakeyi dakyau cikin Dan basarwa sbd danne duk wani Abu dayake yunquro Masa cikin Rai. Mummunan bugawa Mai qarfi zuciyarsa tayi wadda bayajin yataba samun wannan bugawar. Sam Bai nuna halinda yashigaba saima juyawa da yayi ya wuce ciki Yana musu a sauka lafiya. Mutuwar tsayece da daukewar hankali na daqiqu agurin ya Kama Hadiza Saida Haj balaraba ta Dan girgizata tana ambatar sunanta. Kasa motsi tayi sai kawai sukaga tana neman zubewa sbd duhun dayake Neman rufe idonta da qyar ta iya bude Baki murya a hargitse ta furta" BP Dina ya hau sosai please ku kaini gida Nasha magani bana gani sosai. Hankali tashe Haj balaraba da Abdulsamad din suka kamata ta shiga mota dukkanin jikinta na rawa a rude sukabar gidan. Da tausayin umma Hadizan su Inayah suka koma cikin gida Bata tsaya komaiba ta nufi sashen mahaifinta. Zaune yake numfashinsa na Dan fita da sauri Qananun zufa na tsatsafo Masa a goshi da alama Yana Jan numfashi ne dake Neman qwace Masa da qyar. Da gudu tayo kansa tana Kiran sunansa hankali tashe da firgici Dan Bata taba ganinsa hakaba. Bai dago ya kalletaba ya karba tissue din datake goge Masa zufa Ya Dan kame kansa Yana kokarin basarwa a hankali yace" Ya Isa haka, I'm okay kije Kawai. No Abbi bakada lfy Kana gumi fa. Ahankali ya furta" I think my BP dropped. Wat?" Tafada da sauri tana kallon yanayinsa. Juyawa tayi da sauri tana cewa" Bara naduba. BP monitoring machine harma dasu sphygmomanometer ta dauko da sauri tadawo cikin damuwa sosai. A tsaye ta taddasa kaman ba Wanda tabari Yana Dan hada gumi ba da jajayen Ido. Da mamaki ta tsaya da Kaya a hannunta tana kallonsa cikin mamaki da kulawa tace" Abbi? Magana zatai ya Dan waiwayo ya kalleta a Dan kame yace" Kibarshi kawai ya wuce Zanyi baqi yanzu ki koma ciki. Kallonsa tayi a marairaice da fuska Zata Kira sunansa da 'dan daga murya yace" Nace kije Inayah. Hawayen tashin hankali da tsoro taji suna Shirin gangaro Mata sbd yaune karon farko da Abbi yayi Mata tsawa tunda dai ta girma tasan kanta. ##MAMUH# #AYSHATOUH MRS AA MAJEED #LOVE/ROMANCE/MARRIAGE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/26, 8:44 PM] Sweet sis: *_27_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Kasa riqe hawayenta tayi suka gangaro Mata ta juya a sanyaye tana Satan kallonsa Zata fice ya sauke wani boyayyan numfashi tareda ajiyar zuciya Mai tafe da hucin zafin da Kai da kirjinsa suka dauka a natse Yana sake kame kansa da basar da yanayin dayake ciki ya bude Baki yakira sunanta a natse. Da sauri ta juyo ta dawo Dan dama bason tafiyar takeyiba ta kallesa tana share hawayenta tace" Na'am Abbi. Sake sauke ajiyar zuciya yayi wannan karon kansa na qara daukan zafi Mai tsanani kawai dannewa yakeyi Yana basarwa kada hankalin 'yarsa ya tashi babban burinsa a yanzu ya karkata akan baya kauna ko kadan bare fatan wani illa yazo ya gifta a cikin auren Nan da zaa daura gobe dan kuwa wannan karon aka fasa auren 'yarsa Allah ne kawai zai Raya Masa ita sbd gargadin da likitanta yabasu akan sake shigarta tashin hankali., Komai zai iya faruwa da ita idan takuma shiga wani mummunan shock na tashin hankali, Ganin wannan matar ya girgiza kansa da tun tsawon shekaru masu tsayi kan ya bushe, Ganin mahaifiyar Abdulsamad babbar masiface tabbas Zata bayyana Dan kuwa idan itace mahaifiyar Abdulsamad akwai gagarumar matsala. Meyake Shirin faruwa da 'yarsa idan komai ya lalace a daidai wannan gabar? Sake Kiran sunansa Inayah tayi cikin sanyin murya ganin yanda yayi shiru kaman Yana nazarin wani abun. Waiwayowa yayi ya kalleta da fuskar kulawa yace" Kukan barin gidan ya isa haka Inayah, Idan kina wannan kukan zan daga auren zuwa nxt month saiki sake cire kewan gida da kyau. Murmushi tayi tana share hawayenta tace" Na Dena kukan Abbi. Wani murmushin Dole ya saki Yana sake boye damuwarsa yayi maga Yan maganganun dasuka sanyata sakewa sai gata tana dariya Wanda shikuma hakan yasake caza kansa akan abinda zai iya zuwa ya komo. Lokacin sallar ishai dayayine yasanta ficewa daga palon Abbin Takoma. Tana fita ya sauke wata nutsatsiyar ajiyar zuciya idanuwansa na neman sauyawa. Miqewa yayi ya fice zuwa masallacin gidansa sallar ishai. Ana Gama sallar yadawo ya rufe sashensa ya zauna Dan tattara abinda yake yawo cikin kansa Yana Neman juyawa. Dafe gashi yayi Yana Jin gaban kansa kaman zaiyi bindiga tsabar nauyi da zafin daya dauka. Innalillahi wainnan ilaihrrjiun, Meyesa wannan matar da Baya fatan sake ganin fuskarta har abada Zata bayyana rayuwarsa da 'yarsa a daidai wannan lokacin Kuma ta bullo ta mabulla mafi firgici da tashin hankali. Tun a shekarun baya tsanarta ta ginu cikin ransa tsanarda tasa ya rufe shafinta ruf daga rayuwarsa gabaki daya Dan ko a kamanni baya fatan sake ganin Mai kamarta, Shin ita dince ma kuwa wadda yake tunani kokuwa? Bazai taba manta kamannintaba sbd itace ta taka mahimmiyar rawa gurin ruguza rayuwarsa a karon farko, Itace wadda ta wargaza buri da gatansa na zama cikin iyaye da 'yan uwansa tasakashi a matsatsen hali mafi matsuwa da Muni. Kamanninta Zane suke da baqin alqalami a idanuwansa, 'yarsa Inayah da girman mahimmancinta da qauna Mai tsanani ta uba da 'ya dayake Mata yasa ya yafewa matar Nan Amma Kuma har abada bayajin zai iya cire tsanarta Mai girma a ransa bare kallonta da daraja ko qima. Haduwarsu ta farko da ita Bata Zama Alkhairi ba Dan hakan ko yanzu yasan bayyanuwarta rayuwarsa ba Alkhairi bane a rayuwarsa data 'yarsa Dan haka Dole yanason Jin amsa biyu rak daga bakinta daga ya samu amsoshinsu bazata Kuma ganinsaba dagashi har 'yarsa har abada. Shi idan Yana cikin damuwa ko tashin hankali Sam baa wani ganewa sbd alokacin nutsuwarsa da kamewarsa take fin yawa, Shiru yakeyi Yana nazari batareda buqatan hayaniya ko katse Masa nazariba shiyasa su Inayah dasun gansa irin yanayin suke yin tsit gidan duk da dama ba hayaniya ce dasuba gidansu. *******Qarfe goma da mintuna Ashirin ya fito harabar gidan sanye da black hoodie Thom Browne Riga da wando masu kauri ya nufa White jaguar motarsa ya bude ya shiga tareda tada motar ya nufi gate dama tuni Bosco yaga fitowarsa da sauri ya bude Masa gate ya fice. Yana fitowa daga street din gidansa motar Abdulsamad Tasha hanasa tareda danno Masa full light. Wani banzan numfashi ya saki tareda Dan juyar da kansa cikin takaici da baqin ciki ahankali yace" Wannan matar tabbas zatasan waye AA MAJEED. Babu tantama yasan itace a motar Abdulsamad din Itama Babu tantama dama tasan yau komai dare saiya fito nemanta sbd dukkanin Susan amsar tambaya daddaya dake zukatansu kafin daurin auren gobe Dan kuwa amsoshin tambayar dake ran kowannensu itace future din yayansu da zaa daurawa aure gobe Dan haka a wahalce ta saci jiki ta fito bayan tasa Abdul yabar musu motarsa incase idan ciwonta zai tashi da dare su wuce asibiti ya samesu acan. Batada lafiya sbd jininta yakai kololuwar hawa ko tsayuwa Bata iyawa sosai Amma bazata iya kwana ayauba batareda tayi magana da mahaifin Inayah ba, Zuciyarta bugawa zatai da sake sake da fargaba harma da tashin hankali matuqar yau batai magana dashiba taji abinda takeson ji. Da wani irin speed ya fizgi motarsa yabi ta gefen motarta ya wuce Yana Jin tsohon tabon baqin cikin daya dade Yana dannewa yana taso Masa. Ribas tayi ta rufa Masa da gudu itama duk da qarfin haline kawai takeyi Dan sosai takejin kaman zuciyarta Zata fashe, Tsohon famin baqin ciki da quncin da tarin Dana sanin gaske datake dannewa shekaru masu yawa ne suke birkito Mata tako Ina tanajin zuciyarta na azabar zafi da qunci. Baisan tasan Lagos ba sosai Dan haka ya ringa ratsa manyan anguwannin dazai bacewa ganinta saidai sosai ta nace tana binsa idanuwanta ma tuni suka fara tsiyayar hawaye Dan kuwa hakan ya tabbatar Mata da tunaninta Gaskia ne akansa shine Wanda ta gudu tabarwa Jaririyarta AYSHATOUH. A daidai gaban ma'aikatarsa ya faka motarsa tareda qin fitowa zuciyarsa na qara daukan wani irin zafi da bacin Rai da baqin ciki Mai zafin gaske. Baya kaunar ganin fuskarta sbd ganin fuskarta na tunatar dashi kowace daqiqa na lokacinda ya rabu da gatansa da iyayensa harma da farin cikinsa akanta. Jajir idanuwansa suka kada sosai sbd tsananin zafi da zuciyarsa ke dauka. Bude motar tayi ya fito ya wuce zuwa ciki tabi bayansa da sauri itama hawayenta na tsananta gudu kaman yanda bugun zuciyarta da tashin hankalinta ke tsananta. Cak suka tsaya a tsakiyar office dinsa koina tsit ba kowa sai securities din ma'aikatarsa. Zubewa tayi agabansa tareda fashewa kawai da kuka Mai tsanani da taba zuciya sbd Batasan me Zata fara fadaba ko tambaya. Kukanta sake zafafa ransa yakeyi Musamman wannan sautin kukan shine ta ringa Yi Masa a wancan lokacin batareda da duba girmewar datai masaba ta lalata rayuwar 'dan matashin dake tsakiyar karatunsa cikin kwanciyar hankali da kulawar iyaye. Wani mummunan 'daci da qunci Mai nauyi ya hadiye ta wuyansa tareda juyowa ya kalleta da idanuwansa dasukai jajir Kai tsaye Yana danne fushinsa da nutsuwa yace" Bansankiba ko wancan lokacin hakama bansakinba a yanzu, Banda alaqa kowace iri dake bayan wadda zamu qulla a goben ta auren 'yayanmu Kuma itama zan bar 'danki ne kawai ya auri 'yata sbd farin cikinta dakuma kaucewa abinda zai sameta idan akai fashin auren Dan haka ki amsa mun tambaya daya rak itama sbd kaucewa Mummunan Al'amari. Kuka takeyi sosai sbd tasan Babu abinda daga ita harshi sukewa tsoro kaman alaqar 'yayansu Saidai kafin komai yabiyo baya na abinda ya faru a baya shine susan makomar alaqar dake Shirin qulluwa goben wadda tuna abinda zai biyo batama tashin hankali ne da wata babbar masifar. Cikeda baqin ciki yakuma kallonta Jin batada niyar amsawa sai kukan datake Yi kaman zata shide., Zafi da quna ransa ke qarawa Dan haka ya juya yanajin kansa na sake yamutsewa da babban tashin hankalin da Inayah Zata iya Shiga akan wannan matar... Yanada zafin zuciyan gaske Mai tsanani Amma tunda rayuwarsa ta sauya ya iya boyewa da dannewa Babu Mai gane yanayinsa duk kafiyarka Amma yau zafin zuciyan tasa ya gagara dannuwa a zafafe ya buga glass table din dake gefensa take ya tarwatse da qara Mai tsanani Saida Hadizan ta firgita tana dagowa da jajayen idanuwanta dasuka rine take sbd tashin hankali Mai tsanani da kuka. Miqewa tsaye tayi hawayenta har lokakacin basu tsayaba Dan ba tsayawar zasuyiba muryarta na rawa tace" Ina AYSHATOUH??? Wani matsiyacin kallon baqin ciki da takaici yayi Mata yanajin duk duniya Babu Wanda yakai Hadiza sonkai Ya dauke Kai Yana kokarin danne kansa daga zafin fushin dake taso Masa Kai tsaye yace" Idan kece kika haifi Abdulsamad menene alaqarki da 'yar da kika Yar???? Gangaro Mata hawayen daci da danasani sukai muryarta a dashe tace" 'yatace nice na haifeta da ita da Abdulsamad duk nice na haifesu Kuma mahaifinsu daya idan Inayah itace AYSHATOUH to uwarsu daya ubansu daya da Abdulsamad.......""da kuka ta qarasa zancen Dan kuwa babbar masifa ta diro ta sameta a zazzafan tabon ciwon qunci.. Idan Abdul Mai samu Inayah ba haukacewa zaiyi"" innalillahi wainnan ilaihrrjiun Na shiga uku Ni Hadiza rayuwata tasake shiga wata babbar jarabawar Mai nauyi... Mutuwar tsayece ta samu AA MAJEED Dan kuwa yayi fargabar Jin hakan Amma Bai yarda da zaiji tabbatar hakan daga bakintaba. Qarasa rikidewa idanuwansa sukai jajir yanajin wani gumin zafi da babban tashin hankali na shigarsa. Abinda yakeson tabbatarwa kenan daga bakinta dan shakku da fargaban daya shigesa na iya yiyiwar hakan Kuma ta tabbatar Masa Dan haka baida sauran buqata da ganinta kona second daya Dan a Karo na biyu ta sake wargaza rayuwar 'yarsa. Juyawa yayi Yanayinsa na ninkuwa ada sauti Mai 'dacin gaske yace" Zaki iya komawa ki sanar da danki dagani har 'yata yanzu bamuda alaqa daku Auren anfasa. Juyawa yayi zai fice Dan hankalinsa gabaki daya yagama yamutsewa qarshe kaman kansa zai buga Inayah yakejin tashin hankalin yanda Zata karba kaddarar rashin auren Abdulsamad sbd bazai taba fada Mata dalilinba Dan kuwa bazai taba barin Hadiza ta kusantar Masa 'ya ba. Da saurin Hadiza Tasha gabansa tana rokonsa cikeda tarin nadama tace" Dan Allah kafadamun idan Inayah ce Ayshatouh na, Har abada nasan bazan taba samun yafita a zuciyarkaba Amma Dan Allah kada ka hanani Ayshatouh Inayah, Wlh nayi Dana sani nayi nadama..... Sauraronta tafasashi sukeyi tako Ina Dan shi kansa komai ya kunce Masa a yanzu. Wucewa yayi Yana daga wayarsa zuciyarsa a quntace ya saka kirana Mr Al-amen Yana dauka Kai tsaye yace" Ai Mana booking tickets da komai na tafiya nida familyna gobe kafin 12 zamu bar qasar.... ##MAMUH ##MARRIAGE/LOVE ##AYSHATOUH INAYAH AA MAJEED _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/26, 8:45 PM] Sweet sis: *_28_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Tashin hankali Hadiza tashiga Jin abinda ya fada a firgice Tasha gabansa tana rokonsa cikin mummunan hali na kuka tana rokon ya hadata da 'yarta Ayshatouh Inayah. Numfashi ya sauke a hankali tareda ajiyar zuciya Mai dumi kafin ya Dan dago ya kalleta kadan cikin nutsuwa kaman Wanda zuciyarsa ba tsananin quna takeba da 'daci takeba yace" Babban taimakon da zakiyiwa kanki da Abdulsamad shine ki cirewa ranki da kanki tunanin sanin mahaifin Inayah bare ita Inayah din, Inayah 'yatace Kuma Babu Wanda zaizo Rana tsaka yacemun shine ya haifeta, Bansankiba Baku nada alaqan komai dake.. Ki nema yarki a Inda kikasan son zuciya yasa kin barta. Zafi maganganunsa suka farai Mata sbd duk yanda tayi aikin son zuciya abaya Inayah dai yartace Kuma tayi danasani daga ranar data gudu ta barta. Wlh bazata yardaba taga yarta sannan ya dauketa su bar qasar tasan bazata Kuma ganintaba har abada Dan haka cikin rashin tunani da tauna zancen abinda yafada matan tace" Har abada saidai ka Kira kanka matsayin mariqinta uban daya raineta Amma bazaka taba sauyata daga nice wadda na dauka cikintaba na haifeta. Bai tsaya saurarentaba ya fito Kai tsaye yashiga motarsa Yana cewa security a rufe Masa koina. Cikin zafi ga figi motarsa da matsiyacin speed yabar gurin batareda yajira ganin fitowartaba. Ikon Allah ne kawai da nutsuwa dayayita kokarin sakawa kansa sbd kada su Inayah su gano halinda yake ciki yakaisa gida lfy. Yana parking ya fito ya nufi kofar dazata kaisa palonsa na farko direct batareda yabi kofar dazata bi dashi ta palon su Inayah ba kafin ya Isa nasa palon. Yana Shiga palonsa Kai tsaye hanyar bedroom dinsa ya nufa ya shige tareda Zama kan luxury italian sofa dake dakin ya rintse idanuwansa dasukai jajir. Ajiyar zuciya yafara jerowa da numfashi Mai zafi yanajin damuwa da tashin hankali Mai tsananin wannan auren da Allah yasa baa dauraba da tako Ina masifun da tashin hankalin bullowa zaiyi, To Amma babban tashin hankalin da damuwar shine ta yanda Inayah Zata karbi fashin aurenta akaro kusan na hudu. Tayaya zai iya taro matsalar da Zata iya samunta? Innalillahi wainnan ilaihrrjiun. Miqewa yayi ya nufa toilet ya sakarwa kansa daya dauki tsananin zafi ruwa yanajin zafin kan na tsananta. Da ruwan dumi yayi wanka ya fito ya saka blue pyjamas sai sanyayyan Chanel na jiki ya kashe wayarsa tareda jefarwa gefe ya hau gado zauna Dan yasan yau koda qyaftawar Ido bazai rintsaba sbd fitina da tashin hankalin dayake jiransu da safe. Umma Hadiza ma cikin masifaffen tashin hankali da tsoron AA MAJEED yabar qasar da inayah ta iso gida jikinta Babu Inda baya kakkarwa ta silale tashige dakinta batareda kowa yasan fitarta da dawowartaba ta rufe daki tareda zubewa qasa tafara kuka Mara sauti tana cewa" Ya Allah kagani rashin mafita da madafa da Sharrin shedan ya hanani tawakkali na gudu nabar 'yata badan bana tsananin sontaba ya Allah nayi shekaru cikin qunci da damuwa da tawakkali ya Allah kada kabari wannan bawa naka ya tafi da 'yata wata qasarda bazan Kuma jinsu ko ganinsu.,,ya Allah ka duba maraicina ka hadani da 'yata, Allah ka kawo Mana sassaucin wannan masifar data kunne Kai da tashin hankalin dazai biyo goben sanadin fashin auren yaran Nan. Kuka takeyi sosai tana rokon Allah sassauci da mafita. ****Daga AA MAJEED har umma Hadizan Babu Wanda ya rintsa yanda sukaga Rana haka sukaga dare da safiya. A gidan A MAJEED da zallar farin ciki iyalan gidan suka tashi Dan ko su Anty Hafsat duk a gidan takwana da yaranta gasu Safnah da Neesah dasu Daman tuni suka tare sai Yan uwan umma yaganah guda biyu dasuka zo bikin Dan tayata Murna dakuma samun abun arziki. Dr farhat dasu Mimi ma tunda safe suka iso gidan kaman dasu aka kwana. Kowa farin cikinsa bayyananne ne sbd duka aurarrakinta da ake fasawa Babu Wanda yazo ranar Daurin auren  sai wannan yau gashi Allah yayi anzo daurin auren a wanni kadan ne suka rage tazamata cikakkiyar matar Heart dinta Abdulsamad salees halak malak. Cikin kayan baccin data kwana dasu Riga sa wando masu santsi tafito da hula akanta fuskarta da dukkanin fatar jikinta sunyi fresh sai sheqin kyau da gyara sukeyi gashi yanayin data fito din kaman wata qaramar yarinya. Kai tsaye dining ta nufa tana cewa" Yunwa nakeji zubbi kawon tea nafara sha. Tea da doughnuts masu laushi guda uku zubbi takawo Mata tana cewa" Mint tea din Sir is ready Zaa shirya Masa ne a dining kokuwa? Tana Shan tea dinta tace" No ki shirya zan Kai Masa palonsa yau da mutane a gidan bazai shigo ciki ba, Harda dessert din kin kammala hada Masa? Yes Ma. Ok kije ki hado zan Kai Masa. Ok Ma. Juyawa tayi ta koma kitchen din Dan hadowa takawo Mata. Wayarta ta daga tana kokarin Nemo numbern Heart sai gashi kiransa yashigo wayarta da farin ciki bayyane kan fuskar ta dauka da Yar muryarta Mai shagwaba tace" Good morning Heart. Wani sanyin farin cikine yakuma cika ransa sbd ranar yau din daqyar yaga garin ya waye Cikin wani irin girmammen farin ciki yake Mai nutsuwa, Allah yau yacika Masa burinsa na mallakar Inayah amatsayin matarsa dazata Zama uwar yayansa. Ji yayima farin cikin yasaka jikinsa sanyi Musamman data Kuma kiran sunansa da HEART. Muryarsa a sanyaye yace" Morning baby, Kin tashi lfy? Yaya shirye shiryen da hayaniyar su Anty Hafsat? Murmushi kawai tayi Tana cewa" Idan anty Hafsat tajika Zata sa a 'daga tafiyan Amarya yau sai wani satin. Wat? aikuwa Dana tare a gidan Abbi Nima. Dariya tayi tana cewa" Zan kaiwa Abbi breakfast zankiraka idan nafito Kisses. Murmushi kawai yayi Yana kashe wayar gabaki daya muryarta ta kashe Masa jiki yayi sanyi sosai, Jin yayi har zuciyarsa na yin sanyi. Daukeda tray ta nufi hanyar palon Abbi tana murmushin wayar data Gama da Heart. Knocking kofar tayi ahankali tareda budewa ta shigo da sallama tana kallon palon da Babu kowa sai Sanyin AC dake aiki da Qamshin turarensa daya Gama Kama koina na palon. Hanyar bedroom dinsa ta kalla tana ajiye tray din kan table. Tabaro wayarta bare takirasa ta sanar Masa tana Palo Dan haka tana ajiyewa  ta juya ta fice. Breakfast ta tadda duka kowa nayi wasu a dining wasu a dakin umma yaganah Dan haka tayi joining Dinsu itama tana cin Doyan da aka soya kadan. Har qarfe Tara ta buga da mintuna Abbi Bai fitoba sbd baisan ta Yaya zaifara cewa su Inayah su shiryaba zasu bar qasar ayau datake ganin ranar Daurin aurentane. Yarasa ta Ina zai fara, Ta Ina zai tarbo wannan rikitaccen matsatsen yanayin. Innalillahi wainnan ilaihrrjiun. Gashi jama'a da dama manyan tunanensu sai kiransa akeyi ana tayasa Murna wainda bazasu samu damar zuwaba basa qasar dama wainda suna qasar uzuri bazai basu Daman halartaba. Kansa Neman bugawa yakeyi, Duk wannan masifar damuwarsa da tashin hankalinsa na Inayah ne da Zata shiga mummunan hali daga lokacinda aka Kuma fasa aurenta dakuma wannan mummunan labarin da har abada baya kaunar tajisa cewan bashine mahaifinta Wanda ya haifetaba,ko alaqan Jini basuda a taqaicema baisan mahaifinta da mahaifiyarta ba Dan zuciyarsama badan ya tattabar akansaba cewa uwa na iya yafe danta da bama zai yarda da cewan Hadiza ce ta Haifa Inayah ba Dan uwa Bata iya Yar da 'danta To Amma hakan tafaru dashi sbd tasa uwar ta yafesa sbd zarginsa na aikata abinda Bai aikataba bayajin ma zai taba iya aikatawa. Tayaya zai Bari Inayah tasan wannan 'datacciyar Gaskiar? Baya fatan ko kadan ta 'dandana 'daci Mai kaifin gaske da ciwon uwa mahaifiyarka ta gujeka sbd wani dalilin banza Wanda Koda bakada uba tunda qaddara ta Samar da Kai baka cancanta hakanba. ****Hadiza Koda safiyar ta waye tagama fita nutsuwa da hayyacinta, Bata ji Bata gani matuqar ba 'yarta Ayshatouh AA MAJEED yadawo Mata da itaba, Tayi gangancin rabuwa da yarta shekarun baya Amma yanzu ko zaisa a daureta asibitin mahaukata sbd arzikinsa wlh bazata yardaba saiya Bata yarta tadawo hannunta ciki kuwa harda Koda Zata qaryata kanta agurinsa da cewa ba itace ta Haifa Abdulsamad ba idan yaso a daura auren su tafi da Inayah Adamawa suna zuwa can ta fada Gaskia a Raba auren 'yarta dai tadawo hannunta. Wannan rubabben tunanin shedan ya qissima Mata ta tashi hankali tashe Musamman ganin lokaci na tafiya tasan rasai AA MAJEED din zai bar qasar da inayah kafin lokacin daurin aure Dan haka a rikice ta iya watsa ruwa ta kimtsa kanta sbd kada Wanda yagano halinda take ciki na firgici da tashin hankali. Da mamaki su Haj balaraba suke kallonta lokacinda ta fito dakinta a shirye tsaf harda gilashin fuska sbd kada a gano tsananin kumburin da idanuwanta sukai Gashi iyaye maza yanne da qannen mahaifinsu Abdulsamad din sun iso yanzu da safen daga Adamawa suna hanyar isowa gidan kafin lokacin daurin auren yaqarasa Amma ta fito tana cewa zataje karbo saqo tadawo. Kafin Haj balaraba data saki bakin kallonta tayi mgn umma Hadizan ta wuce hannuwanta na rawa sosai keys din motar ma daqyar ta iya damqesu suka tsaya a hannunta ta Isa motar ta bude ta shige da gudu tabar gidan tana kallon agogo. A daidai wannan lokacin Abbi yagama yanke shawarar tura Inayah da umma yaganah su fara wucewa qarfe goma Sha daya jirginsu zai tashi shikuma zai tsaya ya bawa mutanensa dasuka zozzo hakurin fashin auren batareda Inayah tasan fashin auren akaiba idan yaso Bayan kwana biyu zai samesu acan yasan yanda zai rarrasheta ya fahimtar da ita fashin auren ta wata hanyar. Dan hakan Kai tsaye yakira umma yaganah a waya ya sanar da ita ta shirya itada Inayah akwai Inda zasu qarfe Sha daya kafin lokacin daurin aure. Yana fadan hakan ya kashe wayarsa sbd kada tayi Masa tambayar komai. Agogo ya kalla yaga qarfe goma da kusan rabi Dan haka ya miqe ya nufi toilet yayo wanka cikin nutsuwa. Daure da Brown towel mai kauri a qugunsa ya fito farar fatarsa sai tsiyayar ruwan wanka takeyi so freaking fresh. Gaban mirror ya nufa ya tsaya ahankali Dan baya Zama gaban mirror kaman mace saidai ya tsaya a tsaye yayi komai. Lumin body moisture ya shafa tareda fesa spray din Paco Rabanne Yayi brushing sumar kansa tareda sauran Shirin daya saba yagama ya wuce closet din tarin kayansa. ##MAMUH# ##MARRIAGE/INAYAH. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/26, 8:45 PM] Sweet sis: *_29_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Qarfe goma da minti arbain su Umma yaganah da Inayah suka fito tana shirye cikin Tsadadden red Australian lace mara nauyi dinkin fitted gown daya zauna jikinta da kyau Shafaffen cikinta zuwa hips dinta dake Dan baje sun fito da kyau cikin kayan ta yafo 3D veil dinta kayan touches na lace din. Zallan qamshi Mai sanyi da nutsuwa take fitarwa Kyakkyawar fuskarta sai sheqin farin cikin dake ranta take fitarwa. Suna fitowa harabar gidan Abbi ma na fitowa Sanye cikin wata fitinanniyar farar shadda Mai tsadar gaske da laushi. Basu taba ganinsa da babbar rigaba sai yau shima sbd Inayah data nace abbin saiya saka Kaya masu babban Riga a aurenta sbd kada mutane da dangin mijinta su ringa cewa babanta Bai manyantaba sosai. Qamshinsa ne ya gauraya iskar gurin suka zuba Masa Ido dukkaninsu Musamman Inayah dake washe bakin farin ciki tana cewa Abbinta na Musamman ne aduk Inda yaje. Neesah kuwa dasu Safnah take kowaccensu taji da Abbi matsayin yayan Inayah ne ba mahaifiba Babu abinda zai hanasu aurensa. Umma yaganah ma cikin kulawa da farin cikin ganinsa cikin Shiri da adon auren Inayah a hankali tace" Masha Allah laquwata. Allah yaqaro girma da 'daukaka Yabaka tsari da kariya Yayi maka albarka tareda kawo dawamammen farin ciki rayuwarka data zuriarka. Amin" Su Safnah dasuka jita suka amsa suna dauke idonsu daga kallonsa sbd grima da kwarjininsa. Ahankali ya kalli fuskar Inayah ganin farin cikin dake tattareda kowane irin yanayinta, Ta Bangare daya baisan tayaya zai Samar dasuba qasar zasu Bari yau. A natse fuskarta daukeda murmushi tace" Abbi you look handsome, and... Katseta yayi a nutse da cewa" Inayah kuje karkuyi latti Inda zaa kaiku. Kallonsa tayi a natse tana cewa "Abbi Ina zamuje? Dan rufe idonsa yayi ya bude tareda kallonta cikin tsananin kulawa yace, "Idan kunje Zaki gani. Da murmushi akan fuskarta tace" Okay. Umma yaganah ya kalla sukai gaisuwar safe d basuyiba tunda ba haduwa sukaiba. Su Neesah ma da Safnah cikin girmamawa sosai suka Masa Ina kwana kafin ya kalli umma yagana a natse cikin Dan takaita magana yace" Idan kunje komai na hannun Ahmed zai damqa miki komai Zanzo daga baya. Tsit suka Dan Yi da mamaki suna kallonsa duk da basu gane komaiba akan Inda zasuje sai jikin umma yagana yayi sanyi taji zuciyarta na Neman shiga wasi wasi. Inayah ma jikin nata taji yafara sanyi take ta kalli abbin da rauni Amma batace komaiba. Juyawa yayi yana kokarin Isa motarsa aka bude gate motar CM tashigo ko qarasa rufe gate baayiba motar Dr Abdul ta Sako Kai itama. Umma Hadiza ce aciki Kuma tanayin parking idonta ya sauka kan Ayshatunta take taji wasu hawayen da tsananin kaunar yarta suna finciko Mata tako Ina, Kaunace Mai tsananin gaske wadda uwa kewa 'danta Bayan tacire ran samu ko ganinsa har abada. Hawaye takeyi sosai tana kallon Inayah din tanajin tamkar taje ta rungumota tayita kissing dinta tana fada Mata yanda take kaunarta da qaddarar datashiga akan cikinta. Wani zafi da tirnikin bacin Rai da tashin hankali ne ya taso Mata ganin suna kokarin shiga mota tasan wlh qasar zasu Bari suna fita gidan yau bazata Kuma ganin 'yartaba Wanda haukar da Allah ya taqaita Mata lokacinda tayi danasani tashiga Neman yarta to haukar zatayi yanzu matuqar takuma rasa Ayshatouh. Hankali tashe ta fito motar da gudu ta nufosu Inayah tana Kiran sunanta. Dakatawa umma yaganah tafarayi tana kallon Hadizan kafin Inayah itama ta dakata suna kallonta cikeda mamaki. Inayah kuma umman na isowa gabansu ta kalleta da kyau taga yanda idanuwanta da fuskarta sukai jajir tashin hankali bayyane kan fuskar umma Hadizan Wani mummunan bugawa zuciyar Inayah tayi har Saida ta dafa Neesah dake gefenta. Muryarta na rawa itada umma yagana ma data shiga zullumin abinda zasuji Dan dagani ba lafiyaba murya a hautsine sukace" Umma Hadiza.... Kasa tambayar abinda ke faruwa sukai sbd tsoron abinda zasuji. Kai tsaye Inayah taji wani jiri na Neman dibanta kafin tayi kokarin dafe kanta taji muryar Umma Hadiza a hargitse tana cewa" Dan Allah kadaku tafi wlh qasar zaku Bari kuna fita, Aurenki Inayah da Abdul bazai fas.... Inayah Bata gama jiba qafafuwanta suka yanke zuciyarta na neman bugawa ta tabbatar fasa aurenta yanzuma akai ko ake neman Yi. Innalillahi wainnan ilaihrrjiun" Mezan gani hakan Ni yaganah, Innalillahi, innalillahi. Hawayene ke kokarin gangarowa Inayah Amma tashin hankali yaqi Bari umma yaganah dasu Neesah da duk suka shiga tension din suka fara kokarin kamata sukoma ciki da ita Umma Hadiza ma cikin tsananin tashin hankali da dimuwa ta ringa maimaita ba fasawa nace anyiba Dan Allah Inayah karki shiga wani hali, Babu fashi aurenki da Abdulsamad, Zaa daura zamu tafi dake adamwa zan Baki duk wata soyayyar uwa da Baki samuba, Inayah, Inayah. Sam Inayah Bata gane kalma daya da umman Abdul din take fada sbd zuciyarta bugawa takeyi sosai da tashin hankali da attack data samu take Dan hakan komai Bata ganewa sai rawa da jikinta keyi. Su umma yaganah kuwa take ta fara tunanin daqyar idan umman Abdul nada lafiyar qwaqwalwa sbd duk tabi ta rude da Kiran Inayah da suna biyu. Abbi da hankalinsa nakan CM dayazo daukansa su wuce daurin auren tare Bai lurada Hadiza ce tashigo a motar Dr Abdul ba Saida yaji salatin da umma yaganah ke qwalawa da qarfi hankalinsu duk yakoma Kai cikeda mamaki da zafin zuciya Mai qarfi ya kalli umma Hadiza Yana kallon 'yarsa dake Neman siqewa cikin tashin hankali numfashinta na neman gagararta. Cikin bacin Rai Mai qarfi ya qaraso gurin tareda kallon umma yaganah yace" Ku kaita ciki Dr farhat ta dubata da sauri. Kan umma Hadiza dake kokarin binsu hankali tashe ya maida kallonsa idanuwansa na Neman sauyawa yace" Ni Zaki sama da duk abinda kikazo dashi, Me kika fadawa Inayah yasata cikin wannan halin? Ganin su umma yaganah Basu qarasa shigewa da Inayah ba yasashi juyawa tabiyo bayansa tana cewa" Dan girman Allah da manzansa kaban 'yata, Ka sanar da ita nice mahaifiyarta, Dan Allah kada ka cutatar da uwar dake cikin qunci tsawon shekaru ta hanyar Hana Mata 'yarta.... Babban palonsa suka shigo ta tsaya gabansa idanuwanta na zubda hawaye sosai cikin mawuyacin hali tafara rokonsa akan ya sanar da Inayah itace mahaifiyarta. Mamakine ya Kama CM dake tareda A A MAJEED din tako Ina. Idan ya fahimta Kuma yagane wannan matar Inayah take Kiran 'yartace. Itace mahaifiyar Inayah? MAJEED da idanuwansa ke bayyanarda tsananin bacin ransa da fushinsa ya kalla yasan yau kam ransa yakai kololuwar baci tunda ya bayyanarda fushinsa. Bai iya cewa umma Hadiza komaiba sbd baimasan mezai fada mataba, Da alama tanada ciwon Kai Dan hakan tako Ina lalata Masa Al'amura zatai. Cikin kosawa da ganinta gabansa ya bude Baki a gundure yace. "Me kika fadawa Inayah da har kika data cikin wancan halin datake ciki? Idan kin sanar da itane matsayinki a gunta kinyi babban kuskuren da.... Cikin sauri da bayyanarda gaskiyarta ta katsesa da cewa, "Banfada Mata komaiba Maganar aurenta da Abdul kawai nake fada musu. Wani irin rufe Ido yayi ya bude cikin baqin ciki da takaici yace" Kinsan shima hakan matsalar da Zaki haifar mata? Kinsan halinda Zata iya Shiga akan hakan? Meysa zakiyi kutse acikin Al'amarin da bakisan Yaya yake tafiyaba? Numfashi Mai zafi ya sauke tareda fitarda ajiyar zuciya Dan bazai iya wannan tashin hankalinba yanzu. dauke kallonsa daga kanta yayi a natse yace" Idan harkina kaunarta a matsayin uwa kaman yanda kika fada kibarta taci gaba da rayuwarta batareda kin dandana Mata 'dacin rashin karbuwa daga uwar data haifeta kokuma dacin hanyar da aka samar da ita. Maganarsa ta qarshe tayi mummunan girgiza, Kenan shima daukan yake ta hanyar banza ta samu Inayah tunda yaga ta gudu tabarta? Wasu hawayen baqin ciki Mai tsanani ne suka gangaro Mata ta dago da jajayen idanuwanta ta kallesa zuciyarta na quna da bacin Rai tace" Na tsaya rokonkane ka bayyanarwa 'yata nice na haifeta sbd nabaka haqqinka amatsayin Wanda ya reneta da Amana ba cutatarwa bawai Dan narasa damata ta uwa agaretaba. Kanason nuna dukiya ka rabani da 'yata rabuwar har abada Amma hakan bazai taba karbuwaba gurina. Wlh bazan yardaba Sharia Zata karbamun 'yata tadawo hannuna. Mamaki tafara basa ta yanda take iya furta kalamai batareda taji kunyar kantaba na abinda ta aikatawa 'yar a baya harma dashi. Idan tana maganar qarfin ikone To zai nuna Mata qarfin iko akan Inayah. Cikin sautin bayyanarda gajiya da lamarinta yace" Wannan shine Karo na qarshe da Zaki iya zuwa gidana ko kusantar daya daga cikin iyalin gidana, Zaki iya tafiya. Kallon baqin ciki da damuwa lokaci daya take Masa tace" Zantafi Amma kasani nice uwa dana Rena cikin Inayah nakuma haifeta har abada babu wani ko sunan dazai sauya mun matsayi akanta, Nice nafi kowa cikakkiyar dama da iko akanta, Kaikuma damarka da ikonka akan Inayah ya tsayane a matsayin mariki Kuma zai tsaya ahakan ne har abada. 'ya mace ce duk iko da isar da zaka nuna akanta saitabarka har abada sbd aure zatayi take gidan wani Kuma a qarqashinsa Dan hakan idan kafi qarfin hukuma bazakafi na shari'a ba, Sharia Zata dauke inayah daga hannunka tabani 'yata, Idanma shariar kafita ikone zamuga wannan sbd duk ikonka akanta bazaka taba aurentaba Dan kuwa aurene kawai zai riqe 'ya mace aguri wani ikon ya kasa dauketa dauketa Kuma da yardar Allah Inayah bazata rufa wata a hannunkaba saina karba Yana Koda ta hanyar kawo Mata wani mijin auren ne. Rintse idanuwansa yayi cikin takaici da baqin cikin ganin Hadiza agabansa. Duk shekarun mace hankalinta da tunaninta na banza ne lokuta da dama, Sam kansu toshewa yakeyi hat basusan me suke fadaba. Idan Hadiza na tunani haryanzu akan shari'a Zata karba Mata Inayah a hannunsa to zai sakata a spot dinda ko shariar bazata iya dauke inayah daga hannunsaba a gurin. Bai iya kallontaba sbd siqewa kai tsaye yace. Kije Ina jiran shariar. A fusace da baqin ciki ta juya tana hawaye sbd ba haka tasoba son tayi ya amince ya hadata da 'yarta idan Tai Masa barazana da sharia sbd tasan bazai taba son duniya tasan Inayah ba 'yarsa bace. CM da kansa yayi matuqar daurewa da daukan zafi kusan yagama gano kan zancen shine Inayah dai ba Amininsa neba ya haifeta Kuma wannan matar itace mahaifiyar tata. Baisan ya zancen yafaruba Amma tabbas a wannan tsukakken yanayin yasan akwai matsala Babba matuqar wannan Al'amarin zai shafa daurin auren yau. Agogo A MAJEED ya kalla yaga Sha daya da rabi harta fara wucwa. Bai iya cewa Amininsa komaiba yace su tafi kawai. Shima CM tunda ba qaramin yaro bane yasan yanzu ba lokacinda zai tsaya tambayar MAJEED din meyake faruwa bane saidai idan an natsa zafi da dacin ransa ya sauka. Suna fitowa Kai tsaye yabawa Bosco odar kada akuma barin motar Abdulsamad tashigo gidansa matuqar bashineba aciki. Kai tsaye babban masallacin dake kusada gidan iyayen CM suka nufa Inda anan ne zaai daurin auren dama. Mutane ne tako Ina sun cika anguwar ga securities da jamiaan tsaro kusan tako Ina sbd akwai manyan mutanensu dasun iso tuni Dan mintuna goma Sha takwas suka rage ga daurin auren. Wani irin zafi da 'dacin zuciya yakeji ganin tarin jama'ar dasukazo Dan sheda daurin auren ga dangin Abdul ma da dama sun iso shi kansa Abdulsamad din ya iso gurin cikin shigar alfarma ta angon dake cikin tsananin farin ciki. Qarfe goma Sha biyu daidai aka nutsu aka fara daurin auren Wanda CM ne da kansa yayi wakilcin Amarya mahaifinsa Alhaji babbah yayi wakilcin Ango sauyin daya faru tsananinsu take agurin. Kafin iyayen Abdulsamad su Ankara sukaji ana shelar an daura auren ABDULMAJEED ABDALLAH da INAYAH A MAJEED. #MAMUH# #AFADA ALKHAIRI KO AYI SHIRU/#MASU YI DANI A BAYANA. *_ZAFAFA BIYAR_* *_INAYAH_* _Mamuhgee_ *_GURBIN IDO_* _Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/26, 8:45 PM] Sweet sis: *_30_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Kusan da yawan jama'ar gurin Basu fahimci wane ABDULMAJEED din ake nufiba sai Amin kawai suke amsawa da ita suna qarawa da adduar zaman lafiya da albarkar aure sbd sunan Abdul din da aka ambata cikin sunan basu wani bambamceba tunda dai kowa yasan sunan Ango Abdul. Iyayen Abdulsamad Wakilansa sune suka saki Ido da Baki cikin zallar mamaki da firgici Jin andaura da wani Abdul din daba nasuba Dan Babu Wanda ya tsaya kawo wani rubabben tunanin AA MAJEED mahaifinta ake nufi. Shi kansa Abdulsamad kasa tantance meyake faruwa yayi saiyafara tunanin ko matsalar fadan sunan aka samu Mai fadar be kila ya rude ya fada sunan mahaifin Inayah a matsayin uba Kuma yadawo ya fada amatsayin Miki Wanda aka daura auren dashi. Jin zuciyarsa dai takasa yarda sai tsinkewa data farayi yasashi kokarin baro Inda yake Dan zuwa gaban wakilan daurin auren yaji wane rudadden ne Mai sanarwar dazai saka kansa kuncewa da zancensa. Kusan dai jama'a tsakani da Allah duk Basu ganeba idan ba wainda suke Yan uwan Abdulsamad ba sbd suka Sarai sunji ba sunan angonsu aka fadaba Sauran jama'a da Basu ganeba tunda ba hankali mutane ke badawa sosaiba gurin daurin aure sai an daura zu amsa da Amin da fatan Alkhairi su tafi Dan haka aka ringa gaggaisawa ana Allah sanya Alkhairi ana neman fara watsewa. Ciki mamaki Mai tsanani da kokarin danne bacin Rai yayan Marigayi salisu ya kalli CM da Alhaji babbah kafin ya maida kallonsa kan AA yace" Alhaji MAJEED mufa bamu gane abinda yake faruwaba anan, Auren da zaa daura biyu ne Daman kokuwa dai Wanda zamu daura dinne aka daura da wani 'dan ba namuba? Dan idan naji daidai sunan yarinyar dai shine wadda zaa daurawa danmu da ita. Duk Inda damuwa da 'dacin Rai Dana zuciya suke sune a dabaibaye da A MAJEED, Bai taba samun kansa a yanayi Mai 'daci da qaqa nikayiba irin wannan Rana, Ko a wancan lokacin daya hadu da qaddarar samun Inayah baishiga damuwa da quncin dayake cikiba yanzu. Me zaiyi da auren 'yarsa ta kansa? Wace mummunar masifa Hadiza ta sakasa daya qare qarshe a auren Inayah 'yarsa?? Innalillahi wainnan ilaihrrjiun, Yau shima yahadu da qaddarar Sharrin shedan Dana zafi da yanke hukunci cikin fushi. Duniyama idan taji shine ya aura 'yarsa zai anyi Allah wadai da tunaninsa. Gashi garin yanke hukunci kada Hadiza ta ra'bi Inayah har Inayah tasan bashine mahaifinta ba yaje cikin fushi da bacin Rai yayi abinda ba iya Inayah kadaiba da bayason ta taba sanin bashine ya haifetaba duniyama kowa zai sani yanzu Wanda harga Allah yaso riqeta amatsayin ya har abada batareda kowane Dan Adam yasan bashine ya haifetaba sbd daga lokacinda mahaifiyarsa datafi kowa saninsa da tarbiyarsa ta tuhumesa tareda yarda da zai iya aikata Zina harma ya Haihu a hanyar Zina yasaka a ransa ya karbi Inayah amatsayin 'ya dabazai taba barin wani yasan bashine ya haifetaba ciki kuwa harda mahaifiyarsa saigashi Rana tsaka Hadiza ta sakasa a mummunan tarko. Hadiza itace masifar rayuwarsa yau ya tabbatarda hakan sbd akaro na biyu takuma sakasa masifar da kusan tafi ta baya yaqare da rataya igiyoyinsa na aure a wuyan 'yarsa baisan wane mummunan Al'amarin Zata Kuma kawo masaba a gaba Dan yasa zaifi wainnan zauta Kai da qwaqwalwa. CM ne yayi saurin kallonsu Alhaji buhari ganin ransu yafara baci sosai sunason Jin bayanin abinda yake faruwa Dan haryanzu sunkasa yarda da auren matar 'dansu aka daura da wani sbd har lokacin Babu Wanda yakawo da AA MAJEED aka daura auren tunda ba abune Mai yiyuwaba uba ya aura 'yarsa Dan hakan kaf gurin Babu Wanda yakawo ABDULMAJEED mahaifinta ake nufi suma su CM da Alhaji babbah sunqi barinma agane wane ABDULMAJEED Dadi da qari kusan duniya da AA MAJEED tasansa bada cikakken sunansaba ABDULMAJEED ABDALLAH. Cikin qarfin hali Abbin yataso Yana sallama da mutanensa dake wucewa suna Masa Allah ya sanyawa auren 'yarsa albarka Yana amsawa da amin. Kaurewa da gurin yayi da jiniyar motocin 'yan sanda da civil defense ga yawan jama'a kowa nata kokarin miqa barkarsa ya wuce shiya taimakawa su CM gurin Jan su Alhaji buhari zuwa cikin gida palon Alhaji babbah Wanda shine da kansa ya iya fara tankwafarsu sbd fadan tozarci dasukagani qarara dasuka fara yi. Alhaji buhari ne mai iya dan danne tsananin bacin ran dasuke ciki su Alhaji kabiru 'yan Nan Hadiza kuwa kasa dannewa sukai suka fara zuba masifar tashin hankali Dan duk Inda ake wulaqantawa an wulaqantasu ankuma tozartasu sun debo jiki tun daga adamawa sunzo Lagos daurin aure ace suna zaune suna kallo kaman wasu gumaka andaurawa amaryar aure da wani koma Dan uban waye ai Basu cancanta wannan tozarcinba. Abdulsamad a rikice cikin tashin hankalin daya zaburo Masa tako Ina ya ringa kutsa jama'a Yana neman iyayensa maza dasune wakilan Amma Bai gansuba Dan haka ba Shiri ya zare hular kansa Yana Jin akwai gagarumar matsala Mai tsananin girman gaske kuwa. Saida mutane suka rake sosai aka fara Ankara da abinda yafaru ganin rudewa da tashin hankali da Abdulsamad yake ciki da yawa wainda suka dauka sune basuji sunan daidaiba suka fahimci cewan daidai sukaji Ashe auren ne dai bada Dr Abdulsamad aka dauraba. Take kurar hayaniya tafara kaurewa daga gurin Ganin Abdulsamad na Neman zarewa yasa Abbi daya Gama sallamar baqinsa ya Kama hannunsa sukai cikin babban gidan na Alhaji babbah. Qanin CM Professor Ibrahim shine ya tsaya yaqarasa sallamar sauran jama'ar aka watse wasu nata sake sawa auren albarka wasu Kuma na shiga mamaki da son Jin yanda wannan mugun Al'amarin yafaru hakama wasu take suka ringa maimaitawa wainda basujiba cewan sunan fa AA MAJEED ne aka daura dashi. Mamaki da firgici wasu suka Kuma shiga Jin sunan Wanda aka daura dashi din aikuwa take tun anan suka fara shigar da gulmar Internet. An watse tsaf ba kowa Dan hakan Alhaji babbah ya kalli su Alhaji buhari dake cikin mummunan yanayi na bacin Rai da fushi. Cikin sanyi da taushin murya ga Wanda baa kyautawaba yace" Alhaji buhari kuyi hakuri nasan baa kyauta mukuba tako Ina Musamman da baa sanar daku komaiba ko fahimtar daku komaiba Saida kukazo cikin baynar jama'a hakan tafaru. Dr Abdulsamad dake tsiyayar wasu ruwan zufan tashin hankali da fita hayyaci ya kalla duk saiyaji jikinsa yayi sanyi da tausayin Abdulsamad din sbd duk Wanda ya kallesa yasan yana tsananin son Inayah so Mai tsanani, Tayaya Za'a kallesa ace Masa uwarsu daya, Uban ne kawai Basu saniba ko dayane tunda A MAJEED cewa yayi uwar kawai yasani itama a bisaga qaddara. Shi kansa Dr Abdul idanuwansa duka da hankalinsa suna kan Alhaji babbah sbd ya fahimci agurinsa zasuji abinda suke buqatan ji Wanda zuciyarsa ayau harbawar datake yasan ta wuce kowane irin tsari da akeson zuciyar Dan Adam ta buga. Babu wani yaren dazai gane ayanzu idanba na maganar aurensa da Inayah bane. Dan jinjina maganar dake bakinsa Alhaji babbah yiyi tareda dauke idanuwansa daga Abdul ya maida kan su Alhaji buhari dasuke manya zasu fahimtarsa a natse yace" Ita wannan yarinya Inayah wadda mahaifiyar Abdulsamad ke Kira da Ayshatouh 'yar mahaifiyar Abdulsamad ce wadda ta jima da Bata tun jarinta Wanda A jiyan bayan haduwar mahaifin Inayah Wanda yanzu zance mijinta da ita mahaifiyar tasa suka tabbatarda Dr Abdulsamad da Inayah uwa dayace ta haifesu, Dr Abdulsamad da Inayah uwarsu daya Kuma kaman yanda duk muka sani Babu aure tsakaninsu, Sauyin Wanda aka daura dashi Kuma wannan nine Nan na tayasa yanke wannan hukuncin sbd kaman barazana da ita mahaifiyar yarinyar takeson tayiwa MAJEED Dan hakan muka yanke hukuncin ya aureta. Dan haka a taqaice ABDULMAJEED shine ya aura AYSHATOUH INAYAH, Shine mijinta ayanzu, Sauran bayanin Inda ita mahaifiyar Dr ta samo yarinyar har suka Zama uwa daya da Dr wannan saidai aji daga gareta. Wani mummunan shock da matsiyacin zufane ya fesowa Alhaji kabiru zuciyarsa na harbawa da mamaki ya juya ya kalli malam Umar Dan uwansa Wanda harya fisa jiqewa jagab da zufa. Alhaji buhari daya Gama samun qullewar Kai da mamaki da Yar rudewa yace' Inayah kuma Yar Hadiza? Tayaya? Garin Yaya? Yaushe? Shaqewa muryar Alhaji kabiru tayi a Rikice murya na yankewa yace" Inayah itace AYSHATOUH???? 'yar da Hadiza ta Haifa ranarda mahaifiyarmu ta rasu?? Da tashin hankali malam Umar ya karba da cewa" Innalillahi wainnan ilaihrrjiun Tabbas Hadiza ta haifi 'ya takuma saka Mata Ayshatouh., Idan har ya tabbatarda Hadiza ce dimun wadda tabar Masa 'ya to tabbas kuwa wannan 'yar ta Hadiza ce halak malak sbd ranarda ta haifeta ranar tabar gida. Sai alokacin zufa ta karyowa Alhaji buhari Jin dai ta tabbata Hadiza haihuwa tayi ba aure bayan rasuwar salisu. Da sauri malam Umar daya fahimci tunanin dake zuciyar Alhaji buharin yace" 'yar Hadiza 'yar halak ce 'yar sunna Dan kuwa cikinda salisu yabarta dashine muma sai daga baya muka Ankara da hakan Dan haka 'ya 'yar halak ce Uwarsu daya ubansu daya da Abdulsamad gashinan zaun....." Ya qarasa fada Yana waiwayawa Inda Abdulsamad ke zaune sai kawai sukagansa zube baya numfashi da alama ya jima da sumewa Basu saniba sbd tashin hankalin da kowa yake ciki. Arikice Alhaji buhari yayi kansa shida malam Umar suna Kiran sunansa Amma da alama ba sumar kadai yayiba kaman harda attack yasamu. Innalillahi wainnan ilaihrrjiun""Alhaji buhari yake fada Yana kamo Abdulsamad din da qarfinsa Ba arziki Dole zaman bayanin yaqare sukai asibiti dashi hankali tashe. Bayan fitarsu kallon Abbi Alhaji babbah yayi yana nazarin halin tsananin damuwar dayake ciki da rashin ta Ina zai Kama wannan rakitaccen Al'amarin. Tausayinsa ne Dana Abdulsamad ma dayafi kowa tausayi yanzu Dan yasan Al'amarin zai daki yaron sosai sudai dama saukinsu da hamdalar dasuke shine da baa daura aurenba da komai yafi lalacewa uwa daya uba daya. Bayason qarawa MAJEED damuwa da wasu zantukan Dan haka ya taqaita da cemasa, "MAJEED kaje gida kasamu ka nutsa kanka ya sake kafin shima Abdulsamad asamu lafiyarsa saiku zauna duka kuyi taron fahimtar juna, Itama yarinyar kada kace zaka kasa karban wannan qaddarar sbd ko ahakan Allah ikonsa ne ya nuna, Haisawa sukace matar mutum kabarinsa Allah yayi itace matarka shiyasa Bai baka ikon aureba tun kuruciya har gashi manyanci nason zuwa hakama rabon zamtowarta matarka ya hadaka da mahaifiyarta harta dawo hannunka dan ka tarbiyantar da matarka da kanka Dan haka shi Allah Babu ruwansa idan ya jarabta mutum to akwai tanadin dayayiwa wannan bawan idan har yayi tawakkali yacinye wannan jarabawar. Allah yasa mudace, Allah Kuma yabaku zaman lafiya yasawa wannan auren albarka. "Amin" CM ya amsa adduar ta Alhaji babbah Yana cewa" Allah yaqara girma. A natse MAJEED shima yayiwa Alhaji babban godia kafin suka fito. Dayake da lafiyayyar Lexus din CM sukazo Dole shine ya maidasa gida. Suna Isa gidan Yana ajiyesa harabar gidan yakira matansa yace kowaccensu ta fito su koma gida sbd yasan ba qaramar rigima zaayiba idan zancen auren ya Isa cikin gidan tunda duk matane bare ita kanta Inayah din Gwara idan zatai Rigimar ya Zama ba kowa a gidan. ##MAMUH# #LOVE/MARRIAGE/ROMANCE# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[10/31, 9:42 PM] +234 703 926 9802: *_31_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Sake Shan jinin jikinsu dukkaninsu sukayi Jin cm yace sufito atafi gida Nan suka sake tabbatarda ba lafiyaba Amma Kuma bilyamin qanin Anty Hafsat ya tabbatar musu da an daura aure, To Kuma menene matsalar? Sudai koma menene suna ganin da sauki idan har andaura auren Inayah da Dr Abdul dinta. Ita kanta Inayah data dawo hayyacinta tuntuni zaune take tana jiran ta Inda labarin halinda aurenta yake ciki zai bullo. Lokacinda bilyamin ya sanar dasu cewa andaura auren wani irin Al'amari taji atattare da ita shi ba farin cikiba hakama ba baqin cikiba Tadaisan jikinta ya mutune kawai Dan haka daqyar ta iya sauya Kaya kaman yanda su Anty Hafsat suka takura Mata sbd Ango na tafe da jama'arsa suyi hotuna takuma gaisa da abokansa da zasu bi jirgi a ranar su koma. Tafiyar su Anty Hafsat shine ya fara daga hankalin umma yaganah harma da Inayah Dan haka da kanta ta Kira cm din a waya tace Inayah tace Dan Allah abar Mata Hafsat da Safnah har zuwa anjima. Bai Musa ba yabar Anty Hafsat da Safnah Dan haka gidan yayi tsit daga umma yaganah sai Anty Hafsat da Safnah da Neesah Dr farhat ma ta tafi gida sai zaa wuce da Inayah din tace akirata. Babu Mai wata doguwar walwala acikinsu sbd sudai anbarsu a duhu basusan meyake faruwaba sai jiran tsammanin zuwan Ango da jama'arsa suke Amma basuga alamar hakan Zata faruba ga wayarsa da Inayah ke Kira kaman zata zare Amma batama shiga kwata kwata. Sanin Abbi yadawo yasa ta miqe jiki mace ta nufa gefensa tana sake trying din Abdul. Kodata Isa knocking daya tayi tabude kofar tashiga daukeda sallama Mara sauti sosai. Baya Palo da alama Yana bedroom dinsa Dan haka ta zauna kan kujera tana sake trying din Abdul. Tunanin Kiran ummansane ya shigota ta nema numbern umman aikuwa tafara ringing. Harta katse baa dagaba Dan haka ta fara rubutawa Abdul text. Kofar bedroom dinsace ta bude Dan haka ta dakata rubutun tareda dagowa tana kallon kofar. Sanye yake da ash Lululemon wears navy blue dasuka fidda hasken fatarsa sosai da alama wanka yayi ya shiryo cikin kayan Dan samun nutsuwa, Qamshinsane ya gauraye palon take ya qaraso da yimata kallo daya yanajin wata qululuwar damuwar auren da aka daura Yana dawo Masa. Cikin boye damuwarta da Yar sakakiyar murya tace" Abbi kadawo Ashe tun dazu? Abbi Ina Heart ya....kasa qarasawa tanajin nauyin qarasa zancen sbd ita wani lokacin mantawa takeyi da kunyar fadan wani zancen. Dan juyowa yayi kadan ya kalleta ganin damuwa a tattare da ita cikin dan yanayin kawar da zancen Kai tsaye yace" Abdul na asibiti ya Dan samu attack ne aka wuce dashi asibiti. Zaro ido tayi cikin tashin hankali da firgici Amma ganin ba fuskar Kuma wata tambayar agurin Abbi yasata miqewa ta silale Takoma. Koda ta Isa a tsattsaye ta taddasu kowanne ba acikin cikakken hayyacinsaba, Tashin hankali da firgicin data gani ataredasu duka yasata bude Baki da qarfi cikin firgici tace" Badai Heart wani abun yasamaba kuma daga asibiti??? Umma yaganah kanta yakasa daukan abinda CM yafadawa Hafsat a taqaice na cewa A MAJEED shine mijin da aka daurawa Inayah aure dashi yau. Wani irin zufa takeyi tanajin kaman iskar dake gurin Bata isarta Dan haka da sauri Neesah ma dake cikin tsananin shock ta Kama umma yaganah sukai daki taqara Mata AC tareda bude suka windows tana cewa" breath, just breath kada ki Bari Jan numfashi ya tsaya Miki kiyi kokari kijasa. Kasawa umma yaganah tayi Saida Inayah tashigo dakin tana kallonsu a haukace tana cewa" Dan Allah ku fadan abinda yake faruwa, Wane tashin hankali ne zaisaka umma wannan halin? Anty Hafsat is crying, Kema Neesah sai zare Ido kikeyi Kun kasa fadamun komai, Kuka ta fashe dashi tana cewa" Idan Heart ne ya rasu Dan Allah ku fadamun. Kasa riqe maganar bakinta Neesah tayi cikin mamaki da qin yarda da abinda sukaji tace" Inayah Abbi ne fa ya aureki, Dashi aka daura auren wai, Shine mijinki yanzu, Dama akwai aure tsakanin uba da 'ya??.... A jere take Watso kalaman sbd takai kololuwar kasa danne mamakin firgicin dake ransu ita nata kalaman ne suka Riga na kowa fitowa a hargitse. Kallon rashin fahimta Inayah ke Mata kafin ta kalli umma yaganah da duk tayi wani iri Dan kuwa CM bazai musu qaryaba, hakama tafi kowa sanin MAJEED ba jahili bane bakuma mahaukaci bane da iliminsa Idan harya auri Inayah hakan na nufin bashine ya haifetaba kenan tun asali....to wannan wane irin masifa ce Zata sakasa auran yarinyarda take matsayin 'yarsa Koda ba shine ya haifeta ba tasan Dole ba auran dadin Rai ne yayiwa Inayah ba. Anty Hafsat ce tashigo tana sake samun tabbaci daga uban mijinta Alhaji babbah cewa Inayah dai ba 'yar MAJEED bace Kuma shine dai mijin daya aureta yau Dan haka suyi kokarin ganin sun tausar da ita batareda taqara Masa tension ba akan Wanda yake ciki yanzu. Da rikitaccen yanayi Inayah ta maida kallonta kan Anty Hafsat data shigo dakin cikin kosawa tace" Anty Hafsat meke faruwa dan Allah?Bazan iya daukan wannan shirun da kowa kemun ba, Maganar Neesah ma Ni Sam bangane itama me take nufiba. Ahankali Anty Hafsat takama hannunta suka nufi Inda umma yaganah take ta zaunar da ita itama ta zauna suka sakata tsakiya itada umma yaganah ahankali ta kalleta cikin sanyin murya tafara cewa" Inayah bamusan komai dayasaba kokuma yazama sanadi komai for now Amma dai abinda yake gaskiyar zance shine aurenki da Abdulsamad Bai yiyuba Amma aure kam kaman yanda aka sanar Mana tabbas andaura Miki aure da... Dan shiru tayi tareda kallon umma yaganah dake saurarenta itama Dan Hafsat din tafisu sani da fahimtar komai da kyau tunda itace tayi waya da mijinta yayi Mata bayanin komai hakama Alhaji babbah yayi Mata bayanin komai qarshema yanzu driver na hanyar zuwa daukansu su duka zuwa gurin Alhaji babbah din Dan shine kadai zai iya yiwa Inayah bayaninda kila Zata fahimta. Kaman daga sama sukaji Inayah din tace" Da aka fasa aurena da heart sai aka daura mun da Abbi??? Right? Shine abinda kikeson fada mun? Shigowar zubbi da sakon isowar driver daga can family house yasa Anty Hafsat dojewa amsa tambayar Inayah din Dan haka ba Bata lokaci takama hannun Inayah din Umma ba Bata jira komaiba ta sauko gadon tareda miqewa ta zari mayafi suka fito Dan kowa matse yake da a wayar Masa da Kai akan wannan sauyin lamari Mai wuyar ganewa. Koda suka Isa gidan Alhaji babbah na masallaci sallar la'asar Dan haka Saida suka jira ya dawo a babban Palo Haj mama na sake yimusu nasiha a fakaice Dan ita saima taji tafi jin dadin MAJEED daya aure Inayah Dan kuwa da tun farkoma sun San bashine ya haifetaba baida alaqar Jini tako Ina da ita da tuni sun matsanta Masa ya aureta yafi fashe fashen aurenta da akaita Yi shima Kuma ga lokaci yaja Bai taba aureba ace haryanzu matsayin saurayi yake Dan haka Kai tsaye ya bayyanarda farin cikinta ana fada saidai Kuma ta tausayawa Inayah sosai ta yanda Rana tsaka Zata karbi zamanta ba 'yar mahaifintaba datake tsananin so da kauna amatsayin ubanta ita daya. Kusan Banda Inayah data kasa fahimta bare yarda har lokacin Sun Gama fahimtar dai Abbi bashine ya Haifa Inayah ba Kuma shine mijinta a yanzu. Duk sun gane wannan abinda basu ganeba shine meya Hana a daura auren da Abdulsamad. Alhaji babbah na dawowa daga masallaci suka dunguma palonsa lokacin har CM ma ya iso Yana gidan. Zama kowa yayi jiki a sanyaye Musamman Inayah da kusan komai Bata ganewa Takoma kaman wata mutum mutumi. Ita Alhaji babbah yafara kalla cikeda tausayawa da kulawa kafin ya maida kallonsa kan umma yaganah datake Babba zatafin fahimtar komai Kuma idan ta fahimta komai zaifi tafiya daidai Dan itace Zata ringa dorata a hanya akan auren da haqqoqinsa tunda tare suke rayuwa gida daya. Gaisawa suka fara Yi kafin ya Dora da fadar" Haj yaganah ya fama da hidima da jama'a? Allah yasa angama lafiya yakuma sanya Alkhairi. To wani babban Al'amari yafaru tsakanin shekaran jiya zuwa jiya da Kuma yau din kafin daurin aure Wanda yasa aka samu sauyi cikin qurarren lokaci., Shi aure nufine na Allah Dan haka kada kuyi Wani mamaki da Al'amarin ubangiji, Inayah dai kaman yanda a da MAJEED shine jigonta yanzuma shine jigonta Kuma ma'ishinta Dan kuwa shine mijinta haryanzu yafi kowa iko akanta. Basai an tsaya tone toneba anan ko dogon bayani Wanda Zata samu daga baya idan ansamu komai ya lafa MAJEED dai bashine mahaifinta ba Kuma yada alaqar Jini tako Ina da ita bamu kadaiba duniyama Bata taba sanin da hakanba sbd riqon Amana da Gaskia da yayi Mata da zuciya daya Kuma a wannan duniyar abune Mai wuya samun irinsa Dan kuwa ko 'dan jininka baka riqewa ba Amana irin hakan Amma shi ya riqeta ya reneta da Amana da kauna bai taba barin tasan bashine mahaifinta ba idanba yanzu da hakan ta bullo ba Rana tsaka shima Kuma hakan da yayi yayine duk akanta sbd har gobe itace kulawarsa. Shi Dr Abdul dai anfasa aurensane sbd uwarsa daya ubansa daya da Inayah Wanda shi wannan bayanin ba hurumin shigata bane Dan hakan Ina fatan Kun fahimci yanayin da aka shiga dakuma wandama zaa Shiga Nan gaba sbd Koda Wasa karnaji anyi wata fitina kokuma tashin hankali akan wannan auren, Shima MAJEED din danasan yafi kowa shiga mugun yanayi akan wannan auren nai Masa nasiha Kuma Inshallah Ina fatan ya dauka. Dan hakan Haj yaganah sai anyi kokari gurin fahimtar dasu wasu abubuwan aure ya wuce mutum yayi Masa daukan dayaga dama, Allah ya sanyawa auren albarka, Suma can Allah yabasu ikon warware komai lafiya. Waiwayowa yayi zaiwa Inayah nasiha akan itama saita dauki qaddara sbd da tashin hankali samun kanka irin wannan yanayin sai ganin sukai tana Jan numfashi alamar attack Zata samu Kafin suyi wani yunqurin tasamu attack take Dan haka a rikice suka dauketa zuwa cikin gida. Allah yasa akwai likita taredasu Neesah taredasu Amma bada ita akaje palon Alhaji babbah ba itace tayi gaggawar fara taimakawa Inayah din wadda takejin kaman zata rasa ranta sbd yanda numfashinta ke Neman yankewa Neesah na taimaka Mata gurin janyosa da karfi. Ganin kaman Al'amarin zaiyi girma sosai Dole suka Kira Dr farhat wadda kafin ta iso suka dunguma da Inayah din zuwa asibiti sbd tuni umma yaganah takira Abbi ya sanar Masa yace su wuce asibiti gashinan zuwa asibitin. ##MAMUH# #LOVE/ROMANCE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [10/31, 9:43 PM] +234 703 926 9802: *_32_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Private hospital din dake anguwarsu Alhaji babbah aka kaita sbd kafin suce sunje AA specialist wato private hospital dinsu akwai nisa daganan da hakan suka tsaya tanan kusa. Cikin gagawa suka karba Inayah din Neesah ma bata barmusu aikinba su kadai da ita sukayi Dan sunada fahimta tana sanar dasu itama likitace suka barta ta taimaka musu tunda dama itace kusan tasaba taimakawa Inayah idan irin hakan ta taso. Umma yaganah gabaki daya kanta neman sake cakewa yakeyi da wannan Al'amuran daketa faruwa daga wannan sai wannan, Har cikin ranta takejin kauna Mai tsafta da tsanani akan MAJEED da Inayah sbd sune danginta itace danginsu Dan lokuta da dama sukan mantama basuda alaqar jini da juna. Badan a yanda yanayin komai ya fallasa kansa ba lokaci daya ba zato ba tsammani da Babu Wanda zai kaita murnar Auren MAJEED datake addua da fatar gani tsawon shekaru. Hakama auren Inayah wani babban burinta ne shima datake fatan Allah ya nuna Mata ya cika a yau din sai gashi Allah yacika Mata burin Auren dukansu a yanayinda Babu wanda yataba tsammata, Ku kansu basuma San farin ciki zasuyiba ko damuwar sanin ba Abbi ne ya haifi Inayah ba. Anty Hafsat ma zuciyarta kusan Kashi Kashi take kasuwa tana rarraba Mata tunani sbd ayanzu Bayan Jin bayanin yanda Al'amarin yake daga bakin Alhaji babbah taji zuciyarta na farin ciki da auren Dan kuwa Inayah Allah yayimata kyakkyawan sauyin dayafi duka tarin mazan data rasa abaya sbd Abbinta yakai kowanne level da ake kwadayin namiji yakai badan tashin hankalin halinda Inayah tashigaba da a fili Zata fara bayyanarda farin cikinta akan wannan tsintar damu akala da Inayarsu tayi Dan kuwa Abbi kam Masha Allah. Sbd wadda tasaba ji da matsalarta na kusa yasa ma'aikatan asibitin Basu Sha wuyar taro yanayinta ba tadawo hayyacinta saidai take bacci ya dauketa sbd kusan wannan attack din yafi wainda tasaba samu abaya. Kwantawa hankalinsu yayi ganin tadawo daidai tasamu bacci Amma kallo daya zakawa fuskarta ka gano baccin na tattareda yanayin firgici data shiga. Suna zaune a dakin datake anty Hafsat na kokarin daidaita ACn dakin da yayi yawa umma yaganah Kuma na zaune tana kokarin amsa wayarta da Mimi ke Kira saigashi ya iso yashiga dakin cikin nutsuwa sanyeda Lululemon wears har lokacin da alama Bai tsaya sauyawaba zuwa wasu manyan kayan. Fresh skin dinsa daya bayyana sosai cikin kayan anty Hafsat da Neesah suka kalla suna sake tabbatarda kyau da tsarin da Allah yayiwa Abbin Take suka sake Jin tabbas ta wannan fannin Inayah Dinsu tagama dacen miji illa kawai baqin cikin dazata Shiga sanin Abbinta datafi so fiyeda komai baida alaqan Jini da ita Tsintar yayi,kyautarta akai Masa kokuma tayaya ya sameta Allah ne kawai yasani saishi da umman Abdul din. Cikin girmamawa anty Hafsat da Neesah sukai Masa sannu da isowa Da qaramin sauti ya amsa Yana dan kallon Inayar kafin ya kalli anty Hafsat sbd umma yaganah na waya yace" Doctors din sungama dubata ne? Neesah ya nisan yanayin nata? Firgici ne kawai data shiga ya daketa sosai Amma Inshallah lafiyanta kalau yanzu anmata allura ne sbd tayi baccinda kanta zai Dan warware ya rage Mata tashin hankalin. Gyada Kai yayi ahankali tareda sake kallon Inayah datai wani iri cikin lokaci qanqani. Dan gajeran numfashi ya sauke tareda juyawa yafita zuwa ganin likita Dan bayason ta kwana a asibitin gida zasu koma tunda suna tareda qwararrun likitoci a gidan. Fitarsa da mintuna biyar sai gasu Mimi sun iso asibitin a gigice sbd tashin hankali biyu, Na farko Jin auren MAJEED da Inayah dakuma Jin uwarsu daya ubansu daya itada Dr Abdul ga qarin halinda Inayar tashiga. Jigum jigum sukai a dakin wasunsu na sake Dan jajanta wannan alamari da masu godewa Allah da baa Riga an daura aurenta da Dr Abdul dinba dan da abin yafi lalacewa. Umma dai bayan taga Inayah ta tashi babu abinda take fata Dan ita kanta yanzu tanajin dacin da Inayah Zata Shiga,. A sanin dataiwa Inayah kuka da baqin cikin dazata Shiga na zaman Abbi ba mahaifintaba zaifi Mata ciwo da radadi fiyeda auren Dan kuwa tafi buqatan ace alaqar jini suka hada Bata auratayyaba. Har yamma lis suna asibitin Inayah Bata farkaba sai magriba. Tana farkawa takasa kallon kowa a dakin sbd yanda duk sukai jigum jigum yabata tabbacin abinda yafaru kafin zuwanta asibitin Gaskia ne haqiqanin Gaskia Kuma Dan haka Batasan ta Ina Zata fara bayyanarda babban abinda takeji tokare da zuciyarta da maqoshinta. Cikin kulawa da sanyin jikin yanayin da Inayah din ta nuna umma yaganah da Anty Hafsat suka fara kokarin magana saiga shigowar Abbi Wanda Yana shigowa qamshinsa ya gauraya dakin suka tsit suna jiran abinda zai faru Kuma ga Inayah din ga Abbi a amatsayin ma'aurata. Yanayinsu yasashi basarwa tareda Dan kamewa ya kalli Inayah data dago ta zuba Masa Ido tana Neman fashewa da kuka yace" Kina farkawa Kuma Zaki fara wani kuka agurin. Neesah dake gefenta ya Dan kalla yace" Ku shirya gida zaa koma da ita yanzu. To" Neesah tace tana kallon Inayah din dake kokarin fashewa da kuka Amma takasa sbd abun datakeji ya girma qwaqwalwarta. Juyawa yayi ya fice suka biyo bayansa. Anty Hafsat motar CM zatabi itada Mimi da Safnah Su Kuma su Inayah din motar Abbi zasubi Dan haka suka nufa motar Kai tsaye umma yaganah na riqe da hannun Inayah dake kokarin zubewa sbd tangadin datake na Bata cikin cikakkiyar nutsuwarta. Kaman yanda suka Saba fitarsu da Abbin idan takama Inayah ce a gaba Dan haka yau dinma itace agaba sai umma da Neesah a baya. Bayan sanyin Ac na motar da qamshinsa daya cika motar Yana zagayawa Babu Mai ko motsi acikinsu kaman ba kowa a motar kowa da tunanin daya shiga Banda Inayah da har lokacin qwaqwalwarta Bata fara aiki daidai ba dif take Bata ji Bata gane komai yanzu. Suna Isa gida Dole Neesah ce ta kamota suka nufi ciki tana kokarin kaita bedroom dinta ta qwace Takoma Palo tana kokarin bin bayan Abbi cikin dimauta tana cewa" Abbi ne kawai zaifadamun Gaskia na yarda da abinda duk ake fada, Abbina ne kawai zan yarda da maganarsa. Da sauri umma yaganah ta riqota tana cewa" Ki nutsu Mana Inayah, Me zakije kice Masa yanzu? Bakiji anfada Miki yanzu mijinki bane, Qarya zamu taru mu Miki ne? Alhaji babbah zai Miki qaryane? MAJEED din dakikeson saiya fada Miki komai Yana cikin damuwa sosai bakya gani? Zaki sake daga Masa hankali da kukan Nan nakine idan kikace rikicewa zakiyi. Rikitaccen Kuka ta fashe dashi Mai tsananin qunci tana cewa" Ni bazan yardaba wlh abbin ne mahaifina, Banason kowa a mahaifi sai Abbi, Har umman Abdul din banaso amatsayin uwa Ni Abbi ne kawai uwa Kuma ubana... Da sauri umma ta rufe Mata Baki jikinta na rawa sbd jikinta daya fara sanyi itama da irin kukan da Inayah din fasawa Wanda tunda take Bata taba yin irinsaba sai yau. Rirriqeta sukai ta zube qasa tana sake tsananta kukanta zuciyarta na Mata wani irin zafi da radadi... Idan ba abbine mahaifinta ba ai ita asaran duniya da baqin cikin duniya tana cikin cikinsa da wannan mummunan labarin da gwara ayita fasa aurenta har abada akan wannan labari... Bazata taba yarda da maganar kowaba sai taji daga Abbinta cewa gaske bashine ya haifetaba. Dukkanin sautin kukan datake yanajinsu Amma Bai iya zuwa Inda suke dinba Dan kusan yafita baqin ciki da wannan bankadar, Dan yaso ya tsaya a ubanta na har abada saidai qaddara Bata bar hakan ba Dan kuwa Koda warware auren Nan akayi har abada ita zaa Kira da matarsa ta farko wadda tafara daukan igiyoyin aurensa haka itama har abada shi zaa Kira da mijinta na farko daya fara riqe martabar aurenta. Kuka Inayah da tashin hankali sosai tashiga lokaci daya Wanda ya gigita umma yaganah da Neesah harma dasu zubbi da Salimat sun Shiga tashin hankali da damuwa sosai ganin halinda Inayah din ke ciki Ta bangare daya shi kansa Mai gidan babu Wanda yakuma ganinsa har washe gari, Abincin gidan ranar haka aka daukesa aka fitarwa Bosco ya rarrabawa securities din anguwar abokanansa sbd Babu Mai nutsuwar cin wani abinci. Da zazzabi Mai zafi Inayah ta kwana Dan kaman yarinya qarama Takoma musu daqyar baccin wahala ya daukeda jikinta da mugun zazzabi. MAMUH# #LOVE/ROMANCE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_33_* *_Arewabook@Mamuhgee_* Da zazzabin ta tashi da safe Dan haka sallah kawai ta iya Yi Takoma ta kwanta sbd tsananin ciwon Kai Dana kirji, Ana Gama breakfast umma yaganah ta sallami baqinta aka kaisu aka sanya mota tareda Dan abin arziki gidan yasake daukan tsit. Su zubbi tuni suka shirya komai a dining na breakfast kaman yanda suka Saba. Umma dai a dakinta tayi breakfast din Neesah ma bata fito dining ba Dan a daki Tasha tea Danma sunyi sunyi Inayah ko tea din Tasha taqi. Har lokacin bata daina tsiyayar hawayeba, Takasa yarda da wannan qaddarar lokaci daya wai ace Abbinta shine mijinta, Tayaya Zata fara fuskantar wannan maganar, Har abada bazata taba iya karban Abbi amatsayin mijintaba sbd haramun nema agunta kallon Abbi a matsayin Miji ba uba ba. Daga Neesah har umma sunyi rarrashi da nasihun harsun gaji Amma Babu sassauci a lamarin, Gabaki daya fuskarta ta sauya sbd kuka. Anty Hafsat ma tazo tayi nata rarrashin Amma Dole haka zasu hakura sbd dama bazai yiyu ka karbi irin wannan ba lokaci daya. Gabaki daya wunin basuga Abbi ba sbd yafita tun safe gurin sallamar baqinsu na nesa dazasu wuce Kuma akwai wainda zaiyi meeting dasu kafin su wuce din. Da farko mantawa yayi da auren daya rataya akansa jiyan sai daga baya bayanma ya daga waya zai Kira Inayah. Dan rinte Ido yayi tareda maida wayar ya ajiye Yana fitarda Dan numfashi Mai zafi. Miqewa yayi ya nufi toilet ya sakarwa kansa ruwan Yana gogawa fatarsa sabulun mountain water soap na Creed. Sai bayan wasu Yan mintuna yafito daureda blue towel a qugu yafara shiryawa. Cikin dark blue kaftans yafito da blue hular kube Bai wani shiga can palonsu ya fice daga gidan sbd jiransa da ake. Sai Bayan azahar Inayah ta iya tashi da daqyar takai kanta toilet tayi wanka. Sallah tayi tazauna tareda janyo wayarta tana sake saka kiran Heart dinta Wanda yanzu Kuma hankalinta ya karkatane akan taji yanda yake sbd tasan Yana cikin matsanancin halin shima. Wayarsa har lokacin bata Shiga Dan haka tasake daga hankalinta da wata qarin damuwar. Dole anty Hafsat da Neesah da umma yaganah sukai Shirin tafiya dubosa asibiti Dan dama suma duk sun damu dason sanin halinda yake ciki din tun iya basuda labarin komai akansa da mahaifiyarsa Kuma mahaifiyar Inayah. Abbi umma yaganah takira ta sanar Masa zasu tafi dubo Abdul din Bai hanasuba yace suje. Har Zata kashe Kai tsaye a nutse cikin kamewa yace" Kar kuje da Inayah ta zauna gida. Ok shikenan. Inayah taji lokacinda Abbi yace kada aje da ita Dan haka hankalinta yaqara tashi da sauri tadauki wayarta tareda saka kiransa. Ringing wayar tafara Lokacin Yana tareda dasu CM da wasu school mates Dinsu da duk sunzo daurin auren sbd kowa nata kokarin hulda dasu shida CM yanzu sbd ganin sun Zama abokan manya sbd kudi. Dan waiwayawa yayi gefensa da wayar ke ajiye ya kalli wayar a natse yaga Inayah ce me Kiran yakuma San Sarai roqonsa zatai akan binsu shikuma bazai taba barin ta hadu da Hadiza ba ayanzu Dan haka ya dauki wayar a kame yace" Yes,Inayah. A marairaice da alamar kuka tace" Abbi Dan Allah zan bisu inason dubo Heart Nima, Abbi Dan Allah kada ka hanani.... Bakida lfy Babu Inda Zaki kina wannan kukan Kisha magani ki kwanta. Kashe wayar yayi tareda ajiyewa Yana  maida hankalinsa kan maganar dasukeyi. Hawaye tafara tana kallon wayar Su umma na ganin haka suka fice suna cemata saisun dawo. Zaunawa tayi bakin gadon dakinta Tana cigaba da tsiyayar hawaye sbd tana tsananin buqatan son ganin Heart Dan taga yanayinda yake ciki. Wurgi tayi da wayarta kan gado tana cusa fuskarta cikin tafukan hannuwanta zuciyarta na radadi. Hannu takeson dorawa akai ta ringa zumduma ihu da birgima ko zataji sassaucin tsananin qunci da damuwar dake ranta. Tayaya Zata iya cire soyayyar heart daga ranta bayan yayiwa zuciyarta kyakkyawar Shiga? Tayaya zasu iya rabuwa da juna sbd kalmar uwa daya uba daya da ake dangantasu da ita? Batada uban daya wuce abbi Kuma batajin Zata daina daukansa ahakan kokuma daina kallonsa ahakan. Abbinta fa ake maimaita Mata kalmar mini agurinta. Kasa riqe kukan tayi ta kwanta agurin tafara rero kuka tana sake Jin zuciyarta kaman zata kama da wuta. ***Su umma yaganah kuwa koda suka Isa asibitin da Dr Abdul yake hankalin Yan uwansa da mahaifiyarsa atashe yake sosai fiyeda tunani Dan kuwa Dr Abdul dai jiki ya rikice. A jiyan da aka kawosa asibiti daqyar aka samu ya farfado ya kalli mahaifiyarsa da hankalinta ya rarrabu cikin tashin hankali masu girma sbd labarin auren MAJEED da INAYAH ya gigitata sosai, Zancen ya daketa har Batasan lokacinda itama ta zube qasaba jininta na Neman hawa. Tabbas AA MAJEED ya nuna Mata shi namijin duniya ne, Ya Sha gabanta ta hanyar aure Inayah sbd baida niyar bata 'yarta, Tabbas Babu shari'a yanzu Kam da Zata karbar Mata Inayah daga hannunsa Amma Kuma idan har Inayah Bata son wannan auren Koda abinda ta mallaka zai qare duniya kowa ya juya Mata baya saita tsaya Sharia ta raba auren anbata 'yarta. Su Haj balaraba dasu Alhaji buhari saidai su Alhaji kabiru sukai musu bayanin cikin daya bayyana jikin Hadiza bayan shekaru Wanda yayi sanadin dasuka koreta daga gida Saidai yanda komai yafaru Bayan barinta gidan shine Basu saniba saisunji daga gareta dashi AA MAJEED din Dan yanzu sune kadai zasu qarasa warwarewa kowa wannan qullin da tunanin dasuka shiga. Haj balaraba kuka ta ringa rerawa tana yiwa salisu addua suna qara godewa Allah da baa daura wannan aureba da basusan iya Ina tashin hankalin zai kaisuba. Hajiyarsu suka kira suka Dan sanar da ita komai a taqaice to dayake tasan da maganar cikin da haihuwar bayan barin Hadiza gida daga bakin jama'a Amma tayi shiru ta lafe sbd tunanin ko cikin banzane Hadizan tasamo daga Lagos sbd kada a dangantasu da cikin Tai shiru taqi Kuma barin 'yayanta ko daya yasani dan kada suce zasu karba tunda ba tabbas hakama Hadiza ta sameta takanas da jaririyar Amma shedan yaqi Bari ta amsa. Tsufa ya kamata sosai yanzu Amma itama haka ta ringa kukan danasani da farin cikin da aka samu Ayshatouh take zancen yafara fita a dangi saidai halinda Abdul ke ciki yafi daga hankalinsu akan murnar bayyanar wadda basuma San da itaba a zuriar. Dr Abdul mummunan shock din daya shiga ya daki zuciyarsa zuwa qwaqwalwarsa sosai Dan haka ya jima Bai farfado ba Kuma ya a farfadowa ummansa yafara zubawa indanuwansa dasukai mummunan ja yana kallonta cikin karaya da mutuwar dukkanin jiki yace" Umma since Inayah 'yarki ce itama kece kika haife shiyasa bazan auretaba Abbi ya aureta Ni nakasa gane komai So kawai naji daga bakinki idan kece mahaifiyar Inayah tayaya AA MAJEED zai Zama ubanta? Umma Dan Allah kicemun ba kece kika haifetaba, Kicemun bakida alaqar komai da ita sai wadda zamu qulla yanzu ta auratayya, Umma Dan allah kice bakece uwar Inayah ba bakida alaqan komai da ita...umma bazan iya rayuwa Babu Inayah ba kinsani akanta zan iya rasa hankalina da nutsuwata, INAYAH ce farin cikina,rayuwata da nutsuwata.....umma kice wani abun Dan Allah Amma ki janye maganar kece mahaifiyar INAYAH. Kakkarwa jikinsa keyi idanuwansa na sake fitowa da tashin hankali. Saikowa yayi gadon Yana Neman faduwa sbd jiri sukai saurin riqesa umman cikin kuka ta riqosa tana kallon yanda yake kokarin haukace musu tace" Abdul hakuri zakayi da wannan kaddarar ka runguma sbd bazan iya goge alaqar jinin dake tsakaninka da Ayshatouh Inayah ba, Kai Dan uwantane na Jini, Nice na haifeta kaman yanda na haifeka, Uwar daya ubanku daya Babu Mai iya goge wannan sbd rubutacciyar kaddara ce, Abdulsamad ma dauki danganar rasa Inayah sbd har abada Babu aure tsakaninku bazaka taba aurentaba Koda ku biyu zaku rage a duniya. Dan Allah Abdul ka karbi wannan kaddarar da hannu babbiyu sbd zuciyata bazata iya daukan wannan tashin hankalin dakake saka kanka acikiba Dan Allah Abdul. ##MAMUH# ##KUYI HAKURI AMIN UZURI NASAN CHAPTER DIN IS TOO SHORT.🙏 _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_34_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Umma Hadiza hankalinta yagama rabuwa daban daban, Tana buqatan fuskantar MAJEED akan abinda yayi na auren Inayah badan komaiba sai Dan nuna Mata iko akan Ayshatouh.. Ta Bangare Daya tasan Inayah ma na can cikin matsanancin halin itama, Babbar damuwar Kuma ganin Abdulsamad na Neman zauce musu sbd yaqi sauraren kowa bayan zantukan tashin hankali da qin yarda da uwarsa daya da Inayah kaman yanda itama Inayah batama yarda da tanada wata uwarba Dan ko acikin tarin damuwarta umma Hadizan Bata shigob ita tashin hankalinta Abbi daya zamana ba mahaifinta ba ko auren daurawa kawai akayi batajinsa ajikinta kwata kwata. Zuwansu umma yaganah yasa hankalinsu Haj balaraba tashi sbd mummunan halinda Abdul yakuma shiga Dan kuka ya ringa yiwa su umman da Anty Hafsat Yana maimaita sunan Inayah cikin karyewar zuciya. Umma yaganah dayake tanada saurin kuka take itama tafara hawayen tausayin Abdul tana cewa" Abdulsamad sai hakuri Jarabawar ubangiji ce duk zaa cinye idan anyi hakuri da tawakkali Inayah tariga ta Zama ta waninka dole dangana zaa dauka abarwa Allah... Kalaman umma yaganah suka qara Karya zuciyarsa yaci gaba da zubda hawaye Yana sunkuyar dakai zuciyarsa na Masa wani irin ciwo. Anty Hafsat ma jikinta mugun sanyi yayi da tausayin Abdulsamad Mai tsanani Dan kuwa Basu dauka abin yayi tsanani hakanba., Abdulsamad din dasuka sani Dan gayu da kwalisa shine ya garare cikin kwana daya sbd masifar ciwon rashin Inayah. Neesah kuwa itama jitayi tausayinsa da Inayah harma Dana Abbi yasa hawaye ciko idonta sbd kowannensu yana cikin matsanancin halin da Babu mafita sai dauka da dungumar abinda ya samesa. Irin naci da daga hankalinda Abdulsamad yayi nason zuwa ganin Inayah yasa umma yaganah miqewa su tafi sbd ko hauka bazata sakata tafiyada abdul dinba ko basa damar zuwa ganin Inayah ayanzu sbd bayan haqqin mariqi da MAJEED yake dashi akan Inayah yanzu shine Mai gabaki dayanta Dan haka bazatai wannan wuce gurinba ko gangancin zuwa dashi Dan haka suka miqe suka fito jiki a sanyaye Koda, Inayah ma Babu Wanda yayi musu maganarta sbd kowannensu baimasan me zaiceba akanta Dan haka sukai shiru kafin suga sun fara samun daidaituwar Abdul tukuna ayi zaman wannan maganar dake buqatan iyaye da manya aciki sbd tsanar da MAJEED yayiwa Hadiza Saida manya a zancen zai yiyu. Abbin ne yarigasu isowa gida Kuma yasan Babu kowa a gidan sai Inayah Dan haka daya dawo direct ta palonsu ya biyo tareda nufar bedroom dinta. Yana isowa zubbi na fitowa daga dakin daukeda tray din abinci da Inayah din bataci ba. Zubbi na ganinsa tayi saurin Dan yi gefe Tana cewa" Welcome Sir. Tray din hannunta ya kalla ganin Babu abinda aka taba daga abincin. Dan rintse Ido yayi ya bude tareda cewa a natse, "Kiyi warming abincin ki dawo Mata dashi. Ok Sir" tafada tareda barin gurin. Dayake kofar abude take Koda suke maganar Dan haka Inayah taji Qamshin turensa tasan abbi na kusa sai gashi taji muryarsa a hankali. Da sallama Mara sauti sosai yashigo dakin Yana kallon yanda take zaune kan gado daga fuskarta har idanuwanta sunyi mugun kumbura gabaki dayama kusan kamanninta sun sauya sbd kuka da tsananin tashin hankali. Sofa dake dakin ya nufa ya zauna ahankali tareda Dan takaita kallonsa akanta sbd ganin fuskarta ahakan damunsa zaiyi sbd baitaba barinta tun yarintaba tashiga damuwa irin haka. Yana zaunawa ta miqe tsaye ta nufosa. Wani kallo yayiwa qafafuwanta dasukai haske sosai ga sai zanen maroon lallen da akai Mata na aure yafito da Babu safa ko bedroom feetwear a qafafun tana kallon ta dakata tareda komawa baya ta dauki feetwear dake gefen gadon masu taushi na bargo ta saka kafin ta nufosa Dan yawo ba feetwear ko safa wani abune da abbinta koyar da ita tun qanqanuwarta Duk tsafta da kyan gidansu basa da yanda tsarin gidansu yake na komai fes Bata tafiya ba takarmin ko safa a qafarta sbd wasu qananun qwayoyin cuta ta qafa suke saurin shigar mutum. Gefensa ta qaraso jiki a sanyaye ta zauna tana kokarin yimasa wani kukan Dan dama tun jiya takeson ganinsa tayi Masa kukan dake cinta Amma taqi barin kowa ya gansa ya shigewarsa. Fara hawaye tayi tana kallonsa tace" Abbi Dan Allah kada kacemun bakaine mahaifinaba, Ni Kai nasani Kuma Kai zanci gaba da sani a wannan matsayin Bazan taba karban kowaba amatsayin uwa ko uba Dan Allah Abbi kabarni da matsayina na 'yarka ta Jini nafison. Umma yaganah ce ta bude kofar dakin tashigo Kai tsaye sbd dawowarsu kenan. INAYAH Bata tsaya da abinda take fadaba tacigaba da cewa" Abbi Dan Allah kada karka bari a sauya mini wani sunan bayan Wanda ka sanyamin, Ni banason kowa amatsayin jinina sai Kai, Abbi Ni Kai kadai ne jinina, Danasan yanda zanyi na hada Jinina da naka ya gauraya daya da naka Abbi wlh danayi ayau dinnan....... Umma yaganah dake kokarin juyawa tabasu guri Batasan lokacinda ta tsaya cak ba tareda dawowa da wuri tana buge bakin Inayah din cikin kunyar zancenta. Shi kansa MAJEED din Dan muskutawa yayi tareda fuskewa sbd Inayah dai idan zatai zance ba ruwanta yanko abarta kawai takeyi. Lokuta da dama Dan umma yaganah na kwabarta ne Amma zantukan datake yankowa gaban Abbin mamaki suke basa matuqa Dan shi wasu abubuwan na halayen Mata dabai taba saniba sbd Bai mu'amalantu dasuba sosai a gurin Inayah yake ji da saninsu. Ahankali ya kalleta Bayan ya kalli umma yaganah da bakin Inayah yake Bata takaici wasu lokutan. A natse cikin yace" Inayah wannan wata Gaskia ce da Dole zamu hakura na dauka sbd nafiki Jin dacin rashin Zama Wanda ya haifeki Amma hakan Allah ya qaddara. Wannan kukan kidaina Babu Wanda zai tafi dake koina, Dr Abdul Kuma idan kin daina kuka kin nutsu zan Bari kije ki dubasa. Gangaro Mata hawaye sukai tace" Abbi maganar auren fa? Da gaske an daura mun aure da...... Sake buge bakinta umma yaganah tayi cikin wani sabon takaicin tace" Waiki bakinki baya shiru idan bakisan me Zaki fada bane? Qarya zamu Miki baa shine mijinki ba? Baice komaiba ya miqe ya fice Yana cewa" Wannan kukan idan Baki dainaba ko gate bazaki sake fitaba bare zuwa duba Dr Abdul. Yana fita anty Hafsat da Zata wuce tashigo dakin tana kallonsu, umma ta zauna gefen Inayah cikin takaici tace" Ke bakinki baya haila ko? Kullum Ina kwabar bakin Amma kin kasa iya kamesa ko? Da kike maganar dakinsan yanda Zaki hada Jini dashi da kin hada ayau Saurin uban me kikeyi idan a gauraya Jini kikeso ai zaa zo gurin saikiyi bayani da kanki, Kullum kwabarki nakeyi bakyaji Yanzu dai mijinki ne idan zakiyi hankali kiyi Dan kuwa bakin Nan naki kaiki zaiyi yabaro tun baayi nisaba ki gane barno gabas take. Murmushi Anty Hafsat tayi sbd ko baa fadaba tagano kan zancen ta kalli Inayah datai tsit idonta yake hawayen fadan ummsn cikin kulawa tace, "Yi shiru Inayah Amma ki koya fadan magana bako wace iriba agaban Abbi yanzu sbd yanzu mijinki ne wata maganar idan kinyi kina tadowa kanki aikine tunda wuri wuri Wanda bazaki iya daukaba. Kinga shikansa yanzu bai Gama karban yanayin ba Dan haka ki ringa Kama bakinki kisan me zakina fada. Karma ta Kama taci gaba ita Zata bada labari Ina zaune Ina kallo Badai gaurayan Jini kikesoba Zaa gauraya Inda rai kuwa. Umma Dan Allah ayi Mata hakuri da kyakkyawar manufa ta fada sbd yanayin data samu kanta da Wanda ta dauka mahaifinta ne, Ita kanta Batasan wata manufar abinda tafada tabadaba. Duk da hakan Inayah nada buqatan sanin abubuwa da dama na sanin Kai tunda yanzu aure yahau kanta Dan haka Hafsat ke wannan aikin ya sama saiki bada himma gurin ganar da ita. Da farin ciki anty Hafsat tace" Umma ai wannan aikin Dole ma kuwa Musamman angon na Inayah shakkarsa duka muke muma dake yanne Kuma iyaye Amma ahakan zakisha kallon hudubar da zanwa mutuniyar tawa. Allah yasa ta dauka idan ba zuwa zatai tana fada Masa abubuwan da kike koya mataba Wlh databarki da kunyar duniya" Umma yaganah ta fada tana dariyar abinda zai biyo baya kuwa idan hakan ta kasance. Dariya anty Hafsat tayi tana cewa" Dakuwa mun Bata da ita idan tamun wannan gangancin Yanzu mijine bakomai Zata fada masaba sabanin adah dayake matsayin uba. Ganin Zata shiririce yasata miqewa Tai musu Saida safe ta wuce sbd anzo daukanta. Bayan fitar anty Hafsat umma ma miqewa Tay ta wuce dakinta INAYAH tabi kofar dasuka fice da kallo tanajin sun datse Mata maganarta da Abbi batareda sun gamaba. Miqawa tayi ta nufi toilet tashige sbd alwalar sallar magrib da ake Kira. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/2, 10:00 AM] It's Queen Meenali👑: *_35_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* *_'YAR ZURU Maman ZEE ZEE Best kayan mata_* Shin ko kunada labarin Yar Zuru mamar ZEE ZEE Mai maida tsohuwa yarinya wadda ta shahara wurin hada kaya kamar haka ❤️kamar su Kaza Zabo Zakara Ciccibi Zuciya Tsimin kankana d rake Tsimin tabaje Zumar dabino d kwakwa Zumar gorun tula syrup Garuka masu kama jiki kamar su ❤️ Bita zai zai Dan wata bakwai Madarar mata Bata🤐🤐🤐 Ba kishiya ba Ko mugun mutan d mugun aljani sai sun barki Matsin kinfi budurwa Kalolin gumba dsauransu Address maberar jariri bayan FGC sokoto Phone 08068526455 Instagram Yar Zuru mamar ZEE ZEE kayan mata. Karku Bari kuwuce Baku gwada kayan Maman zee zee best kayan Mata ba.. *_35_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Da daddare tun 7:30 sukaci abincin dare Amma banda Inayah dataqi fitowa shima Kuma abbin tambaya daya yayi umma tace Inayan ba yanzu tace zataciba Baikuma maganaba yagama cin abincinsa ya fice yabar umma da Neesah a table suna sake jinjina taurin Kai irin na Inayah sbd son zuwa ganin Abdul Zata dagawa kowa hankali. Cikin damuwa da takaici umma yaganah tace" Babban damuwata akan Inayah Ga abinda yakamata ta fuskanta wato Wanda aurensa ya rataya akanta Amma Sam ita ko yarda da zancen taqiyi bare bawa zancen mahimmanci hauka kawai ta dauka munayi tunda abokan wasantane mu, Idan Ni ta rainani ai Alhaji babbah da Abbin nata bazasuyi Mata wasaba ko shirme irin nata datake tunani. Neesah ajiyar zuciya ta sauke tana ajiye spoon din hannunta tareda Shiga tunani tana kwatanta irin rayuwar da Aminiyarta Zata zuba a cikin gidansu Kuma gidan aurenta da Wanda Koda qazantar mafarki Bata taba mafarkin aurensaba, To Amma yanxu da hakan ta kasance tayaya zata karba auren harsu samu cika burikan dasuka dauka zasuyi da mazajensu idan dukkaninsu sukai aure., Babban qarin abin shiga tunanin shine abbin da kusan baiwani San mataba, bama kusan ba Baisaniba kwata kwata tunda bashine ya Haifa Inayah ba to tabbas kenan "he's virgin" tafada a bayyane tana zare Ido cikin Murna Mai tsanani sbd burin Inayah kenan auren wanda Bai taba sanin kowace maceba sai akanta,,, ""ohh my God, Abbi is still a virgin???? Tafada da Dan farin ciki tana kokarin miqewa zuwa gurin qawarta suka hada Ido da umma yaganah dake sake Baki duka tana kallonta cikeda tsoro da mamakin yanda yaran Nan suka Gama lalacewa basuda masaniya akai. Wata irin kunya ce takama Neesah tana ganin irin kallon da umma ke Mata tasan itama ta sake layi Dan daga ita har Inayah din bakin nasu wani lokacin ba burki bare ribas. Dan fuskewa take kokarin Yi ta hanyar komawa ta zauna Dan qarasa cin abincin da Zata Bari sbd zumudi Umma a kasalance da mamaki tace" Aa karki koma ki zauna jeki Inda kikai niyar zuwa Dan yanzu Kam na Gama tabbatarda kunfi qarfina yaran Nan Musamman Inayah,. Yanzu ko kunyar Allah bakwaji zakije kuyi maganar MAJEED Bai taba sanin ma.... Kasa qarasawa tayi tana girgiza Kai cikeda kunya da takaicin fada da bakinta. Kallon yanda Neesah tayi tsamo tsamo tayi tace" Jeki kuyi abinda zakuyi din, Nagamo da ita tana maganar gauraya Jini kekuma gakinan yanzu kema kina Taki maganar banzar, Allah ya shiryaku ya sakamu kunya irin ta 'yaya Mata Dan kuwa Naga sai mun dage da adduar kunyi nisa, Ita ansamu tun batai tsamari ba an aurar Saura ke Kema Kuma hankali na kwantawa zanfadawa Fatima suyi Miki aure. Kaman munafukar Neesah tabar gurin a ranta tana cewa" Allah yasa umma yaganah kinawa momy magana ko wata kada na qara Amin auren ai inaso. Da mamaki umma tasake bin Neesah da kallo jin ta amsa adduarta ta qarshe da cewa" Amin" a bayyane. Neesah Kai tsaye dakin Neesah ta Isa tana murmushi da dauke gira daya ta qarasa kan gadon da Inayah din ke kwance tana waya da Abdulsamad wadda sai alokacin suka samu Jin juna tunda wannan abun yafaru. Tunda ya Kira wayar ta dauka take rero Masa wani irin kuka ahankali tanajin kaman ta bude Masa zuciyarta yaga matsayin sonsa aciki. Kukanta kawai yake saurara Yana zubda hawaye shima sbd bazai iya magana ba shima, Daga zuciyarsa har kirjinsa da kansa zafi suke Masa, Yakasa yarda ko karban Inayah amatsayin 'yar uwa, Bazai iyaba, Bazai iya daukaba, Hakama zuciyarsa bazata iya daukaba bare kwakwalwarsa data gama yamutsewa akan son Inayah tuni. Ganin halinda suke cikine yasa jikin Neesah sanyi ta kalli Inayah dake kuka sosai har hancinta Saida yayi jajir Bayan idanuwanta da fuskar gabaki daya. Karbe wayar Neesah tayi tareda dorawa akan kunnenta cikin tausasa murya dakuma damuwa tace" Dr wannan kaman kuna neman butulcewa qaddarar da Allah yake jarabtarku da itane, Inayah matar wanice yanzu daga ita har Kai kunsan me ake nufi da hakan Badan kana matsayin muharramintaba dasai nace wanna haramun ne kuke aikatawa mezaisa bazaku danganaba ku dauki hakan wani babban rabo daga ubangiji ku gode Masa da kuka kasancema Jini daya qarshen kauna, Shi Abbi Yana baqin ciki da takaicin rashin zamtowarta jininsa kaikuma data zamo jininka kuna Neman batawa kowa da komai Dan wannan lalata komai zaku qarasa yi. Kashe wayar tayi ta dungurar Mata gefe tareda kallonta cikin fara Dan siqewa da yawan kukanta akan soyayyar Dr Abdul tace" Inayah can you stop all this stupidity, Yanzu ke kunya bakyaji ki zabi wani kinata kuka akan wani duk kin kasa tsayawama ki duba babban abinda ya rataya akanki. Tsoki tayi tareda juyawa tabar gurin ta fada toilet Dan yin wanka sbd ita duk sun fara Bata haushi. Rayuwa saukine da ita, Ansan ba abune Mai saukin karbaba wannan yanayin dayazo Amma Kuma ba abinda zaka daga hankalinka bane sbd abbin dai dayafi Mata komai da kowa yasake zamowa nata dukkaninsa ba maganar kukan rabuwa dashi Amma haukan soyayyar wani na Neman rufe Mata Ido waninma 'dan uwanta da aka tabbatar Mata da Babu aure tsakaninsu. Inayah dake hawaye komawa tayi ta kwanta kawai batareda ta iya magana ba sbd bazata iya cire soyayyar Dr Abdul arantaba lokaci dayaba, Tafi tausayinta sosai akan kanta na wannan yanayin dasuka samu kansu sbd sanin yanda yagama zurfafa da haukacewa a Sonta. Aurenta Kuma da Abbi Bata Gama yarda dashi bane sbd tasan abbin ma bazai taba karban aurenba sbd Babu yanda zaayi suyi rayuwa ko zaman aure Dan tamkar haramunce garesu. Ita maganar uwarta da akeyi Kuma batajin Zata taba iya daukanta a wani matsayin Bayan na mahaifiyar Abdulsamad kawai Sbd aduk matsayinda Abbi zai dauketa hakan itama Zata dauketa Mai kyau ko sabaninsa sbd har abada Abbinta shine komai nata Kuma maganarsa zataci gaba Dabi har qarshen rayuwarta. Koda Neesah tafito har lokacin Inayah din takasa daina hawaye sbd yanzu kukan rashin sanin kanta takeyi. Shin marainiyace ita kokuwa 'yar gaba da fatihan dagaske¿ Yarasa tayaya uwarta Zata jefar da ita kokuma guduwa tabarta kokuma kaita gidan marayu tun jarinta, Tayaya ta fada hannun Abbinta, Wace irin tsana uwarta Tai Mata da Zata jefar da ita tana jaririya ta dauki Abdul daya girmeta Amma ita ta jefar da ita. Ganin kukan datakeyi yayi yawa Kuma akwai tsananin damuwar abin da quncinsa a bayyane da Inayahn yasa Neesah tahowa ta zauna gefen Inayah din tareda Dan rungumota batareda tace komaiba Dan kada ta katse Mata damuwar datakeson ragewa ta hanyar kukan da tunanin. Sun jima a hakan kafin Inayah ta janye jikinta tareda zamewa ta kwanta kan gadon tana rufe idanuwanta. Shiryawa Neesah tayi itama cikin kayan bacci masu gajeran wando tazo ta kwanta gefen Inayah sbd tana period bare tayi sallar ishai. Tanajin yanda jikin Inayah yayi zafi sosai alaman yauma da zazzabin atareda ita Dan haka ta miqe tadauko Mata magani tabata Tasha suka kwanta tanajin jikinta duk yakuma sanyi. Washe gari ma Bata fito breakfast shima Abbin Bai fitoba su kadai sukayi daga umma yaganah sai Neesah. Bayan sun Gama umma yaganah da kanta takai breakfast din abbin palonsa ta jiye ta fito. Neesah Kuma tayi Shirin na Inayah takai Mata daki itama. Zazzabinta ya tsananta Dan haka hankalinsu ya tashi Amma dai duk da hakan umma Bata sanarwa Abbin ba sbd kada damuwar suyi yawa Dan haka suka samu suka Dan lallabata Neesah Tai Mata allura bayan awa biyu jikin nata ya Dan saki tasamu qwarinsa tasamu tayi wanka tayi sallar azahar. Tana idarwa ta zare kayan sallar ta miqe ahankali ta zura slippers ta fito dakin sbd tasan Abbinta baisan batada lafiyaba tunda Bai nemetaba Dan haka Kai tsaye tana fitowa Bata nufi koinaba sai hanyar palonsa jikinta ba qwari tafiyarma ahankali takeyi. Tsit taji gidan duk da dama basuda wani manyan motsi a gidan Amma tsit taji da alama kaman umma yaganah basa gidan. A dining yake zaune yana Shan ruwan yakasa cin abincin dake jere gabansa idanuwansa sun sauya sosai sbd yau wani irin daci ne da quncin zuciya tareda damuwar shekaru suke tasowa suna komawa sababbi fal Kaman yanda komai yafaru alokacin bayan..., Baitaba sanin zai Kuma fuskantar maimaicin abinda yafaru dashiba alokacinda yake cikin radadi da zafin maraicinsa abayaba. Rintse idanuwansa yayi cikeda daci Mai tsanani dayake sake cika maqoshinsa... Qamshin Turaren Inayah duk da Bata wani sakaba da yawaba yasashi bude idanuwansa dasukai jajir Yana kokarin basarda yanayinsa sbd kada tagani ta daga hankali da tambayarsa abinda yake damunsa. Jin takunta ya nufi wani direction din yasashi waiwayowa ahankali ya kalli hanyar. Riga da wandone ajikinta na masu Fadi sosai Amma basuda nauyi ko kadan sai suke saka kirjinta da bra rawa qaramar hular kayan ce kawai akanta Bata Gama rufe baqin gashintaba da akaiwa gyaran aure Amma auren baiyiyuba. Dauke kansa yayi daga kallon gurin tareda miqewa ya nufito ganin hanyar palon dazatakl kaita gurinsa ta nufa Kuma yasan su Alhaji babbah da dangin Hadiza da Hadizan suna ciki sbd maganganun da zaayi... Shigarta hakan gurin zai iya bayyanarda raunin tarbiyarta ga Hadiza da danginta dake gurin harma da Dr Abdul Wanda zai Mata kallon da zai iya Zama laifi ga ubangiji. Qaramin palon daya rabasu da palon Abbin ta Isa Zata shige taji anriqo hannunta ta baya. Batada qarfin razana Amma duk da hakan a tsorace ta waiwayo sbd riqon bana mace bane hakama tasan basuda namiji a gidan dazai shigo har nan bayan Abbinta. Tana juyowa acikin idon Abbin idonta yafara fadawa akaron farko dataji tsoro da fargaban kallon idon Abbin... Da sauri ta maida kallonta kansa tana bayyanarda tsoronta da damuwarta tace" Abbi.. Kasa magana tayi sbd idanuwanta dake kokarin cikowa da hawayen da batamasan na menene ba ita dai tasan Abbinta shagwabarta akansa ta qare Dan haka yanzuma tasan bazata iya dainawa sbd kallonsa kawai nasa taji duniyarta alhmdllh sbd samun tsayayyen uba kamansa sai Mai saa irinta. Matsowa tayi tana sake riqe hannunsa cikin hawaye tace" Abbi Dan Allah kayi hakuri idan fushi kakeyi sbd na nace Akan zuwa asibiti dubo heart... Tun jiya Banda lafiya sosai abbi baka.. Saketa yayi tareda zare hannunta daga riqon datai Masa Tabisa da kallo tana jin sabon kuka na zuwar Mata sbd ganin kaman fushi yake da ita sbd ta saba riqe hannun mahaifinta ko bayan ta girma Bata daina riqe hannunsa Amma yau din ya zare batareda ya kalletaba. Juyawa yayi Yana komawa palon ya zauna Yana cewa" Akwai baqi aciki koma ciki anjima zansa Dr farhat tazo ta dubaki. Kuka ya fashi dashi tareda zuwa gabansa ta durqusa tana hawaye masu gudu tace" Abbi Dan Allah kayi hkr idan nayi laifi, Kamun hukuncin laifin ma Amma Dan Allah kada kabari a rabani da Heart Abbi..... #MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/2, 10:00 AM] It's Queen Meenali👑: *_36_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ahankali ya waiwayo ya kalleta Ganin irin kukan datakeyi yasashi Dan sauke ajiyar zuciya Yana nazarin halinda tashiga duk tabi ta sauya sbd kuka da damuwa da tashin hankali lokaci kankani. Dr Abdulsamad ne ya sulale daga palon batareda sanin kowaba ya shigo ciki Yana Jin idan ba ganin Inayahn yayiba bazai fahimci dukkanin abinda akeson fadaba a zaman. Umma yaganah data lura da fitarsa ta miqe ta biyo bayansa sbd fargabar abinda shedan zai iya sawa su aikata shida Inayahn idan sun hadu, Itakuma yanzu Kam tunda aka daura auren INAYAH da MAJEED batajin tanada abinda yakai Mata wannan auren mahimmanci sbd dai basuda yanda zasuyi aure an daura Dan haka kowa hakuri zaiyi a runguma wannan qaddarar gabaki daya. Shigowar Dr Abdul yasa Inayah dakatawa daga rokon datakeyiwa Abbi ta zubawa Dr Abdul din idanuwanta tanajin kaunarsa na sake karyar Mata da zuciya.. Meyesa ummansa Bata tashi bayyanaba sai alokacinda zasu mallaki junansu. Dr Abdul ma kasa riqe hawayensa yayi dukda zamtowarsa namiji agabanta. Qarasowa yayi ya durqusa gaban Abbin shima tareda sunkuyar da Kai Yana tsiyayar hawaye cikin yanayi na damuwa Mai tsanani da quncin dake cinsa cikin zuciya yace" Sir Dan Allah kada ka rabani da Inayah idan ta haramta aguna matsayin Mata Dan Allah kabani ita matsayin 'yar uwa tunda hakan Bai haramtaba. Kukan tausayin Dr Abdul din yakuma zuwarwa Inayah ta kalli abbin dayaqi ko kallonsu yayi shiru cikin nasa nazarin. Idanuwansu sun rufe suna roqonsa Inayah roqonsa takeyi akan ya warware auren da aka daura sbd har abada bazata iya karban Abbinta amatsayin mijiba. Irin kukan datakeyi shine yake Sosa ransa ba girman kalaman datake fadaba, Har cikin ranta take bayyanarda quncinta na auren, Bazata iya karban wannan aurenba, Ta zabi yaci gaba da Zama ubanta har qarshen rayuwarta... Umma yaganah dataga irin kuka da Inayah keyi ya daga hankalinta sosai Musamman ganin shima MAJEED din yanda idanuwansa suka sauya sosai batareda ya juyo ya kalli su Inayahn ba. Miqewa yayi tsaye ahankali ganin tana neman shaqewa sbd kuka numfashinta Yana hardewa alamar wani attack dinne Zata Kuma samu... Idanuwansa ya juyo ya zuba Mata Yana kallon yanda numfashinta ke kokarin rabuwa da kirjinta duk akan aurensa daya rataya akanta, Meyesa tun farko ya aminta da auren sbd tunanin shine mafitar da Zata Hana kowa karban Inayah daga hannunsa... A zuciyarsa kusan yafi kowa Jin kunci da shiga matsananci hali akan wannan yanayin dahar yakai ga wannan auren Wanda shima yasan yin auren kawai akai bazai taba kallon 'yarsa amatsayin maceba bare matar da....kasa qarasa tunanin yayi sbd nauyin da dacin kalaman. Da gudu umma taqaraso tana kokarin kamo Inayah Inayahn ta miqe da sauri tana sake rarrafawa gaban Abbi tana roqonsa numfashinta ko fita daidai bayayi. Cikin tashin hankali umma yaganah ta sake tarota tana miqar da ita tsaye tace" INAYAH kinada hankali kuwa? Kinsan me kike fada? Wane auren kikeda qwarin gwuwar cewa araba? Cikin kuka tace" Umma yaganah wlh bazan iyaba, Bazan iyaba, Rayuwar auren da akeson ayi tsakanin ma'aurata bazan iya yinta da Abbi ba wlh, Rayuwar auren dazanyi bazan taba yinta da Abbi ba, Umma bazan iya kwanciya gado...... Suka umma yaganah takaiwa bakin tanajin baqin ciki da takaici harma da tashin hankali sbd yanayin MAJEED duk kannewarsa Yana bayyanarda bacin Rai da griman tasirin da maganganunta keyi a ransa. Ajiyar zuciya Mai sanyi abbin ya sake Yana kallon yanda numfashinta ke kokawa da Isa yasake sauke numfashi Yana Dan dauke idonsa daga kallon kirjinta dake harbawa sosai sbd halinda take ciki. Fuskarta ya kalla ahankali cikeda kulawa ya kalleta tareda riqo hannunta daga jikin Umma yaganah ya zaunar kan kujera tareda kallonta Yana nazarin kalamanta dasuke bayyanarda haqiqanin Gaskiar abinda yake ranta. Cikin nutsuwa da sautin muryarsa Mai nutsuwa da kamewa yace" Inayah!!!!! Kasa dagowa tayi ta kallesa sai hawayenta dake gara gangarowa daga Idanuwanta dasukai mummunan kumbura. Kukan dakikeyi Zaki jawa kanki ciwo akan wannan unnecessary Al'amarin, Auren ne yasaki wannan halin right? Gyada Kai tayi wasu zafafan hawaye na Kuma ganganro Mata. Kai tsaye Bai tsaya komaiba yace" namiki alqawarin sauke Miki wannan auren daga lokacinda kika yarda da qaddara kika San aure tsakaninki da Abdul ya haramta, Zan sauke Miki auren ki koma hannun mahaifiyarki da Abdulsamad kimun alqawarin bazaki Bari shedan ya Shiga zuciyarkiba kiyi watsi da tarbiyar Dana Baki. Dago jajayen idanuwanta tayi da basa iya budewa sosai ta kallesa Jin Zata bar hannunsa Wanda ita Batasan wannan yarenba kwata kwata bazata taba barinsa Koda Zata rasa kowa a duniya. Juyawa yayi ya kalli umma yaganah zaiyi magana umma yaganah tayi saurin zubewa qasa tana neman fashe Masa da kuka tace" Dan girman Allah MAJEED kada ka furta kalma daya data danganci rabuwar wannan auren..... Rintse idanuwansa yayi Yana sake hadiye yanayin dayake ciki ya kalli Inayah dake kallonsa Ido na tsiyayar hawaye tana jiran kalamansa da zasu warware auren su koma matsayinsu na uba da 'ya. Tunda umma yaganah take Bata dukan Inayah ba bare ma agaban Abbi sai yau dataji kaman tayiwa Inayah din duka tashi Kisha ruwan gishiri Dan haka Batasan lokacinda ta ringa dukan Inayahn da mayafin Jikintaba tareda damqar hannunta tayi ciki da ita bayan ta kalli cikin tsakiyar idanuwan Dr Abdul dake zubarda hawaye shime ta buga Masa wani irin mummunan gargadin dayasa shi kallon Abbi Wanda yakasa cewa komai sbd kansa daya toshe Yana sake daukan zafi. Wucewa yayi yabar Dr Abdul din a tsaye gurin Yana bin hanyoyin dasuka bi da idanuwa cikin tashin hankali sbd Koda yasan bazai taba auren Dan Inayah ba zaifi samun nutsuwa da sauki idan yasan ba auren kowa kanta. Umma na shiga daki da Inayah tayi wurgi da ita tsakiyar dakin tareda kallonta cikin tsananin takaici da bacin Rai tarasa wane irin duka zataiwa bakin Inayahn, Cikin kuka Inayah ta cusa kanta cikin tsakiyar qafafunta tana jin hankalinta Kuma na tashi da kalman Abbi na miqata ga matarda ake Kira da mahaifiyarta wadda haryanzu basu sake haduwaba tun ranarda tazo gidan komai ya lalace. Daqyar umma yaganah ta samu danne zuciyarta Takoma palon Wanda dama MAJEED ake jiran yazo afara maganar da zaayi. Koda Isa palon zaman taron yaqara yamutsewa sbd Dr Abdul da jikinsa ya rikice Dole suka bar gidan. Umma Hadiza kaman zata Dora hannu akai tayita rusa ihu takeji sbd wannan masifar dake Neman dawo Mata, 'danta daya Wanda take ganin ta Kama qwaqwalwarsa na Neman juyewa sbd son 'yar uwarsa Gashi tana neman rasashi batareda wannan datake ganin tasamoba Bayan shekaru tazo hannuntaba. Bataso tafiyaba saita hadu da Inayah Amma MAJEED ya hanata ganin 'yarta sbd yaqara nuna Mata ikonsa akanta. Bayan barinsu gidan umma yaganah qin zuwa Inda Inayah take tayi sbd wannan karon tayi mummunan Kona Mata Rai. Matuqar auren MAJEED yabar kanta Bata tunanin Inayah Zata samu mijinda zai kaisa agurin kulawa da ita Dan haka zatai iya kokarinta gurin ganin wannan auren baitaba rabuwaba Koda hakan na nufin da qarfin hali ta cusa Inayah gun MAJEED ya dirka Mata ciki taga yanda auren zai rabu kowama ya huta har Hadizan da 'dan su huta dasu akan raba auren. Ranar gidan ko abincin dare Babu Wanda ya fito ci sai Neesah kawai data fito itama snacks kawai taci takoma daki ta kwanta. Acikin daren Abbi yayi booking ticket na zuwa Abuja akwai Wanda zai gani daga can zai wucewarsa Dan Yana buqatan kansa ya sake. Washe gari qarfe 8 na safe yayiwa umma yaganah txt driver ya wuce dashi airport jirginsu ya tashi qarfe Tara. Koda INAYAH ta tashi da safe jiki a mace tasan Bata kyautaba Musamman da umma yaganah ta matse fuska sosai Bata wani sake Mata ba Duk saitaji tasake Shiga damuwa dan haka ko wanka bataiba da Riga da wandon bacci masu tsantsi ta wuce palon Abbinta Dan basa hakuri sbd Bata iya juran fushinsa akanta ko kadan, Kuma ta wani bangaren gaskiyarta ce tafada bazata iya rayuwar aure da Abbinba sbd asalin life takeso arayuwar aurenta wanda Zata iya nuna soyayyar mijinta agaban kowa Kuma shima zai iya nunawa agaban kowa Dan haka Babu ta Inda Zata iya wannan rayuwar da Abbi Wanda takewa kallon ubanta Kuma uwarta. Shine ya koyar da ita yakuma Bata tarbiyar fadar Gaskia komai dacin dazata kawo shiyasa koyaushe ake ganin wautarta Dan ita tasaba gaskiyarta take fada daga zuciya ba boye boye ko munafurci. Kayan jikinta umma yaganah ta kalla lokacinda ta gaisheta tareda juyawa Zata nufa sashen Abbin. Floral pyjamas ne na bacci ajikinta masu santsi farare, Babu bra ajikinta Dan haka kirjinta dasuke tsaye qyam suna bayyanarda basa cikin bra din. Ko hips dinta sosai suka fito a wandon kayan sbd santsin kayan yasa suka Dan lafe a jikinta. Da adah ne umma yaganah hanata zuwa takeyi gaban Abbinta da kayan bacci sbd kusan rayuwar Inayah din babu ruwanta kusan koyaya tana iya zuwa gaban mahaifinta da towel ne kawai Bata iya zuwa gabansa sai guntayen Kaya Amma Dan kayan bacci dasu leggings duk ba komai bane agunta. Umman na sane Sarai ta qyaleta ta Kama hanyar palon nasa batareda tace Mata taje ta sauyaba kokuma sanya wani Abu akai. Ja'irar yarinya Allah ya nunan ranarda wannan bakin naki zai mutu yayi hankali. Shima MAJEED din da haryanzu yake biye Miki yaqi bude Baki ya magantu dakyau ki dawo hankalinki. Inayah nakaiwa kofa massage din MAJEED nashigowa wayar umma na cewan yayi tafiya. Sanyi jikinta yayi tanajin tausayin MAJEED din sbd abubuwan sun Masa yawa gashi wannan Yar banzar na Neman qara zafafa Masa kai da haukarta. Cikin gatse tace" Hajiya saiki dawo MAJEED din yayi tafiya yace Saiki dawo kici gaba da kuka tunda Baki aura Dan rayuwar dakike burin samun aureba. Maganar umma na cewan abbin yayi tafiya yasa hankalinta sake tashi saidai Bata nunaba sbd umman karta cigaba da Mata wannan fadan na baqar magana Dan haka ta juya jiki mace Takoma dakinta. Tana shiga daki ta zauna tareda daukan wayarta Kai tsaye tasaka kiransa tana sake Shiga damuwa Mai tsanani, Abbinta akaron farko dasuka kwana suka wuni basuyi wayaba basuyi maganar arzikiba, Yanzu Kuma yayi tafiya batama saniba hakama umma yaganah kawai ya fadawa. Hawaye taji idanuwanta na cikowa dasu indai kuwa akan Abdulsamad Abbinta zaiyi irin wannan fushin da ita Zata hakura dashi... Tama hakura dashi Zata bawa Abbi hakuri bazata sake ko maganar Abdul dinba barema ummansa. Kiran wayarsa tahau yi Amma takasa samu Dan haka taji kaman wani zazzabin na neman kamata Dan haka ta silala tayo wanka ta shirya cikin doguwar Riga breakfast dinma Dan Dole ta fito taci tana qarfafawa kanta sbd Abbi yadawo anjima ya taddata ta sake zaifi saurin yafe Mata sbd fushin Abbi shine abinda Bata taba dauka da wasaba. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/3, 10:19 AM] It's Queen Meenali👑: *_37_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Sukuku ta wuni ranar zuciyarta ba Dadi hakama umma har lokacin ta fuske Mata ga Neesah nata shirye shiryen tafiyarta ga abbin sai Kira takeyi takasa samunsa duk saitaji kaman tayita rusa kuka Gashi umma na fushi ko tayi kukan tasan ba rarrashinta umman zataiba. Har qarfe biyar na yamma tana jiran dawowar abbin sbd Bata tunanin tafiyarsa Mai nisace kokuma kwana bare barin qasa dazai tafi Bata saniba tana matsayin 'yarsa daya tal...... Shiru tayi daga wannan tunanin sbd tunowa da auren da har lokacin Batajin ta sauko ta karba auren, Ta hakura da Dr Abdul sbd kaucewa fushin abbin Amma ita maganar aurenta dashi batajin Zata taba karban wannan. Ganin zaman Yana neman Cinna Mata hauka yasa ta fito Palo tana kokarin nufar hanyar dakin umma yaganah saiga qarar akwai baqi a kofa. Duk da tasan ba Abbi bane Amma sbd tana buqatan ganinsa yasa taje da sauri ta bude tana adduar Allah yasa shi dinne. Anty Hafsat tagani da CM da sauri ta rungume anty Hafsat tana Jin hawaye na ciko idonta kawai sbd Daman tana neman Wanda Zata fadawa kukanta. Cikin kulawa Anty Hafsat ta dago bayan ta zare jikinta tace" Muna tareda baqi Inayah behave yourself idan mun nutsu mayi magana. Fuskarta still da sauran hawaye ta juyo ta kalli baqin. CM tafara kallo cikin nutsuwa tace" Daddy Ina wuni? Murmushi yayi cikin kulawa shima yace" Lfy kalau Inayah, Yaya umma yaganah? Ki gaidata idan Kun shiga bazan tsayaba sauri nake saidai idan nadawo. Anty Hafsat ya kalla yace" zanje na dauko Alhaji babbah sbd suma su Haj Hadizan suna hanyar qarasowa nan din kafin su iso akai su hajiya suyi sallah su huta sun biyo hanya. Juyawa yayi ya kalli farar dattijuwar dake tsaye gefe cikin ash Australian lace da lafaya baqa a nade da ita yace" Hajiya ku qarasa Bara na dauko Alhaji idan kafin Ku huta. Gyada Masa Kai kawai tayi ahankali tareda maida kallonta kan Inayah data kasa daukewa Ido. Cikin nutsuwa Inayah ta kalli matar wadda itama tsura Mata Ido yayi sosai sbd haskenta sosai da Kuma ganin kamanninta sosai da Abbinta Dan kuwa kusan Tama fisa kyau sbd tana mace saidai kawai manyancin datai sosai. A natse cikin kasa boye mamakinta sosai tace" Ina wuni? sannu da zuwa. Sam hajiyar Bata amsaba Wanda ita Inayah Sam Bata luraba juyawa tayi Takoma ciki tana sake saka Kiran Abbi a wayarta. Cak hajiyar tayi agurin taqi saka kafarta a palon. 'yarta dake gefenta wadda a shekaru tafi anty Hafsat shekaru sosai ta kalli hajiyar zuciyarta na quna kaman yanda ta hajiyar ke quna Kai tsaye ta bude Baki ba boye boye tace" Hajiya inaga mu koma gida kowai kokuma kokuma muje gidan Alhaji babbahn shida kikazo sbd alfarmar daya nema ta zuwan naki. Batareda hajiyar tace komaiba kuwa suka juya Anty Hafsat ta juyo da sauri tareda binsu a rikice tana bawa hajiyar hakurin su dawo. Hajiyar tafiyar kawai takeyi Amma zuciyarta a rufe take.... Ciwon hawan jininta Dana zuciya daf yake da tashi sbd dacin da zuciyarta ke dauka.. Kasa jurewa tayi ta tsaya cak tana Dan dafe kirjinta. Da sauri anty Hafsat da 'yar tata wadda anty Hafsat takira da Anty juwairiyyah suka riqota suna Kiran sunanta da cikin kulawa. Ganin tana neman faduwa agurin yasa ba yanda anty juwairiyyah ta iya suka Jata suka koma cikin gidan. Umma yaganah data fito palon Jin ance sunyi baqi Bata ga kowaba tana Shirin juyawa suka shigo da hajiyar a rirriqe. Da sauri cikin kulawa tace" Subhanallh, Hafsat baqin namune ba lafiya? Bari Akira Dr farhat da sauri kafin Nan Bari Neesah ta fara dubata. Ciki umman tayi takira Neesah saidai Ashe Neesah din ta fita Dole sai dr farhat suka kira da gaggawa. Agurin wayar anty Hafsat tace" Umma yaganah ki sanar da ita umman AA MAJEED ce da kanta da Allah ta iso da wuri........ Wuta umma yaganah ta dauke tareda bude dukkanin idonta tana kallon hajiya. Sai alokacin taga zallar kamannin MAJEED atareda hajiyar dan haka take jikinta Dana Inayah data fito lokacin mutuwa sbd tsananin farin ciki. Umma na aje wayar kuwa ta kalli anty Hafsat tace" Mahaifiyar MAJEED ce kikace? Eh umma itace. Maida kallonsu kan hajiya sukai itada Inayah lokaci daya fuskar Inayah daukeda farin ciki Batasan lokacinda ta furta" Yau Naga daya da cikin kakannina kenan... Ashe munada dangi muma, Abbi na ummansa na raye.. Da sauri umma yaganah ta Dan kwabeta kada ta sauka layi Cikin sakin fuska da bayyanan farin ciki tafara yimusu sabuwar sannu da zuwa tana miqewa Anty juwairiyyah ruwan roba da aka kawo Mara sanyi tace" Bata Tasha Zata Dan ji dama Dama kafin Dr farhat din tazo. Daga hajiyar har anti juwairiyyah Babu wanda ya iya magana har lokacin sbd Babu Wanda zuciyarsa Bata cikin dacin rai na shigowa gidan. Ganin yanayinsu yasa umma datake Babba ta fahimci akwai damuwa Dan haka tace Inayah tayi ciki har hajiyar ta samu nutsuwa tukunna. Babban dakin bakinsu dake gefen na umma yaganah aka gyara take duk da Baya buqatan wani gyaran sbd komai na dakin fes yake Kuma Babbane da toilet. Dubari su Anty Hafsat suka ringa yiwa hajiyar ana mata firfita duk da sanyin AC sbd asamu Dr farhat ta iso. Dr farhat na isowa aka Kama hajiyar aka Kai dakin da aka Gama gyara musu sanyin AC da qamshi sai tashi yakeyi. Ba wata matsalar bace kawai jinintane ya hau take. Maganinta da batazo dashiba shi Dr farhat tasa aka kawo suka Bata Cikin Yan mintuna kuwa sai gashi tadan samu tafara dawowa daidai. Fita akai aka bawa hajiyar da Anty juwairiyyah guri su but suyi sallah da sauransu tukuna. Bayan fitarsu ganin yanayin hajiyar yasa Anty juwairiyyah data Gama cika da baqin ciki aranta tun na shekarun Dana yanzu datake gani gabanta yasa bataiwa hajiyar maganar komaiba ta nufi toilet tashiga Dan yin alwala. Hajiyarma saita huta Zata iya sallar sbd tanajin jiri har lokacin da bugawar zuciya da sauri Dan haka rufe idanuwa tayi daga kwancen tanajin zuciyarta na karye fiyeda shekarun data debo bada ABDULMAJEED dintaba sbd Bata saniba Ashe Yana Nan ya Gina sabuwar rayuwa da sabuwar uwa...Jin tayi hawaye na taruwa acikin idonta Amma kaman koyaushe Bata barin su gangaro sbd zubda hawayen uwa akan danta matuqar bana farin cikiba babbar masiface ga 'da. Inayah kuwa cikin farin ciki take Neman wayar abbin Amma still Bata samuba sai taji murnarta ta Kai sbd duk Wanda Zata samu a rayuwarta matuqar Bata daidai da Abbinta Bata cikin farin ciki da nutsuwa Dan haka take murnar ta sace Mata ta zauna daki tareda zubawa wayarta Ido. Umma yaganah kuwa hidima tashiga kitchen da kanta tafara yiwa su hajiyar MAJEED din sbd tasan matsayinsu sun wuce abar 'yan aiki da hidimarsu Dan haka tahau aikin abinci Lafiyayye Mai lafiya. Saida akai Kiran magriba aka Gama komai aka kwasa a jere da kuloli aka Kai dakinsu har lokacin daga hajiyar har Anty juwairiyyah Babu Wanda ya saki fuska ko nuna sakewa Amma hajiyar taji sauki tana zaune tana waya a sanyaye da babbar yarta. Umma yaganah Bata damu da rashin sakewarsuba bil haqqi take musu hidima tana sake bayyanar musu da mahimmanci dasuke dashi Mai girma a gidan duk da yau suka fara zuwa. Acan Kuma Inayah nason magana da anty Hafsat Amma anty Hafsat din ta hana sbd Dr farhat na gidan Bata wuceba Kuma Batasan da MAJEED aka daura aurenba a qataice bakowane yasan meye dalilin fasa auren Inayah da Dr Abdul ba hakama bakowa yasan da waye aka daura aurenba sbd duk har lokacin a uban Inayah suka Sansa. Dr farhat na tafiya saiga su Alhaji babbah sun iso daidai tareda motarsu umma Hadiza da 'yan uwanta. Dunguma sukai suka shigo ciki gabaki daya babban palonsu umma yaganah. Tunda umma Hadiza tashigo take rarraba idon Neman ganin Inayah cikin gidan. Inayah tunda taji su umma Hadiza sunzo gidan taqi fitowa ko Alhaji babbah tanason fitowa ta gaidar Amma batajin Zata iya barin umma Hadiza ta ganta matuqar bada izinin Abbinta ba sbd shine kawai yakeda iko akanta na yanda zaiyi da alaqarta da Hadizan. Umma yaganah ma Gaisawa kawai tayi dasu Alhaji babban ta miqe Zata komawarta ciki sbd yanzu da mahaifiyar MAJEED take Nan ba buqatan zamanta agurin dama can Dan tana matsayin uwa ne. Cikin nutsuwa Alhaji babbah yace" Yaganah dawo ki zauna ai komai dake zaayi kece MAJEED yanzu tunda Baya Nan. Dan murmushin yaqe tayi tareda dawowa ta zauna tana dan kallon Inda hajiyar MAJEED take zaune fuskarta ba walwala ko kadan. Kusan kowa ya zauna ya nutsu, Alhaji babbah ne da CM a gefe daya Sai umma Hadiza da Haj balaraba a dayan gefen Alhaji buhari dasu malam Umar ma dasuka matsu dason ganin Inayah duk suna zaune sai Dr Abdul daya rakube cikin yanayi na tausayi da ciwon dake damunsa. Hajiyar MAJEED ma da Anty juwairiyyah da umma yaganah sai Anty Hafsat gefensu daya. Cikin nutsuwa Alhaji babbah yafara magana da cewa" To dukkaninmu dai kusan bamusan junaba anan MAJEED da INAYAH ne ya hadamu anan, MAJEED yayi tafiya wadda Nima ban hanasa duk da nasan zaayi wannan zaman sbd Yana cikin yamutsin Kai Dana zuciya Yaron Yana buqatan nutsuwa sbd abubuwan duk sun taru sun ratayane akansa Dan haka gwara abarsa ya samu nutsuwa kada pressure da damuwa din mahaifiyarsa gatanan data matarsa data hajiya Hadiza dama Tamu duka ta sanyasa cikin wani hali. Hajiya Asma'u wannan itace hajiya Hadiza da 'yan uwanta gasunan mahaifiyar Inayah 'yar MAJEED da kuka sani a baya matarsa Kuma a yanzu. Hajiya Hadiza wannan Kuma itace mahaifiyar ABDULMAJEED data haifesa. Ayanzu wannan taron dai na fahimatar junane dakuma warware duk wata damuwa da qaddarar data Riga ta wuce. Inayah dai ba 'yar MAJEED bace hajiya kaman yanda kike tunani Amma dai yanda tazo hannunsa ne Babu Wanda yasani sai Allah saikuma MAJEED din da Hadiza gatanan zaune. Hadiza ki warwarewa hajiya komai sbd kawarda zargi da Kuma damuwar qaddarorin dasuka gifta abaya data rabu da 'danta akan hakan. Dagowa Hadiza tayi jiki a sanyaye ta kalli hajiyar cikeda kunyar Zama mugun sanadin daya kawo abubuwa da dama. Kan su Yaya Umar da Yaya kabiru ta maida kallonta sbd kusan suma sune sanadin komai. Inayah data tsaya bakin kofar dakin umma yaganah sbd tanason taji yanda tazo hannun Abbinta da kunnenta batareda wani ya fada Mata ya rage Mata wani abun.... SHEKARUN BAYA.... #MAMUH## #LOVE/ROMANCE/LOADING _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/3, 10:19 AM] It's Queen Meenali👑: *_38_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Tana fitowa gidansu rungume da jaririyar tata dake lafe kirjinta tana bacci taji qafafuwanta na Neman sanyi Amma sukasa riqeta sbd wani irin nauyi da kirjinta kemata tareda radadi a maqoshi.. Sake rungume jaririyarta tayi da kyau ahankali kafin ta dago ta kalli hanya da idanuwanta dasuka qafe sukai jajir sbd kuka tuni ya qafe daga Idanuwanta. Ahankali ta daga qafafunta tafara tafiya tareda kauke kanta qasa sbd Yan anguwa wainda suka lura da ita suke kallonta da ma'anoni da maganganun zunde da zagi. Bakowane yasan tadwo daga Lagos dinba da ciki saidai sukaji haihuwar tareda rasuwar mahaifiyarta shiyasa kusan duk Wanda ya bude Baki tir da Allah wadai yake furtawa gareta da jaririyar 'yarta. Ahankali take takawar sbd rashin qarfin jiki dakuma qarin data samu agun haihuwa gakuma rashin abinci ko abinsha Dan haka batada wani babban kuzarin takawa da sauri harta fice daga layin batareda ta waiwayo ba Dan tanajin idanuwan mutane akanta Wanda tasan mummunan fatar rashin ganin me kyau suke Mata a duniyar da Zata shiga. Kasa hawa titi tayi sbd Batasan Inda ta dosaba, Batasan gurin waye Zata ba a wannan mummunan halin datake ciki, Batada uwa Bata uba batada miji waye gareta Mai tsaya mata? Samun kanta tayi da zaunawa bakin wata bishiya sbd kwakwalwarta datake neman Dena aiki. Jaririyarta tafara kuka Wanda na tsananin zafin ranar dake dukansu ne Yaye zanin datake dunqule aciki tayi ta Dan kalli fuskarta taga yanda fuskar tayi jajir take sbd azabar Rana Sai alokacin taji zuciyarta data daskare tana narkewa da tausayin kanta dana jaririyar Dan haka batada zabi daya wuce ta tunkari gidansu salisu ko ummansa Zata karbesu tunda jikartace su taimaketa ta zauna gurinsu ta Rena Ayshatouh idan ko shekara tayi saita barta takoma gidansu idanma sbd itane su Yaya Umar suka koreta daga gida. 'yar qaramar jakar kayanta ta bude tafara duba kudin datake dasu., Dari uku da ashirin tagani take jikinta yakuma mutuwa saidai halinda zuciyarta take ciki Batajin akwai abinda zai fisa daci., Miqewa tayi ta qarasa bakin titi Anata kallonta sbd Jin yanda jaririya ke kuka sosai a jikinta Dan haka Bata tsaya juran napep ba ta tsayarda Mai mashin ta hau suka tafi. Gabanta tsananta faduwa da shiga qunci yakeyi sbd hajiyar salisu ma batasan yaya zata karbesuba... Mai mashin na ajiyeta kofar gidan ta Ciro dari da hamsin ta miqa Masa ta juya ta shige qaramar kofar gidan tana sake qamqame yarta jikinta. Tun kafin ta qaraso ciki Yara suka fara Isa gurin hajiyar suka sanar Mata Hadiza tazo. Dan shiru hajiyar tayi kafin ta kalli yaran ta korasu waje ta dawo da hankalinta kansu balaraba dake gidan ta sallamesu suka wuce inda zasu ta kofar baya batareda sun tsaya Gaisawa da Hadizan ba Dan dama a sama sama suke da ita tun salisu nada Rai bare yanzu da basuda alaqa da ita. Da wata irin dasasshiyar sallama ta shigo hankali sbd muryarta ko fita batayi. Da mamaki hajiya ta kalleta idanuwanta na sauka kan jaririyar dake hannun Hadizan. Idanuwan Hadizan zuwa fuskarta ta kalla dakyau take tagane jegone tareda Hadizan Dan haka ta tattaro hankalinta da mamaki a bayyane kan fuskarta tace" Hadiza¿ Kece nake gani? Lafiya da Rana tsaka haka? Ba zaman karban gaisuwar Aishatu akeba. Kasa magana Hadiza tayi sbd jirin dake dibanta Dan haka a sukwane ta qaraso ta durqusa gaban hajiyar tareda sunkuyar dakai idanuwanta na sake rinewa. Sake Shiga firgici hajiya tayi tana qin nuna taga jariri atareda hadizanba tasake cewa" Hadiza nace lfy kuwa? Kiyi mgana kikai shiru kina bani tsoro... Dagowa Hadizan tayi tana kallon hajiyar sbd tasan bazatace bataga abinda ke hannuntaba Idanma Bata ganiba bazatace batajin kukan da Ayshatouh ke tsalawaba. Sunkuyar dakai tayi tareda bude jaririyar dakyau agaban hajiyar muryarta na a disashe da tsananin damuwa da qunci Mai daci tace" Hajiya haihuwa nayi su Yaya Umar sukace nabar gida, Bansan Inda zaniba sbd ko Abokai banda shine nataho Nan.... Dauke wuta hajiyar tayi daga zaune tana kallon Hadizan Baki sake ko fuskar jaririyar taqi kalla. Qofa tafara kalla ta leqa tsakar gida taga ba kowa tadawo da sauri ta kalli Hadizan cikin tsananin mamaki, firgici da takaici Kai tsaye tace" Me Zan Miki anan hadiza? Haihuwafa kikace kinyi? Haihuwa ba aure fa? Wace qaddarace wannan takaiki ga wannan mummunan sakamakon? Shine Kuma Zaki zomun Nan? Ko kunyar 'danki dake gidan Nan bakijiba kika kwaso jiki da jaririn shege kizomun anan? To Kinga Hadiza tun kafin Raina ya baci Kuma tum kafin wani yaji tashi ki fice, Mune mukafi kowa hauka a duniya ne dazamu Baki gurin zaman renon barna...... Rawa hannuwan Hadiza suka fara hankalinta yasake mummunan tashi tana kallon hajiya da idanuwanta jajir tace" Dan Allah hajiya ki yarda Dani ki fahimceni Kima kaini a dubani idan ana dubawa wallahi tallahi banyi kowace irin barnaba nasamu cikin Nan, Wallahi cikin salisu ne...... Wata irin mummunan zabura hajiyar tayi tana kallon Hadiza a gigice sbd mamaki da baqin cikin zancenta Dan ta Gama raina Mata hankali kokuwa dai mahaukaciya ta dauketa? Amma dai Bari ta tabbatar...kallonta tayi a Rikice tace wane salisun Hadiza? Muryarta Bata fita sosai sbd shaqewar maqoshi tace" Salisu baban Abdul.... Kasa magana hajiyar tayi ta rufe idonta daya fara sauyawa sbd tsananin bacin Rai da masifar Rainin da Hadiza tazo dashi Dan haka Bata buqatan ma Jin komai ta nuna Mata hanya tace" Fice Hadiza kibar gabana Dan Allah. Dagowa Hadiza tayi ta kalli hajiyar sai alokacin hawaye suka ciko jajayen idanuwanta suka fara gangarowa. Magana takeson yi Amma zuciyarta tayi nauyi bazata iyaba sai wani irin quntataccen kuka Mai ciwo daya zuwar Mata. Ganin ba tashi zataiba kada wani yashigo yagantama kokuma yaji haukar datake fada yasa hajiyar Kama hannayenta ta miqar tsaye tareda janta takaita har waje ta Kuma gargadeta akan sake zuwa da wata jaririyar gidan da sunan salisu abakinta. Kuka sosai Hadiza keyi tanajin wani irin azababben ciwo a zuciyarta, Jin takeyi kaman zuciyarta zata mutu, Ganin mutanen dake wucewa sunfara Mata kallon mahaukaciya yasata Jan jiki tabar kofar gidan. Tafiya kawai takeyi sbd Batasan Inda zataba, Jin jaririyar tayi baccin wuya itama yasata tsayawa ta goyata taci gaba da tafiya. Tafiya Mai nisa tayi wadda batamasan tayiba har Saida yamma tayi sosai ta nema bakin wani gidan abinci ta zauna tareda sauke jaririyarta ta saka cikin hijabinta tafara Bata nono. Kasa Shan nono 'yar tayi sbd tuni ciwon zazzabin wahala ya rufeta sbd ba qaramar Rana sukashaba. Fara jijjigata tayi tana sake cusa Mata nonon Amma Bata amsaba Dan haka ta maidata ta goya. Shagon dake gefen gidan abincin ta qarasa ta siyo ruwan roba na sauran canjinta dasuka rage Takoma Inda ta baro ta zauna tasake saukoda 'yar ta bude ruwan ta ringa zubawa a murfin robar tana Bata. Ruwan ma batasha saidai wasu sun shiga cikinta kadan... Kuka jaririyar keyi sosai Wanda ya qarasa gigita Hadiza.. Batasan ya zataiba sbd kanta zazzabi da ciwone Mai qarfi a jikinta. Gabanta radadi yake Mata sbd qarin haihuwa da rashin ruwan zafin gasa gurin ga doguwar tafiya cikin azabar Rana Dan haka itama take a gigice. Kukan 'yar yasa Dole tabar gurin ganin hankalin jama'a yafara yawa kanta. Cikin wasu mabarata dake gaba kadan bakin wasu super market taje ta zauna tana sake fama da Yar dake kuka har lokacin. Nanma bata tsiraba sbd anfara Mata kallon zargi da 'yar Silalewa tayi tabar gurin kafin ayi Mata dukan Satan 'ya takama hanya taci gaba da tafiya gashi duhun dare yafara Dan har anfito sallar magriba. Tafiya Mai Dan tsayi takuma Yi taji bazata iyaba sbd radadi da azabar da tsakiyar cinyiyinta ke Mata, Azabar datakeji tafi Mata naqudar haihuwar datayi sbd gurin ya goge sosai sbd tafiya Dan haka tasamu wasu shaguna da Yan gudun hijira suke ta zauna daga can gefe itama. Ruwan robar data siyawa yarta itama taciro daqyar ta iya karban kadan ta shimfida zaninta agurin ta kwanta tana fidda numfashi daqyar jikinta na rawar sanyi. Babu Wanda ya lura da ita sbd suma kowa ta kansa yakeyi Bata wani ba dan kowa agurin abin tausayine. Yarta na dungule cikin jikinta itama tayi bacci. Hadiza Batasan inda kanta yakeba sbd kusan suma tayi saida sanyin asuba da kukan yarta ya dawo da ita Ta bude idanuwanta daqyar tana Neman tashi Amma takasa. Daga kwancen ta sake rungume jaririyarta ta Ciro nono tasaka Mata a Baki. Ana Gama sallar asuba duka mabarata da Yan gudun hijira dake gurin suka fara watsewa sbd baa barin Zama gurin da daddare kawai suke zuwa su kwanta da gari ya waye kowa yatafi gurin bara. Daqyar ta iya daddafawa ta tashi tabar gurin Tafiya kadan tayi tasamu guri ta zauna sbd bazata iyaba. Anan gurin ta Rana ta fito ta sameta Mutanen dake wucewa suka fara Bata sadaka sbd sun dauka Bata takeyi Dayake tana buqatan taimakon ana bata haka ta ringa karba har Allah yasa ta hada 400 ta tashi daqyar ta siya ruwan zafi gurin me shayi ta Sha na hamsin ta siya wasu na hamsin din ta wankewa 'yarta jiki ta gogeta ta maida Mata kayanta da daudarsu da komai. Har yamma tana garari a hanya Dan haka tasake komawa gidansu salisu Hajiyarsa Bata tausayawa mataba tayi Mata korar wulaqanci harda munanan kalamai akan 'yarta Dan haka ta sake komawa Inda ta kwana jiya anan ta Kuma kwanciya. Washe gari ma haka ta sake zuwa gidansu salisu a karon karshe hajiyarsa tayi Mata mummunan gargadin sake zuwa tareda tabbatar Mata da har abada bazasu karbi shegiyar data haifaba amatsayin 'yar salisu. Ranar tayi kukan data jima batasamu tayiba sbd maganganun hajiyar dakuma ciwo Mai tsanani daya sakota gaba da 'yarta. A ranar ko bacci Bata samu tayiba a zaune ta kwana tana kallon yarta wadda da alama sanyi ne yayi mummunan shigarta tana numfashi daqyar. Gabaki daya duniyar tayi mata zafi, Qunci da nauyi takeji a zuciyarta Mai tsananin gaske.. Washe gari da safe data samu qarfin jikinta ta tallaba takai jaririyarta wani qaramin asibiti datagani a hanya. Karon farko ana dubata akace Mata 'yar batada lfy sosai, Zuciyarta Bata bugawa yanda yakamata hakama sanyi na Neman shigarta. Gado aka Bata Amma sbd batada ko kudi suka korota ta fito tana bin hanya Ahankali idanuwanta na tsiyayar hawaye. Yau Bata samu gurin kwanciyaba sbd yan hijirar dasuka qara yawa Dan haka Nesa dasu sosai tasamu ta kwanta. Hankalinta a tashe yake da Inda ta kwanta din sbd itace a nesa qarshe sosai Wasu irin sauro da cinnaku suka ringa cizonta tanaji Amma Bata ko iya motsawa sbd zuciyarta data Gama mutuwa. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/3, 7:34 PM] +234 808 746 2576: *_39_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Koda garin ya waye daga ita har 'yarta  gabaki daya jikinsu kurajen cizan sauro sun bayyana ajikinsu ita hardana cinnaku dasukai Mata kaman Mai wani ciwon take fuskarta ta kumbura. Tashi tayi ta nufi Inda suke gyara jikinsu ta gyara ta fito ta miqa hanya goye da 'yar tata. Kwananta hudu agurin aka rarraba musu kudin sadaka a gurin akan kowa yabar gurin tana karban nata ta tattara tsumman kayanta ta nufi asibiti takai 'yarta data fara nisa. Kwantar dasu akai tareda sakasawa 'yar oxygen Wanda ya cinye kudin nata batareda ansamu na siyan sauran maganiba. Daqyar takai safe cikin tashin hankali Mai tsanani da qaqa nikayi sbd jikin 'yar jaririyarta daya sake gabaki daya. Rashin Imani da rashin tausayin asibitin haka suka sallameta sbd rashin magani da rashin kudin siyansa ta rungumo 'yarta ta fito tana hada hanya. Yau kam komai yasake yimata tsananin da takejin mutuwa take buqata Ido rufe. Uwarta da ubanta da salisu takeson bi Ido rufe sbd ta huta da qunci da baqin cikin duniyar datake ciki. Kuka aranar tayisa har idanuwanta basa gani sosai sbd kumbura. Tahau titi rungume da 'yarta wadda take tsoron dubawa ko ta mutu ko tanada sauran Rai. Mutuwa take Kira take Kuma fata sbd Babu Inda takejin sassauci a wannan rayuwar. Wani azababben ciwon gaba take fama dashi da ciwo ciki Mai tsanani, Ta bangare daya qwaqwalwarta tafara kasa daukan tashin hankalin da masifar datake ciki Dan haka wunin ranar attempting kashe kanta kawai takeyi Amma tsananin qaunar datakewa yarta Yana hanata idan ta kalleta. Tamkar mahaukaciya tafara komawa sbd taba qwaqwalwarta da abin yafara Musamman mummunan infection din daya shigeta sosai sbd rashin kulawa da gurinda ta Haihu. Tun tana iya controlling kanta akan yanayinta dayake son juyar da qwaqwalwarta haryazo tafara tsoraran yanayinda jaririyarta da itama kusan Rai ne kawai ya rage Mata Zata shiga idan wani Abu ya sameta. wani masallaci takai 'yar ta ajiye Zata gudu tabarta ko zaa samu Wanda zai tallafeta Amma saita kasa barinta agurin tadauketa tana hawaye tana jujjuyar dakai tabi hanya tana surautai ita kadai. Batasan ya akaiba sai gata kwatsam takai kanta hanyar Tasha tana tafiya. Kaduna ne? Ina zuwa ne? Kano ne? Katsina ne? A kunnuwanta kalmomin ke sauka suna sake yamutsa qwaqwalwarta... Jikinta rawa yakeyi sosai kanta na sake juyawa sosai. Ahankali sama sama takejin cikin nutsuwa wani yayi magana a bayanta. Assalam alaikum, Malama Zan wuce ko Zaki Dan matsa. Waiwayowa tayi da sauri a firgice  tareda kallon Mai maganar. Saurayine matashi Wanda zatai qani dashi bamai tazaraba sosai. Sanye yake cikin qananun Kaya Riga ash da wandon jeans black. Cikin sauri Dan tashar masu mota ya qaraso Yana daka Mata tsawa da cewa" Dalla matsa ki wuce daga Nan Kinzo kintare hanya Idan bara zakiyi ki matsa can. Yallabai Kace gombe Abuja ne ko? Kallonsa matashin yayi kafin ya kalli Hadiza data Matsa gefe ta rabe rungume da abinda yake sakaran 'da ne sbd yanda ta rungume zanin cikeda so da shauqi. Hannu ya saka aljihunsa ya Ciro Dubu daya ya miqa Mata cikeda kulawa batareda yace komaiba. Hannu ta miqa a hankali ta karba tareda kafesa da Ido tana zuba godiya Kuma takasa tafiya. Cikin qaguwa ya kalli masu lodin motar yace" Saura mutum nawane motar tacika hanyar kunsanfa bawani kyaune da itaba. Yallabai Saura mutum uku motar tacika. Muje zan biya kudin sauran gurin. Angama ranka yallabai. Hadiza dake rakube tanajin haka sai kawai tasamu kanta da biyo bayansa tafara kokarin Shiga motar sbd Jin zaa biya koba komai gwara tashiga duniyar tunda hakane qaddararta. Kokarin hanata shiga motar direba yafara yana cewa" Ke tsaya, tsaya Ina zaki? Wane gari Zaki? Abuja" ta furta Kai tsaye muryarta na 'dan rawa. Ina kudinki na mota? Waiwayowa tayi ta kalli gefenda matashin yake zaune cikin nutsuwa Yana duba wayar hannunsa. Ganin tana kallonsa ya fahimci batada kudin motar Dan haka yacewa drivern tahau gurin mutum daya cikin kudin mutum biyu daya biya. Kasa kallonsa tayi bare tasake Masa godia saima sauke kanta datayi qasa tana sake rungume jaririyarta. Hanya aka dauka aka fara tafiya Mai nisa kowa yayi tsit a motar Yana aikin gabansa masu bacci Kuma nayi. Ahankali ahankali idanuwan Hadiza suke cikowa da hawaye tanajin wani irin masifaffen ciwon Kai da zabar ciwon ciki. 'yarta take ji, Ita take tausayi ba kantaba, Jin kanta na neman juyewa yasa tafara jin kaman tace a tsaya ta sauka. Yanayin yanda take sake qanqame babynta yasashi Dan dagowa ya kalleta dakyau yaga tarin tashin hankalin dayake ciki kafin ya maida kallonsa kan babyn cikeda kulawa yace" Ki Dan sassauta riqon Kina matse babyn sosai Inaga. Da sauri kaman qaramar yarinya tayi saurin sassauta riqon tareda bube jaririyar gabaki daya Dan Tasha iska. Wani irin mamaki da firgici ne ya kamasa ganin babyn wadda alamun rashin lafiya sosai da yin nisa ya bayyana atareda da ita, Gabaki daya babyn yunwa tagama kamata tako ina. Dauke kansa yayi daga kallon jaririyar sbd zuciyarsa bazata iya jurewa kallontaba. Tafiya suka cigaba dayi mai nisa da gudu.. Guri biyu aka tsaya siyan abinci Kuma ya siya Mata yabata sbd lurada akwai yunwa tareda ita. Duk abinda ya siya Mata ya bata bataciba suna jikinta dunqule sbd bazata iya ciba ita kadai tasan tsananin halin azabar datake ciki. Daga Nan Basu sake tsayawaba a hanya suka cigaba da zuba gudu a hanya. Qarfe Tara da mintuna arbain da takwas suka isa birnin tarayya. Kowa fitowa yayi daga motar yana haramar daukan kayansa ya wuce. Daga shi sai jakarsa dake rataye a kafadarsa ya fito Yana sake saka Kiran Wanda aka aiko daukansa daga gida. Ahankali Hadiza ta tako gefensa ta kallesa qafafuwanta na 'dan yin rawa. Tsalle zuciyarta keyi ga abinda zuciyar tata ke ingizata ga aikatawa. Jin takeyi zuciyarta ta kwanta data barmasa 'yarta ta gudu sbd yanada tausayi da Jin qai Dan kuwa ita batada tabbacin zatakai labari ayanda takejin azaba da radadi cikin jikinta. Bazataso wani Abu ya sametaba 'yarta ta gararanta... Jin mutum kusa dashi yashi juyowa da Dan sauri sbd ya Dan firgita. Kallonta yakeyi da mamaki sosai batareda yace Mata komaiba. Ganin kallon dayake Mata yasata kallon 'yarta cikin kokarin daidaita kanta tace" Nagode sosai Allah yasaka maka da Alkhairi. Amin" kawai ya iya furtawa Kai tsaye Yana cigaba da wayarsa. Yana aje wayar drivern ya tura aljihun jeans dinsa drivern gidansu yace Saura kadan ya iso. Jakarsa ya juyo zai dauka daga qasa gefensa idanuwansa suka sauka kan zani kan jakar tasa. Da sauri ya waiwaya Babu kowa gefensa da bayansa. Sake jujjuyawa yayi Yana Raba idon matar data bar Masa zanin. Jakar ya riqe zai dauka ya watsar da zanin agurin sai zuciyarsa ta kasa Dan haka yakai hannu kawai zai janye zanin yaji alamun Abu aciki Batareda ya taba tunanin ganin komaiba bare 'dan mutum ya bude zanin aikuwa yayi Ido biyu da babyn. Zaro Ido yayi da sauri tareda mayarda zanin ya rufe babyn zuciyarsa na rawa. Da sauri tafara waigawa koina Yana zazzare idon Neman Hadiza. Daukan babyn yayi dan Dole ya rungume Yana sake jujjuyawa Neman Hadiza. Fara tashi hankalinsa yayi dayaga dagaske yakasa ganin uwar babyn. Kokarin komawa yakeyi gurin motar dasuka iso sai kawai ya hangota tana sauri zatabar tashar tana zazzare idon kada ya ganta. Da sauri ya bita tana ganinsa ta sake sauri ba Shiri ta tare Mai mashin ta haye suka bar gurin da sauri. Tashin hankali da tsananin mamakine da firgici yasashi Neman wani mashin din ya hau Amma tuni Hadiza da me mashin dinta suka bace Masa. Me wannan matar tayi ne? Me take nufi? Da gangan tana sane ta bar Masa babyn ta gudu fa. Innalillahi wainna ilaihrrjiun.. Meyasa zatayi haka? Dama mahaukaciyace Basu luraba? Meyesa Zata gudu tabar Masa baby ? Ina zai Kai babyn to? Yawo ya ringa Yi dame mashin hankaki tashe Amma sun kasa ganin hadiza ko Mai Kama da ita. Dukkanin qwaqwalwarsa tsayawa tayi cak shima Ya tsaya rungume da baby ajikinsa Yana Jin jiri na Neman zubar dashi, Ya zaiyi da wannan babyn? Bazai iya komawa tashaba sbd baisan wazai bawa babynba, Baimasan wazai fara tunkaraba a tasha da babyn sbd Babu ruwan kowa babuma Kuma Wanda zai karba. Innalillahi wainna ilayhirrajiun" yafara maimaitawa dukkanin jikinsa na saki. Mai mashin ya fadawa Inda zai kaishi Wata qaramar police station yaje da babyn suka qi karba sukace yace babban station kawai. Wata station din yakuma zuwa sukuma sukaqi karban 'yar suna zargin kodai yarda Yar kawai yakeson Yi. Wata sabuwar masifar yakuma Shiga lokacinda yagama yawo da babyn Babu wata mafita ko daya. Yanayin babyn kawai ya tabbatar masa da babyn sosai tayi nisa batada lafiya Dan haka ya tattara a nufi wani private asibiti yakaita su duba. Suna karbanta take sukai dakin jarirai da ita. Fada suka fara yimasa sosai ganin yanayin datake ciki. Duk abubuwan zasuyi Mata sunyi suka sakata a kwalba sbd ma sai allah Kam idan Zata rayu. Tashin hankali sabo yakuma Shiga lokacinda suka zayyano Masa cututtukan dasuke cin babyn. Biyan komai yayi kafin ya samu ya wuce gida yabar babyn anan sbd akwai masu kula da babies a dakinsu. Koda ya Isa gidansu mahaifiyarsa na ganinsa cikin tashin hankalin rashin daukan wayarsa da rashin ganinsa da driver yayi har kusan qarfe daya da rabi na daren yayi. ABDULMAJEED..Ina ka shiga daga isowarka? Lafiya kuwa? Ajiyar zuciya ya sauke ahankali idanuwansa na qanqancewa da tashin hankali da damuwa yace" Hajiya umma kaina kaman zai fashe Zanshiga nayi sallah tukuna. Cikeda kulawa tace" Jeka kayi wanka da sallar ka huta da safe mayi magana. Juyawa yayi Yana hada hanya ya nufi hanyar dakinsa Yana jin kansa na sake tsananta ciwo. Zubewa yayi qasa tsakiyar dakin Yana dafe kansa, Daqyar ya tashi ya qarasa isa ya tube kayansa ya shafa toilet. Wanka yayi ko zai samu kansa ya Dan sake tareda alwala yafito. Jallabiya da gajeran wando kawai yasake yayi sallah ya miqe a daddafa ya Isa kan gadonsa ya hau ya kwanta tareda rufe fararen idanuwansa dasuka qanqance sbd tashin hankali da damuwa. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/4, 11:05 AM] +234 813 979 4675: *_40_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Babban tashin hankalinsa shine a yanayinda babyn Nan take ciki bazai iya bada ita ga Yan sandaba kokuma gidan marayu sbd tana cikin mawuyacin hali, Haka Kuma mahaifiyarsa a yanda ya santa mace ce Mai tsananin kishin 'yayanta Musamman shi ta tsani wani ya rabesa Dan haka yasan bazata taba yarda da abar babynba hannunsu harta danyi wayo tukuna akaita gidan marayun Idanma baa ga uwar babynba kenan Dan zuciyarsa takasa yarda da uwa Zata iya jefar da 'danta ta gudu duk tsananun rayuwa kuwa.. Washe gari tun kafin kowa ya tashi daga masallaci sallar asuba ya fice zuwa asibiti da mota Yana Jin rashin nutsuwa matuqar ba zuwa yayi yasan halinda babyn ke cikiba. Banyi baccin nutsuwaba sbd Jin yake babyn mutuwa zatayi a halinda dai yabarta. Tunaninsa gabaki daya ya karkata akan uwarta ta gudu ne tabar 'yar sbd rashin lafiyar babyn da bazata iya daukaba wannda hakan zallar rashin imani da tausayine. Koda ya Isa asibitin babyn ba laifi tarta fara daidaituwa sbd Madara da aka kwana ana bata duk Bayan mintuna sbd yunwace da tsananin wahala da sanyi suka Kama babyn sosai. Fes aka shiryata cikin kayan sanyi masu tsananin taushi farare tas daya siya tun jiya a asibitin aka shiryata. Har Inda babyn take aka Isa dashi tareda kallonsa likita yace" Ina uwar babyn take ne? Tayi sakaci da ganganci sosai akan wannan babyn gskia. Wani irin sanyi yaji zuciyarsa tayi batareda ya dauke idonsa daga kan babynba dake bacci idanuwanta a rufe murya a sanyaye yace" Batada uwa. Dakatawa daga rubutu a file Dr yayi yana dagowa dukkaninsa ya kalli ABDULMAJEED din da mamaki yace" Ka kuwa gane abinda na tambaya? Mahaifiyarta nake nufi, Wadda ta haifeta. Wani daci yaji yakuma cika ransa ambatar sunan uwar babyn... Yana kallonta tana kallonsa da 'yarta a hannu tahau mashin ta gudu tabarsa da 'ya jaririya Yana yawo tsakar dare nemanta. Mezaice gameda wannan uwar? Mezai fadawa kowa gameda uwa irin wannan aduk Inda ze Kai babyn yasan bazaa taba kaunarta ko kulawa da itaba Kamar uwarta Koda kuwa a halin talauci da qunci ne. Numfashi ya sauke a boye tareda dagowa ya kalli likitan Kai tsaye yace" Mahaifiyarta ta rasu. Numfashi Dr ya sauke tareda tausayawa babyn Saikuma ya dago ya kalli ABDULMAJEED din dakyau Dan haihuwa Kam ya Isa ya Haihu tunda matashine Amma Kuma yanayin wayewa da hutun daya gani tattareda dashi yasan zaiyi wuya ace yayi saurin aure bare harda haihuwa A qiyasa bazai wuce 300level hakaba zuwa 400 a karatun jami'a. Duk tunanin dr iya lissafinsane kawai Dan haka kai tsaye yace" But you are the Father right?? Yes" kawai yace Masa Dan bayason tambayar. Sauran abubuwan da baayi bane jiyan aka qarasa yi qarshe dai bai baro asibitin ba sai qarfe goma Sha daya sbd babyn Kam Saida aka hada da Oxygen. Daga asibiti report yaje yasaka na Neman uwar babyn Wanda yasan zaiyi wuya a sameta tunda tana sane ta gudu ba wai batane babyn tayiba. Koda ya dawo gida hankalin hajiya umma yagama tashi hakama duk Inda ranta yake yagama Kai qololuwa gurin baci. Musamman su Anty juwairiyyah dasuka Gama qara hawar da ita akan zancen ABDULMAJEED yafi daukan mutanen waje da mahimmanci akanta. Hajiya umma wadda asalin sunanta yake AYSHATOUH mahaifiyace ga ABDULMAJEED da yayunsa Mata guda biyu. Anty juwairiyyah itace Babba sai Anty safiyyah saikuma shi ABDULMAJEED daya kasance qarami Kuma auta. Son da mahaifinsu da hajiya umma kewa ABDULMAJEED sosai ya zarta abinda Yan uwansa zasu iya dauka sbd bambamci ne afili. Mahaifinsu justice Abdullahi Isah babban former justice ne a high Court dake Abuja, Yayi retire tareda barin qasar yakoma South Africa tsawon shekaru kafin yadawo Nigeria sbd ABDULMAJEED dake shaawar karatu da rayuwarsa a Nigeria. Dagowarsu da qanqanin lokaci akai auren juwairiyyah da wani babban barrister anan Abuja haihuwarta daya auren ya mutu tadawo gida itakuma anty safiyyah dama Bata samu mijinba aikinta kawai takeyi Dan itama aikin mahaifinsu tabi lawyer ce. Anty juwairiyyah da Anty safiyyah tun ABDULMAJEED dasu suna qanana Allah ya sanya musu kishinsa Mai tsanani Wanda ta wani fannin yake surkuwa da baqin ciki sbd fifici da banbancin da iyayensu suke nuna musu sosai akansa Musamman hajiya umma. Abbansu Yana iya kokarinsa gurin yimusu adalci da Basu iya tasu kulawa da kaunar Amma Kuma ko yayane baya iya boye fificin kaunar ABDULMAJEED. Ita hajiya umma nata shine yafi tabasu sosai sbd Babu tunanin illar hakan take nuna nata fificin. Sunkoma tamkar wasu 'yayan riqo a hannun iyayensu sbd ABDULMAJEED Wanda hakan ya Gina rashin kauna tsakaninsu da 'dan uwansu. Bayan rasuwar abbansu Haj umma sosai ta sake qwallafa ranta akan majeed Bataji Bata ganin kowa sai shi, Su Anty juwairiyyah dasuka fara nuna rashin Jin dadinsu a fili sai kawai ta tsana zamansu a gida kullum cikin musu fadan rashin fidda mijin aure takeyi sun fara tsufa a gida. Wannan kalaman nata ya tsananta duk wata tsanar dasukaiwa Dan uwansu sunajin kamar shine duk wata matsakarsu da baqin cikinsu na rayuwa. Haj umma tsananin kaunar datakewa 'danta yasa ta kasance cikin irin iyayen dake tsananin kishin 'yayansu Kishi Mai tsanani, Sam batason kowa ya rabi 'danta tafison kulawarsa da komai akanta ita kadai, Shikuma Allah yayisa Mai tausayi da taimako tareda mutunta mutane Musamman marasa qarfi kusan sune mutanensa Dan yafison yayi mu'amala da wainda zasu ringa qaruwa dashi suna samun taimakonsa dan kawar da tasu matsalar. Mahaifiyarsa kuma hakan ne yasata ta tsani duk wasu marasa karfin dake taredashi sbd ganin sunason samun kusanci dashi, Ba abinda yake Basu bane baqin cikinta Dan idan duka zai Basu dukiya batada damuwa ita damuwarta kada kowa ya samu kusanci da 'danta Bayan ita. A American University of Nigeria yake karatunsa badan Haj umma tasoba tabarsa yake karatu a wani garinba sai Dan hakan mahaifinsa yaso, Burin mahaifinsane ganin yayi karatunda zai mallaki komai nasa ya Gina kansa da kansa. Fara karatunsa da yanda yake Dan jimawa baya gida yasa su Anty juwairiyyah suka fara samun shiga gurin Haj umma har suka fara kawo sabani tsakaninta da ABDULMAJEED ta hanyar saka Mata zargi Mai girma akan yafara 'yan Mata hankinsa akansu yake Nan gaba ma mace Zata Raba tsakaninta da 'danta. Hankalin Haj umma tashi yayi sosai sbd yanda idonta ya rufe akan kaunar da kishin danta yasa komai aka fada Mata yarda takeyi Musamman da ABDULMAJEED din yayi budurwa kullum cikin kiransa take Dan tun Kiran Sumayya din na damunsa harya daina damunsa Dole ya saba. Soyayyar MAJEED da sumayya ta daga hankalin Haj umma sbd sosai yanzu ta tabbarda mace Zata rabata da Dan ta Dan haka ta rufe Ido tamasa kaca kaca da fada takuma hanasa kula Mata saiya kammala karatun ita Zata Nemo masa matanda zai aura. Ganin yanda ranta ya baci sosai yasa MAJEED din takaita muamalarsa da sumayya kwata kwata baisake bi takanta. Amma duk da hakan shikenan Haj umma taringa saka Masa Ido takasa yarda dashi. Wannan yakawo babban gibin dayasa su Anty juwairiyyah qarasa saka zargi da rashin sukuni a tsaninin Haj umma da majeed kusan yanzu kullum cikin fitinarta da fadanta yake akan Yana hulda da 'yan Mata shiyasa yake jimawa a makaranta kafin yadawo hutu gida. Wannan ne babban matsalar data fara kunno Kai a tsakaninsa da mahaifiyarsa wadda kwata kwata Bata yarda dashi sosai yanzu. Su Anty juwairiyyah kuwa yanzu zancensune abin yardarta Duk abinda suka fada mata hawa takeyi ta zauna daram tayita fada Abbansu baya raye bare ya ganarda ita gaskiyar rashin kyautawa da tunani akan abinda takeyi. *******Shigowarsa gidan Kai tsaye Palo yashigo lokacin daga hajiyar sai Anty juwairiyyah da rumanah 'yar anty juwairiyyah suna zaune palon anty juwairiyyah na bubbude kayanta dasuka iso daga Dubai yau na tsadaddun laces da abayas datake saidawa sosai. Ko kallonsa hajiya bataiba lokacinda ya zauna kusada ita Yana riqo hannunta cikeda kulawa yace" Umma... Zare hannunta tayi tana juyowa ta kallesa fuska ba walwala tace" Meya hadaka da asibiti kake warin asibitin? Tun asuba fa akace ka fita¿ Ina kaje? Ajiyar zuciya yayi cikin Hana kansa Jin rashin Jin dadin zancenta sbd takasa daina saka Masa dokar duk Ina yaje da Inda zashi saiya fada Mata bayan Shiba yaro bane da girmansa take Masa irin hakan, Amma Kuma uwace Babu yanda zaiyi da ita bakuma zai iyajin haushintaba sbd yanda take kaunarsa haka yake tsananin kaunarta shima Dan tafiye Masa komai a rayuwarsa. Ahankali ya bude Baki zai fada Mata abinda yake faruwa saiya dakata sbd tabbas yasan atake zatace Bata yafe yakoma gurin babynba yabarta can asibitin Susan yanda zasuyi da ita. Ajiyar zuciya yayi tareda sakin murmushin boye damuwarsa yace" Dubiya naje wani asibiti a kubwa. Kasa yarda hajiyan tayi tana kallon fuskarsa dake kokarin Tona asirinsa sbd Bai iya qaryaba baikuma taba yintabama. Miqewa yayi ya wuce dakinsa yayi wanka ya shirya yakuma sulalewa ya fice gidan batareda sun saniba. Har dare Bai dawoba sai guraren 10 yadawo ya shige ya kwanta. Washe garima daqyar ya iya tsayawa yasha ruwan tea kawai ya Kuma ficewa zuwa asibiti. Kwana biyu kowa gidan ya saka Masa Ido ganin duk yabi ya rikice baya wani cikin nutsuwa gashi sai boye boye yakeyi sbd harga Allah bazai iya barin babynba shima hakama mahaifiyarsa yasan bazata taba Bari su dauki 'yar ba Dan haka hankalinsa ya tashi sosai, Yayi yawon bincike akan gidan marayu Amma Babu Inda yaji bayanin daya kwantar Masa da hankali Dan haka yasake shiga tsaka Mai wuya. Ta Bangare Daya ya rikice ya haukace gurin Neman uwar babyn harya gaji Babu labari, Komai yafara tsananta lalace Masa ne bayanda anty safiyyah ta ringa bin diddiqinsa tagano asibitin dayake zuwa kullum harma da babyn dayake jinya mai amfani da sunansa ABDULMAJEEDs. Hankali tashe cikeda firgici da mamaki takawo labarin gida Inda suka dunguma sukaje suka ganarwa idonsu Kuma suka tabbatarda babyn dai ta ABDULMAJEED dince ta hanyar bayaninda nurse Tai musu shine mahaifin babyn. Uwar babyn suka tambaya tace musu ta rasu gun haihuwa. Dayake suma asibitin sun dade dafara gulmarsa akan kila baasan ya haifi yarinyarba shiyasa yakasa kawo 'yan uwansa su tayasa hidimar babyn. Gida suka koma hankali tashe suka zayyanewa hajiya komai. Kasa yarda tayi da Abdul dinta zaiyi abinda suke fada kula Mata da aikata Zina harma da haihuwar 'yar gaban fatiha. Sunsan zaayi hakan Dan haka suka dauketa suka kwasa zuwa asibitin Cikin saa kuwa suna zuwa suka taddasa rungumeda babyn an jikinsa cikin tsananin kulawa. Sallamarsu ake tunanin Yi zuwa gobe dan haka yake Jin sanyi ta wani bangaren Kuma tashin hankalin yanda zaiyi da babyn. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/4, 11:05 AM] +234 813 979 4675: *_41_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ahankali Haj umma ta qaraso tana kallon babyn hannunsa a Rikice tace" MAJEED babyn waye wannan? Da sauri ya dago Yana kallonta dasu anty juwairiyyah. Miqawa nurse babyn yayi yana kallon hajiyan yace" Umma muje gida Zan Miki bayani. Kasa motsawa tayi sbd fargaba da tsoro tace" Majeed bazan koma gidaba wlh saikamun bayanin Inda kasamo wannan babyn. Mezan gani majeed? Mezan ji? Ta tabbata kenan fasiki ka Zama har kayi nisa haka¿ Innalillahi wainnan ilaihrrjiun" zuciyarsa dake rawa tafara karantowa. Cikin dacin kalaman mahaifiyar tasa ya dago ya kalleta Jin sunan fasiqi data kirasa dashi. Zuciyarsa na daci ya bude Baki zaiyi magana anty juwairiyyah ta taresa da munanan kalamai tareda kiransa da sunayen mazinatai kala kala. Kasa dago kansa yayi cikin tsananin tashin hankali da baqin ciki ya dakatar da Anty juwairiyyah da cewa" Anty juwairiyyah me kika fada? Sunayen mazinata fasikai kike kirana, Idanma nine mahaifin babyn akwai yanda zakuyi ne da qaddarar Allah?... Ba zato sukaji qarar saukan Marin da hajiya tayi sakar Masa tana kallonsa ciki tsananin bacin Rai da baqin ciki tace" Wallahi wannan 'yar bazamu taba karbantaba idanma Kaine ubanta, Idan Kuma wani gurin kasamota kayi gaggawar maida ita.. Kai koma Kaine ka haifeta bazaka karbetaba wuce muje gida. Jajir idanuwansa sukayi sbd baqin ciki da damuwa, Su Anty safiyyah kuwa ta Inda suke shiga bayanan suke fitaba take hankalin hajiya yaqarasa tashi hawan jinin datake fama dashi yayi sama take Ba Shiri suka Jata zuwa gida har ABDULMAJEED din Wanda jikinsa yayi dukkanin sanyi. Isarsu gida Bai qarar da komaiba sai sabon tashin hankali Dan kuwa bayanai ne daga Yan sanda sukazo anga Hadiza Kuma ta tabbatar musu da 'ya 'yarsace. Kasa yarda da zancensu yayi saida aka kawo Hadiza wadda gabaki dayanta batada bambamci da mahaukaciya sbd yanayin shigarta da rashin lafiyarta. Saida aka fara tambayarsa ya tabbatar musu da itace mahaifiyar babyn kafin aka sake tambayarta itama tace babynsa ce. Ganin yanayinta na tabin hankali yasa aka sallameta ta tafiyarta dayake yan sandan sunga gurin samun kudi sai suka Kama MAJEED din akan yayiwa mahaukaciya fyade ta Haihu. Take Yan sanda suka sauya zancen Kuma suka tabbatarda Hadiza ta tafiyarta sbd karma aci gaba da tambayarta tadawo daidai tafada wani zancen Bayan wannan. Babban tashin hankali yashiga Yana son mahaifiyarsa kadai ta yarda dashi ta fahimcesa Amma tuni taji tana danasanin fifita sonsa akan sauran 'yayanta. Kasa danne abinda takeji tayi zuciyarta take tafara Neman bugawa aka kwasheta zuwa asibiti. Acan station kuwa ba Imani yan sandan suka rufesa tareda cike Masa laifin dabai aikataba. Zafi zuciyarsa da kansa sukeyi kaman zasu fashe, Wace irin masifaffiyar qaddara ce wannan? Tayaya mahaifiyarsa da 'yan uwansa zasu yarda da zai iya Koda kallon wannan matar so ukuma bare iya wani abun da ita sbd tsananin qyanqyamin dayake dashi. Bai taba kukaba tun girmansa Amma ayau baisan lokacinda wasu hawayen baqin ciki da qunci suka gangaro masaba. A rufe ya kwana Saida yakuma wuni a rufen kafin alhj jamilu qanin Haj umma yazo yayi belinsa shima ransa amatuqar bace da abinda MAJEED din yayi. Ko sauraronsa baiyiba yayi Masa diban albarka da maganganun dasuke kaman Yana Masa Baki. A gidan ma saida ya zubda hawaye ga maganganu marasa Dadi da 'yan uwansa suka ringa jifansa dasu Mahaifiyar tasa kuwa ko qaunar ganin batayi hakan ta ringa hawaye tana jujjuyar dakai batason ganinsa yatafi yabarta kawai. Nauyi zuciyarsa tayi ta yanda baisan mezaiyiba, Mahaifiyarsa ta tsanesa Bata son ko ganin inuwarsa, Yan uwansa ma sun tsanesa, Yan uwan mahaifinsa Dana mahaifiyarsa sai Allah wadai sukeyi dashi. Kiransa akai daga asibiti akan yazo ya tafi da babysa. Baida wani zabi bayan zuwa ya karbota sbd bazai iya barinta acanba ayanzu da kowa yagama alaqanta shine mahaifinta. Koda ya karbota ya dade Yana tunanin Inda zai kaita sbd dagashi har ita bazasu taba karbuwa ba a gidansu. Hakanan ya daure ya iso gidan da ita saidai tun kafin ya shiga ainihin gidan su Anty safiyyah suka tabbatar Masa bazai zauna da 'yar ba a gidan. Zabi zaka dauka ko ka kaita gidan marayu kokuma kasan Inda zakaje ka raineta Dan bazai taba yiyuba ayi renon 'yar qaddaraba a gaban hajiya sbd baka damu da damuwa ko baqin cikinka ya kasheta. Bai tsaya ya sauraresuba ya wuce ciki da 'yar a hannunsa rungume ya nufi dakinsa. Cikin fada sosai da tsawa anty juwairiyyah tace" Bakaji abinda safiyyah ta fada bane? Ina zaka wuce ana magana? Ka fice kakoma tun dare baimaba kakaita gidan marayu idanma bazasu karbaba ka maidawa mahaukaciyar uwarta idan taga dama ta Yar da ita... Tsananin zafi da quncin da zuciyarsa me Masa yasa tafara bushewa a fusace yace" Duk abinda zanyi da ita da Inda Zan kaita ba ruwan kowa bane matsalata ne tunda nine nakawota.. Idan sbd wannan 'yar alhakin aketa tada hankali to naji nine ubanta zai raineta daga Nan har girmanta Kuma Babu Wanda ya Isa ya hana hakan..... Nima ban isaba Amma Kuma na Isa danace kabar gidan Nan da ita tunda gidan bana uban nata bane. Kai yanzu MAJEED har kayi nisan da yannanka suna magana kana mayar masu Kai me 'ya? To wlh wallhi wannan 'yar dai bazata zauna a gidan banba, Banason ganinku daga Kai har ita ka tattara ku koma gidan marayun har Kai sbd kaima kazama marayan daga yau... A Rikice ya kalli hajiyar idanuwansa na sauyawa Muryarsa na rawa yace" umma nabar gida????? Ban Isa bane? Ai kakai tunda kazama uba yanzu. Innalillahi wainna ilaihrrjiun"" Umma........ Daga Masa hannuwa tayi tareda fashewa da kuka Mai ciwo da qunan zuciya tace" Idan Ina ganinka zuciyata bugawa zatayi MAJEED Dan Allah ka tafi na daina ganinka da 'yar nan. Kaci amanar tarbiya da tsananin kaunar dana fifitaka akan 'yan uwankw.. Maganganunta dukan zuciyarsa sukeyi suna yamutsa qwaqwalwarsa tareda zafafa kansa. Daqyar ya daga qafafunsa zai matso gabanta ta Kuma fasa kuka tana ja da Baya. Wani nauyi ne ya danne Masa zuciya ya juya ahankali ya shiga dakinsa ya tattaro kayan dazai buqata ya zubo a jaka ya fito. Su Anty safiyyah na kallonsa da mamaki sosai ya fice gidan batareda yasake cewa komaiba. Yana fita kuwa hajiya jikinta ya rikice Nan tafara numfashi daqyar Hankali tashe aka kwasheta zuwa asibiti. Baitaba sanin haka 'dacin baqin ciki yakeba sai yanzu, Zafi,ciwo,radadi,nauyi da tiriri zuciyarsa keyi duk lokaci daya, Gidan Alhaji jamilu ya nufa Amma cin zarafin dayayi Masa yafi Wanda akayo Masa daga gida Dan haka yana baro gidansa Kai tsaye hotel yanufa yakamata daki ya kwantar da babyn tareda komawa gefe ya zube Yana riqe kansa dake neman tarwatsewa. Babban qunci da dacin zuciyarsa yanda mahaifiyarsa da Yan uwansa dasuke jininsa suka zabi aibatasa da kalmomi mafi muni tareda tsanarsa.. Shin idan da gaske shine qaddarar haihuwar babyn ta sama haka zasu gujesa kenan? Me yayiwa wannan baiwar Allah dazata ruguza rayuwarsa haka? Kansa dake Neman bugawa ya juyo ya kalli babyn dake bacci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.. Wani irin tausayinta yaji tareda qaunarta, Me tayiwa mahaifiyarta dazata jefar da ita haka ga mutuminda batasaniba, Batasan halayyarsaba, Shin idan ga wani mugun mutum ne ta jefarda 'yar Yaya takeson rayuwar wannan 'yar alhakin tayi. Kansa da kirjinsa sun toshe baida tunani komai. Alwala yayo yafito yayi sallar magriba da aka Kira. Yana idarwa babyn ta farka ya taso ahankali ya tsaya akanta Yana kallon yanda take motsawa ahankali tana fidda harshe alaman yunwa. Numfashi ya sauke a sanyaye kafin ya juya gurin jakar kayan madaranta da nurse ta koya Masa yanda zai hada. A sanyaye ya hada mata madaran da ruwan roba kafin ya debo ruwan dumi ya saka madaran yayi dumi. Ajewa yayi gefe kafin ya dauki babyn yafara Bata ta karba take tana zuqa ahankali. Qura Mata fararen idanuwansa dasuka sauya yayi Yana Jin tausayin kansa da ita, Meyasa iyayensu zasu zabi jefar dasu akan qaddara? Meyasa iyayensu suka zabi rabuwa dasu akan abinda suma basune suka samarwa kansuba? Uwa mace da akafi sani da qawa zucin 'danta Amma su nasu uwayen Mata ne suka fincikesu daga rayuwarsu suka 'yar batareda nazari ko tunanin halinda zasu shigaba. Shi tasa uwar data fincikesa daga rayuwarsu ta Yar yanada girman dazai kula da kansa Amma ita wannan babyn me tasani. Har tagama shan madaran tayi bacci bai saniba sbd nisan dayayi a tunani. Har lokacin sallar ishai tayi Yana zaune rungume da babyn. Sallar ishai yayi wadda Yana idarwa ya nema guri yazauna tareda rufe idanuwansa yanajin yanda kansa ke tsananin ciwo. Babban saukin daya samu babyn bamai rigima bace Dan haka har safe batai Masa rigima ba sai Madara datakesha sosai Dan haka baiyi wani baccin safeba. Garin na wayewa guraren qarfe goma Dole cikin ma'aikatan hotel din yasamu wata ta sauya Masa kayan babyn ta shirya Masa ita ya dauketa suka sake koma gidansu. Wannan karon Yana Isa babban tsaro yasamu a gate akan kada abarsa ya Shiga gidan. Kiran wayar hajiyar ya ringa Yi Amma Sam Bata dauka daga karshe aka kashe. Numbern anty juwairiyyah yafara kira itama bata dauka. Ta anty safiyyah yakoma Kira itama Bata dauka. Anan ya kusan wuni da babyn cikin Rana ganin Zata wahala yasa yakoma hotel din. Washe gari haka yakoma gidan Amma saiya samu labarin sun wuce Lagos gabaki dayansu gurin ganin likitan hajiya. Tashi hankalinsa yayi Dan haka ya ringa Kiran wayar hajiyar Bata Shiga qarshe ya Kira anty juwairiyyah. Kalaman data fada masa sune yaka saddaqar da duk wani sauran burinsa na zama cikin Yan uwansa da mahaifiyarsa. Ta sanar dashi hajiya umma Bata kaunar jinsa ko ganinsa, Idan yakuma zuwa ko kiranta Zata iya tsine Masa. Wainnan kalaman sun girgiza duk wata jarumtarsa da karfin zuciyarsa, Amma Kuma sun daskarar da zuciyarsa data tarwatse lokaci daya, Tabbas zaiyi nesa da Inda Haj umma Zata gansa bare yazama sanadin mutuwarta da 'yan uwansa suke fada. Yana barin gidan yakoma hotel ya tattara kayansa guri daya, Yayi wani irin kukan baqin ciki da maraicin rashin mahaifi a duniya, Yayi kukan rabuwa da uwa wadda yasan itama tana cikin quncin wannan hukuncin nata saidai Kuma bazai taba Zama sanadin ciwonta ba dakuma tsinuwar data ambata garesa. gari na wayewa ya nufi Tasha yahau motar komawa Yola. A motar tun agurin Lodi ya sanar masu mahaifiyar 'yarsa ta rasune zai koma gida gurin danginsa. Da wannan ya kawarda kallon zargin da ake binsa dashi fa babyn. Wasu sun yarda wasu Basu yardaba ahaka dai akai tafiyar Amma saida wata dattijuwa ta karban Masa babyn sbd ganin yanda yake fama da babyn. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/4, 11:05 AM] +234 813 979 4675: *_42_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Wuni cur sukai a hanya kafin suka Isa, Saida ya sauka mota hankalinsa yayi mummunan tashi sbd baisan yanda zaiyi da babynba, Baisan wazai tunkara ba, Baisan tayaya zaiyi rayuwar makaranta da babynba. Tunanin farko daya fara zuwa kansa shine ya fara Kama hotel na kwanaki sbd bazai iya Zama da ita a gidansaba sbd bashi kadaineba tare yake da friends dinsa ashir da Nuraddeen. A hotel din daya Kama yakwana da babyn gari na wayeba baida zabi daya wuce yakaita gurin renon marayu sbd bazai iya yawon makaranta da itaba. Kudin daya bada sosai ne kadai yasa suka karban Masa ita amatsayin 'yarsa da mahaifiyarta ta rasu gurin haihuwa. Kwana biyu yayi yana yawo tsakanin makaranta da zuwa duba babyn, Sabon yanayi ya shiga na rashin sauki fa sukuni, Hankalinsa ya rarrabu, Ga damuwa da quncin dake maqale cikin ransa. Ahaka yayi kusan sati biyu Take kudadensa sukai qasa sosai. Babban abinda ya sake basa tsoro da firgici ga halin mutanen duniya shine duk kudi da Madara dayake siya na baby metron kashe kudin takeyi Bata siya Mata abubuwan buqata Ko gyaran jiki dayace aringa Mata da wipes sbd asibiti dasukai masa gargadi akan rage yawaita Yimata amfani da ruwa sbd sanyin daya kamata a baya, Amma sbd rashin tausayi da imani Ashe ruwa suke Mata amfani dashi ko Pampers basa siya maqale kudin sukeyi ko fitsari tayi ruwa suke saka zuba Mata sosai. Ciwo yafara Neman kama babyn damuwa tasake kamasa sosai gashi bayajin zai iya miqa babyn har abada gidan marayu. Haka yanaji Yana gani ya bar babyn hannun metron sbd watanni kadan suka rage Masa ya kammala karatun. Komai nasa yaqare, Kudin hannu da account dinsa sun qare tas dan haka yafara shiga yanayi sosai. Babban sauyin daya samesa na rayuwa shine gabaki daya ya rasa walwala da fara'arsa, Zancen abinda ya samesa tuni ya yadu tsakanin Abokai da jama'ar dasuka sansa Dan haka Ya tsame kansa ya kame daga hulda da kowa yanzu dama can bamai hayaniyar shiga mutanen ne Shiba, Cikin tsananin hali ya kammala sauran watannin dasuka ragewa karatunsa bayan ya Saida duka agogansa da wayarsa sun qare ga hidimar baby INAYAH wadda yasawa sunan Da karatunsa. Yana kammalawa ya tattara sauran abinda ya rage Masa ya fita neman hayar dakin dazai zauna ya nema aikin dazai kula da kansa da Inayah. Wata irin qauna Mai tsanani yakewa Inayah a yanzu daya Gama tabbatarda batada kowa saishi kaman yanda baida kowa sai itan. Kiransa da metron keyi da abban Inayah yasa kauna da shauqin abin ya shigesa sosai harya sabarwa kansa da amsa sunan. Gashi Inayah din tayi girma ta warware kaman kowane Lafiyayyan baby. metron ce tayi Masa tayin gidan hayarsu Baida zabi haka ya amince duk tsananin qyanqyaminsa da rashin iya Zama cikin mutane. Ganin yanayin gidan da jama'a sosai yasa ya ringa karbo Inayah wasu ranakun tana wuni hannunsa kafin ya maidata da daddare. Rayuwa Tai Masa tsanani sosai sbd baida komai baida hanyar koman, Ga metron tafara gajiya da renon tunda baida abin Bata yanzu saiya samo daqyar. Rayuwarsa tagama sauyawa tako Ina, Baya shiga mutane sbd kusan duk Inda yaje zundensa akeyi akan 'yarsa Inayah wasuma jifansa suke da zargin sai Allah idan ba lalata 'yar tasa zaiyiba. Girma da tsananin dacin kalmomin ya sanyashi tashi gidan bayan ya hada kudin hayar daki wani gidan daqyar da aikin wahala. Dayake yaga alaman metron ma ta gaji da renon Inayah kawai karbota yayi ya dawo sabon gidan daya samu mai dakunan haya birjik a jere Mai daukeda mutane dabam dabam masu halaye daban daban. Dagashi sai tabarma da abun rufa yadawo gidan sai yan kayansa na sawa dasuka Gama fita hayyacinsu sbd kodewa. Kayan Inayah ba duka suka basufi kala huduba Dan haka dakin nasu fili fayau ne. Madara yabata tayi bacci yafara kaida kawon tsakiyar dakin da ita a kafada Yana tunanin yanda zaiyi da ita yanzu. Zuciyarsa ta qame ta bushe akan Al'amarin mutanen duniya da basusan komaiba sai kansu. Cikin yardar Allah da zashi masallaci yafito da ita a kafada yana tunanin yanda zaiyi da ita yaje sallah. Umma yaganah ce ta lura da hakan Kuma tunda ya tare ayau din aka fara tsegumsa tanaji sunayi abinka da gidan haya gulma ba taushe hannu. Karban Masa ita tayi tace yaje sallar yadawo. Ba musu yabata sbd Yana buqatan hakan. Daga masallaci gurin neman aikin qarfi yadan zagaya yi Amma bai samuba sai daya dawo yasamu a anguwar ya samu tsaron shago Amma na idan an siya Kaya yakai mota yace ya amince. Koda yadawo umma yaganah tayi Mata wanka da ruwan zafi tas ta Goyata sbd itama tanada tsananin sha'awar Yara Amma Allah Bai bataba ga manyanci haryazo. Godiya yayi tareda bar Mata Inayah din sbd kada a datse mata bacci. Tun daga ranar renon Inayah yakoma hannun umma yaganah wadda ta fahimci baya tareda uwar Inayah tunda dai shine mahaifinta. Rayuwa taci gaba da tsananta Masa sbd komai ya qarasa juye Masa, Aikin tsaran shago da aikin gidan ruwa ya hada biyu yanayi dashi yake daukan dawainiyar Inayah. Ahaka har lokacin service Dinsu yayi yatafi yabarwa umma yaganah Inayah sati biyu acikin camp ya fito yadawo yafara bautar qasarsa. Fara service dinsa ya taimake rayuwarsu sosai sbd monthly allowance dinsa dashi yake musu komai. Kauna sosai ta tsakanin uba da 'da yakewa Inayah, Duka a lokacin burinsa na inganta akanta yaqare, Baida abinda yafi Masa Inayah sbd kaunarta ta taimaka gurin danne Masa radadi da ciwon dake daskare cikin zuciyarsa. Ahaka yagama yake fita aikinsa na service Yana dawowa kuma ya hada Dana aikin gidan ruwa. Koda ya kammala service dinsa Inayah tayi wayo sosai tasan mahaifinta wasu lokutan daqyar ma take komawa gurin umma yaganah. Haduwarsu da yagana yazama wani babban taimako daga Allah dan kuwa badan itaba baisan tayaya zaiyi renon jinjirar 'ya shikadaiba. Bayan Gama bautan qasa komai yasake tsananta alokacin ne yafara aikin wahala da qarfi kala kala Dan inganta rayuwar 'yarsa wadda yanzu a hannunsa take tabar hannun umma yaganah. Tare suke cin abinci tare suke kwanciya Wani lokacinma tareda ita yake fita aikinsa na wahala tana zaune cikin inuwa yake aikin yagama sudawo gida. Ganin kaman sanyin dakin zai Mata yawa yasa yasiya mata karamar katifa shikuma Yana kwanciya a tabarma, Duk wani abun buqata da Zata buqata baya sanya koda wahala saiya Nemo ya ajiye Mata. Ita kanta tunda tayi wayo tasan mahaifinta wata irin kauna da shaquwa Mai tsananice ke tsakaninsu, Batada abinda yafi Mata Abbinta a rayuwarta sai umma yaganah data sani, Sam Bai taba barin tayi kuka ko kewan rashin uwa ba, Shine uba Kuma shine ya maye gurbin uwa, Mata wani irin kallo yake musu na rashin tunani da rashin tausayi da imani shiyasa duk wata mace ta fice Masa arai, Mahaifiyarsa data qyamacesa sbd wannan qaddarar Bai tabajin ya tsanetaba Amma Kuma yasan tabbas Bata kyautaba Dan batai aiki da ilimin da Allah ya Bata. Inayah itace tazamo sanyin idanuwansa Kuma qarfin gwiwarsa sbd duka gwagwarmaya dayayi a halin dasuka samu kansu yayisune sbd inganta rayuwarta, Yayi alqawarin ingata tasa rayuwar da tatane sbd su rayu kaman kowane 'yaya marayu sbd daga shi har ita marayin Allah ne. ********** Hadiza bayan barinta gidansu majeed hanya tabi tana Jin kanta na juyawa sosai ga uwa uba tafiyar datakeyi kaman Mai koyan tafiya Dan kuwa gabanta tuni yafara zubarda Jini sosai na yamutsin dayake ciki. Batai doguwar tafiyaba taji tana Neman haukace tuburan Dan haka ta nema bakin wata hanya ta zauna tana rusa kuka sosai tana tasa Inda ke mata sauki a jikinta. Kukan datakeyi ne tana yagar jikinta yajawo hankalin mutanen dake kusa suka fara kallonta suna tausaya mata wasu Kuma Mai Mata video sbd ganin haukacewa zatai alokacin da alama asiri akai mata suke zargi. Kayan jikinta take kokarin yagawa wata Mata dake kokarin Shiga motarta tayi saurin zuwa ta tareta tana masifa da masu Mata video. Cikin kuka da azaba sosai Hadiza ta bude Baki daqyar tana cewa" Dan Allah ki taimakeni kikaini asibiti su ciremin gabana wlh azaba, Ciwo,zafi,radadi duka inaji. Kallonta matar tayi da mamaki tana sake riqe Dan kareta da handbag dinta masu sbd daukanta. Da mamaki tace" Me yake Miki azabar? Me kikeji? Kasa magana Hadiza tayi tana sake bubbuga gabanta cikin ficewa hayyaci tace" Dan Allah ku taimakeni..... Da sauri matar ta tari taxi ta cewa Hadizan ta shiga batareda ta kamataba sbd tsoro da tsaro. Tata motar tashiga tacewa taxi driver din yabiyota. Wani asibiti suka nufa tasa aka shigo da Hadiza wadda ta fice hayyacinta tini bayan gurnanin azaba da wahala Babu abinda take. Da gaggawa suka karbeta zuwa ciki suka fara dubata. Gaban nata dataketa duka suka fara budewa suka duba. Wata qara suka ringa saki cikin tashin hankali da tsoro. Dayake wadda ta kawota asibitin likitace take suka taru suka gano haihuwa tayi gabanta yasamu matsala. Cikin gaggawa da tashin hankali suka fara taimakonta. Dayake gurin ya lalace sosai Saida aka hada da yimata Yar qaramar tiyata. Bayan taimakon data samu sun Gama Mata komai an maidata dakin dazata kwanta tana bacci batareda tasan waye akantaba. Dr iklimat itace ta biya komai na Hadizan tukuna ta wuce gida. Kwananta uku a asibitin kafin yadawo cikakken hayyacinta ta zauna daidai tana Jin komai Yana dawo mata sabo yanda yafaru. Tashi hankalinta yayi tafara kuka Mai tsanani na Dana sani da Neman 'yarta. Da farko Dr iklimat ta dauka Hadizan nada ciwon qwaqwalwa ne Amma data zaunar da ita ta rarrasheta ta sanar da ita komai sosai hankalin Dr iklimat ya tashi Dan haka Hadizan na samun sauki suka dunguma Neman gidansu MAJEED. Kasa gane anguwar tayi bare gidan Dan haka suka ringa yawon stations suma Kai report Amma ba wani labari. Tashin hankalin da Hadizan tashiga yasa take Neman rasa nutsuwa da lafiyarta sbd ahankali yafara taba qwaqwalwarta. Dr iklimat data fara tsorata da Al'amarin haka ta samu ta lallaba Hadizan takaita Inda tafara ganinta tace tayi tanuni daganan ko Zata iya game gidansu MAJEED din. Kaman qwaqwalwarta bazata tunaba sai gashi ta tuna suka ringa bin Inda take tunawa har Allah yasa suka Isa kofar gidan. Basuga tashin hankali ba Saida aka tabbatarda MAJEED da babyn baasan Inda sukeba. Take agurin Hadiza ta suma, Haj umma ma Jin maganar dake bakin Hadiza yasata zubewa itama tana dafe kirjinta dake kokarin tashewa da tashin hankali Mai tsanani. Daqyar su Anty safiyyah da taimakon Dr iklimat ta Dan dawo daidai. Kuka tafara tana yiwa Hadiza Allah ya Isa akan abinda tayiwa MAJEED ta rabasa da uwarsa akan 'yarta Mara uba da asali. Hadiza Kam saidai akai asibiti da ita. A asibiti tana farfadowa Bata iya kukaba sbd zuciyarta dake barazanar daina bugawa. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_43_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Daga gidan Dr iklimat Hadiza sake komawa tayi gidansu hajiyar MAJEED wannan karon tana kuka tana komai Amma irin wulaqanci da tozarcin dasu anty juwairiyyah sukai Mata baisa ta hakuraba haka ta ringa zuwa rokonsu su fada Mata Inda MAJEED ya tafi da yarta. Tun tana zuwa tana samun ganinsu har takai idan tazo Mai gadi ke yimata korar wulaqanci yana zaginta. Daga qarshe police suka saka aka kamata daqyar tasamu Dr iklimat ta karbota bayan ta sanar dasu Hadizan nada matsalar qwaqwalwa. Tun daga lokacin tashiga wani mawuyacin hali na ciwo da nauyi a zuciya. Gabaki daya bata gane komai batajin komai sai kukan jaririyarta, Kuka tuninya Dena zuwan Mata ya qafe.. Ta dan samu lokaci ahakan cikin masu aikin gidan Dr iklimat kafin Dr iklimat tafara janta ajiki Dan ta warware tafara dawowa daidai. Da fari Al'amarin yayi wuya Amma da dr ta dage sosai Kuma lokaci yaja sai gashi tafara sakewa sbd kyautatawa Dr iklimat dataketa dawainiya da ita. Itama aikin ta dauketa cikin gidan na abinci data iya. Ganin qwarewarta a iya abinci yasa Dr iklimat ta maidata restaurant dinta sbd taga qaruwar da zatai da Hadizan. Dayake tasaba aikin restaurant sai Bata wani Sha wuyaba tasaba da aikinta sbd Sam yanzu Babu wani digon farin ciki ko daya a rayuwarta, Zuciyarta rufe take ruf da tarin baqin ciki da damuwa Amma a fili tana iya kokarinta gurin mu'amala me kyau da mutane. Dr biyanta albashinta takeyi Mai kyau ba gayya Kuma kullum ta gamo aiki a can da daddare gidanta take dawowa ta kwana Saida sassafe ta koma. Ahaka yayi fiyeda shekara daya a tareda Dr wadda Takoma tamkar wata babbar yayarta sbd sabo da kulawa, Fes Takoma tayi fresh abinta sbd nutsuwa da cigaban data samu sosai. Ana hakan abokin babban yayan Dr wani soldier yaganta yayi shaawan aurenta sbd yafi shaawan auren macenda batada kowa ganin yakeyi tafi maka biyayya hakama Zata riqeka amatsayin kowa nata tabika duk Inda kakeda ra'ayin juyata ko kaita. Dr iklimat tana duba ribar da Zata samu a komai na rayuwa Dan haka MJ Muhammed na bayyanarda buqatansa na auren Hadiza tasan cigabansu sbd yanada arzikinsa sosai saidai yawan auri saki Amma yanzu kila ya daina tunda ya samu irin wadda yakeso wadda bazata iya Musa Masa komaiba sbd batada kowa. Hadiza batada ra'ayi ko shaawan aure yanzu ko kadan aranta Dan haka Bata boyewa Dr iklimat ba ya fada mata batada ra'ayi. Dr batai qasa a gwiwa ba ta ringa lallaba Hadizan tana cusa mata ra'ayin da auren kawai Zata samu sukuni da nutsuwata rayuwa tareda komawa cikin 'yan uwanta dasuka gujeta, Aure ne kadai rufin asirinta Kuma shine zai Bata Daman sakin kudi ta nema majeed da 'yarta duk duniyar daya gudan Mata da 'ya. Zancen Ayshatouh da Dr tasaka yayi tasirin sauya Mata raayi Akan yin auren. Ba bata lokaci kuwa Dr tafara karban kudi sosai gurin MJ Muhammed aka fara gyaran Hadiza daman gata da sauran kuruciyanta. Gaggawa Dr iklimat tasaka akan auren Wanda yasa Hadizan kejin damuwa Amma Kuma bazata iya fasawaba tunda tabbas batada qarfin dazata nema 'yarta sai tana tareda Mai qarfi. Batada ra'ayin komawa gida Amma Dr iklimat ta dage akan suje gidan a daidaita Yan uwanta su daura Mata auren da kansu sbd kaucewa wata fitinar gaba. Bayan ankai ruwa Rana itada Dr da Yan uwanta suka karbeta Bayan sun tabbatarda Mai kudine sosai Wanda zata aura. Tunda Hadiza tadawo gida Babu Wanda ya tambayi Inda yarta takeba sai Inna wadda take fushi sosai dasu kabiru tun Bayan barin Hadiza gidan. Ita kanta hadiza Bayan dawowar tata bayan gaisuwa Babu abinda yake hadata da Yan uwanta da matansu da 'yayansu, Ta kebe kanta ta tsame daga cikinsu sbd tasakawa kanta Bayan Inna da Dr iklimat batada kowa a duniya. Wata biyu tayi da dawowa gida akan daura aurenta da MJ Muhammed ta tattara Takoma Abuja gidanta itada Mai aikinta guda daya. Tunda akai auren hankalinta baya kan mijinta sai akan Neman 'yarta wadda idan ciwon rashinta yataso Mata kaman zautuwa takeyi. Tun mj na daurewa har abin yafara damunsa sosai auren ma yafara fice Masa akai. Rawa auren yafara tun Bai Gama cika shekara ba Dr na ganin hakan ta tashi tsaye akan Hadiza da fada sbd idan tayi gangancin rasa auren tayiwa kanta. Ga rayuwarta tuni ta sauya tasamu wadata da Jin Dadi Amma zuciyarta takasa nutsuwa ta rungumi qaddara. Inna Dr iklimat ta daukowa Hadizan wadda ta zauna tareda ita tana lurar da ita illar datakeson yiwa rayuwarta idan Bata dauki qaddara ta rungumaba. Ba kunya hardasu Yaya Umar suka ringa kawo Mata ziyara akai akai suna Mata nasihan riqe aurenta. Tayi iya kokarinta gurin danne damuwarta cikin ranta tafara kyautatawa mj Wanda yake tsananin kaunarta da Gaskia yanzu. Rayuwar aurenta ta gyaru sbd ganin yanda dangi da Yan uwa kowa nayi da ita sosai sbd abun duniyar datake dashi yanzu Dan haka saita sake nutsuwa da kulawa da mijinta sbd koba komai auren yazama rufin asirinta dayasa kowa ka binta a Yan uwa. Duk yanda taso cire damuwar yarta Bata iya cirewa duka Wanda hakan yasa mj ya dauketa daga Abuja Inda take tuna babyn ya maidata Lagos yadawo da uwar gidansa Abuja. Rayuwarta a Lagos tafi ta abujan kwanciyar hankali da nutsuwa sbd ta rage damuwa sosai ta fuskanci gabanta. Kaman yanda ake cewa dukiya daban take to kusan ta tabbarda hakan, Yayunta dasuka fara aibata 'yarta sundawo sune suke gwagwarmaya sosai gurin bincike da Neman Ayshatouh wadda suka yarda da cewan ba shegiyar bace yanzu idanma da Allah suka yarda ko Dan quncin dasuka luradashi kwance qasan ranta Wanda suka tabbatarda har abada bazai goguba, Kokuwa Dan kudin datake sakar musu sosai gurin binciken Neman 'yar ne? Kwadayi da dukiya sunsaka anbata danta Abdulsamad Wanda tasaka a makarantar kudi anan lagos Yana karatu cikin kwanciyar hankali da wadata, Yan uwan salisu da dama yanzu zumunci da hulda sukeyi da ita sosai Dan kuwa Babu qyashi a zuciyarta tana musu Alkhairi, Yaya Umar da Yaya kabiru sune tsundum aduk Dan abinda ke gareta sbd mj ba mai Zama bane shiyasa daga ita har uwar gidansa uwar yayansa dukiya yake musu sosai. Ahaka rayuwarta ta sauya Babu wani labari ko bayanin ganin Ayshatouh da Abdul majeed. Shekaru sunja sosai manyanci yazo akan dole ta dangana ta cire ran ganin Ayshatouh har abada a qarshema ta sanyata cikin adduar datakewa salisu dasu mama na Allah yayi musu rahama. Abdul baitaba sanin yanada 'yar uwaba sbd zancen da aka rufe gabaki dayansa aka barsa amatsayin qaddarar data wuce. Dr iklimat tazama uwa kuma 'yar uwa gareta Dan haka bayan mj yayi retire tadawo abuja da Zama Amma sai zaman lfy na Neman gagararta da uwar gidanta Dole aka rabasu ita Takoma Adamawa nata gidan sbd ta nuna Masa tafi ra'ayin Zama acan sbd Kota koma Lagos din tunda yabar Lagos yakoma Abuja ba wani amfani Dan haka tafison Adamawa. Da wannan ta tattara tadawo adamwa qaton gidanta da MJ yasiya Mata Mai girma daga ita sai Inna da masu aiki sai Dr Abdul idan yazo sbd aiki dayake a asibitin Dr iklimat dake Abuja. Yaya Umar da Yaya kabiru ma tuni suka zama cikakkun masu rufin asiri da Yar wadata ta sanadin mijin Hadizan daya sakasu cikin wasu Yan haurkokinsa na business Kuma suna samu sosai aciki Dan haka suka sake tsayawa sosai akan duk wata hidimar Hadiza da iyalinta duk da Bata sake haihuwaba tun tsawon shekarun Wanda Dr iklimat tayi Mata bayanin tasamu matsala tun wancan lokacin data samu matsalar gaba ba lallai takuma haihuwaba shiyasa ta dauki tsananin son duniya ta dorawa Dr Abdulsamad sbd ga dukkan alamu shikadaine Dan dazata samu a duniya. WANNAN SHINE ASALIN ABINDA YAFARU. *************************** Tsit kowa yayi Banda kukan Haj umma Dana Hadiza saina umma yaganah Babu abinda yake tashi. Alhaji babbah da cm dama sauran duka mazan gurin duk jarumtarsu jikinsu saidaya yayi tsananin sanyi. Cm da umma yaganah ne suka Dora da irin gwagwarmayar wahalar rayuwar dayaSha iya wadda suka sani gurin kulawa da Inayah da sauran wahalhalun har arzikinsa. Duk Wanda yake gurin ya jinjinawa AA MAJEED da irin karfin zuciyarsa. Ita kanta hadiza jikinta sanyi yayi tareda sabuwar danasani ga girmansa daya cika Ido da zuciyarta sbd duk Wanda ya riqe 'Yar dabai hada komai da itaba irin hakan Basu taba tunanin zaa samu Mai wannan zuciyarba. Tun farko nutsuwar da zuciyarta tayi dashi a ganin farko yasata guduwa tabar Masa 'yarta batareda tunanin komaiba Amma bataba dauka kyan zuciyarsa da karfin zuciyarsa yakai hakan ba. Hawayen kunya da damuwar abinda tayi dama na tausayin kanta dana majeed take tsayayowa tana sunkuyar dakanta qasa sbd Babu Kuma wani abun fada daya ragewa kowa. Hajiya umma tafi kowa shiga baqin ciki da Dana sani sbd ko a bayan da hadiza tadawo neman yarta tafada musu gaskiyar su juwairiyyah Basu Bari hajiyar ta yarda da duk abinda Hadiza ta fadaba shiyasa suka hanata bayyanarda damuwarta akan rashin majeed dinta da karfi da yaji Amma tun daga wancan lokacin Bata Kuma isashiyar lafiya ba sbd ciwone da qunci a dunkule ranta na 'danta datafi so fiyeda komai da kowa. Su Yaya Umar kusan sunfi kowa kunya da baqin cikin abinda suka aikata dan kuwa kusan sune sanadin komai Dan tun farko dasun rungumi qaddarar Yar uwarsu da duka baa cutatar da wanda baijiba Bai ganiba aka tarwatsa Masa rayuwa aka rabasa da iyayensa. Alhaji babbah yaji tausayin MAJEED da Hadiza fiyeda kowa sbd kusan kowa mafita take nema a halin matsuwar dasuka shiga Amma tunda kusan komai yazo qarshe Kuma kowa wahalarsa ta wuce tazama tarihi sai kawai a rungumi qaddara sbd duk wannan Al'amarin idan anduba rabon aurene dake tsakanin majeed da Inayah yasa komai yashigo ta hanyar tsanani. Anty juwairiyyah kunya da takaicin Hadiza harma Dana 'yarta ya hanata cewa komai har zaman ya tashi kowa ya watse aka bar Yan gidan kawai sai Haj umma da Babu Inda Zata sai 'danta yadawo Dan bazata iya sake tafiya tabar majeed dintaba sanyin idanuwanta dayaSha gwagwarmaya da wahalar rayuwar duk tarin arzikinsu. Ta bangare daya jin tayi zuciyarta na Dan qonuwa da Inayah sbd akanta 'danta ya zabi ya barta, Ya bar mahaifiyarsa sbd ita, Ya fifita kaunarta Mai tsanani da duk duniya tasan da Babu abinda yake kauna sbd ita duk da tayi imanin da kaunarta na qasan ran majeed dinta sbd bazai taba daga so da kaunar wani akantaba. Amma Kuma duk da hakan ya fifita Inayah akanta qarshe yanzu karshen rashin rabuwa ya aureta Wanda ita Sam batajin danta ya cancanta wannan auren sbd tako Ina danta ya cancanta rayuwar Jin Dadi da farin cikin daya rasa shekaru. ##MAMUH# #HOT LOVE/ROMANCE #MAJEED/INAYAH _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/7, 11:34 AM] +234 805 800 0496: *_44_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Inayah da kafafuwanta suka kasa riqeta sbd kukan datake Mai tsanani Mara sauti ahankali ta juya tana dafa bango ta nufi dakinta... Daqyar ta iya Kai kanta daki sbd ko ganin gabanta batayi sbd kuka hannuwanta na toshe da bakinta. Tana Isa bakin gafo ta silale Wasa ta zauna tana sake sabon kuka. Abbinta kawai zuciyarta kewa wannan kukan sbd sam ita batajin tanada wani abun tausayi tun jarinta har yanzu sbd Abbinta bai taba Bari ta Zama abar tausayawaba tun tana cikin zanin goyan da uwarta ta yarda ita ta tafiyarta. Taji tausayi da kaunar mahaifiyarta saidai Kuma har lokacin kaunar kaunar Abbinta daban take a ranta Musamman yanzu datake qaunar tasa na qara nauyi da cikin ranta Dan kuwa har abada Batajin Zata karbi mahaifiyarta matuqar ba abbin ne ya yafe Mata ba ya hadata da ita. Neesah ce ta fito toilet taga yanda Inayah din ke kuka ta qaraso tana kallonta cikin mamaki da firgici tace" Lafiya? Wani abin yakuma faruwa ne? Haryanzu Baki samu abbin bane a waya? Kasa magana tayi ajiyar zuciya datake jerowa idanuwanta sunyi jajir. Umma yaganah ce tashigo dakin fuskarta jajir da alamar kukan datasha sbd tausayin MAJEED datake Jin itama kaunarsa da girmansa  sun ninku a ranta sbd ya tabbata Mai tautasayi da kyakkyawar zuciya duba da yanda itama ya riqeta da Maigidanta kafin ya rasu har zuwa rayuwarta daya Gama ingantawa yazama gatanta Mai kare mutuncinta da martabarsu yabasu suna da mutunci a idon duniya. Tabbas har abada daga ita har Inayah basuda tamkarsa Kuma zasuci gaba da Zama a qarqashin ikonsa da sunan Daya Basu, Yazama ubansu gatansu Kuma zaici gaba ra zama hakan har abada da yardar Allah. Inayah na ganin umma yaganah ta sake fashewa da kuka tana fadawa jikinta tana cewa" Umma yaganah Abbina nakeson gani kawai yanzu,.bana samun wayarsa Dan Allah ki kirasa yadawo gida na Dena duk wani rashin jin magana,,, Ni har aurenma na karba zanyi auren dashi Dan Allah kice ya Dena fushi Dani yadawo. Umma yaganah data kasa cewa komai bayanta kawai take Dan bubbugawa tanajin kaunarsu su dukan duk da Inayah tako ina bata Zama abar tausayiba Dan kuwa rayuwarta tagama samun haske tunda MAJEED ya tsaya Mata. Umma yaganah Bata sake Jin tsananin kaunar auren MAJEED da Inayah dinba sai yanzu Da komai ya bayyana. A duniya Babu Wanda ya cancanta da Inayah dai Abbinta majeed Wanda shi wannan auren ya zamarwa dukkaninsu RIBA BIYU. Rarrashinta umma yaganah tayi tareda Neesah wadda take sauraran maimaicin zancen komai abakin umman wadda ke fadawa Inayah komai batareda tasan taji komai ba. Sun jima a daki suna rarrashin juna kafin a dakin Inayah din dayafi kowane daki girma da tsaruwa a gidan Banda na Abbinta daya banbanta da nata ta hanyar tsarararren palonsa dake hadeda master bedroom dinsa Wanda shima komai na cikinsa milk ne sbd tsananin tsaftarsa yafison komai me haske bazai bayyanar Masa da komai qaqantar datti Dan ya rabu da ita. Gidan tsit kaman ba kowa saisu zubbi da Salimat dake aikin kaida kawon abinci da maimaicin tsaftace gidan, Haj umma da Anty juwairiyyah na daki Anty juwairiyyah sai kame kame takeyi sbd kunyar kanta data mahaifiyarsu saidai Kuma tana maimaitawa Haj umma girman lefin MAJEED dayaqi waiwayo gida ya zabi 'yar tsintuwa akan mahaifiyarsa. Itadai Haj umma Bata tankataba sbd yanzu Babu wani Hadi dazai sake rabata da 'danta ciki kuwa harda Inayah wadda ta tsaya Mata arai sbd kaunar da aketa maimaita majeed dinta nai Mata. Sai dare kowa ya fito cin abinci suka hade a dining kowa na kallon dan uwansa Banda Inayah wadda kafin ta fito sai yawon zuwa kiranta tazo taci abinci kowa keyi daga umma yaganah har masu aikin da Neesah. Saida suka fara cin abincin ta fito sanyeda Gucci Riga da wando gajere Wanda ya bayyanarda fararen qafafunta masu kyau da lafiyar fata. Rigar batada Fadi sosai Kuma Bata saka bra ba sbd kusan Shirin baccine tayi. Slippers ne a qafarta da wayarta a hannu tana sake saka Kiran Abbinta Wanda duk yakira bai shigaba sai idonta yacika da hawaye. Qamshinta kawai yasa Anty juwairiyyah sake Baki tana kallonta sbd tasan Qamshin Turaren da tsadarsa tunda tana yawon qasashe. Haj umma kuwa kayan jikin Inayah din da yanda take wani irin Bata fuska kaman zata fasa kuka take kalla cikeda mamaki, Lallai yarinyar tasamu sake fiyeda yanda suke tunani. Zama Inayah tayi Kai tsaye batareda ta kalli anty juwairiyyah ba ta gaida haj umma da cewa" Haj umma Ina wuni? Ita kadai ta gaida Dan haka kowa yayi tsit, A natse hajiyar ta amsa itama batareda takuma kallontaba. Cikin daure fuska umma yaganah tai Mata nuni da juwairiyyah wadda ke juran Inayah din tawi gaidata Tai mata fada tatas ba ruwanta da gatan dataga yayiwa yarinyar yawa. A hankali ta gaida anty wadda ta haifeta nesa ba kusaba Dan kuwa yarta ta fari ta girma Inayah din sosai. Wannan auren datakeyi yanzu yayanta biyu Dan haka yayanta uku Auren ne irin na yayan masu kudi bawani Zama takeyiba kusan koyaushe taso tana gidansu kokuma yawon wata qasar dauko kayan business, Anty safiyyah ce kawai take Dan Zama gidanta itama sbd aikinta datakeyi Dan haka Bata wani yawo ko tafiya sai wadda ta danganci aiki Itama yayanta uku bayansu Bata qaraba ko yanzu da Alhaji babbah dakansa ya aiko nemansu Bata samu biyosu Haj umma ba sbd aikinta da Bata Wasa dashi shiyasa sukazo su kadai. A taqaice anty juwairiyyah ta amsa gaisuwar tana zuba abincin dazataci. Zubbi Inayah tafara zubawa tuwon semo da vegetables soup dataji Naman rago da ganda da kifi. Tana Gama zuba Mata ta kawo Mata ruwa Mara sanyi dan ita batashan ruwa Mai sanyi Yana daya daga cikin koyarwar Abbinta tun tana qarama baya barinta da sanyi kowane iri ne sbd sanyin dayaso shigarta tun tana jaririya. Da spoon takecin tuwon Dan haka hankalinta ya rabu akan abincin da wayar hannunta. Dungurar da wayar tayi da qarfi akan dining tana sakin qaramin tsokin rashin samun Abbinta Dan zuwa yanzu hankalinta yafara tashi da rashin jinsa. Sudai su Haj umma mamakin duniya yagama cikasu da kallon Inayah wadda shagwabar da ita da akayi take a fili... Budurwar yarinya likita guda Amma duka halayyarta da dabi'unta kaman wata qaramar baby. Bata Gama cin abincinba ta miqe zatabar gurin umma yaganah ta dakatar da ita cikin kulawa tace" Inayah Ina zaki bakici komaibafa a abincin? Meyasa kike Wasa da cin abinci yanzu? Shi abbin naki idan yaji bakya cin abinci aikinsan fadan dazaiyi. Ba dazu kika Gama cewa afadawa Abbinki kin daina rashin jiba? Dawo zauna kici abinci. Zubbi da sauri tasake matsowa cikin kulawa tana kokarin zuba Mata wani abincin sbd wannan ya huce Inayah din tace" Barshi zubbi zanci wannan din ahaka. Dawowa tayi badan tasoba ta zauna tana tura abincin. Kasa riqe mamaki anty juwairiyyah tayi tana Satan kallon Haj umma cikin ranta tana cewa" Akwai matsala kuwa babba Dan haj umma tazo qarshen kishin 'danta kila Dan wannan yariyar da alama tagama nisa a tabara Mai lasisi gurin MAJEED. Koda aka gama cin abincin Saida umma yaganah tasa aka hada fruit salad takaiwa Haj umma daki da kanta harya zauna sukai Dan fira duk da bawani fuska sosai gurin Haj umma din. Danta MAJEED kawai take buqatan yadawo ta rungumi abinta tashafa kansa ta tsiyayar da hawayenta na shakarun rashinsa dake qasan zuciyarta. Inayah kuwa hankalinta tashi yayi sosai Dan hakan Bata taba faruwa da itaba na rashin Jin Abbi Kuma Bai sanar da itaba Ina yatafi Dan haka hankalinta yayi masifan tashi daqyar taga safiya. Duk Wanda yake gidan tun qarfe 6 na safe ta tadasu bacci da tashin hankali harsuma duk saitasa hankalin kowa yatashi sbd kowa yakira wayarsa baya samu Kosu Haj umma dake basuda numbernsa anbasu kowa yayita Kira baa samu. Kuka da tashin hankali Babu wanda Inayah bata shigaba ba shiri aka nema CM suka Samar dashi. Baiso sanar musu tafiya AA din yayiba Saida yaga yanda Inayah ta dagawa kowa hankali tukuna ya kwantar musu da hankalin tafiya majeed din yayi Kuma wayarsa da basa samu sbd layin baya Aiki acan ne. Hankalinsu ya Dan kwanta anty juwairiyyah Saida tayita fadan yanda Inayah ta dagawa mutane hankali Batasan Haj umma nada hawan jini bane Zata kashe musu ita tunda batada asara. Itadai Inayah batace komaiba sai Haj umman dataje tabawa hakurin daga Mata hankali datai taqara da cewa bazata sake ba. Har dare ma still abbin bai kirasu ba haka jiki amace Inayah ta kwana, Washe gari neesah Zata wuce Dan haka itace da kanta takaita airport tareda Safnah suka rakata ta wuce. Daga airport gidan anty Hafsat suka wuce. Acanma anty Hafsat rarrashinta tayi tareda Bata qwarin gwiwa akan auren a fakaici Dan kuwa suma basusan yaushe wannan auren zai Zama cikakke ga ma'auratanba Amma dai kam Zata dage gurin ganin ta ingiza Inayah tako Ina tunda baruwan Inayah din ba doguwar Noke Noke ta iyaba Babbar matsalar da fargaban na gurin AA MAJEED Wanda kwata kwata matan ne basa gabansa bare Inayah dayakewa kallon 'yar cikinsa. Sai yamma tadawo gida bayan umma yaganah tayita kiranta tadawo gidan hakanan. Koda ta dawo anyi sallar magriba Dan haka daki ta wuce Kai tsaye tayi alwawala tayi sallar magriba ta zauna tana sake gwada kiransa Dana Neesah Amm duka Bata samesuba. Ajiye wayar tayi ta nufi dakin Haj umma ta gaidata kafin ta fito ta wuce dakin umm yaganah ta taddata tana waya da Yan uwanta dake maiduguri. Zama tayi gefenta tan saurarenta harta Gama tukuna tace" Umma yaganah ke kisake gwada Kiran Abbi ko zaa samesa. Bara mugani to" Nemo numbernsa tayi tasaka Kira Amma Bata shigaba Dole suka hakura. Fira umman kewa Inayah Mai Kama da nasiha saiga Kiran Hadiza yashigo wayat umman ta kalli Inayah tace" Ga mahaifiyarki Nan nakirana. Dauka tayi da sallama suka gaisa Hadizan ta tambaya ko AA MAJEED din yadawo daga tafiya umma ta sanar Mata Bai dawoba. Inayah ta tambaya cikin sanyin murya da jiki. Kallon Inayah umma tayi kafin tace" Lafiyanta kalau gatanan zaune Bata nabata ki gaisa..... Aa,aa kyaleta tunda naji lafiyartama ya Isa zanci gaba da jira har AA din yadawo kaman yanda nayi alqawari Inshallah Zan jira sai ranarda ya yafemun ya hadani da ita Dan kansa Zan tunkareta. Tausayin Hadizan yasa umma Dan rintse Ido tana cewa" MAJEED baida matsala Inshallah idan Anbi komai a hankali zakiga da kansa zai hadaku. Godiya Hadiza tayi kafin sukai sallama suka aje wayar. Inayah shiru tayi batace komaiba Itama umman tana aje wayar batacewa Inayahn komaiba. Tashi sukai Sakai sallar ishai suna gamawa Inayah tayi dakinta jikinta a mace tanajin wata irin damuwa da tashin hankalin rashin ji daga Abbinta. Wanka tayi tana fitowa ta sanya D&D off-white Riga da wando masu Dan kauri Amma guntaye Dan wandon Bai Gama kaiwa gwiwarta ba Amma yanda Fadi sosai Rigar kuwa daidai jikinta ce saidai yau tasaka condom bra. Kanta farar qaramar wulace akanta data bayyanarda kusan Rabin gashinta dayake sauran gyaran aurenta har lokacin. Slippersta ziro ta fito qamshinta Mai dadi Yana tashi daga jikinta ahankali. Tun kan ta iso palon anty juwairiyyah tajiyo Dan qamshinta Dan haka ta waiwayo tana tallon hanyar kofar dakin Inayah din. Dukkaninsu me zaune a palon har Haj umma da umma yaganah sun Dan zatawa sama sama. Zuwansa yasa Haj umma kallonta ta dan dauke kai sbd kayan Inayah din kullum Babu na arziki tasaba da rayuwar turai da sakewa a gida ba ruwanta. Umma yaganah data lura da yanayin haj umma da Anty juwairiyyah dakewa Inayah kallon mamaki Saita miqe a Dan fuske ta kalli Inayah zatai Mata magana aka bude kofar palon Kai tsaye Wanda yasasu juyawa duk su dukan sbd Babu mai shigowa Kai tsaye batareda Danna doorbell ba idanba Mai gidanba dakansa. Cikin nutsuwa kuwa yashigo sanyeda black Armani's fuskarsa fes tana daukan idon kwarjini Mai tsanani, Take qamshinsa ya doke Wanda Inayah tacikasu dashi. Cak kowa ya miqe suna kallonsa dukkaninsu shima cak din ya tsaya yana kallonsu....... Inayah data Gama kallonsa cikin tsananin farin cikin ganinsa da Murna taje a guje ta fada jikinsa ta maqalqalesa da wata irin kyakkyawar rungumar datasashi dafa kofa. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/7, 11:34 AM] +234 805 800 0496: *_45_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Kofa ya dafa da kyau sbd ba zato yaji ta jikin nasa.... Yaune Karo na farko data rungumesa tunda tayi girma tazama budurwa sosai, Kuma yau shine Karo na farko da mace ta taba rungumarsa har kirjinsa dana mace ya hadu. Saurin janyeta yayi daga jikinsa Yana kallonta cikin yanayi na Dan kame yanayin da dan fada kadan yace" Ki nutsu mana, Bakya girma ne haryanzu Inayah. Bata fuska tayi idanuwanta nacikowa da hawayen dabatasan Kona menenba ta sake riqo hannunsa tana riqewa sosai tace" Abbi kasan yanda hankalina yatashi da tafiyar Nan taka? Kowa anan yadamu Amma nafisu damuwa sbd baka taba fushi Dani irin hakaba... Tafin hannunta ta sake sakawa cikin nasa tafin hannun ta riqe tana cewa" Dan Allah kayi hkr Abbi bazan sakeba. Dagowa yayi Yana kokarin janye hannunsa duk da tasaba riqe hannunsa sosai ko bayan girman nata Amma yau din akwai mutane. Kasa amsa Inayah din yayi idanuwansa nakan matarda yake son tabbarda idan mahaifiyarsa ce daya rasa shekaru masu yawa, Ummansa da Babu lakacinda zaizo qasar baije ya bincika lafiyartaba yaji yanda take agurin Mai gadin gidan Wanda ya tabbatar Masa da Karya taba fadawa kowa zuwan nasa. Anty juwairiyyah da ita mamaki da takaicin duniya yayi Mata yawa na Inayah ya kalla ya tabbatarda itace take ya yarda da ummansa ce agabansa cikin gidansa Yaka gani. Sukuwa dukkaninsu mamaki rashin kunyar Inayah sukeyi Mai girma Banda umma yaganah datasan halin kayarta tasaba da hakan Amman yau abin yayi wani irine sbd agaban hajiyar MAJEED dinne da yayarsa Wanda data kusada Inayah yashigo riqeta zatayi bazata Bari tajeba koba komai ga kayan dake jikinta dasuka Santa su hajiyar mamaki tun farko Dan su komai Inayah tayi haryanzu a mazaunin rashin kunya da da'a suke sanyashi duk da sunada wayewa suma sunyi yawon qasashen Amma dai na Inayah ciwo yakewa Haj sbd kishin kusanci da gata Mai tsanani da MAJEED yayiwa Inayah. A hankali cikin nutsuwa da yanayin na mamaki da bayyanarda rauni sosai Wanda su Inayah Basu taba ganinsa dashiba ya tako ya nufi gurin hajiya umma Yana sake danne zuciyarsa ga raunin dayake bayyanarwa sbd baisan dalilinsu na Neman Inda sukeba sukazo...ko haryanzu fushi ummansa keyi dashi. Haj umma data fara hawayen ganin 'danta daya rabu da ita Yana matashinsa yazama tamkar babban mutum, Yazamar Mata wani kamilallan Alhaji komai nasa ya rikida Yakoma tamkar mahaifinsa lokacinda yake daidai shekarunsa. Kasa jiran ya Isa gabanta tayi sbd sanyin jikin daya nuna na shakkar fushinta akansa ta tako ta qaraso gurinsa itama da sauri ta rungume abinta tana fashewa da kukan farin cikin ganinsa da jinsa. Akaro na farko tun Bayan barinsa gida Yana dan matashinsa daya zubarda hawaye daga idanuwansa. Mahaifiyarsa dayake tsananin kauna a duniyarsa ta yafe masa, Ta sauka daga fushinta na shekaru, Yau itace agabansa tana kukan farin cikin ganinsa. Daqyar hajiyar ta sakesa ta dago tana kallon fuskarsa da shima ita yake kalla muryarsa a sanyaye yace" Umma..kin yafemun? Gyada Kai tayi da sauri tana hawaye tana murmushi duka alokaci daya tace" Na yafe maka MAJEED, Na yafe maka, Nice nayi kuskuren bakaiba.. 'dana yadawo gareni ya Allah nagode maka. Ahankali ya Dan sunkuyar dakai Yana hadiye hawayensa cikin nutsuwa da farin ciki Mai yalwa shima yake yiwa Allah godia,. Kuma dagowa yayi ya kalli anty juwairiyyah dake tsaye itama tana kallonsa duk tunanin duniya ya ninku akanta sbd ganinsa ya tabbatar Mata da arzikin dasuka gani ma kenan Wasa ne, Majeed din yakoma wani hakimtaccen namiji Mai zallar kwarjini da cika ido, Ita kanta datake yayarsa Jin tayi tana Neman kasa hada Ido dashi Saida tayi da gaske Bata Ankara ba taji bakinta na furta" Sannu da dawowa MAJEED. Qayataccen murmushinsa yasake cikin nuna farin cikin ganinta itama ya miqa mata hannunsa daya Yana cewa" Ina farin cikin dawowarku rayuwata kema anty juwairiyyah. Dayake sun saba da shaking hannuwa tun suna Dan kaunar juna Dan haka ta miqa hannu takama nasa tana bayyanarda farin cikinta na ganinsa itama. Hannunsa cikin na hajiya da Anty juwairiyyah ya juyo ya kalli umma yaganah da Inayah dake tsaye tana kallonsa da idanuwanta dasuka Dan sauya da yanayi Dan Jin wani iri Abbinta zai Zama ba nata Ida kadaiba yanzu tunda family dinsa zunzo Bayan tasaba da Baya hadata da kowa bare komai. Kasa sakinsa hajiyarsa tayi Dole anan suka zauna duk da gajiyar tafiyarsa ta sakesa take sbd farin cikin ganin mahaifiyarsa. Cikin nutsuwa da sanyinsa yace" Umma yaushe kukazo? Waye yakawo? Ya kukasan Nan? Cikin farin ciki tace" Majeed bazan taba iya rabuwa dakaiba yanzu sbd haryanzu Bayan ganinka ciwon da zuciyata take na rashinka Bai dainaba.. Alhaji babbah da kansa yayi aikin mutum har gida aka taho damu Bayan Kiran waya dayayita yimun.. Banda zabi Bayan zuwa din sbd Nima Ina Neman 'dana Ido rufe, Meyasa katafi baka dawo gareniba MAJEED? Meyasa baka taba waiwayataba majeed? Kuka ta fashe dashi tana bayyanarda tsananin radadin da zuciyarta tashiga na rashinsa duk tsawon lokacin. Anty juwairiyyah ce dashi suka ringa rarrashinta Yana sake Bata hakuri akan kuskuren rashin komawa dakuma kuskuren zaban tafiya yabarta, Bai tsaya Jan tado zancenba ya yarda da suka shine mai lefin yabata hakuri tareda alqawarin insha hakan bazata Kuma faruwaba. Umma yaganah ma ta Dan saka baki tasake bawa hajiyan hakuri da adduar Allah ya tsare gaba. Inayah data matsu sugama tayi magana da Abbin ta matso tareda Zama gefensa daya tana kallonsa cikin yanayin son magana zatai magana ya Dan saci kallon hajiyarsa Dan yasan idan ba yanzu ta sauyaba zataji damuwar shigewar da Inayah Tai Masa Dan haka cikin Dan kulawa da nutsuwa ya kalli Inayah din yace" Inayah kina gaida hajiya yanda yakamata tunda tazo kuwa? Kallon hajiyar tayi tace" Eh Abbi kullum safe da yamma har dare ma wani lokacin. Kuma tare muke cin abinci a dining. Dan murmushi yayi Yana cewa" Kin kyauta to. Jeki ki saka kayan sanyi Ana wannan sanyin Zaki fito haka? Umma yaganah ya kalla yace" Da mutane a gida shine take yawo hakan? Kallon Inayah tayi tace" Kasan Inayah ba Jin maganata takeyi sosaiba. Abbi banajin sanyi fa, Nidai Zan sauya Kaya Amma saika yafemun kadaina fushi Dani, Abbi Dan Allah kayi hakuri ka daina fushi Dani wlh nafadawa umma yaganah nayi alqawari ko sunan Heart bazan Kuma ambataba, Ni har aurenmu ma na karba zanyi Amma Dan Allah Abbi ka yafemun..... Hawaye tafara tana riqeda hannunsa cikin yanayi da dana sanin lefin data aikatadin duk da batasan takamaimai akwan wanne daga cikin lefin take fushi da itaba. Nauyin mahaifiyarsa mai tsanani yakeji Musamman ganin duk sunyi zuru suna kallon ikon Allah Dan Inayah dinnan tafara wuce tunaninsu Gashi kaman majeed din biye Mata yake da alama shiyasa tabarar tata take yawa. Zame hannunsa yayi Yana kallon umma yaganah yace" Kuje ciki zamuyi magana gobe idan na nutsu. Gangarowa hawayen Inayah sukayi tace" Abbi gobe? Nidai bazan iya bacci ba idan baka dena fushi daniba ka yafemun. A natse ya juyo ya kalli fuskarta cikin kulawa yace" Bana Hana wannan kukan ba? Kije ki saka kayan sanyi Anjima zamuyi mgn. Ok Abbi" tace muryarta a sanyaye. Tashi tayi ta wuce umma yaganah tabita suka Basu guri yabisu da kallo kadan sbd yasan Inayah saitayi kukan idan suka Isa daki. Baki sake Haj umma suke kallonsa Ya dawo da kallonsa kanta Yana sake Jin farin ciki. Bata Bari Inayah tashiga damuwarta akan danta ba sbd tasan Babu Wanda zai taba samun matsayi irin nata a zuciya da rayuwar 'danta. Anty juwairiyyah Kuma mamaki da tunanin zaman da Haj tace zatai a gurin 'danta takeyi Dan kuwa akwai matsala. Haj na kishin 'danta Inayah ma da alama batason kowa ya rabi Abbinta sbd ta taso da kaunarsa da kulawarsa akanta ita kadai Bai taba hada kaunarta da kulawarta da komaiba Dan haka a take tagano Inayah ma zatai kishin wani ya rabi Abbin nata Wanda yake mijinta yanzu duk da ba mijin ta daukaba haryanzu a Abbinta yake. Hmmmnn""ta sauke ajiyar zuciya a fili. Sun dade a palon sosai suna magana kafin yasamu ya nufi dakinsa. Akwatinsa daya dawo da ita yafara ajewa closet kafin ya tube ya fada toilet. Wanka yayi tareda alwala yafito sanyeda bathrobe fara ya nufi gaban mirror yafara tsane jikinsa. Bawani dogon shiri yayiba yagama ya tada sallar magriba da ishai dake kansa. Inayah kuwa suna Isa daki ta zauna kan sofa tana kokarin tsaida hawayenta, Umma yaganah Bata zaunaba tana kallonya daga tsaye tace" Ki nutsu Inayah kisan yanzu bamu kadai bane a gidan akwai mutane, Mahaifiyar majeed ake magana bazance kakarkiba yanzu saidai nace uwar mijinki ce, Bakowane shiga zakina yiba yanzu sbd Bai kamataba, Dacan dakikeyi baa hanakiba sbd mune kadai a gidan Kuma Kinga wancan lokacin Abbinki mahaifinda ya haifeki muke mgn Amma yanzu hakan zai iya saka wani abin daban Musamman agaban hajiyarsa sbd yanzu Kam mahimmancinta yafi na kowa da komai a gunsa... Shiru Inayah tayi Jin abinda umman tafada Kuma ya taba zuciyarta sosai dahar take sake Jin zafi da ciwon rashin zamanta jinin Abbin. Har umma yaganah ta fice shiru take tana kokawa da 'dacin ranta na cewan yanzu akwai Wanda yafita matsayi gun Abbinta. Hawaye taji suna neman cika idonta na kishin hakan itama, Saidai duk matsayin hajiya agunsa batajin nata matsayin itama zai sauka sbd Abbinta ai yanzu harda mijinta ya Zama Dan haka itama matsayinta biyu akansa bazata yarda a qwace Mata matsayinta na Yar gatan Abbinta ba Kuma ai itace sanyin idaniyansa kaman yanda kowa yasani Dole itama Haj umma tayarda da itace Yar lelen Abbi. Ranta a cunkushe ta dauki wayarta dake ringing taga sunan anty Hafsat ta dauka tana farawa da cewa" Anty Hafsat Abbi yadawo, Amma yanzu Haj umma ce..... Tareta anty Hafsat tayi da cewa" Ashe tashin hankali yaqare tunda yadawo Kuma ya tadda hajiyarsa Fatan dai Kun taru Kun tayasa Murna? Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa" Eh mun Masa Murna sosai ai tun baima dawoba kinsani. Sanyi jikinta yayi ahankali tace, Yanzu anty Hafsat Abbi zaifi son Haj umma akaina ko? Murmushi Anty Hafsat tayi tana tausasa murya tace" Inayah mahaifiyarsa cefa, Tayaya bazaifi Sonta akan kowaba? Ai uwa ba Wasa bace, Kema Taki uwar duk abinda tayi haka zakiyi hakuri ki rungumeta sbd itama shedan ne kawai yashiga zuciyarta bawai Dan bata sonkiba. Banajin haushin umma Hadiza anty Hafsat Amma dai zuciyata tafi kaunar Abbi haryanzu akanta sbd bansantaba, Bantashi da kauna ko soyayyar uwaba saita uba Wanda kaunarsa ta ginu araina shi kadai tun ina qanqanuwa, Abbina Ni kadaice tasa Amma yanzu da hajiyarsa tadawo yafi Sonta akaina. Kasa cigaba da magana tayi Tai sallama da Anty Hafsat din ta jefar da wayar. Zubbi ce tai knockin tashigo dakin cikin kulawa tace" Umma yaganah tace kifito zakuci abincin kowa yafito. Gyada Mata Kai kawai tayi a gundure tace" Kije am coming. Bayan fitar zubbi Saida ta dauki mintuna tana danne damuwar zuciyarta kafin ta miqe ta nufi closet dinta ta dauko dogon wandon Burberry kawai ta saka batareda ta sauya rigaba ta fita. ##MAMUH# ##LOVE/ROMANCE/A&I *_ZAFAFA BIYAR_* *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_46_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Tana fitowa Kai tsaye dining room ta nufa jikinta sanyaye da sabuwar damuwar data saukar mata arai. Da kallo suka bita data iso sbd ganin Bata sauya kayanba kawai dogon wando ta Sako ta suturta dogayen qafafuwanta dake bude a fili dazu. Zama tayi ahankali batareda tace komaiba. Drink din da Umma yaganah tazo dashi daga kitchen ta ajiye kan table tana cewa" Inayah kije ki sanarda MAJEED table yazama ready. Tanajin haka ta miqe har lokacin jikinta a sanyaye ta juya Zata tafi saiga qamshinsa yafara isowa take tasan yana hanyar shigowa ta dakata tana kallon kofar. Reebok hoodie wears ne ajikinsa farare sai black Valentino slippers. Fuskarsa fresh as usual kaman sabon saurayi ba damuwan komai saidai nutsuwa da sanyinsa daya Riga ya kama rayuwarsa tun barinsa gida Dan haka wannan walwalar da faran faran ba lallai yadawoba. Inayah ya kalla da fararen idanuwansa take yagano sanyinta. Ajiyar zuciya ya sauke a Dan takaice kafin ya kalli qafafunta yaga ba safa ga kayanta dai ba wani na arziki bane. Da kulawa yace" Menene Kuma yanzu kike Bata fuska? Ba nace abar kukan hakaba? Biyosa tayi tana sake marairaice murya tace" Abbi ni haryanzu Banga ka yafemun bane ai to. Da nutsuwa yace" Saikin Dena yawan kukan Nan da Kuma Jin maganar umma yaganah. Zama sukai a dining Haj umma na kallon 'danta tana Masa adduar kariya daga mugun Ido da mugun Baki sbd 'dan nata tubarkallah yakoma Mata tamkar ba itace ta haifesaba fes kaman Dan baqaqen larabawa. Cikin girmamawa ya sake gaidasu Haj umma kafin suka fara cin abincin. Inayah ta zuba Masa abincin iya yanda tasan yanaci sai gashi ko farawa baiyiba Haj umma tace" Majeed ko abinci bakaci sosai kenan yanzu? Murmushi yasake ahankali Yana diban brown rice din yakai bakinsa yace" Kusan komaiba ya canja umma ai. Murmushi tayi itama tana cewa" Duk da hakan Bai kamata kana Wasa da abincinba duk busy din dazaka Zama kuwa, Yaganah haka kuna kallo yake Wasa da abinci? Wani rolling da Ido Inayah tayi cikeda mamakin zancen hajiyan tace" Abbi da daddare ne bayacin abinci sosai Amma ba ranarda Zan bar Abbina da yunwa tun dama can.... Dangwalar cinyarta umma yaganah tayi alaman tayi shiru Amma hakan kawai takejin bazata Bari Haj umma ta nuna tafiya son Abbinta ba. Cikin nutsuwa da kulawa Abbi yace" Keep quiet Inayah. Ba abinci kike ciba har kike tsayawa zance. Bakin nata ne ai Ni Naga gabaki daya kaman bakwa kwabarta, Kaida yaganah Kun taru Kun sangartata qatuwar budurwa kaman wannan da ta Isa ace tuni tana gidan miji Amma tana zaune ka Gama tabarar da ita magana daya biyu sai kuka, Wannan ma banajin likitar gaske ce Dan ko kanta Bata Gama saniba bare marasa lafiya. Shiru dukkaninsu sukayi suna sauraron jininin hajiyar wadda sangartar Inayah tafara isarta Dan kaman MAJEED din yagama shiriricewa akan 'yar Sam Baya wani tsawatarta. Inayah kuwa raurau tayi da Ido tareda kallon Abbin zatai magana da fararen idanuwansa yayi Mata alaman tayi shiru kartayi magana. Hadiye maganarta tayi tareda kokarin miqewa Zata tafi sbd abincinma ya isheta Dan dama Bata wani Jin yunwa sbd ranta dake cunkushe. Come back here Inayah, Ina zaki? Kinfara Wasa da abinci ko? Zauna kici banason wannan shirmen naki, Haka Zaki ringa fushi da abinci idan anmiki fada? Zauna banason Jin komai agurin. Dawowa tayi ta zauna tareda fara cin abincin batareda tace komaiba saidai ranta yayi sanyi da Abbinta ya nuna haryanzu kulawansa akanta yana Nan fiyeda komai. Murmushi tafara sbd takasa boye farin cikin hakan ta dago tana kallonsu Haj umma dakecin abincin cikin mamakin majeed Amma dai batace komaiba. Anty juwairiyyah kuwa cewa tayi" Zaa fara kenan¿ Dan kuwa ita dama wuri Zata wuce bazata zaunaba taga alaman MAJEED din yanzu yafi qarfin reni duk da Yana qaninsu, Dukiya kuwa idan akace a miqa Masa gadonsa arzikinma yawa zai Masa Dan duk tarin gadonsa ba komai bane akan tasa dukiyar daya tara da guminsa saidai abin takaici da baqin ciki kusan duk yawancin dukiyar sunan Inayah ne akai, wannan Inayah dai tazamar musu qarfen maqoshi tun ba'aje koinaba. Koda aka Gama cin abincin Abbi na miqewa ta miqe ta goge Baki da tissue ta bisa zuwa palonsa kaman yanda suka Saba kafin taje ta kwanta. Suna Isa palonsa ya zauna tareda daukan remote ya kunna tv Ta qaraso ta zauna gefensa tana cewa" Abbi bakace ka yafemunba? Waiwayowa yayi kalleta dakyau ganin harda Rama tayi duk tabi ta Hana kanta nutsuwa kwana biyu cikin kulawa yace" Tunda kince kindaina shikenan na yafe lefin Amma yanzu tunda umma tana Nan zakina Kama wannan bakin naki karki yarda naji kina Mata maganganun dakikeyi gaban umma yaganah sbd ummana Bata daukan shirme. Kinji,right? Gyada Masa Kai tayi ahankali tareda cewa" Anan Zata zauna taredamu daga yanzu? Gyada Mata Kai yayi ahankali idonsa na kan tv. Turarenta ne yaketa son damunsa sbd kansa na Dan ciwon gajiyan tafiya Dan haka ya juyo yace" Ok kije kije kiyiwa ummana Saida safe kije kiyiwa ummana yaganah ki wuce ki kwanta gobe Zaki koma aikinki. Bata Masa wani musu Dan haka ta miqe tareda yimasa saida safe ta wuce dakin Haj umma Tai mata Saida safe ta wuce gurin umma yaganah tasake rage darenta acan kafin ta wuce bedroom dinta tana shiga ta zare dogon wandon data saka ta nufi toilet tayo brush da sauran abinda zatai ta fito ta kwanta. Washe gari tun bayan sallar asuba data koma ta kwanta Bata farkaba sai 9 na safiyar, Wanka tafara Yi ta shirya tafito sanyeda dark green fitted jallabiya da qaramin black veil nade akanta sai handbag da wedges takalmin Chanel. Fuskarta ba make sbd Bai wani dameta Amma sai tasaka eyeliner da lipbalm Shikam qamshi ba'a ma maganarsa Dan kuwa Sam ta manta da cewan aurene yanzu akanta saka Turaren haramun ne gareta idan Zata fita. Tana fitowa Palo Kai tsaye hanyar palon Abbinta ta nufa duk da tasan lokacin Yana wuya idan ba bacci yakeyi ba idan har ba fita yayiba to a irin wannan lokacin bacci yake komawa bayan yayi geamin. Baya Palo Yana bedroom dinsa Dan hakanta juya ta fito tana waya da Neesah data Isa gida lfy. Dakin Haj umma taje ta gaidata da Anty juwairiyyah wadda har lokacin Bata wani sakar Mata fuska sbd ganin taqi zuwa daki ta rufe kanta tayita kuka ita uwarta ta yarda ita ta gudu Wanda ita Kam Sam bataga abin Kuma garetaba Dan hakan yafaru sbd Allah Bai bari ta tagayyaraba, Allah yakawo uban daya Zama gatanta fiyeda masu uwa da uban Dan haka bazataiwa Allah butulciba tayita kukan akan hakan Dan ita Sam lamarin Bai wani damu zuciyarta ba babban abinda zai damu zuciyarta shine abinda zaisa ace zaa rabata da Abbi Takoma hannun uwarta wadda har lokacin takasa Jin shauqin dawowarta gareta, Ta jima tana fatan ganin uwar data haifeta saidai Bata taba tunanin ta hakan uwar Zata bayyana garetaba Dan a tunaninta Abbi da koma wace uwar tata suka haifeta. Tea Tasha sai plantains da kwai ta goge bakinta ta fito da key din motarta a hannu ta fada mota ta fice zuwa asibiti. Tana parking motar Dr Abdul na parking gefen tata. Fitowa tayi Tata motar riqeda Jakarta da Lcoat dinta a hannu tana kallon motarsa. cikeda mamaki take kallon Dr Abdul daya fito motar shirye tsaf kaman bashiba Amma yayi Rama sosai wadda take bayyanarda quncin da zuciyarsa take ciki har lokacin shima Kuma yau din yadawo aiki... Kallon kallo sukai kowanne yarasa abinda zai fara cewa Dan uwansa.. Umma Hadiza ce tafito daga cikin motar daga bangaren drivern motar da alama itace takawo Dr abdul din aiki. Kallon umma Hadiza din takeyi sosai idanuwanta a sanyaye harma da jikinta da yayi sanyi da ganinsu lokaci daya. Mahaifiyarta,uwarta data haifeta itace wannan agabanta Kuma itace ta Haifa Dr Abdul dinta. Maida kallonta tayi kan Dr Abdul din dashima ita yake kallo tuni. Ahankali ta bude Baki murya a sanyaye da nutsuwa tacewa Umma Hadiza" Good morning. Hadiza dakejin kaman ta janyo Inayah ta rungume cikin jikinta ta qanqame taji dumin yarta daqyar ta bude Baki kwadayin Jin yarta ajikinta a fili tace" Inayah kin tashi lfy? Ya kike? Ya umma yaganah? Lafiya kalau" ta amsa a takaice sbd Batasan me zataceba. Dr Abdulsamad ta kalla a hankali ta furta Masa gaisuwar shima. Kasa amsawa yayi Saida umma Hadiza tayi saurin tabasa tana cewa" Abdulsamad karkayi haka Shedan ne zaiyi Wasa da tunaninka yakaika ga aikin kunya da danasani, Inayah Yar uwarkace anyita maimaita maka Dan haka yimata kallonda ya fita Sharia zai kaika ga hanyar 'batane. Inayah najin haka ta juya ta silale ta wuce tabarsu agurin tanajin wani iri na gata ga mahaifiyarta da Dan uwanta Amma ba a yanayi na dokin junaba da maraba da juna. Bata sake ganin Dr Abdul dinba harta tashi aiki sbd Bai nemetaba itama batasan yaya zasu iya tsayawa su fuskanci junaba kaman da Dole sai zuwa gaba idan kowannensu yasamu ya Gama rungumar wannan Al'amarin tukuna. Sai 3 tadawo gida a gajiye Dan haka kaman yanda ta saba Bata Shiga da kayan data dawo asibiti dasu dakinta Musamman idan tayi aiki sosai a ranar. Kai tsaye hanyar gefen kitchen dazai kaita dakinsu zubbi ta tsaye ta zare nadin kanta tareda bawa zubbi Jakarta da takalmi takai Mata daki ita Kuma ta tsaya ta zare doguwar rigarta agurin Takoma daga ita sai dogon skin tight dake jikinta black da black singlet data kwanta jikinta dakyau. Kitchen tashiga tana amsa gaisuwar Salimat suna Dan fira sama sama ta wanke hannuwanta ta dauki ruwan roba ta fito tana Sha ta nufi dakin umma yaganah suka gaisa ta fito Zata wuce dakinta saikuma ta juya ta nufi dakin Haj umma itama ta gaidata kafin ta shige. Kai tsaye dakin ta shigo tana rufe robar sauran ruwan datasha. Abbi da Haj umma da Anty juwairiyyah ne suka juyo dukkaninsu atare suna kallonta. Ba damuwar komai tace" Haj umma Ina wuni? Ya jiki jiki? Anty juwairiyyah Ina wuni? Tare suka amsa kadaran kadahan. Gun Abbinta ta maida kallonta tareda sakin qayataccen murmushin farin cikin ganinsa tayo gurinsa Kai tsaye tana cewa" Abbi kana gida ashe yau. Da sauri Haj umma ke kallonta ganin da gaske gurinsa ta nufo din da shegun kayan dake jikinta Wanda zallan shape dinta suke bayyane Musamman shafaffen cikinta dayasa kirjinta dake cikin push-up bra fitowa dakyau. Abbin kuwa Jin yayi kunyar ummansa ta kamasa da sauri ya miqe sbd fita da Inayah din saidai Yana miqewa tana qarasowa ba damar dakatawa sbd tariga ta qaraso ba tsammani kirjinsu ya hadu. ##MAMUH# #LOVE/ROMANCE #AA/AYSHATOUH INAYAH. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/7, 11:34 AM] +234 805 800 0496: *_47_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Firfito da idanuwa Haj umma tayi tana dauke kanta daga kallonsu batareda tasan tayi hakan sbd rudewa. Anty juwairiyyah ma dauke kan tayi tana shafawa Al'amarin Inayah Ido Kuma daga Nan. MAJEED Daya riqe balance dinsa da kyau sbd kiris yarage su Fadi har ita cikin yanayi na kokarin daidaita kansa da 'dan fada a shaqe yace" Inayahhh,,,me ke damunki ne? Ki nutsu mana... Matsar da ita yayi daga jikinsa batareda ya kalli kowaba yaja hannunta suka fice dakin. Itama kasa cewa komai tayi sbd Batasan yariga ya tasoba kodata iso idonta nakan Neman Inda Zata ajiye robar ruwan hannunta Dan haka ba zato tajisa ya miqe Bayan tariga ta iso dad dashi. Suna fitowa Palo su zubbi dake gyaran yamma da sauri suka sauke Kai qasa daga kallonsu. Umma yaganah data fito lokacin taci Karo dasu Yana gaf da shigewa da ita dakinta tabisu da Ido cikeda mamaki sbd ita kanta Batasan Yana gidaba alokacin. Tsakiyar bedroom dinta ya tsaya da ita tareda dakinta ahankali ya dago Yana dauke idonsa daga kan jikinta da kayan jikinta suke lafe cikin yanayi na Dan fada yace" So nawa Zan fada Miki kin girma ki ringa nutsuwa? So kike Haj umma tayita Miki fada tunda bakya ji ko? Meye hakan kike sakawa kina yawo cikin gidan bayan akwai mutane yanzu... Sanyi jikinta yayi shikenan ita yanzu Abbi fada zaita yimata komai tayi tunda Haj umma bataso, Ta saba yawo da qananun kayanta na Shan iska acikin gida ko yananan Amma yanzu shikenan sbd Haj umma Abbi fada yake Mata. Zuciyarta taji tayi sanyi har idanuwanta suka nuna hakan Jiki a sanyaye tace" Kayi hkr Abbi bazan Kuma ba. Juyawa yayi zaibar dakin saikuma ya dakata batareda ya juyoba sbd yanajin kukan datakeson yi ajikinsa Dan yasan halinta Sarai. Ajiyar zuciya yayi Bai juyo dinba sbd tana ganin ya juyon Zata fara hawaye Dan sauya Masa ra'ayi. Kofa ya nufa ya fice yabarta da kayan jikinta da dakin dasuka Dan dauki kamshinsa. Hawayen dataso saukewa agabansane suka gangaro Mata zuciyarta na Mata nauyi Dan kuwa komai na sake tabbata Haj umma Zata wargaza duk wani matsayinta agurin Abbinta. Daqyar ta iya lallaba kanta ta nufi toilet ta tube ta shiga ruwan zafi a bathtub ta lafe tanajin rashin Dadi a ranta. Tajima a toilet din kafin ta fito daureda towel blue fuskarta ba wata walwala. Neu Oil kawai ta shafa tareda spray da mist kadan ta saka free doguwar Riga har qasa Mata nauyi da qaramin hannu tayi sallar la'asar tana idarwa ta koma kan gadonta ta kwanta tana Dan dudduba wayarta kafin ta ajiye tana rasa meke Mata Dadi. Karshe tashi tayi ta nufi dakin umma yaganah acan yayi kwanciyarta tayi baccin yamma na kusan mintuna arbain zuwa awa daya kafin ta tashi. Sallar magriba tayi ta sauya kayanta zuwa Rigar sweater da wandon jeans ta saka babbar jacket coat da qaramar hijab iya wuya ta fito riqeda wayarta sai key din motarta Zata tafi asibiti Dan tana leqawa wasu lokutan da daddare. Umma yaganah ce kawai tasan fitarta Dan abbin baya gida Dan haka tana fitowa Kai tsaye ta wuce ta shiga mota ta fice. Ta Dan samu wasu patients Dr Abdul dayake asibitin shima yanata fama dasu dayar anmata aiki Amma kaman ta jiwa kanta ciwo gurin yunquri Mai qarfi dayan Kuma jininta yayi qasa sosai gashi likitoci da nurses na fama da ita taqi tsayawa a qara Mata jinin. Wannan aikin yasa ta tsaya asibitin har kusan qarfe goma batareda Tama lura da time ba. Suna gamawa taje ta wanke hannuwanta ta fito tareda zaro wayarta dake aljihun jeans dinta taga misscalls na Abbi kusan guda shida dana umma yaganah guda biyu sbd wayan a silent take. Ya Salam" ta furta a gajiye tana saka Kiran Abbi. Harta Isa mota ta bude Bata samu Kiran yashigaba Dan haka ta ajiye wayar gefenta ta tada mota tabar asibitin. Tana shiga harabar gidan Abbinta tafara hangowa tsaye Yana waya da alama fita zaiyi sbd harda key din mota a hannunsa. Jallabiyace milk a jikinsa duk da dare ne tana iya hango yanda jallabiyan tayi Masa kyau kaman wani Dan matashin black Arab. Duk wadda ta auri Abbinta tasamu the best miji..... Au itace matansa ko? Yanzu Abbinta shine mijinta? Wani murmushin farin ciki tasaki a fili tana cewa" Koba komai dai tariga ta alaqantu dashi har abada Dan haka Haj umma matsayinta daban nata dabam. Da farin ciki kan fuskarta kan fuskarta ta fito sbd mood dinta daya sauya take sbd wannan tunanin datai na tuna shi din fa mijintane itace matarsa. Gurinsa ta nufa tana sake kallon kyakkyawar fuskarsa dako yaushe take cikeda kwarjini da kaunar 'yarsa akai. Cikin yanayin shagwaba tace" Abbi kayi hkr banji kirankaba wayan na silent kuma hankalinmu ya dauki akan wata patient... I'm sorry Abbi""'ta qarasa cikin wani yanayi na sangarta. Kashe wayar dayake yayi batareda ya gamaba sbd can bangaren anajin abinda take fadan. Kallonta cikin idanuwanta yayi yaga gajiyan dake tareda ita ya sauke numfashi kadan tareda cewa" Idan ba call duty zakiyiba ki Dena kaiwa dare haka a asibiti Idanma Yakama kinyi daren ki kirani Zan daukoki da kaina..na soke tuqin dare da fitan daren Nan ke daya. Murmushi tasake tana kallonsa tace" Ok Abbi. Ciki suka nufa tana basa labarin aikin dasukai da daren. Kaman yanda ta saba suna shiga ta aje wayarta da takalmanta tareda zare Jacket coat dinta ta miqawa zubbi data bude musu kofa. Kokarin balle maballan rigarta takeyi sbd tanada singlet aciki sukai Ido biyu da Abbi Wanda ya dauke kansa Yana Dan kame fuska yayi gaba batareda yace Mata komaiba. Tunowa tayi da fadan dayayi Mata dazu akan hakan Dan haka ta fasa cirewa ta nufi dakinta tana karban wayarta da sauran kayanta. Wanka tayi ta saka kayan bacci masu santsi Riga da wando ta haye gado daga kwance tayi addua sbd ta gaji sosai take bacci ya dauketa. Washe gari Bata fita aiki da wuriba sbd ciwon Kai data Dan tashi dashi na lattin bacci. Tana fitowa a shirye palon Abbi ta nufa Kai tsaye. Shima a shirye ta samesa zai fito sai qamshinsa Mai sanyi yake zubawa ta zubawa fuskarsa idanuwa tana tunani wahalhalun dayasha da gwagwarmaya akansa take taji idanuwanta na cikowa da hawaye zuciyarta na qara cuduwa da kaunarsa Mai girma. Jin shiru yasanyashi dagowa daga wayarsa dayake dauka ya kalleta a natse. Ganin yanayinta da irin kallon datake Masa yasashi Dan kame fuska Yana nufan kofa yace" Tsayuwar me kikeyi kina lattin fita aiki. Bayansa tabiyo tana cewa" Good morning Abbi. Dan juyowa yayi ya kalleta murmushin fuskarta Bai tafiba saima qaruwa da yayi Da mamaki yace" Are you okay? Kinada labari Mai dadine kike Jin dadi. Ba zato ta riqe hannunsa tana cewa" Abbi farin ciki nakeyi ganinka kawai. Dakatawa yayi batareda ya juyoba ganin su haj umma dasu umma yaganah dasuka fito rakiyar anty juwairiyyah da Zata wuce. Kallonsu kowa keyi sbd umma yaganah batama San ta tashiba harta shirya ta nufi gurin Abbin, Itakuma Haj umma mamaki takeyi meyasa haryanzu wannan 'yar batada kunya ko tunani. Ahankali ya zare hannunsa Yana Dan kokarin basarwa cikin nutsuwa yace" Harkin shirya kenan anty juwairiyyah? Muje na ajeki airport din saina wuce. Haj umma Inayah ta kalla cikeda kulawa asake tace" Ina kwana Haj umma? Anty juwairiyyah Ina kwana? Tafiya zakiyi yanzu? Bazaki zaunaba kema kaman haj umma. Janyota umma yaganah tayi gefenta tana matse hannunta qasa qasa tace" Kiyi shiru idan bakisan abin fadaba Inayah. Abbin da duk yabi ya rasa abin fada tayi ganin harda Haj umma zaa ta baro gurin umma yaganah tana cewa" Abbi zanbiku a ajeni asibiti na kwana akan hannuna ciwo yakeyi bazan iya driving ba. Da kulawa ya juyo Yana kallonta a natse yace" Wat? Shine kike tsaye anan tun dazu kina surutu? Umma yaganah ta shafa Miki balm kafin kifita ki zauna Charles zaizo yakaiki asibitin. Shiru tayi tana kallonsa Jin bazaije da ita dinba. Qin kuma kallon Inda take yayi ya nufi kofa Yana cewa su Anty juwairiyyah su fito. Anty juwairiyyah ce ta kalleta tana cewa" To saina Kuma dawowa Inayah, Allah yabada zaman hakuri. Amin" umma yaganah tace cikeda sakin fuska tana Mata Allah ya kiyaye har kofa. Suna ficewa tadawo gurin Inayah tana cewa" Da gaske kike ciwon hannun muje na shafa Miki ko rub kokuwa wani sabon halin kuka samu keda Neesah na hakan? A dungure tace" Kaina ne keyi yanzu ba hannunba Na wuce saina dawo. Tun su abbin Basu Gama ficewaba itama ta fito da tata motar ta fice da gudu ta wucesu Yana kallo Bai nuna yaganiba Amma hankalinsa ya rabu da tuqin nata kusan zuciyarsa kasa samun nutsuwa tayi su umma na gani yabi hanyar databi yayi dogon zagaye dasu har Saida yaga isarta asibiti lafiya ya wuce dasu airport batareda yasan da suna lureda uban zagayen dayayi dasuba Dan ganin Yar gaban goshinsa ta Isa aiki lfy. Suna Isa airport ba wani Bata lokaci anty juwairiyyah ta shige sbd lokacin zasu tashi. Gida yadawo ya ajiye Haj umma ya wuce aiki. Gidan yau yaqara yin tsit sbd anty juwairiyyah cema keda Yar hayaniyar wayoyinta da jama'ar kasuwancinta. Da wuri tadawo yau Dan tare sukaci abincin Rana da ita Tana Gama cin abincin Rana ta koma daki Dan tanada vid conference call dasu Neesah da wasu abokan karatunta da zasu qarawa juna sani akan aikin nasu Wanda sukeyi akai akai sbd da yawan wasu sunfi wasu qwarewa Musamman su dasuke Dan saka shiriritata itada Neesah. A daki taqarasa wunin ranar tana conference din da abokanta saidatai sallar magriba ta fito sanyeda kayan Shan Isa gashinta a daure tsakiyar kai kaman wata Yar baby sbd fatarta daketa daukan idon hutu da gyaranta na aure da haryanzu yakeda saura. Palo ta zauna gurin su Haj umma dake Dan fira sama sama da umma yaganah wadda wadda yanzu Ta Kama kanta a abubuwa da dama gidan sbd Haj umma dake nuna matsayinta na uwar maigidan. Suna zaune palon Abbi yadawo yashigo idanuwansa akan Inayah datake kwance jikin umma yaganah kaman Mara lafiya. Gaisawa yayi dasu dukan kafin ya wuce palonsa zuwa bedroom dinsa sbd a gajiye yake. Wanka yafarayi yayi ya saka pradas na Shan iska ya zauna Yana duba sauran aikinsa acikin iPad Yana Dan amsa waya akai akai. Lokacin magriba nayi suma duk suka tashi zuwa dakunansu sallah. Sai qarfe 7 da mintuna suka hallara dining cin abinci. Yauma kusan Haj umma nunawa tayi baa kulawa da majeed din yanda yakamata Dan haka da kanta taqara Masa salad akan Wanda Inayah ta zuba Masa Kuma ya nuna Jin dadin hakan a taqaice sbd haryanzu yakasa sakewa yakoma yanda yake ada gaban mahaifiyar tasa itama Bata damuba sbd tasan sai ahankali ko wannan sabo da shaquwar tasu ta dah Zata dawo sbd shekaru kusan ashirin da hudu zuwa da biyar ba wasaba. Fira taringa jansa cikin kulawa Yana amsawa shima cikin kulawar, Inayah da umma yaganah Yan kallo da saurare suka koma Karshe dai haka inayah tagama ta tashi ta komawarta daki sbd ganin yau ko kallonta Abbin nata baiyiba hankalinsa nakan Haj umma. Umma yaganah ma tariga tashi tabar dining din ganin yau Haj umma Dagaske Jin 'danta takeyi Dan haka kowa ya silale ya shige yabarsu. Babu Wanda yasan lokacinda suka Gama harsuka koma Palo suka qarasa firar acan suka shige. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 0913484810 [11/7, 11:34 AM] +234 805 800 0496: *_48_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Washe gari da wuri ta fita aiki ko Abbi dataje gaidasa bai fitoba wucewa tayi bayan ta kirasa awaya kashe da alama Bai tashiba. Ko yau ta hadu da umma Hadiza asibiti sbd umman hankalinta Bai kwanta da barin Abdul da Inayah dinba batareda ta rakosa tana sake tunatar dashi illar da shedan ke masaba na maqalar Masa da tunanin Inayah. Duk da ya tabbatarwa umma Hadizan zai nesanta kansa da duk wani tunanin daban Amma takasa yarda dari bisa dari dashi, Tasan bazai aikata abinda yafita musulunciba Amma Kuma batason ya shigewa Inayah din sosai sbd ko kadan bazata so a shiga haqqin AA MAJEED ba bayan datasan girmansa da sadaukarwarsa akan Inayah, Ayanzu ko ita data Haifa Inayah din tayi alqawarin dakatar da kanta daga zuwa gunta matuqar ba MAJEED din ya Basu Daman hakanba. Yauma kaman baqi haka suka gaisa da juna saidai har umma Hadizan ta fice Inayah na zaune cikin mota tana kallonta. Fitowa tayi ta nufi ciki tana saka wayarta silent tareda sakawa cikin jaka. Kaman yanda suka Saba kusan tareda Dr Abdul tayi aikin wunin ranar na duba patients Dan haka tafara Jin sakewa dashi kaman yanda suke can farko. Sai yamma sosai yau tadawo Dan haka Bata tsaya koinaba sai bedroom dinta tafada wanka. Tana fitowa sallar magriba tayi tareda saka kayan bacci tayi kwanciyarta a  daki tana Jin ciwon Kai na Dan damunta na gajiya. Ta Bangare Daya jinta takeyi wani sukuku sbd gabaki daya wunin batai magana da Abbinta ba abinda baitaba Kuma baya faruwa a rayuwarta, Abbinta shine abokin firarta akoda yaushe kusan da safe da Rana kusanma dai time to time suke waya idan har baya gari Idan Yana gari kuwa tunda safe saitaga Abbinta take fita hakama kafin tadawo Zata kirasa da darema tare sukecin abinci a dining Kuma tabisa palonsa kafin taje ta kwanta Amma yanzu komai Yana neman canjawa duk sbd auren Nan dakuma zuwan Haj umma. Da zaaci abincin dare Bayan kowa ya zauna zasu fara baiga tafito Kuma yau duk baijitaba shima. A natse ya dago ya 'dan kalli umma yaganah yace" Inayah Bata dawo daga asibiti bane? Tadawo, Batajin dadine kanta na ciwo tun dazu. Baice komaiba ya ajiye tissue din hannunsa tareda miqewa tsaye zai wuce Haj umma ta riqe hannunsa ahankali cikin kulawa tace" Ka zauna, Ina zaka bakaci abincinba? Bari a kuma kiranta. Dan shiru yayi tareda Dan juyowa gefen zubbi dake kokarin ajiye juice data kawo yace" Ki kirata ta fito taci abinci. Idan jikin yana damunta sosai Dr farhat zatazo yanzu ta dubata. Yes Sir" zubbi tace tareda juyawa ta nufi dakin Inayah din. Tana zuwa ta taddata kwance idanuwanta a rufe saidai ba bacci takeyiba waya takeyi da Neesah ahankali sbd batako son doguwar magana yau. Magana sukeyi da Neesah akan damuwarta na abinda yake sauyawa daga rayuwanta da Abbi. Cikin kulawa zubbi tace" Abbinki yace a kiraki kifito kuci abinci. Ajiyar zuciya Inayah sauke ahankali zatai magana Neesha tace" Babes kice bakida lafiya sosai bazaki iya fitaba kodan abbin yanuna Miki kulawansa dakika rasa kwana biyun. Shiru Inayah tayi tana nazarin maganar, Bata yiwa Abbinta Karya sbd Bai koyar da itaba Amma Kuma tanason kulawansa datake neman rasa sbd zuwan Haj umma Dan haka ta amsa shawarar Kai tsaye tace" Babes saimunyi mgn. Kashe wayar tayi tareda ajiyewa gefe ta kalli zubbi a kasalance tace" Zubbi bazan iya fitowaba kaina na ciwo sosai na koshi da abincin. Juyawa zubbi tayi abinta ta isarda sakon ta juya ta koma kitchen. Shiru kowa yayi Haj umma na jiran ganin idan tashi zaiyi. Umma yaganah ma jiran take taga abinda zaiyi. Ajiye spoon din hannunsa yayi yanason miqewa Amma Kuma Haj umma da kanta tayi serving dinsa cikin tsananin kulawa da kauna da maimaicin yaci abincin. Katse shirun Haj umma tayi da cewa" Yaganah Akira likitan dazata dubata Mana tun kafin dare yayi Amma nafisa ran stress ne na aiki kawai may be idan tayi bacci zuwa safe Zata wartsake. Dan yakamata ta saba da duka irin wannan stress din tunda likitace, Kun sangartata shiyasa komai qanqantan Abu take maidasa Babba, Saiga kuna rufe Ido kuna koyar da ita wani bangare na rayuwar Ba'a sangarta da shiririta rayuwar Zata qareba Aure zatayi Batasan kalan rayuwar dazata tadda b...... Tissue din daya goge Baki ya ajiye tareda miqewa Yana musu Saida safe gabaki daya. Umma yaganah ma kasa shiru tayi cikin 'yar Wasa tace" Aure Kam ai tariga tayi saidai ta muyita fama ta nutsu tasake sanin abinda takeyi, Inayah kam dama ai akwai shiririta taqi girma indai tana gaban MAJEED. Aikuwa Dole tasan ta girma tunda majeed din ba zauna zaiyiba zaman jiran tayi hankali, Aure yakamata yasan yayi Dan shekarunsa yanzu yakamata ace yafara Tara Yara Amma gashinan aurenma baisan yayiba Dan shirmen Inayah, Idanma batai hankaliba ai shikam bazai zauna jiran ranarda Zata hankaltuba aure zaiyi manyanta yakeyi ba saurayi yake sake zamaba. Tsit umma yaganah tayi tana sauraron abinda Haj umman ke fada cikeda mamaki da shakka, Me kuma yakawo maganar MAJEED da wani auren yanzu ana zaune kalau, Auren dake kansa yanzuma baigama samun mazauniba a rayuwarsa ake maganar wani auren yanzu? Kenan Haj umma Bata dauki auren Inayah din da majeed aureba sai hanyar dakatar da Hadiza kawai. Jin tayi jikinta yayi sanyi bakuma gurin sauran gurin shigan abinci acikinta sbd maganar Haj umma Dan haka ta Dan saki yaqen murmushi tana yiwa Haj umma din Saida safe ta tashi. Itama Haj umma tagama Dan haka ta miqe ta nufi dakinta Kai tsaye tana sanarda Salimat ta hado ruwan zafin gasa Mata qafafunta. Inayah dake daki tana jiran zuwan Abbinta dubata taji shiru Babu Wanda yazo tsawon mintuna. Sanyi jikinta da zuciyarta ke kokarin Yi matuqar Abbinta baizo dubataba to tabbas yanzu ba kaman dah bane kenan, A sanyaye ta zame ta qarasa kwanciya tana Jan bargo ta rufa. Shigowar umma yaganah ce ta sanyata dagowa a sanyaye ta kalleta. Itama umman jikinta a mace yake Amma Bata Bari Inayah din taganeba ta qaraso tareda Zama gefenta tana cewa" Yaya kan? Ya rage ciwo? Dago kanta tayi daga kan pillow ta kwantar kan cinyar umma yaganah tana lumshe idanuwanta. Ahankali tace" Umma yaganah Ina Abbi? Yana gurin Haj umma ne? Numfashi umma yaganah ta sauke tareda dafa kan Inayahn cikin nutsuwa da kulawa tace" Inayah kina buqatan cire duka wani tunanin MAJEED kada ya kusantu da kowa bayan ke, Haj umma mahaifiyarsa ce wadda duk duniya Babu Wanda yakaita matsayi agunsa, Duk yanda yake tsananin kaunarki idan kina nuna Jin zafi ko kishin kusancinsa da Haj umma Zaki iya jawa kanki matsala, Ki cire tunanin komai ki maida hankali kan aurensa dake kanki Dan yanzu duk wani shashanci ki ajiyesa ki fara sanin aurene akanki. Kuma ki koyi hadiye Abu Dan Allah Inayah sbd banson afara samun damuwa tunda wuri tsakaninki da mahaifiyarsa tunda dai ba zaunawa zatai har abada ananba dole wataran Zata tafi, Nima zuwa gaba kuna fara taramun 'yan jikoki Zan barku ayita kaimun renonsu..koba haka ba? Ko har shirin auren da kukai keda Neesah ya wargaje sbd Abbi ne mijin ba'a aura masu rawar Kai ba.. Da 'yar tsokana ta qarasa zancen tana shafa kan Inayah sbd ta sake Dan tasan Zata iya kwana da damuwa aranta. Murmushi kawai Inayah tayi tana safe lafewa tace" Umma yaganah ai Abbi ma kila ya manta da cewa nifa yanzu matarsace.. Nidai umma yaganah kiyi Masa tuni nifa yanzu ba 'yarsaceba kawai Ni matarsace Dan Allah ya...... Buge bakin umma yaganah tayi tana cewa" Zaki fara ko? Ba nace ki ringa Kama bakinkiba idan bakisan me Zaki fadaba. Umma yaganah fa kinaga ko Dan kallon mace bayamun saina 'yar baby Inayah wadda ta....... Bazakiyi shirunba kenan? Shiru tayi tana hadiye sauran zancen Dan ita idan matsayin Mata zaisa kulawan Abbinta yadawo Mata Zata zabi hakan da sauri. Zubbi ce tayi knocking kofar dakin tashigo tareda Dr farhat wadda taketa zuba qamshi Mai Dadi da adonta na doguwar Kuwait Abaya red fes da ita kaman ba dareneba. Abbi ne yakirata ta taho duba Inayah, Qarasowa tayi fuskarta daukeda murmushi da kulawa tana gaida umma yaganah kafin ta zauna gefen Inayah tana cewa" Oh my baby meke damunki? Abbinki yakira hankalina ya tashi na dauka sosai ne jikin naki, Meye matsalar? Tashi zaune Inayah tayi daga kwancen ta zauna tana cewa" Ciwon Kai ne kawai due to stress na aiki I think, So Inaga dana samu nayi isashen bacci I will be ok by morning. Duk da hakan Bari nai checking pulse naki, Duka wannnan Zaki Saba ahankali ok? Ki ringa samun bacci da hutu sosai. Tea da cake Mai laushi akasa zubbi ta kawo Mata Tasha suna Dan fira sama sama kafin sukai sallama Dr farhat ta fito. Umma yaganah ce takaita har dakin Haj umma ta gaidata. Da mamaki sosai Dr farhat ke sake gaida Haj umma dakyau tana mamakin ba umma yaganah ceba Ashe ta Haifa AA MAJEED. Haj umma itama sosai ta saki fuska suka gaisa da Dr farhat din Dan yanda Dr farhat ta ringa gaidata cikin Jin kunya da girmamawa sosai yasa taga mutuncin Dr farhat din sosai. Bayan tafiyar Dr umma yaganah itama wucewa tayi dakinta ta kwanta. Har Inayah tayi bacci cikin sanyi tana Jin damuwar rashin ganin Abbi. Da safe haka taqi fita aiki da wuri Saida tayi breakfast da kowa. A dining tana zuwa da Abbi tafara hada Ido Yana zaune cikin Navy blue Ralph Lauren suit dasukai masifar yimasa kyau tareda fidda hasken lafiyayyar fatarsa dake cikin hutu. Gabaki daya Qamshinsa ya hadu Dana English breakfast din dake jere a dining ya sauya gurin. Cikin nutsuwa da kulawa da sanyin murya tace" Good morning Abbi. Idanuwanta ya kalla kafin ya dauke idonsa akai anatse Yana cewa" Morning, Yaya jikinki? Complain zatayi umma yaganah ta katseta da cewa" Yaya jikin Inayah? Naji sauki umma, Haj umma Ina kwana? Umma yaganah good morning. Zaunawa tayi tana kokarin fara cin abinci Haj umma tace" Yaya kan? Yayi sauki ko? Eh naji sauki alhmdllh. Fara cin toasted bread tayi tana daukan tea tafarasha. Itace tafara gamawa ta miqe ta Zata fice Abbinta yace tajira zai ajeta asibitin. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_49_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Bai dauki wasu mintinaba ya Gama shima ya goge bakinsa da tissue tareda miqewa yabar dining din A natse cikin sautin Mara qarfi yace" Saina dawo umma. Umma yaganah ya dan kalla itama yace" Saina dawo. Kusan atare sukai Masa adduar adawo lfy. Zaune Inayah take tana chatting sama sama da Neesah dake son Jin labari daga gareta tana ganin ya nufota tafara kokarin saka wayar cikin aljihun skinny jeans din dake jikinta da farar doguwar Riga Mara nauyi wadda gefenta yake yanke daga qasa har gurin qugunta. Cinyoyinta da wandon ya lafewa ya Dan kalla Yana dauke kai kafin ya dakata daga shiga motar ya juyo cikin fada yace" Kije kisa native wear. Kallonsa tayi da sauri tana kallon kayan jikinta.... Me Kuma kayanta yayi? Sake dagowa tayi ta kallesa taga harya shige motar Yana zaune Batace komaiba ta juya Takoma cikin gida ta sauya kayanta zuwa Riga da skirt na atampa dark green da qaramin medium chantley veil ta fito riqeda qaramar Chanel handbag. Gaban motar ta bude tashiga suka wuce. Suna fara tafiya ahankali ta juyo ta kallesa tareda marairaice fuska ta dafa dayan hannunsa dake gefen datake cikin wata sanyayyar muryar shagwabar data Saba yimasa tace" Abbi idan nayi lefi Dan Allah kayi hakuri bazan sakeba. Dan juyowa yayi ahankali ya kalleta da idanuwansa dake sake Jin hawayen shagwaba, Tace please Abbi Dan Allah bazan sakeba. Hannunta ta qarasa dorawa kan hannunsa Ya Dan sake kallonta Tana ganin ya kalleta ta gangaro da hawayen data Tara a Ido tana qara marairaice Masa. Rintse idanuwa yayi ya bude ahankali Yana dauke kai daga kallonta.... Besan yaushe Inayah ta iya wainnan abubuwanba na saurin kuka yanzu Musamman idan tanason Abu daga garesa sbd tasan kukanta shine abu na karshe dazai so a duniya. Ahankali ya sauke boyayyan numfashi cikin kulawa da sanyin lafazinsa yace" Meyasa kike Wasa da abinci? Kina aikin lfy kice bakisan ciwo da dama suna shigaba ta hanyar yunwa? Karna kumajin zaaci abinci kinbada different story daga yau. Okay? Gyada Masa Kai tayi tana sake riqe hannunsa cikin nata. Zare hannun zaiyi tasake riqewa tana cewa" Nacefa bazan sakeba Abbi, Ahaka zamu qarasa ai ni matarkace yanzu Ab.... Wani mummunan burki yaja dasu akan hanya Saura kiris motar bayansu ta dakesu. Kallonsa takeyi da mamaki batareda ta damu da abinda tafadaba cikin kulawa tace" Are you okay Abbi? Juyowa kadan yayi Yana zuba Mata manyan fararen idanuwansa dasuka sata Jin gabanta faduwa a Karo na farko sbd Abbin nata Bai taba zuba Mata idoba sosai Yana kallonta. Koyaushe kallonsa akanta taqaitaccene duk da tsananin kaunar da son dayake Mata amatsayin ubanta. Sunkuyar da kanta tayi ahankali Jin kallon yayi Mata nauyi da karfi ahankali tace" Sorry Abbi. Hannunsa dake cikin nata ya janye ahankali batareda yace komaiba ya ja motar suka wuce. Shiru bakinta yayi sbd tasan ta zaro zancen da umma ke cewa idan batada abin fada ta ringa yin shiru Dan haka tayi shiru Amma Kuma ai Dagaske shi mijintane kodai Abbinta baya Sonta kenan da auren??? Innalillahi wainnan ilaihrrjiun" ta furta a fili tareda dagowa ta kallesa tana Jin kaman hankalinta zai tashi da wannan tunanin. Har suka Isa asibitin Babu Wanda yasake magana Yana parking motar Dr Abdul na shigowa harabar asibitin. Fitowa Inayah tayi tana kallon motar Dr Abdul din kafin tadawo da kallonta kan Abbinta. Bai lurada Hadiza ba dake cikin motar ya sauke glass din motarsa Yana amsa gaisuwar Dr Abdul daya iso cikin girmamawa kaman da can Yana gaidasa. Ba tsammani sai ganin hadiza yayi tana qarasowa gurinsa. Inayah ya juya ya kalla itama shi take kallo batareda ta kalli Inda Hadiza ke tahowaba. Hadiza na isowa cikin Jin kunya da nauyinsa Mai tsanani ta Dan kallesa a sanyaye tace" Ina kwana Abbin Inayah. Daga ita data fada har su duka dake gurin tsit sukai cikin jujjuya zancen. Batareda ya kalletaba cikin nutsuwa ya amsa a taqaice da cewa" Muntashi lfy¿ A natse Inayah ta gaidata tareda kallon Abbin tace" Abbi to waye zaizo daukana idan natashi tunda banzo da motaba? Tada motarsa yayi ya dago ya kalleta cikin kulawarsa da kaunarsa yace" Dr Abdul nasan zai Zama busy May be mamansa idan Bata komai Zata iya maidaki gida, Amma karki biya koina daga asibiti gida direct Zaki koma. Jan motar yayi yabarsu tsaye Inayah nabin motarsa da kallo Umma Hadiza kuwa wanin zallar farin ciki da mamakin MAJEED ne yacikata kenan majeed din ya yarda takai Inayah gida sbd kawai ta zanta da 'yarta.... Tasan bazai iya yafe Mata ko kulata lokaci dayaba Amma ko ahakan ta gode da karamcin. Inayah rasa abin cewa tayi ta kalli umma Hadiza da farin cikinta Bai boyuba tace" Zan dauki drop kokuma na Kira Charles idan natashi sbd Zaki wahala zuwa daukana Kuma ki kaini har gida. No Ayshatouh please kibari nazo na daukeki da kaina Muna buqatan sanin juna Damace Abbinki yabani please. Dan murmushin yaqe tayi tana cewa" Ok Zan tashi 2 yau Inshallah. Zanzo kafin 2 Inshallah. Juyawa tayi ta wuce dama Dr Abdul Bai tsayaba ya wucewarsa. Bayansu umma Hadizan tabi da kallo tana jin farin ciki Mai tsanani ganin yayanta dukasu biyun likitoci ne. Duk da Inayah Bata Gama Zama qwararriyaba Amma zuwa gaba itama tasan Zata Zama abin alfahari gurin marasa lfy dasu iyayenta. Data tuna mahaifiyarta zatazo daukanta saitaji wani iri Amma Kuma ita kanta tanason sanin umman Abdul din. Qarfe daya da arbain kuwa saiga Hadiza ta iso asibitin Dan haka Inayah ta tattara ta fito suka wuce gida. A hanya umma Hadizan keta Jan Inayah din da fira da tambayoyi akan rayuwarta Wanda komai ta tambaya sunan abbine amsar, Anan tasake saddaqarwa MAJEED sbd yariga yayi ginuwar da Babu abinda zai girgizasa Aran Inayah, Shine ciki da Bai din rayuwarta Dan kuwa da ace wani mijin ta aura bashiba zaiyi wuya mijinta baiyi kishinsaba duk da Yana matsayin ubanta sbd kaunar tayi karfi. Kaman daga sama ta jeho Mata tambayar "Ya maganar aurenki da Abbin naki?... Shiru Inayah tayi cikin rausayar dakai tace" Bansaniba, Amma dai Ni aguna tanan bazan taba rabuwa da Abbi ba ko bayason auren nidai inaso yanzu.... Kallon mamaki Hadiza tayiwa Inayar tana tauna zancen, Lallai majeed yagama shagwaba Inayah ta yanda Babu ruwanta duk maganar datazo Mata fada takeyi. Tayaya zakiso auren idan shi baisoba ai Babu au...... Karki min Baki a auren please, Ni inaso Kuma tunda inaso Abbi ma zaiso. Murmushi Hadiza tayi aranta tana cewa" Hmm wanna abbin naki Mai taurin Rai bazai taba kallonki mace ba bare matarda zai iya kwanciyar aure da ita. Suna Isa gida a gate ta ajiyeta batareda tashiga gidanba ta juya ta komawarta. Inayah na shigowa gida a Palo ta tadda Dr farhat tazo sunata fira da Haj umma Umma yaganah Kuma tana kitchen yau da ita ake aikin abincin sbd kwana biyu bataiwa MAJEED abinci da kantaba. Da mamaki Inayah ke kallon yanda har suka Saba a wuni daya daga zuwan Dr farhat din. Gaisawa sukai tana tambayar Dr farhat dalilin zuwanta tace Haj umma tasake zuwa gaidawa da Rana sbd jiya darene Basu gaisa da kyauba. Dakinta ta wuce tayi tube tayi wanka da sallah ta fito sanyeda doguwar chiffon gown Mara nauyi kanta daure da silk scarf. Tunda ta fito itama kitchen ta nufa gurin umma yaganah acan Tasha cornflakes sbd bata iya cin birabisco ba shi sukai da Rana. Da ita aka qarasa aikin tasaka hannu duk da bawani aikin ta iyaba bayan wanke plates da cups sai dafa tea shima Dan Abbinta Nasha sosai yasa ta iya Dole. Daki Takoma ta sauya kayanta sbd batason kamshin girkin dasukeyi. Har dare Dr farhat na gidan da ita sukai dinner tareda Abbi dashima ya danyi mamakin sabonta da ummansa daga zuwa. Gurin cin abincinma haka dai umma yaganah da Inayah suka Zama Yan kallo har aka gama kowa ya tashi. Da Dr farhat Zata tafi har mota ta rakata ta wuce sai yabon Haj umma takeyi itadai Inayah batace Mata komaiba akan aurenta da Kuma Dr farhat din Bata saniba hakama Haj umma Bata Sanar mataba. Kasa bacci tayi Saida ta fadawa Neesah zuwan Dr farhat sukaita maganar kafin ta kwanta. Washe gari Abbi Bai tashi da wuriba Dan haka ta wuce Kuma acan ta tadda umma Hadiza Saida suka gaisa kafin ta wuce. Yauma tana dawowa Dr farhat na gidan yau Kuma wai BP din Haj umma dinne yahau tazo dubowa. Haka takuma wuni dasu sai dare ta wuce. Ahankali ahankali Dr farhat ta maida gidan nasu gurin zuwa fiyeda yanda take zuwa adah, Tayi sabo da Haj umma sosai ba laifi Dan kuwa Haj umma najin dadin yanda take zuwa duba BP dinta akai akai Wanda Kuma a Yan kwanakin tagano irin son da Dr farhat kewa MAJEED sbd hatta kulawar datakewa Inayah Mai girmace duk sbd MAJEED Shikuma baimasan tanayiba. Ta bangare Daya Inayah kwata kwata yanzu Bata wani gane kan Abbinta sbd dukkanin kulawansa Takoma kan Haj umma sbd kwana biyun batajin dadin BP dinta sai hawa yake Yana sauka. Tun suna mamaki itada umma yaganah harsun koma Yan kallo Danma umma yaganah tana kokari sosai gurin dannarta da hanata magana,. Duk tabi Takoma sukuku batada walwala koyaushe a sanyaye take Dan yanzu koyaushe idan dai Abbi na gida to Yana tareda Haj umma wadda yanzune tasan tana tareda kaunar danta tunda ya maida hankali sosai akanta. Ganin hakan yasa Inayah ke dadewa gurin aiki sosai sbd gidan ba Dadi tunda Abbinta baida lokaci sosai. Hadiza kuwa ganin tana samun ganin Inayah a asibiti yasa kusan duk bayan kwana daya saitaje gurin Inayah asibitin su jima suna magana Da hakan tafara sabuwa da 'yarta tunda dama Inayah bamai hayaniya ko riqe Abu bace Ba jimawa tayi sabo da mutum sbd sanyin halinta. Ahankali umma Hadiza ta fahimci abinda ke damun inayah na kishin Abbinta da kowa karya fita kusanci dashi Hakama Sam wannan auren nasu tasan idan akabi ta MAJEED kila ahaka zasu qare amatsayin uba da 'ya. Cikin dubara ta bawa Inayah shawaran ta fadawa antynta Hafsat abinda yake faruwa. Dayake anty Hafsat tayi tafiya jiya tadawo aikuwa da farin ciki ta karbi shawarar. Tana dawowa gida wanka kawai tayi tayi sallar la'asar tayi zamanta adaki zubbi takawo Mata noodles data saka ta dafa Mata da sausage. Wayarta ta fidda ta Nemo numbern anty Hafsat ta saka Mata Kira. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/8, 9:55 AM] Sweet sis: *_50_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ringing biyu wayar tayi anty Hafsat ta dauka tana cewa" Dr Inayah majeed Yar gatan Abbinta Kuma amaryar Abbinta.."" ta qarasa zancen da Yar dariya. Sanyi jikin Inayah yayi tana Jin dadin kirarin Amma Kuma duk wannan yanason kauduwa. A sanyaye tace" Anty Hafsat Yaya gida? Ina my sweet Siyama? Lfy kalau Inayah, Ya kike? Yasu umma yaganah da hajiya? Ya abbin naki Kuma? Bata tsaya amsa gaisuwar yasu umma ba tace" Anty Hafsat Abbina ya canja sosai zuwan Haj umma Kuma umma yaganah ta Hana nayi magana Ni gaba daya Abbina yafara Zama kaman na nawaba. Umman Dr Abdul tace na sauya bangaren Mata Ni banganeba Anty Hafsat kizo gidan kigan yanda muke yanzu duk ba Dadi, Ga Haj umma komai nayi saitace shiriritata da shirme kawai na iya. Yanzu itace Mai kulawa da Abbi fa, Umma yaganah ma yanzu Takoma Yar kallo abinci kawai take Masa. Nidai anty Hafsat wlh bazan iyaba Ina kallo Abbina ya Dena ji Dani kaman da Bayan umman Abdul tace kamata yayi matsayina ya ninku tunda matsayina biyu agurinsa. Numfashi anty Hafsat ta sauke tana jinjina zantukan Dan duk da kusan a shagwabe da damuwa Inayah ke fadan zancen idan ta fahimta Haj umma batai na'am ba haryanzu da Inayah a rayuwar AA MAJEED barema ta dauki auren da mahimmanci. Wani numfashi takuma sakewa tana ajiye ruwan data kawowa CM ta juya ta fice daga palonsu zuwa dakinta Dan bazataso yaji zancen nasuba. Tana Shiga daki ta zauna bakin gado tana cewa" To kodai kina Mata abinda baimata bane Inayah? A sanyaye tace" Wlh anty Hafsat bana Mata komai Kuma Ni bandamu data kaunaceniba Nidai Abbina nakeson ya koma yanda yake kada ya rage ji dani. Inayah duk wannan abin na tabbata Koda qwayar zarra kaunarki da matsayinki a zuciyar Abbinki Bata raguba Bama Zata taba raguwaba qaruwa zatayi sbd har Koda yaushe kece kaman strength dinsa. Kawai dai inaga aurenku ne Bata aminta dashiba sbd ganin kaman bazaki iya kalawa da AA MAJEED dinba kinyi qanqanta.... Aikuwa wlh Ni inason auren yanzu bazaa rabani da Abbi ba, Ko shima Ni Zan fada Masa inason aurena bazan rabu dashiba. Da mamaki anty Hafsat tace" Yanzu Kuma kinason auren kenan? To kinason auren yanzu harzaki tsaya kina kallo auren na Neman fara rawan tun baigama tsayuwa ba, Wannan rashin amintar da Haj umma tayi kome zai iya faruwa Dan kuwa ko auren be rabuba MAJEED Kam zai iya samun matar dazata kular Mata dashi.... Wani mummunan faduwa gaban Inayah yayi ta tashi zaune ahankali dakyau tana cewa" Sai tasashi yayi wani auren anty Hafsat? Shima abbin sai yayi wani auren? Wani mugun sanyi taji Yana shiga qafafunta tayi shiru tana jiran amsar anty Hafsat wadda taji rashin kamatan yin zancen da Inayah Dan haka ta Dan gyara murya cikin nutsuwa da kulawa da rarrashi tace" Idan kika tsaya shirme nake fada Miki hakan kila zai iya faruwa, Dan haka yanzu ki nutsu kema ki ringa kulawa da Abbin kaman matarsa sbd wannan right dinki ne dake Zaki bawa kanki. Kasa cewa komai tayi sbd jikinta daya Gama mutuwa da wani irin tsoro dan kuwa tana fama da zuciyarta akan Haj umma idan Abbi ya auro wata Batasan ya Zata iya dauka. Ganin ta Dena gane abinda take fada yasa Anty Hafsat yimata sallama da cewan Zata shigo gobe Inshallah. Aje wayar tayi hannuwanta na Dan rawar data kasa gane Kota menene. Kasa qarasa cin abincinta tayi ta miqe tareda daukan tray din ta fita zuwa kitchen. Tana ajiye kayan data kawo kitchen kasa juyawa tayi ta tsaya agurin tana shiga tunani Ita gabaki daya kanta ma ya toshe takasa gane komai, Ita Abbinta kawai takeso ita kadai. Juyawa tayi ta fito tana kokarin Isa hanyar bedroom dinta taji Qamshin Boadicea ta dakata sbd tasan Abbinta ne yadawo. Juyowa tayi tadawo palon daidai Yana shigowa sanyeda kaftan Navy blue best kalar dayafi amfani da ita. Ganinsa yasa idanuwanta cikowa da hawaye tanajin wani irin nauyi a zuciyarta da abinda anty Hafsat ta fada dazu. Kallonta ya qaraso yanayi zuciyarsa na tabuwa da kallonda take Masa idanuwanta da Hawaye Wanda yasan na kewansa ne. Ahankali ya bude Baki zaiyi magana ta fada jikinsa ta qanqamesa tana sako hawayenta. Shiru yayi Yana kokarin daidaita kansa sbd ba zatan datai Masa. Qamshin Turarenta na black opium ya shiga hancinsa da kyau Take yaji kansa ya Sara ya bude idanuwansa akanta tareda daga hannuwansa zai zareta daga jikinsa Amma ta ture hannunsa tana sake shigewa jikinsa hawayenta na sake gudu zuciyarta na bugawa da zancen anty Hafsat har lokacin. Maqoshinsa yaji Yana Neman bushewa sbd yanayin yayi Masa nauyi Musamman Haj umma ko umma yaganah wani zai iya samunsu ahakan. Numfashi ya sauke ahankali tareda Dan nutsuwa cikin kulawa yace" Me kikeyi Inayah? Lafiya? Akwai abinda ke damunkine? Taso naji matsalar... Girgiza Kai tayi tana qin sakinsa tace" Abbi Dan Allah karka rabu Dani Ni inason auren.... Wani irin duka zancenta yayiwa zuciyarsa har baisan lokacinda ya rintse Ido ahankali ba tareda budewa zuciyarsa na Neman yin sanyi sbd a bazata yaji zancen. Ahankali ya daga hannuwansa Yakai kan hannuwanta Yana kokarin janyeta kenan saiga Haj umma da umma yaganah kusan atare sun shigo palon kaman aike.... Da sauri Haj umma ta dakata tana kallon ikon Allah lokaci daya tana dauke idonta Kuma. Umma yaganah kuwa juyawa tayi abinta batareda ta tsayaba tana jinjina sangantar Inayah sbd tasan itace me wannan aikin ba Abbin ba. Ganin Haj umma yasa duk yaji yana sake shiga wani yanayi na sanyin jiki ya janye Inayah din zaiyi magana ta sake komawa ta maqalesa tana cewa" Abbi Dan Allah kabarni da aurena zanyi biyayya akan da.... Salati haj umma ta sake tana maido da kallonta kan Inayah dataqi Kota kan idonta tabi. Ba Shiri Haj umma ta kamo hannunta tana janyota gefenta tace" Yaushe zakiyi nutsuwa nikam 'yar nan? Yanzu uban naki kike damuqa haka gaban mutane kina maganar aure. Tashi cikin turawa haukane akace Miki? Maza wuce daki kisan abinda kikeyi Mace da kunya da kamun Kai aka santa. Haj umma idan na Kama kaina to Abbi zai iya auren wata yabarni da wannan auren.. Daga Haj umma har abbin kasa magana sukai sbd zancenta ya mugun Basu mamaki Ya dago ya zuba Mata indanuwansa dasuka sake kashe Mata jiki tanajin kaman zuciyarta Zata fashe akan kishin hada sunansa da wata takuma rabarsa. Haj umma kuwa sake sallamawa Inayah tayi sai takasa cewa komai ta qwalawa umma yagana Kira. Umma yaganah najin Kiran tasan zaa Rina Indai akan MAJEED ne Inayah Bataji hakama Haj umma da alama itama tanada aiki tunda tana cikin uwaye masu kishin yayansu. Umma yaganah na fitowa Abbin na wucewa batareda ya tsayaba Dan baisan mezai iya tsayawa saurara ba kuma. Yaganah meyasa Inayah bakinta baya tauna zance ne? Kunga illar rashin kwabarta Gashinan sai zantuka takeyi marasa kan gado. Cikin nutsuwa da umma yaganah tace" Ya aka iya sai hakuri da addua Haj Inayah din ce akwai kuruciya sosai atareda ita. Fada Haj umma tafara Yi umma yaganah na Bata hakuri aka dai kashe maganar taja Inayah zuwa daki. Bataiwa Inayah fadaba sbd itama zuwa yanzu tafara ganin rashin kyautawar Haj umma saidai Kuma bazata nuna hakan gaban Inayah ba sbd kada taci da ganin rashin kyautawar Haj umma din. Batace komaiba Dan batada abin cewar Dan haka ta juya ta fice Takoma aikin datakeyi kitchen. AA MAJEED na Isa bedroom dinsa zaunawa yayi kan sofa ahankali tareda Dan rintse Ido Yana dafe goshinsa sbd Dan juyawar da kansa keyi. motsawan da zaiyi Qamshin black opium ya Shiga hancinsa daga kayansa na Inayah Dan haka ya miqe ahankali ya zare ya janyo towel maroon ya daura a qugunsa ya nufi toilet Yana Dan sake dafe goshinsa. Wanka yayo yafito ya shirya cikin Kelvin Klein sweatset yana qamshi Mai sanyi ya fito ya nufi masallaci sallar magriba. Tunda tadawo daki haka kawai takasa samun nutsuwa da sukuni tayita hawayenta tagama ta tashi itama tayi alwawala tayi sallar magrib tana idarwa ta dauki wayar Neesah daketa faman kiranta. Sun jima suna waya tana Bata hakuri da qarfafa Mata gwiwa akan aurenta kafin suka kashe. Wanka ta tashi tayi sbd batai niyar fita cin abinci ba tana fitowa ta saka Riga da wandon Balenciaga masu kauri tana kokarin hayewa kujera chatting ta tuna gargadin Abbinta na rashin fitowa cin abinci Dan haka ta miqe da wayarta a hannu tareda zira slippers ta fito tana qamshin black opium Mai sanyi. Tana fitowa ta nufi dakin Haj umma ta Bata hakuri suka fito kusan tare zuwa dining din haj umma na sake nanata Mata ta Dena sakawa ranta banzayen tunani akan MAJEED sbd ubane agunta. Batace komaiba har suka Isa suna Zama saiga Abbin ya shigo cikin nutsuwarsa da kwarjini sai qamshinsa yakeyi komai nasa a kame da nutsuwa. Zama yayi Yan gaidasu umma kafin ya kalli Inayah dake kallonsa cikin sanyi da alaman ban hakuri. Shikenan ya Isa" kawai yace Mata ahankali cikin kulawa. Murmushi tasake tana maida kanta ga abincin da aka dafa tuwon shinkafa da miyar ganye masu lafiya da Naman kaza da kifi. Bata fuska ta danyi sbd Bata cikason tuwoba Dan Haka kadan ta zuba tuwon tanaci da spoon ahankali.. Shima abbin da spoon yakecin tuwon a natse. Wayar Inayah din ce tayi ringing sunan Dr farhat ya bayyana akai ta saki siririn numfashi tareda daukan wayar a gundure tace" Dr farhat I will call you muna cin abinci. Kashe wayar tayi Bata jira amsartaba ta ajiye. Jin Dr farhat ce yasa Bayan ajiye wayar haj umma Dan kallon MAJEED fuska asake tace" Dr farhat nada kokari jiya ta hadani da mahaifiyarta mun gaisa sunada karamci sosai.... Shiru kowa yayi harshi abbin. Jin yanda Haj umma ke yabon Dr farhat yasa Inayah kasa shiru tace" Haj umma Ni kullum fada kikemun Amma kinata yabon Dr farhat, Bayan nice jikarki Kuma.... Da idon umma yaganah tai Mata tsawa tana hanata qarasawa. Murmushi Haj umman tayi tace" Ke dince su yagana sun sangartaki da yawa kin kasa sanin kin girma, Bakisan abinda kikesoba da Wanda bakyaso komai fada kike... Ni yanzu Abbi kawai nakeso bayanshi banason koma.... Qwarewa abbin yayi da abincin dake bakinsa yafara tari ahankali. Da sauri ta dauki ruwan ta taso ta kawo Masa tana cewa" Sorry Abbi,sannu... Matsesa tayi gurin basa ruwan Turarenta yaringa Shiga hancinsa take ruwan suma suka fara kokarin qwaresa ya ajiye cup din Yana daidaita nutsuwarsa yace" Thank you. Kasa magana Haj umma tayi bakinta take ya mutu har aka Gama Babu Wanda yakuma magana acikinsu. ##MAMUH# #HOTLOVE/ROMANCE _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/8, 9:55 AM] Sweet sis: *_51_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Qin wucewa tayi bedroom dinta tabi bayan Abbi Wanda baisan tana bayansa ba Saida yashiga palonsa taji mutum a bayansa Yana juyowa suka hade Saura kadan ta Fadi ya tarota ta dawo jininsa. Shiru tayi tana kallon kyakkyawar fuskarsa dayake kokarin hanawa karban kowane yanayi. Cikin nutsuwa ya zareta Yana cewa" Meyake damunki ne kwanakin Nan Inayah? Murmushi tasake tana kamo hannunsa bayan ya zauna itama ta zauna gefensa tareda shige Masa sosai tana cewa" Abbi Ni bansaniba ko nayi lefi yanzu ka daina ji Dani kaman da,. Ko Dan Haj umma Bata Sona ne?.... Wani kallo ya juyo yayi Mata da idanuwansa dasuka Dan sauya cikin Dan fada yace" Karki Kuma cewa haka, Ki Dena hada matsayinki Dana ummana kowa matsayinsa daban...karna sake Jin hakan a bakinki. Ahankali tace" Sorry Abbi na dena Amma Abbi ai zaka barni a matsayin matarka ko?????..... Rintse idanuwansa yayi da wani irin yanayi na mamaki da fara kosawa da zancen Yaushe Inayah ta Zama haka akan aurene Bai saniba? Bude idanuwan yayi tareda juyowa ya zuba Mata su gabaki daya Yana kallon bakinta da yayi maganar zuwa kirjinta dake harbawa da sama sbd fargabar zancenta Mara control daya sake fitowa bakinta ba Shiri. Farare idanuwanta dake kallonsa cikeda kauna Mai girma ya maida NASA idanuwan Yana kalla.... Hannunsa dake cikin nata takuma kamawa tana kallonsa a sanyaye. Kasa cewa komai yayi Yana kokawa da tunanika dake yawo akansa Yana kokarin kwantarda kansa. Ahankali ta furta sunansa cikin wata kasalalliyar murya wadda ta sanya tsigar jikinsa tashi sbd numfashi Mai dumi data furzo a fuskarsa bayan Kiran sunan nasa. Ganin har lokacin baice komaiba sai idanuwansa Daya dauke ahankali daga kanta Yana maidawa kan tv Dake kunne. Ahankali cikin seta murya yace" Haryanzu maganar aure Bata fita bakinkiba Inayah. Yanda yayi magana da wata shaqaqqiyar murya yasa jikinta mutuwa itama ta kwantar da kanta a kan hannunsa tana cewa" Abbi Ni naka auren kawai nakeso yanzu ai. Sake danne numfashinsa yayi Yana basarwa. Sosai tayita yimasa fira wadda duka yawanci shagwabane ta ringa zuba Masa wadda tagama take neman lalata kamewarsa da wuce tunaninsa akan yanda Inayah din take abubuwan dabaisan a Ina tasaniba. Tana tafiya dakinta ya miqe ya nufi toilet din bedroom dinsa Kai tsaye ya sakarwa kansa ruwan dumi Yana lumshe idanuwansa dasuka sauya Yana sake riqe kansa da kamewa. Ita Kam tana komawa daki sallar ishai tayi zuciyarta cikeda farin cikin yau tayi fira da Abbinta kaman da Tayi Shirin bacci ta haye gado tayi kwanciyarta tana jin yanayi Mai qarfi fa girma a zuciyarta gameda Abbinta Wanda takejin yanafin na dah. Washe gari fes ta shirya cikin haricca long knitted skirt and blouse milk sai vincci loafers ta fito ta wuce aiki Bayan taje ta gaida Haj umma Umma yaganah Kuma tare sukai breakfast Abbinta Kuma Bai fitoba da alama Bai tashiba. Agurin aiki yau ma umma Hadiza tazo sunyi fira sosai kafin tadawo gida. Tun a harabar gidan tasan anty Hafsat tazo sbd taga motar CM daya. Batai tsammanin samun harda dr farhataba a gidan Dan haka duk fitarta da Anty Hafsat Basu wani samu sinyiba gashi Haj umma ta cika kowa da kulawarta akan Dr farhat wadda itama sosai take nuna Jin dadin hakan Dan tasan tagama samun guri a gun AA MAJEED. Har dare Basu samu sunyi maganaba yanda ya kamata saidai sama sama anty Hafsat din tasake nanata Mata akan itace Zata gyara aurenta yazama kaman kowanne aure da kanta. Bayan tafiyar anty Hafsat da Dr farhat rasa abin kamawa tayi saidai ta shiririce gurin waya da Neesah wadda suka qarasa shiriricewa akan firarrakinsu na Yan Mata yanda suka Saba. Sallar ishai tayi ta fito zuwa dakin umma yaganah sbd sunci abinci already tun dazu taredasu Anty Hafsat. Tana Shiga dakin zubbi tace" Abincin Sir yazama ready zaa aje a dining ne kokuma zaa kai Masa dakin Haj umma? Ko a palonsa zaa Kai? Kallon Inayah umma yaganah tayi daga zaune tace" Kije ki Kai Masa palonsa basai an jera a dining ba. Fitowa tayi tareda zubbi batareda taje dakinta ta sauya kayaba ta dauki qaramin tray din da tea ne akai sai faten dankali dayaSha kayan ciki da curry. Kai tsaye palonsa ta nufa da tray din tana shakkar kada abbin yayi Mata fadan kayan jikinsa sbd akwai sanyi gashi Riga da wandon baccine ajikinta masu santsi Kuma wandon ba har qasa bane ko bra Babu ajikinta. Tana shiga palon sanyin AC daya Gama gauraya da turarensa ta shaqa tareda nufan table ta ajiye tray din tana dagowa Yana fitowa daga bedroom dinsa sanyeda pyjamas shima fuskarsa tayi fresh kaman baya Shiga Rana. Akan kayan jikinta idanuwansa suka fara sauka ya dauke Kai Yana qarasowa ya zauna. Zama tayi gabansa tana daukar tea din ta miqa Masa tana cewa" Abbi barka da da fitowa. Numfashi yafara saukewa ahankali kafin ya dago ya kalleta tareda sakin taqaitaccen murmushi yace" Barka Dr Inayah majeed. Dadi taji sosai ta taso daga gabansa ta dawo gefensa kusa dashi sosai tareda dafa cinyarsa Saura kadan ya qware da tea din dake bakinsa tayi saurin janye hannunta tana kallonsa Dan itama batasan a cinyarsa ta Dora hannunba. Daqyar ya hadiye Wanda ya kurba a bakinsa tareda juyowa ya kalleta idanuwansa na gangarawa ga bakinta dake motsi tanason yin magana Amma takasa sbd idanuwansa dake Neman rudar da ita. Qamshinta ya shaqa ahankali tareda Dan rufe Ido ya bude Yana ajiye cup din hannunsa ya juyo gabaki daya Yana kallonta Magana yakeson yin Amma qamshinta yayi Masa yawanda yake kokawa da nutsuwarsa ya hadiye numfashi ahankali zai bude Baki yace ta tafi tayi saurin Kai hannunta kan bakinsa ta rufe sbd tasan korata zaiyi.... Saukar tafin hannunta Mai taushi akan bakinsa yasashi rufe idanuwansa dasuka sauya ya bude ya watsa Mata idon numfashinta na shiga hancinsa tareda qamshinta Kai tsaye Wanda yasa numfashinsa Dan sauyawa. Janye hannunta yayi Kai tsaye Yana fuskewa tareda daukan cup dinsa yakai bakinsa Yana kurba a natse yace" Kije ki saka kayan sanyi ki kwanta akwai sanyi yau. Zuciyarta dake bugawa da qarfi ta dafa da sauri tareda kallon gurin tana Jin yanda bugun zuciyarta ke qaruwa. Juyowa yayi ahankali ya kalleta Jin Bata motsaba Yaga hannunta kan kirjinta dayaketa kaucewa kalla sbd yanayin datake ciki.... Sosai tsatsayyun kirjinta suka nuna basa batareda bra sbd yanda suke motsawa kadan cikin santsin rigarta. Kaman Mara lafiya ya dauke Ido daga kanta yakasa tambayarta lafiyarta data dafe kirji sai kawai a hankali yace" Kije ki sauya kafin sanyi ya kamaki. Bata musaba ta miqe ta nufi kofa ta fice sbd bugawar da kirjinta yakeyi yasata Shiga fargaba da tunanin itakuma. Tana fitowa Palo suka hadu da Haj umma data fito daga dakin umma yaganah dubota da ciwon kan datace tana Dan ji tun yamma. Da boyayyan mamaki take kallon Inayah wadda ke tafiya a sanyaye hankalinta baya ma kan Haj umma din Dan Bata lura da itaba. Kai tsaye dakinta ta wuce tareda fadawa kan gado tana shigewa bargo ta lumshe ido tanajin sabon feeling Mai qarfi akan Abbinta. Daqyar tayi bacci da daren Dan haka tayi lattin tashi... Shima Abbi ranar baisamu wani bacci ba Dan haka tunda safe ya shirya ya fice sbd zuciyarsa dake buqatan iskan da Babu Qamshin Turaren 'yarsa ko kansa zai sake. Da wuri Inayah ta dawo Dan kawai tasamu fira da Abbinta Amma Bai dawo da wuri ba Qarshema ranar sai dare yadawo Bayan sunyita jiransa itada Haj umma Amma sai kusan 10 yadawo Kuma Kai tsaye yayi musu Saida safe ya shige sbd Yana tareda gajiya. Haka Inayah taqi tafiya daki saida ta dafa tea takai Masa tareda cake Mara zaqi sosai sbd Sam bayason zaqi ko kadan. Haj umma na kallo Inayah taje palon nasa Kuma ta dauki mintuna sosai kafin ta fito Wanda itakuma tsayawa tayi yafito daga bedroom Amma tayita jira Bai fitoba Dan haka ta tahowarta ta wuce daki jikinta a sanyaye. Washe gari haka abbin yakuma fitar safe Bai tsaya breakfast ba Kuma Bai dawoba sai dare yauma. Washe gari ma hakance takuma faruwa tun abin na Wasa saigashi Abbi ya rage zaman gida Sam Baya Zama he's always busy Sam yaqi bawa kowannensu time sbd Haj umma tafara tunkararsa da maganar Dr farhat Wanda Inayah Bata saniba batada labari Umma yaganah ce kawai tasani Kuma taqi barin Inayah taji zancen sbd rigimarta. Hankalin Inayah tashi yayi fiyeda komai, Rashin lokacinsu daga Abbinta yasata sukukucewa ta daga hankalinta sbd tsoron ko tayi wani lefin ne tunda itama tasan bataji. Haj umma ma tashi hankalinta yayi tashiga damuwa tareda Dora lefin akan Inayah tayi masa lefi ne shiyasa yake cikin damuwa Dan kuwa damuwa ta nuna sosai akan fuskarsa. Jin Abbinta na cikin damuwa yasa hankalinta ninkuwa atashi Dena fita aiki sosai tana Neman hanyar zaunawa da Abbin tabasa hakuri. A bangare Daya pressure din da Haj umma ke basa akan ya aura Dr farhat yasa ciwon Kai Mai tsanani kamasa qarshe ya Dena fita sbd Yana buqatan kansa ya sake sosai. Ga Inayah duk yanda taso ta kusantoshi bayaso yanzu sbd matsalar da hakan ke basa Itakuma ganin hakan saita rikice da damuwa sbd bayason tana zuwa gurinsa sosai. Dr farhat ce tazo daga gidansu ta dubasa sbd ciwon kan ya tsananta Masa. Rashin bacci ne da damuwa yake damunsa abinda yafadawa Haj umma. Hakan kuwa yasa Haj umma yanke shawaran aurawa majeed din Dr farhat Kai tsaye sbd yasamu Mai kulawa dashi, 'danta yana buqatan kulawar mace Wadda Zata sakasa farin ciki tabasa kwanciyar hankali Kuma bataga hakan atareda Inayah ba wadda bayan shagwaba datake zuba Masa Babu abinda Zata iya Dan haka bazata zuba Ido 'danta ya mutu abanzaba ko jikiki Bata samuba. Anty juwairiyyah takira tanayiwa wannan bayanin akan harta Kira qanin abbansu MAJEED din zaa saka lokaci a je Neman auren. Umma yaganah damuwa da nata tashin hankalin tashiga Jin hukuncin Haj umma din Wanda Kuma Babu Mai iya takesa tunda itace uwar MAJEED Bayan shi Babu Mai iya tsallake wannan zartarwar. Hafsat takira a waya tace tazo tana nemanta sbd Dole sufara shawarar yanda Inayah zataji wannan mugun labarin. Abinda Bata saniba shine MAJEED din ya amince kokuwa? sbd batai maganar dashiba Kuma shima baizo yamataba. Inayah na asibiti anty Hafsat tazo cikeda damuwa sbd umman tafara Mata bayani a waya shiyasa batazoba Saida ta tabbarda Inayah na asibiti. Tagumi suka rafka dukkaninsu biyun cikin dakin umma Bayan umma yaganah tagama yimata bayanin abinda yake faruwa ta Dora da cewa" Hafsat ki kokarta ki sake nutsar da ita tasan abinda takeyi Dan kuwa kishiya da qananun shekarun Nan nata da sangantar datake basune zasu fiddataba Duk kuwa da tsananin son da MAJEED ke Mata idan ya auri wata macen yasamu nutsuwa a gurinta bazata sake gane komaiba. Numfashi anty Hafsat ta sauke cikin takaici da damuwar maganar tace" Umma Inshallah Inayah bazata taba wulaqanta a hannun AA ba saidai Zan dage na sake lurar da ita abinda yake gabanta..Amma dai yanzu inaga kada abari tasan Abbin aure zaiyi kusa....... Inayah dake bakin kofar shigowa dasuka Bari a bude Zata shigo A Rikice qafafunta na rawa tace" Aure Kuma? ##MAMUH# #HOT/LOVE/ROMANCE #MAJEED& INAYAH _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/9, 11:49 AM] +234 816 828 4180: *_52_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Da sauri suka kallo kofar lokaci daya atare cikin mamaki da fargaba. Anty Hafsat ce tayi saurin tasowa tana kokarin riqo hannunta su qaraso ciki tana cewa" Yaushe kika dawo Inayah? Bata amsa tambayar ba sbd batama wani gane me Anty Hafsan ta fadaba qafafuwanta na rawa zuciyarta na bugawa da qarfi tace" Anty Hafsat abbi ne naji kuna maganar zaiyi aure fa? Kinga Inayah zauna muyi maganar a natse ba abinda kikaji din bane wata maganar muke...... Kasa Zama tayi ta tsaya tana kallon umma yaganah da duk tayi wani iri sbd damuwa wadda take bayyane qarara a kan fuskarta Take taji wani mugun tashin hankali da 'daci na cika maqoshinta zuwa bakinta da qyar ta tattaro yawu tace" Anty Hafsat fuskar umma yaganah ta nuna tana cikin damuwa Karki wani boyemin ku fadamun Gaskia idan aure Abbi zaiyi Ni insani.. Yanayin yanda tayi maganar muryarta a harde da tashin hankali da firgici yasa umma yaganah sauke numfashi tana dagowa ta kelleta dakyau cikin sanyi ta janyo hannunta tana cewa" Zo ki zauna Kuma ki nutsu hafsat Tai Miki bayanin komai banason hayaniya ko tashin hankali iya maganace kawai tunda ba auren aka Riga anyiba. Wani nauyi kirjinta ya qara Mai tsanani hartaji numfashinta na Neman toshewa daqyar Anty Hafsat ta zaunar da ita suka kalleta su duka atare cikeda damuwa. Umma yaganah ce taci gaba da cewa" Kofa nutsu karki jawowa kanki ciwo nafada Miki bakomai bane Dan yaqara auren tunda dama ai kinsan koba yanzu ba Dole MAJEED zaiyi aure wata Rana tunda ke naki auren bawani daukansa aure kukaiba kinata shirmen sagarta da shagwaba kin kasa tsayawa kisan me kikeyi Mahaifiyarsa kuma ba tsayawa zatayi tana kallonsa Yana garariba Babu aure ga manyanci na Neman cimmasa. Anty Hafsat ce ya karbi zancen da cewa" Ko ahaka dai ba komai bane Inayah Kishiya kaman Dr farhat ai ba Zaki daga hankalinki ba tunda kinsan halinta tasan naki Kuma kaman yanda umma yaganah tace baa dauraba karki saka damuwa tun yanzu........ Kasa riqe numfashinta dake kokawar toshewa tayi sbd maganganunsu dake fasa zuciyarta tako Ina take idanuwanta suka ringa ganar Mata duhu suna neman rufewa. Innalillahi wainnan ilaihrrjiun, Ke Inayah, Inayah? Innalillahi.. Kanta sukayi suna tarota ganin numfashinta na Neman daukewa. Hankali tashe suka ringa kiran sunanta a rikice suna rasa abinyi Dan kowa bayason Kiran Dr farhat Musamman yanzu da Inayah din tasan abinda ke Shirin faruwa. Waya umma yaganah ta dauka Kai tsaye takira Dr Abdul tareda sanar dashi suna zuwa asibiti yanzu da Inayah. Cikin tashin hankalin abinda sukace yace su Kira gashinan zuwa gidan ya dubata. Lokacinda sukai wayar Yana gida tareda mahaifiyarsa dataqi komawa tayi zamanta a Lagos dama tuntuni MJ Muhammed yafison zamanta a Lagos itace taqi Amma yanzu tunda 'yarta na garin ta zabi Zama anan su Inna kawai ya rage ataho Mata dasu idan Abdul yaje. Tareda umma Hadizan suka iso gidan saidai Kuma bayan sun iso suka rasa yanda zasu bawa Abdul Daman shiga har dakin umma duba Inayah gashi abbin yau ya Dan samu sauki ya fita sbd tafiya yakeson Yi ma kwanakin. Haka dai sukai shahada tunda muharraminta ne suka basa Daman shigowa yaje ya duba Inayah din wadda sosai take neman shidewa da attack din data samu. Dan taimakon dazai Bata yayi tafara Dan dawowa daidai saidai sbd tashin hankalin data sakawa kanta numfashinta yaqi dawowa daidai haka ya fito ya wuce sbd bazai iya ganinta a wannan hakinba Kuma yasan Inayah Bata samun attack saita Shiga wani mummunan shock na tashin hankali Koma me akai Mata ya tabbata ya danganci Abbi sbd abinda ya shafesa ne kawai yake saka Inayah cikin tashin hankali Amma Babu abinda yake damunta harta saka arai sbd koyaushe shine kadai Mai mahimmanci agunta. Yana tafiya Dole Dr farhat suka Kira bayan hankalinsu yakuma tashi da hawayen datake Babu kakkautawa cikin yanayi na daukewan numfashin. Dama yanzu a gidan Kira kawai Dr farhat ke jira Dan haka ana kiranta jiki na rawa ta taho tana nuna damuwa a fili sosai akan meya samu Inayah din Amma Babu wanda ya fada Mata. Zuwa Dr farhat yasa Inayah Jin wani sabon ciwo a zuciyarta tafara bori batason a dubata abarta ta mutu Ita mutuwarma takeso ta huta... Da mamaki suke kokarin tausarta Amma ta tibure ta dinga zuba kuka tana qin Bari ko tabata Dr farhat tayi. Basu umma yaganah ba ita kanta Dr farhat hankalinta tashi yayi sosai tafara tunanin ko kwakwalwar Inayah tasamu matsalane? Haj umma da batasan meyake faruwa ihu da tashin hankalin faman da akeyi da Inayah yasata fitowa bedroom dinta cikin fargaba ta iso dakin umma yaganah da aketa zuba tashin hankalin tana cewa" Innalillahi, Lafiya? Meyake faruwa da ita? Iska ne akanta? Dama tanada iska ne kome? Kasa magana anty Hafsat tayi sai umma yaganah ce tace" Batada iskan komai Kawai ciwo take takuma qi Bari a dubata sai rigima takeyi.... Mamaki sabone ya Kama Haj umma Yanzu akan ciwo da batason a dubata take zuba wannan tashin hankalin? Dr farhat da abin yafara Bata tsoro ganin sosai Inayah ke kuka tana daga musu hankali tace" Kodai zaa Kira AA ne sai awuce da ita asibiti can zaa iya fin karfinta a dubata sbd tana kokawa da numfashinta dakeson daukewa Amma taqi barin na taimaka Mata. Hankali tashe umma yaganah ta dauko wayarta ta saka Kiran MAJEED sbd ganin numfashinta yafara sama sama. A natse ya dauki wayar tareda sallama a hankali. Cikin kokarin daidaita muryarta ta Dan boye tashin hankalin ta sanar dashi Inayar batada lafiya sosai Kuma takasa Bari Dr farhat ta dubata numfashinta na...... Bata qarasaba taji dib alamar ya kashe ne kokuma network ne batasaniba. Kokarin sake saka kiransa tayi taji Amma Sam Bai dagaba cikin sabon tashin hankali tace" Inaga network nada matsalar muje da ita asibitin kawai. Ko asibitin ma win yarda tayi atafi sbd ganin Dr farhat kawai tsananta toshe numfashinta yakeyi Gashi zuwa lokacin ta matuqar galabaita Dan haka cikin fada sosai umma yaganah take tirsasata tashi. Koda umman ke fada batama San me take cewaba sbd idanuwanta dake kokarin rufewa...saiga Abbin ya shigo Kai tsaye zuwa dakin umma yaganah din. Da sauri duka suka juya suna kallonsa baka gane komai a fuskarsa Amma dukkaninsu suna iya hasaso tsananin damuwar dake ransa na ganinta hakan. Yana shigowa Kai tsaye gurin ya nufa anty Hafsat na Kira sunanta kada ta rufe idonta. Tana ganinsa ta maida idanuwanta akansa tana Jan numfashi cikin zafi.. Hannuwansa biyu yasa ya tallafota Kai tsaye daga kan kujera zuwa jikinsa Yana Kiran sunanta cikin yanayi na kulawa sosai da damuwar meya sameta. Daqyar taja numfashi tana tsiyayar hawaye ta bude Baki ahankali tace" Abbi aure zakayi???? Bata fuska yayi cikeda mamakin yanda taji zancen take ransa yayi mummunan baci Amma dayake bakowa ke gane yanayinsa ba duk Basu ganeba. Ruwan da umma yaganah ke miqowa ya karba ya Kai Mata abaki cikin sanyi yace" Relax and breath, Just breath, Yawwa deep breath, Sake Jan numfashin... Yanda yace tayi takeyi ahankali numfashin nata na daidaituwa ahankali ahankali. Sam taqi dagowa ta kalli kowa dakin sbd haushi da zafin kowa takeji hardasu umma yagananta. Ganin tadan dawo hayyacinta yasashi juyowa ya kalli Dr farhat dake kallon ikon Allah Dan tasan Inayah itace mafi so da kauna a rayuwar Abbinta Kuma tasan sangarta da shagwaban Inayahn Amma Batasan yaushe tafara boriba haka kokuwa Dan Bata taba rigima bane gabanta? Qatuwar budurwa na irin wannan tashin hankalin Amma mahaifinta ko damuwa yayi Mata ko 'yar tsawa baiyiba saima kokarin dawo da ita daidai yakeyi cikin sanyi da nutsuwa tareda boye tashin hankalinsa na ganinta hakan. Haj umma dake tsaye sake da Baki cikin mamakin dayafi na kullum ya Dan kalla Yana danne yanayinsa kafin ya kuma maida kallonsa kan Dr farhat Kai tsaye yace" Dr zaki iya tafiya I can handle this, Thank you. Juyawa tayi ta kalli Inayah cikin kulawa ta nufeta zatai Mata magana Inayah tayi saurin fara kokarin miqewa tana kokarin janyewa anty Hafsat ta dafeta tana kokarin tausarta kafin takuma borewa. Ganin hakan yasa Dr farhat dakatawa tana kallon MAJEED Daya dauke Kai ba annuri ko daya a fuskarsa da duka abinda kowa yayi agidan. Murmushin yaqe tasaki tareda yimusu sallama ta yiwa Inayah fatan samun sauki ta wuce. Shiru ya danyi tareda sake hadiye 'dacin ransa ya juyo ya kalli Inayah dake hawaye sosai har lokacin ta dago ta kallesa take taji wani sabon 'daci da qunci na cika ranta matuqar Abbinta zai auri wata mace.... Tasowa tana sakin sabon kuka Zata bar dakin umma yaganah ta riqeta tana cewa" Zan mareki idan bazaki nutsuba Ba'ason hauka kinji ko?? Sabon kuka Mai qarfi ta saki tana cewa" Umma yaganah bazan iya nutsuwaba Ni kubarni natafi banason ganin kowa.... Aurenma banayi na fasa bazan zauna da kowaba da Abbina..... Sai alokacin Haj umma ta fahimci duk wannan tashin hankalin akan meye, Takaici ne da mamaki suka tarar Mata wato duk wanna daga hankalin jama'ar gida da borin kaman me tashin iska da asthma duk akan ance MAJEED zaiyi aure ne? Wannan halin na Inayah na shashanci Yana Bata takaici da damuwa Dan haka cikin siqewa tace" Yanzu dama duk wannan ihun da tashin hankali dakikeyi kika daga hankalin kowa duk akan majeed zaiyi aure ne? To so kike gabaki daya ya qare rayuwarsa gurin tattali da renonki shi Kuma bazai Gina tasa rayuwarba? Da Ina tareda shi tunima dayayi auren Dan bazai zauna saidai yaga 'yaya wasu na tarawaba shine zakizo kina shirmen ihun kuka da...... Cikin kuka Inayah tace" Ni nace bazan Tara Masa 'yayan bane? Ai Nima Zan Haifa Masa idan kika barmu... Fiddo idanuwa Haj umma tayi cikeda mamaki, Su umma yaganah da Anty Hafsat ma tsit sukai yau ciwon bakin Inayah yayi musu Dadi duk da duk kunya ta kamasu da sauri umma yaganah ta buge Mata bakin sbd karta qarasa. Shi kansa abbin kasa magana yayi sbd mamakin bakin Inayah Daya Gama wuce tunaninsa hakama da bacin ran zancen dasuka sanar Mata da wani abin yasameta ayau acikinsu babu Mai abin fada masa sun kashe Masa 'ya ko me?? Numfashi ya sauke a boye Yana sake kawar da bacin ransa ya kalli Haj umma dake kallonsa jiran abinda zai fada sbd duk suna iya hango zallar bacin ransa duk da boyewar dayake kuwa. Daidaita kalamansa yayi cikin nutsuwa yace" Umma Ina dauka maganar auren Dr farhat bamu gama meyasa zaku dagawa Inayah hankali da zancen bayan bawai Kai karshen maganar akayiba. Umma yaganah da Anty Hafsat ya kalla suma yace" Meyasa zaku sanar da ita umma tunda kinsan halinta Yanzu gashi tana neman illata kanta akan hakan, Maganar aurena da Dr farhat Kar akuma tadasa a gabanta sbd ba........ Maganarsa tasa Inayah fashewa da sabon kuka tareda juyawa da gudu tabar wajen tana cewa" Kenan yin auren zaiyi da Dr farhat. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/9, 11:49 AM] +234 816 828 4180: *_53_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Rintse idanuwansa dasuka Dan sauya yayi tareda juyawa yabar gurin shima Yana kansa na Kuma sarawa dama gashi kwana biyun Yana fama da ciwon kan. Yana barin gurin umma yaganah Haj umma suka kalla itada anty Hafsat sukaga yanda tayi zuru da mamaki dashiga tunanin agaban kowa MAJEED zaiyi mata magana Mai Kama da fada kaman shine uban nata. Juyawa tayi jiki a sanyaye ta koma bedroom dinta tanaji wayarta na ringing juwairiyyah na Kira takasa dauka sbd ranta ba Dadi ko kadan bazata iya wani bacin ranba sbd yanzu juwairiyyah Zata sake dorata akan abinda zai quntata ranta. Anty Hafsat Kuma bayan Inayah tabi zuwa dakinta Dan tausarta Amma rarrashinta duniya tayi Inayah din Taki Dena kuka. Har bayan magriba suna fama da Inayah din Haj umma dake dakinta tana Dan jiyo yawon umma yaganah da Anty Hafsat gurin rarrashin Inayah din sama sama tayi banza dasu sbd gabaki daya ganin takeyi su suka Gama lalata Inayah din da bakinta baya tauna magana sam Sam. Ana gap da ishai haka anty Hafsat ta hakura ta tafi gida tabar umma itama tayi nata rarrashin ta hakura ta zubawa sarautar Allah Ido. Abincin dare ma kusan daga ita sai Haj umma ne sukaci Inayah taqi fitowa shima MAJEED din baizoba Koda Haj umma takirasa shayi kawai yace akai Masa. Zubbi ce takai ta ajiye Masa a palonsa ta fito ta dauki da Inayah ma da umma tace ahada Mata takai mata Amma ko motsawa Inayah batayiba tana kwance. Duk dubara da rarrashin umma yaganah Inayah kin Shan ko tea tayi Dan haka jiki a mace umman ta barta taje ta kwanta. Zafi da ciwo zuciyarta ke Mata sosai bayan hawaye Babu abinda takeyi sbd bazata taba iya kwatanta Abbinta da wata macen ba, Wannan zafin datakeji har abbin ma takejin zafinsa akan lamarin. Kwana tayi da ciwo a Rai da damuwa me tsanani Dan haka Koda garin ya waye da wani zazzafan zazzabi ta tashi Mai qarfi. Zubbi da umma yaganah ne akanta hankali tashe umma na rage Mata zafin gashinta da farin qaramin towel Zubbi kuwa chocolate custard me zafi ta hado Mata da farin soyayyan qwai Mara komai aciki. Kasa Shan komai tayi Saida umma yaganah ta nuna Mata rauninta na itama Zata iya kuka idan Inayahn bataciba kafin Tasha custard din aikuwa ko Gama Sha bataitaba amai ya taso Mata da sauri zubbi ta kamata takaita toilet ta ringa Aman cikin wahala sbd rashin qarfin jiki. Bayan tagama ruwan zafi zubbi ta hada Mata tayi wanka ta fito umma ta dauko Mata wata qaramar Riga Mara tsayi Mai taushi ta saka Takoma ta kwanta jikinta na tsananta zafi. Wanke toilet zubbi tayi ta gyare dakin tsaf ta kashe Mata AC ta kunna humidifier bayan tazuba wasu turaruka cika masu dadi suka fice daga dakin har umma. Umma na barin dakin tana Isa nata ta dauki wayarta ta saka Kiran MAJEED. Ta jima tana ringin kafin ya daga murya ahankali yace" Barka da yau umma. Barka MAJEED, Yau baka fitoba Allah yasa lfy dai ko? A natse Yana danne yanayinsa yace" Lafiya kalau alhmdllh, Yaya Inayah? Tana Nan tana Rigimar ko? Numfashi ta sauke a sanyaye tace" Tanata rigima tun jiyan gashi yanzu ciwo yashigo ciki sbd zazzabi Mai qarfi takeyi custard ma datakeso Tasha tayi amansa, Bansaniba ko Dr farhat din zaa Kira tazo ta dubata Amma Kuma wata sabuwar rigamat zatayi tana ganin Dr farhat din. Ajiyar zuciya ya sauke ahankali tareda cewa" Ganinan zuwa zanfara dubata kafin Akira likitan. Kashe wayar umma tayi tareda ajiyewa gefe tana Zama kan kujera tana cewa" Allah yasa ta tsaya taji maganarka. Kwance take tanajin zazzabin sosai bacci na Dan daukanta Yana sakinta duk da hakan tunanin Abbinta da aurensa na maqale cikin ranta. Turo kofar dakin yayi Kai tsaye tareda shigowa a natse sbd shima ciwon Kaine atare dashi. Fararen Fendi wears ne ajikinsa yau Qamshin nasa ma ahankali yake tashi daga jikinsa sbd Bai wani saka turareba Qamshin na jikinsane daya dade da Kama Turaren Mai sunyin Dadi. Cikin nutsuwa ya tako har bakin gadon ya tsaya Yana kallonta ahankali cikin nutsuwa ya lumshe fararen idanuwansa Yana budesu akanta cikeda kaunarta Mara sirki da qarfi wadda take gine cikin ransa shiyasa Sam Baya son bacin ranta ko damuwarta Amma tacika rigima yanzu duk akan aurensa dake kanta data dauka ta saka arai. Bude idanuwanta dasukai nauyi da sauyawa sbd zafin zazzabi Jin mutum akanta tasan Abbin ne sbd qamshinsa daya shiga hancinta. Maida idanuwanta tayi ta rufe tanajin nauyin kirjinta na qaruwa sai kawai hawaye suka fara gangaro Mata. Yana ganin hawayen nata yaji jikinsa yaqara sanyi ya zauna ahankali bakin gadon nata tareda Kai hannunsa dakeda sanyin ACn Daya fito ya taba goshin yaji zafinsa sosai Da kulawa sosai yace" Da wannan zazzabin naki ajikinki kike sake wani kukan Inayah?? Kinason ciwo ya kwantar dake ne? Meyasa bazaki Dena kukanba haka? Juyar da kanta tayi tana sake sakin kuka Mara sauti a wahalce batareda tace Masa komaiba. Shigowar Haj umma ne tareda Salimat data kawo wasu ruwan da towel Zata rage Mata zafin jikinta da umma yaganah tace zubbi takuma Yi Amma zubin na aikin gyaran Haj umma Dan haka ita takawo. Haj umma kuwa duba Inayah din tazo yi sbd rashin lafiyarta yasa gidan kaman anyi mutuwa kowa tsit ba walwala tunda princess din gidan ba lafiya. Salimat na ganin Abbi a dakin ta ajiye ruwan kan bedside drawer ta juya ta fice. Haj umma ma da 'yar kulawa kadan tace" Yaya jikin nata? Allah yabata lafiya Amma saita sakawa kanta salama Wannan kukan Babu abinda zai qara Mata sai ciwon. Amin"MAJEED ya amsa a taqaice Yana sake taba gashin Inayah din daya zafinsa yaji duk ya daga Masa hankali harya Dena Jin nasa ciwon kan. Cikin kulawa yace" Ina Ms Salimat take tazo ta rage Mata zafin jikin kafin Dr farhat tazo ta dubata.. Fadan sunan Dr farhat kawai yayi yasata sake tsananta hawayenta saiga umma yaganah ta bude kofa itama ta shigo da tea me zafi a tray tazo ta ajiye. Umma yaganah ki rage Mata zafin jikin Nan yayi yawa kafin likita tazo ta dubata jikin nata Yana tsananta zafi sosai... Cikin kuka ta tashi zaune daga kan gadon tana cewa" Ni banason Dr farhat ta dubani A Kira Dr Abdul.... Satar kallon Abbi umma yaganah tayi tana matsowa gurin gadon Zata dauki qaramin towel din Fadi tas Cikin kuka Inayah tasake cewa" Ni har rage zafin banason tunda ba zafin danakeji a zuciyata zaa rageba, Wlh abbi idan kayi wani auren zuciyata bugawa zatayi nidai Dan Allah kacewa Haj umma bakason auren Nan bazakayiba Banason kowa ta Zama matarka saini kadai.....Ni ko rage zafin banason umma tamun Kai zakamun idan bakaiba banason kowa yamun abarni zafin ya kasheni na mutu na huta bazanga ka aura kowaba..... Wannan karon salati Mai qarfi Haj umma take saki idanuwanta na rarrabuwa tsakanin umma yaganah da MAJEED taga yanayinsu akan wannan tsabaragen rashin kunyar da iskancin na Inayah Amma saitaga kowannensu yayi shiru kusan itama umma yaganah taji kunyar zancen Amma Kuma majeed yafisu shiga mamakin saidai kaman koyaushe baa cika gane reaction dinsa akan Abu. Matsowa umma tayi tana kokarin Mata fada a fakaice sai kawai abbin ya miqa hannu ya karbi towel din tareda cewa" Ba damuwa Zan Mata. Cikin ruwan ya saka towel din ya Ciro ya matse ruwan ya Dora Mata a goshi har lokacin hawaye takeyi. Ahankali yace" Hawayen ya Isa haka tunda gashi inayi. Riqe hannunsa dake goshinta tayi ahankali jikinta na sanyi da zuciyarta sbd bazata iya fushi da Abbinba A hankali tace" Abbi kayi hkr ka yafemun bazan sakeba. Neman sakewa jikinsa keyi yayi qarfin halin riqe yanayinsa tareda sakar Mata murmushi cikin tsananin kulawa yace" Shikenan Dena hawayen. Kwantawa tayi jikinsa tareda zura hannayenta ta rungumosa daga zaunen dayake tana cewa" Abbi shima auren karkayi Dan Allah. Wani mawuyacin yawu Mai daci ya hadiye ta maqoshinsa Yana sake kokawar dedeta kansa. Umma yaganah juyawa tayi ta fice salin alin batareda dogon motsiba. Haj umma ma dai ganin Inayah ba mutuncine da itaba yasata juyawa ta fice tana cewa" Idan kafito MAJEED Ina nemanka. Daga shi har Inayah din basuji abinda taceba sbd shi kokarin riqe kansa yakeyi da kyakkyawar rungumar da Inayah tayi Masa tareda kwantar da kanta jikinsa yanajin dumin jikinta na Shiga nasa jikin ahankali. Ahaka sukai shiru Babu me magana Saida suka jima ahakan kafin ta Dan dago ta kalli fuskarsa da shima ya juyo ya kalleta cikeda shagwaba tace" Abbi Dan Allah ka fasa auran kowa bama Dr farhat kawaiba. Muryarsa a shaqe cikin nutsuwa yace" Meyasa Zaki daga hankalinki akan hakan Inayahhh???? Lumshe fararen idanuwanta tayi ta bude Masa itama a hankali tace" Zuciyata zafi da ciwon hakan takeyi, Bazan iya hadaka da kowaba Abbi, Kai mijinane Ni daya, Bazan iya gani kaje gurin wataba bayan Ni ko zuwa gurina bakayi haryanzu baka daukeni matarkaba..... Wasu kakkauran yawun yakuma hadiyewa cikeda mamaki da bugun zuciyarsa dake tsananta yakai hannu ahankali ya cire towel din dake kanta Yana kallon tsakiyar idonta dasuke bayyanarda tsananin soyayyar dake dawainiya da zuciyarta.... Matsota yayi jikinsa ahankali fuskarsu ta matsu data juna Numfashinta Mai dumi ya ringa sauka kan fuskarsa da shiga hancinsa Yana bude kofifin hakurinsa da jarumtarsa ta danne abun dayake ransa da jikinsa.... Rufe Ido kadan yayi ya budesu akanta itama har lokacin shi take kalla zuciyarta na kasa daukan zafin sonsa aranta dayayi Mata yawan gaske. Jin jikinsa da zafi yasata Dan zame hannunta Daya ta dauko towel din da sanyin ruwa takai wuyansa ta shafa Masa ahankali tana kallon wasu jijiyoyin wuyan nasa dasuka fara fitowa take. Sake shigewa jikinsa tayi tana ajiye towel din sbd batada karfin jiki karfin haline kawai na ganin Wanda zuciyarta ke bugawa sosai akansa... Towel din ya dauka ahankali daga jikinsa batareda ya gara debo Masa wasu ruwanba ya Kai fuskarta yafara gogawa Yana gangarawa zuwa wuyanta ahankali Wanda hakan yasata Jin wata mummunar kasala tana sake lafewa jikinsa. Yana zuwa wuyanta hannnun rigar jikinta Mai santsi ya zame saman kirjinta ya bayyana take suka saki numfashi lokaci daya Yana goge Mata saman kirjin zafi na keta koina ajikinsa tareda bugun zuciya me qarfi ya ajiye towel din Yana kokarin miqewa Inayah ta tashi tana kallonsa yana miqewa ta yaye bargon jikinta Zata sauko gadon itama saidai rashin karfin jikinta yasata komawa baya ba qarfi kan gadon tana kallonsa da indanuwanta dasukai laushin kasalar ciwo. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/9, 9:34 PM] +234 703 623 7917: *_54_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Rigar jikinta mara nauyice ta yaye ahankali tareda bayyanarda dogayen Lafiyayyun cinyayoyinta marasa tabo ko daya.. Rankwafawa yayi zai gyara Mata kwanciyar tasake riqe hannunsa daya Wanda yasashi kasa riqe qansa ya zauna sbd loosing balance dayake Shirin yi. Janyota yayi ya gyara Mata kwanciyar saidai ajikinsa kawai ta yarda data kwanta din Dan haka Dole yabarta ajikinta ta kwanta tareda shigewa jikinsa da kyau ta rungumesa da hannayenta ta rufe idanuwanta tanaji Yana goge Mata jikinta da towel din Wanda kusan kowace daqiqa numfashinsa fizaga yakeyi sbd hannuwan rigarta data Dan zame sbd kawai ya goge Mata jikin nata. Yanayin yanda yake goge Mata jikin yasata kasa samun baccin datake ji ta bude idanuwanta tana kallon dogayen yatsun hannuwansa fafare suna yawo da towel din jikinta... Tashi zaune tayi ahankali tana kallon fuskar abbin data sauya kaman wani innocent baby... Hannuwa biyu tasa ta sake rungumesa ahankali tana cewa" Abbi na I love you...... Tsit dakin yayi duk da bayaune farkoba tunda tafara wayo take cemasa "I love you Abbi" Amma na yau din sautinsa ya banbanta da Inayah Babynsa. Dago fuskarta yayi Yana kallon bakinta Daya furta hakan... Ganin irin kallon daya kewa bakinta yasata Matsoda fuskarta ahankali takai gap da tasa fuskar numfashinsu na sarkuwa ta lumshe ido ahankali gabanta na tsananta faduwa da abinda zuciyarta keso take Kuma ingizata gayi... Knocking kofar da akayi ne yasata dakatawa tareda dagowa suna kallon juna da Abbin Wanda zuciyarsa tagama daukan dumi da yanayin. Sake knocking akayi batareda Inayah tabar jikinsa ba saima gyara kwanciyarta datai kanta a cinyarsa tayi banza da bugun kofar. Shi kansa Saida ya dauki mintuna kafin nutsuwarsa tadawo daidai ya Dan gyara murya kadan a hankali yace" Yes..waye agurin? Muryar Haj umma yaji tace" Ga Dr farhat Nan tazo duba Inayah din Naga tanajin jikin gwara adubata. Dan juyowa yayi ya kalli Inayah data kallesa idanuwanta na cikowa da hawayen dake sake kashe jikinsa ya lumshe Mata Ido ahankali tareda Dan gyada Kai yace" Kibari ta dubaki Babu maganar wani aure yanzu.. Bawa su Haj umma Daman shigowa yayi Wanda itace agaba kafin Dr farhat din. Duk da shigowarsu baisa Inayah ta tashi ko janyewa daga jikinsaba Kuma taqi bude Ido ta kallesu ahakan Dr farhat ta dubata Tai Mata allura tana sake cukuikuye Abbin sbd batason allurar. Kafin agama allurar Babu Inda Bata Gama goga Masa nonuwantaba da basa cikin bra sbd qin tsayawa tayi ayi Saida ya riqeta. Koda aka Gama Dr farhat ce kawai a dakin Haj umma ganin wata sabuwar lukutar masifar yasata fitowa Dan kuwa tasan MAJEED dinta ko dutse ne wannan abin da Inayah keyi Zata iya lalata masa mutunci da tunani. Dr farhat ma yau kanta a qulle yake da tashin hankalin sabuwar dabiar Inayah Wanda takega Bai kamataba ko rigar jikinta Bai kamata ace tana sanyeda ita agaban mahaifintaba. Suna fita Inayah ta sakar Masa wani malalacin kuka a kasalance tana cewa" Abbi Dan Allah kada ka auri Dr farhat,.... Wata irin damqa yayi Mata batareda yasan yayi hakan ba ya mannata da jikinsa sosai yana kallon idonta zuwa bakinta numfashinsu na haduwa da wata fitinanniyar murya Mara sauti sosai yace" Meyasa bazaki Dena maganar auren nanba? Nafada Miki Zan iya auren wata macen ne uhmmmm? Hakan Daya fada dakuma sautin dayayi maganar dashine yasata Jin wani farin ciki me sanyi tareda manna Masa kirjinta ta rungumesa Bai iya riqe kansansaba ya sbd komai nasa kuncewa yakeyi ya kwantar da ita kan gadon tareda Mata rumfa Yana kokarin Hana kansa kallon nonuwarta dake nuna kansu a idonsa. Daqyar ya fisge kansa Yana kokarin controlling kansa tareda miqewa tsaye daga kan gadon gabaki daya Wanda suka yamutsa da mutsu mutsunta gurin shiga jikinsa da allurar da akai mata. Juyawa yayi ya fice daga dakin gabaki daya... Yana fita Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa ya shiga toilet ya sakarwa kansa ruwan Yana rintse Ido. Ya jima acikin ruwan Saida yasamu kansa ya dan sake kafin yayi wanka yafito daureda towel Yana goge jikinsa. A gaban mirror ya tsaya Yana kallon kansa cikin nutsuwa ya Dan rufe Ido ya bude Yana Jin dumin numfashinta haryanzu a wuyansa.... Inayah takasa gane abinda yasa yake kaucewa wannan kuruciyantata, Maganar auren kowa ba Dr farhat kawaiba shi kansa yasan kaman ya haramta garesane sbd bazai taba iya hada kaunar Inayah da kowa da komaiba saidai Kuma bazai iya kusantartaba a miji sbd tausayinta da ganin rashin qwarinta Dan haryanzu 'yar Babynsa yake kallonta. Shiryawa yayi cikin Kaya marasa nauyi yayi zamansa daki tareda Dan Shan maganin ciwon kan ya kwanta idanuwansa a lumshe saidai zaiyi wuya idan zai iya baccin. Ahakan akai azahar ya tashi ya fita sallah daga can ya fita zuwa wani gurin. Itama bayan fitar Abbinta bacci tasamu ya dauketa zuciyarta mamaye da farin ciki. Sai Bayan azahar ta farka lokacin jikinta yayi Dan qwari Kuma zazzabin ya saukar Mata gaba daya sbd allurar da akai Mata da damuwarta data fita ranta sbd dama rayuwarta Inayah bamai riqo bace sbd tun farko haryanzu idanba qaddarar rashin aurenta da ake fasawa batada damuwa komai saita rashin uwa wadda umma yaganah ta cike wannan gurbin tuni barema gurbine da Abbinta Bai bar filiba yacikesa sbd farin cikinta. Wanka takuma Yi ta fito ta sanya doguwar Riga har qasa amm ko yanzu Mara kauri da nauyi. Sallah tayi tana gamawa zubbi takawo Mata shayi Mai zafi da white couscous da kidney sauce. Umma yaganah ce da Anty Hafsat data zo suka ringa Dan lallabata da fira taci abincin bayan Tasha tea din sosai. Ganin duk sun damu yasata kallonsu cikin sanyi da shagwaba tace" Umma yaganah kiyi hakuri bazan sakeba, Anty Hafsat I'm sorry. Murmushi Anty Hafsat tayi tana cewa" Ni daidai kikamun ba gashi yanzu zaa taqaita Mana zancen aure auren nanba ana zaune kalau Inayarmu ko baby ko daya Bata haifawa Abbinta ba wata zatazo ta rigata" Eh fa Anty Hafsat kiji fa Dan Allah, Ni wlh nafadawa abbi bazan yardaba nice Zan Haifa Masa yaran da Haj umman keso.. Umma yaganah da mamaki sabo duk da sun saba da bakin Inayah Amma kusan mamakin baya denuwa tace" Yanzu Inayah haka kika fadawa MAJEED kece Zaki Haifa Masa 'yayan? Dan gidanku ta Yaya Zaki Haifa Masa 'yayan Baki Gama sanin ciwon kankiba kina wannan zubar Kizo gaban 'yayan ma kinayi. Cikin dariya anty Hafsat tace" Umma yaganah tsaf kuwa Zata Haifa Miki abokan Hira inshallah Nan kusama. Ahankali tana sanar kallon umma sbd kada ta buge Mata Baki tace" Inshallah anty Hafsat. Harara umma tabita dashi tana amsa Kiran umma Hadiza da tun jiya dasuka tafi. Bawa Inayah wayar tayi sukai magana taji Inayah din ba lefi ta warware sukai sallama tana sake Mata fatan sauki cikin tsananin kauna da kulawa. Dakin umma yaganah suka koma acan ta kwanta Haj umma ma tasake zuwa ta dubata, Anty Hafsat ce ta zauna ta ringa koro Mata bayanai tareda qarasa juya kan Inayah din akan idan ba samun ciki tayiba Haj umma bazatabar maganar auren Nan na AA MAJEED ba... Hankalin Inayah kasuwa biyu yayi sbd a bakine kawai take fadar cikin Amma cikin ranta tsoro da fargaba takeji na haihuwar sbd tana ganin yanda Mata me haihuwa abin na daga hankalinta. Juyar Mata da tunani anty Hafsat tayi ta dena kallon wuyar haihuwar sai fashin auren abbin kawai duk da yace Mata baice zaiyiba Amma idan Haj umma ta nace tasan zaiyi. Anty Hafsat Bata bar gidanba sai bayan ishai, Bayan ta wuce daki Inayah Takoma bayan taci abinci kadan sbd zazzabin Daya fara dawo mata, Kasa wanka tayi sbd sanyin datakeji dan haka kayan bacci ya sanya Riga da Wanda masu kauri sosai na Fendi. Tana kwanciya ta rufa jikinta na qara zafi. Wayarta ta lalubo ta dauka tareda Nemo numbern Abbi tasaka Kira.. Ringing tayita Yi Bai daukaba Dan haka ta ajiye wayar tareda tashi zaune ta ziro qafafunta ta sauko gadon ta saka slippers ta nufi kofa sbd damuwar ko shima ciwon kansa yayi tsanani ne. Kowa ya shige Dan haka Kai tsaye palonsa ya nufa tareda budewa ta shiga tana sake saka Kiran wayarsa sbd baya palon tv ce kawai ke aiki ba murya ko kadan sai AC da sanyayyan kamshin turarensa Daya gauraya Dana humidifier dake aiki. Sake saka Kiran wayarsa tayi saiga wayar na ringin a palon ahankali sbd bayason qarar waya shiyasa yawanci wayoyinsa a silent suke. Wanka ya fito daureda blue towel yaji dan ringing din wayarsa a Palo Ya Dan yamutsa fuskarsa ya nufi palon sbd baisan waye zaikirasa a wannan lokacinba kusan 11 na dare. Yana fitowa wayar na katsewa Inayah Kuma na dagowa..... Faduwa gabanta yayi da qarfi ganin Abbinta daureda towel a Karo na farko rayuwarta.... Lafiyayyar fatarsa da Lafiyayyan jikinsa Dayake bayyanarda qarfinsa ta kalla zuwa fuskarsa taji gabanta yakuma faduwa Amma Kuma zuciyarta garesa take ingizata sbd fuskarsa kawai ta bayyanarda gajiyarsa. Kallonta yayi Yana Dan kame fuska ya qaraso ya miqa Mata hannu ta basa wayarsa data dauka. Bata fuska tayi tana kalar tausayi sbd ganin ya kame fuska lokaci daya. Kasa miqa Masa wayar tayi tareda sanyaya murya tace" Abbi na dauka bakada lafiyar ne Naga baka fito kaci abinciba kuma..... Ringing wayarsa Dake hannunta ne ya datse maganarta ta dago wayar atare sukaga sunan Dr farhat baro baro akan wayar. Wani bugawa kirjinta yayi take idanuwanta suka ciko da hawaye ta dago ta kalla Abbin Wanda shima mamakin Kiran Dr farhat din ya kamasa Amma Bai nunaba sbd ganin halinda Inayah take kokarin shiga qafafunta tuni suka fara rawa hawayenta suka gangaro ta saki wayar qasa tareda juyawa Zata gudu tabar gurin cikin kuka me tsanani... Ko takun gudu biyu bataiba ya riqota da sauri Yana Kiran sunanta cikin yanayi na son hanata daga hankalinta sbd sanin daga hankalin kowa gidan dazata iya yanzu ta tada kowa da rigimarta. Qwacewa takeyi hawaye nabin fuskarta tana cewa" Ni Abbi kabarni banason ganinka kaje ka dauki wayarta.... Sosai take Rigimar kwacewa taqi yarda ta tsaya ta sauraresa sai kokarin dawo da ita nutsuwarta yakeyi Yana Kiran sunanta Amma taqi. Jikinta ya sanyata tareda rungumeta Yana cewa" Ya isa, Ya Isa, nace ya Mana Ba daukan kiranta zanyiba, Banma San meyasa ta kiraba at this hour.... Aurenta zakayi shiyasa ta Kira Ni kabarni Abbi zuciyata mutuwa zatayi kawai.... Cikin daga murya da tashin hankalin datake neman sakasa yace" Na fada Miki ba aurenta zanyiba can you shut up and stop being childish. Dakatawa tayi tareda yin shiru ahankali ta dago daga jikinsa ta kallesa da idanuwanta dake kaca kaca da hawaye ahankali tace" Da gaske Abbi bazaka auretaba? Wani numfashi ya sauke tareda juyar da Kai cikin kosawa kafin yadawo da kallonsa kan kyakkyawar fuskarta Yana kallonta da idanuwansa dake cikeda wahalalliyar kaunarta dake wujijjiga rayuwarsa Bai iya cewa komaiba sai rintse idanuwansa da yayi Yana Kai hannu zai janyeta jikinsa ta girgiza Kai tareda sake shige Masa hannuwanta na sake zagaye jikinsa da Babu Kaya sai towel. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/10, 6:01 PM] +234 703 623 7917: *_55_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Daqyar ya iya bude Baki ahankali can qasan maqoshi yace" Nace ki Dena maganan Nan..... Sanyi yaji cikin ranta tareda sake kwantar da kanta kirjinsa Qamshin shower gel dinsa na shiga hancinta.. Sake dagota yayi daga jikinsa ya kalli fuskarta itama shi ta kalla taji qaunarsa na sake cika zuciyarta ta saki wani kyakkyawan murmushi Mai sanyi tana sake gyara hannuwanta dake zagaye dashi. Murmushinta yasashi Jin wasu notikan kansa na kuncewa ya kamo fuskarta da hannuwansa biyu ya matso da ita daf da tasa Yana kallon cikin fararen innocent eyes dinta dasuke kallonsa cikeda kauna... Ahankali ya iya furta" Why? Why Inayah?..... Kasa qarasa cewa komai yayi ya rintse idanuwansa dasuke kokarin Tona halinda tasakasa... Kyakkyawar fuskarsa da idanuwansa Daya rintse ta kalla tanajin a duniya bayan Abbinta Batasan metakaso irin hakaba, Sunansa kawai idan ta fada zuciyarta wani sanyi da cika takeyi.... Wani sanyayyan numfashi ta sakar Masa a fuska Wanda yasashe sake rintse idanuwansa Yana riqe numfashinsa me zafi dakeson fita.... Ba tsammani yaji saukar tattausun lips dinta akan NASA tabashi wani sanyayyan kiss dayasashi bude idanuwansa take akanta... Murmushi ta kuma sakar Masa baisan lokacinda ya Kama fuskartaba ya matse da tasa fuskar Ya hade ta tasa Yana kokarin Hana kansa abinda zuciyarsa ke kasa riqewa..... Kallon idonsa dasuka sauya Inayah tayi tana shaqar numfashinsa me dumi dayake fita kan fuskarta dake hade da tasa fuskar Yana Hana kansa koma menene a zuciyarsa... Bakinta takuma mayarwa ta Dora a nasa ahankali atareda zira harshenta ciki ahankali ta lumshe ido tana cin wani zafi cika kanta da kunnuwanta sbd karon farko da bakinta Dana wani ya hadu a rayuwarta........ Yahh salammm Inayahhh my baby why?why?""" Yake fada a qasan ransa Daya Gama kasa riqe kansa tako Ina Kanta ya Kama da kyau ya kalli fuskarta data fara shiga tsoro da fargaban yanda itama tata zuciyar ke bugawa da qarfi Kai tsaye yakai bakinsa akan nata ya zura harshensa ciki ya zuqo yawun bakinta ya hadiye cikin bakinsa sukabi moqoshinsa zuwa cikinsa suna tada duk wata tsika dake jikinsa..... Kwakwalwarta tsayawa tayi cak sbd dumin harshensa dayake laso duk wani lungu dake bakinta Yana zuqa Take qafafunta sukai sanyi ta sakar Masa jikinta tana sake qanqame bayansa da hannuwanta ke zagaye.... Wani irin Lafiyayyan french kiss yakewa bakinta idanuwansa jajir Zuciyarsa na budewa da samun abinda taketa dannewa... Motsawa tayi ahankali tana sake sakar Masa jikin nata Saijin tayi ya dagata cak dinta zuwa bedroom dinsa. Shigarsu bedroom din yasata bude idanuwanta dasukai taushi ta kallesa shima nasa idanuwan dasuka sauya ya zuba Mata numfashinsu na haduwa Dana juna sbd gashinsu dake hade.... Tsakiyar gadonsa ya kwantar da ita tareda ranqwafowa kanta Yana kallon idanuwanta zuwa bakinta da qamshinta dake cika hancinsa Yana yamutsa nutsuwar qwanyar kansa. Qamshinta shine mafi qarfin Abu dayake yamutsa kansa da nutsuwarsa Dan haka yakai fuskarsa ya cusa ahankali cikin wuyanta Yana shaqarta idanuwansa na qara rinewa.... Gangaro da kansa yayi zuwa kirjinta dake sama Yana qasa sbd bugawar da zuciyarta keyi da qarfi ya tsaida kansa agurin Yana shaqar qamshinta da numfashinta lokaci daya tareda Dan dago Kai ya kalli fuskarta da idanuwanta ke rintse sosai ya maida idanuwansa akan kirjin nata ahankali. Hannunsa dakeda Dan sanyi na wanka dabai Dade da Gama yowaba ya Dora kan wuyanta ahankali Yana shafowa suka ja wani irin numfashi tare ahankali.... Sake safo wuyan nata yayi Yana shaqar qamshinta da qarfi cikin hancinsa idanuwansa na rufewa a wahalce... Qanqamesa tayi da hannuwanta sbd Jin sanyi da taushin hannunsa na wani irin yawo cikin wuyansa zuwa bayanta Hakama numfashinsa dake sauka kan wuyan nata zazzabi Mai kasala yake sakar Mata Dan haka take sake qanqamesa tana rufe Ido a kasalance. Rungumar datake sake Masa yasa yake sake shiga mawuyacin hali Dan haka yakuma dago da fuskarsa daga cikin wuyanta Yana dago fuskarta Yana kallon Dan qaramin bakinta Mai kashesa da maganganunsa yakai bakinsa a Karo na biyu ya Kama bakinta tareda jefa harshensa ciki Yana laso harshenta daya dauki Qamshin mouthwash dinsa na Aesop a kiss din farko... Yanda yake kissing dinta da a mayace cikin zafi Amma tsananin so da kaunar dayake Mata ya Hana yayi gaggawa cikin wata irin zazzafar kauna kissing din ke gudana a tsakaninsu sbd itama yagama juyar Mata da Yar qaramar kwanyarta... Saukan hannunsa cikin rigarta yasata kusan sumewa a jikinsa sbd wata irin shafawa yake bin cibiyarta zuwa saman kirjinta ahankali Yana Jin duniyarsa na juyawa gaba daya.... Kasa taba kirjinta yayi sbd wani mugun shock dayaji Yana Neman bugasa kansa Dan haka ya dago Yana kallonta da jajayen idanuwansa dasuka Gama sauyawa ya Kai hannu ahankali zai zame rigarta gaba daya saiya dakata cak tareda lumshe ido ya rintse ahankali...... Janye hannuwansa yayi tareda mirginawa gefe ya zube kwance tareda rintse idanuwansa Yana sauke numfashi Mai zafi Yana kokarin dawo da kansa hayyacinsa Dan yasan yau kam yayi loosing control na kansa gabaki daya akan Babynsa. Itama lafewa tayi gefensa gabaki daya jikinta a mace Dan ko iya bude idanuwanta bazataiba sbd mutuwar jiki da tsoron Daya Gama cikata koina. Mintuna kusan Tara ya dauka ahakan Yana seta kansa kafin ya tashi zaune ahankali batareda ya juyoba ya nufi toilet ya shige. Ruwan dumi yakuma sakarwa kansa sbd bayajin akwai abinda zai qarasa kwantar dashi sai ruwan. Bai wani jimaba ya fito wannan karon da bathrobe blue ajikinsa ya kalli Inda take kwance ta lafe da alama bacci zatai ahakan. Boyayyan numfashi ya sauke ahankali tareda nufar gaban mirror ya Dan fesa body mist kadan da Mai shima kadan ya nufi closet dinsa ya Ciro fararen pyjamas ya sakata. Gadon ya nufo ahankali tareda zaunawa ya kalleta cikin kulawa yaga bacci yafara daukanta ya sauke ajiyar zuciya tareda Kai hannu ya shafa kanta ahankali yace" Inayah¿ Dare yayi tashi muje ki kwanta kada bacci ya daukeki anan... Bude idanuwanta tayi ahankali tareda kallonsa idanuwanta da bacci aciki dakuma sauran yanayin dasuka so Shiga A shagwabe tace" Abbi anan zanyi baccin ni. Galabaitattun idanuwansa ya zuba Mata cikin kulawa yace" Zakifi Jin Dadi a dakinki Nan bana kwana da AC a kunne zakiji zafi... Maqe kafada tayi tana cewa" Zan kwana ahakan Zan Saba ai tunda tare zamuna ringa bacci. Shiru yayi baikuma cewa komaiba sbd zancen data fara yankowa. Ahankali ya gyara Mata kwanciyar da rufa ya tashi yakoma kan sofa ya zauna ya zuba tea din da aka kawo Masa tun tuni baishaba Yafara kurba ahankali Yana Shiga tunani. Ya jima agurin zaune tsawon lokaci Batareda yaje ya kwantaba yanajin tayaya zai iya barin wani Abu yashiga tsananinsa da Babynsa, Baimasan tayaya hakan zai iya faruwa tsakaninsuba..... Maida idanuwansa yayi kan makeken Lafiyayyan gadonsa datake kwance tana baccinta hankali kwance cikin tattausan farin quilt Mai taushin gaske. Sai dare sosai ya tashi ya nufi gadon ya kwanta a natse gefenta yakai hannu ya kashe hasken dakin gabaki daya. Juya Mata baya yayi ahankali sbd Qamshin Turarenta dayake yamutsa duniyarsa gabaki daya. Ko ahakan Saida ta jima kafin bacci ya daukesa... Qarfe biyun dare ta farka sbd zafin dake damunta ta zare rigarta ta koma ta shige bargon takoma baccinta. Lokacin sallar asuba Yana tashi da ita ajikinsa yafara cin Karo ta shige jikinsa gabaki daya ta rungumesa tana baccinta hankali kwance. Lumshe ido yayi tareda zubawa fuskarta Ido yayi Mata kallon kusan mintuna uku kafin ya zame ahankali ya tashi ya wuce toilet. Brush yafara Yi kafin su alwala yafito ya sauya kayansa zuwa jallabiya ya fice zuwa qaramin masallacin gidan nasu. Bayan fitarsa bada jimawaba itama ta tashi dayake dama ta saba tashin asuba kan lokaci Kuma shine ya koyar da ita hakan harya Zama jikinta lokacin sallah nayi Zata farka. A toilet dinsa tayi alwala ta fasa sabon brush tayi ta fito tayi sallarta anan Takoma ta kwantawarta.... Jin rigarta na damunta ta zareta daga saman tabarta a kirji ta shige quilt Takoma baccinta sbd sanin abbinma baya dawowa wasu lokutan da wuri daga masallaci wani lokacin gym yake tsayawa Yi a gym room dinsa. Koda ya dawo baiyi tsammanin zai sametaba Dan ya dauka Zata koma dakinta kodan nauyin abinda ya faru dasu jiyan. Bai lura da itaba sbd har lokacin dakin Babu haske sosai Dan haka ya zare jallabaiyarsa dagashi sai dogon wandon kayan baccinsa ya hau gadon tareda shigewa rufa sai kawai yaji mutum aciki.. Hannu yakai Dan tabbatarda ita dince ba zato hannunsa ya sauka kan tattausan kirjinta da rigarta ta zame tabari..... Dagashi har ita dake bacci wani mummunan shock suka Shiga Musamman shi da kusan bugawa kansa yayi... Janye hannunsa yayi da sauri Yana dauke Kai daga kallonta ya kwanta Yana lumshe idanuwansa batareda yace komaiba. Itama idanuwanta ta bude zuciyarta na Dan harbawa sbd hannun Abbinta yasata dukkanin jikinta mutuwa. Juyowa tayi ta zubawa kyakkyawar fuskarsa datake sake narkar da zuciyarta akan kishinsa ta saki wani qayataccen murmushi Mara sauti tareda matsowa jikin nasa ahankali ta shige tana zura hannuwanta ta zagayesa ahankali tace" Good morning Abbi. Bai bude idanuwansa ba ya shafa kanta ahankali cikin kulawa yace" Morning. Murmushi takuma sakewa tace" Best morning ever... Bude Ido yayi ya saukar akanta Yana kalla batareda yace komaiba sai lumshe ido dayake akai akai. Bacci takuma komawa abinta shima ahakan yayi bacci Mai Dadi har kusan qarfe goma Basu karfaba Saida wayarsa ta ringa zuba ringing kafin ya tashi.. Wanka yafara shiga Kai tsaye sbd ganin time yaja Kuma yanada baqin dazai gani yau din office. Yana cikin wanka ta farka Dan haka itama Kai tsaye ficewaa tayi zuwa bedroom dinta sbd yau garau takejinsa Zata iya leqawa asibiti. Tana fitowa Babu kowa a main Palo Dan haka dakinta ta nufa Kai tsaye ta fada toilet tayi wanka tana Jin farin ciki koina aranta. Tana fitowa daureda towel brown taji salatin Haj umma na tashi da qarfi hakama umma yaganah kaman suna magana cikin daga murya da tashin hankali. Kasa tsayawa komai tayi ta fito a rude daureda qaramin towel din tana zaro ido cikin tsoron meke faruwa sbd su gidan Basu Saba da hayaniyaba. Tana fitowa dukkaninsu idanuwansu suka dawo kanta cikeda mamaki da tashin hankali suke kallonta Baki sake.. Da sauri umma yaganah da hankalinta yafi na kowa tashi ta kalli Inayah din tace" Ina kikaje tun daren jiyan Inayah???? Haj umma ce ta karbe da cewa" Wlh idan Bata fada Inda tajeba yau duka Zan Mata a gidan Nan idan su Basu taba dukankiba sbd gata Ni yau Marinki zantayi sai fuskarnan Taki Takoma jajir sbd bazan iya kallon wannan shirmen dake faruwaba a gidan nan, Tun tsakar dare yaganah tace taje dubo jikinki Bata samekiba, Zuwanta uku bakya dakin bakya gidan anduba koina bakyanan, Yanzu tunda safen Nan ankira Dr Abdul yace bakizoba Kuma baacan kika kwanaba, Hakama hafsat ankira tace bakizoba, To Ina kikaje? Wace rayuwa Zaki saka MAJEED Kuma yanzu da damuwar wannan sabuwar dabiar?????....... Cikin takaice Inayah ta kalli Haj umman kafin ta juya ta kalli umma yaganah datake kallon MAJEED Daya fito lokacin Ta sake maida kallonta kan Haj umma tace" A dakin Abbina na kwana gurinsa meyesa Baku duba canba??? Maida kallonta tayi kan Abbin tana ciko idanuwanta da Hawaye tareda Bata fuska hawayen na saukowa tace" Abbi Ni ko a Australia na taba kwana ba gida bane? Haj umma tace saina fada inda nakwana Ni kafada Mata agurinka na kwana... Dan dafe gashinsa yayi daya fara Masa wani irin nauyin abinda take fada din..... Ganin haka ta fasa kuka tana kallonsa kafin ta maida kallonta kan Haj umma datai mutuwar tsaye zatai magana cikin kuka tana riqe towel dinta dake Neman faduwa ba tsammani su Haj umma sukaga yayi saurin riqe Mata towel din tareda kallonta cikin Ido a natse da qaramin sauti yace" Ya Isa menene na kuka anan Kuma? Ni Abbi ka fada Mata Inda na kwana taji da kanta.... Naji ya Isa kukan kije ki saka kaya sanyi zai kamaki ahaka.... Haj umma ya juyo ya kalla cikin takaita Rigimar yace" Umma please tayaya zaku fara tunanin Inayah Zata iya zuwa wani gurin ta kwana.... Umma yaganah ya kalla Yana Dan sake kokarin danne 'dacin da zancen yayi Masa yace" Tayaya zaku fara wannan tunanin akanta? ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/10, 4:37 PM] Sweet sis: *_56_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Umma yaganah kinfi kowa sanin halinta da tarbiyarta tunda sbd ke ne kika riqeta... Haj umma please for God sake haryanzu Inayah yarinyace ki Dena biyewa wautanta haryanzu kaman babyna c.... Umn I mean she's too young for all ths manya manyan maganganun..""" Haj umma kasama cewa komai tayi Dan Kuma ai kaman Al'amarin yafi qarfinta tun bayan barin Inayah gurin takasa dauke idonta akan hanyar databi shiyasa ma maganganunsa ba duka ta fahimtaba Dan tashiga tunani Kuma. Umma yaganah Kam sanyi jikinta yayi duk da Daman Bata taba kawo wani banzan tunani ko zargin komaiba akan Inayah Dan MAJEED dinne kawai zai nuna Mata sanin Inayah Amma kome zaa fada ko akawo Mata tasan Inayah bazata taba aikata wani banzan abuba bare kawo tunanin ta kwana wani gurin, Dama tunda ta sanarda Haj umman Bata gantaba hajiyar ta ringa fada tana masifa tareda fadan maganganu marasa Dadi akan Inayar shine fa tafara Kiran MAJEED din a waya Dan ta sanar Masa komai yasan matakin dauka tun kafin 'yar tagama lalacewa ya miqawa uwarta ita tunda so take abata 'yar saiga wannan sabuwar maganar. Barin palon yayi Kai tsaye ya nufi dining room sbd bawani lokacin zai bataba yanada gurin zuwa. Yana Zama Haj umma ta iso itama ta zauna tana kallonsa fuskarta ba walwala ko kadan magana zatai dashi. Umma yaganah Kam Bayan Inayah tabi dakinta Tana shiga ta tadda Inayah din na shiryawa hankali kwance sai Qamshin khumrahs masu Dadi da Black opium dinta ke tashi. Kallonta umma yaganah takeyi dakyau tace" Inayah kinsan idan Baki nutsu kin Dena wannan shashancinba Zan Dena biye Miki, Meyesa Zaki tsaya gaban mahaifiyar ABDULMAJEED kice Mata a dakinsa kika kwana? Kallon umman ta juyo tayi a sanyaye tace" Umma yaganah kiyi hakuri bafa Karya nakeyiba wlh acan na..... Kinga banson ji amma ko can kika kwana be kamata ki kalleta ki fada Mata hakanba Shi kansa MAJEED din kunya kike sakasa agaban mahaifiyarsa. Shiru tayi umma yaganah tayita yimata fada kafin tadawo nasiha da rarrashi. Hakuri Inayah ta Bata kaman yanda tasaba duk qanqantar lefi Bata Jin gazawa ko nauyin cewa ayi hakuri. Cikin fluid Palazzo black da milk Waverly wrap top ta shirya sai scarf da qaramin veil data nado akanta suka fito tareda umman fes da ita fuskarta ba kwalliya Amma lip balm dintanda eyeliner dinda shine abinda yake qarawa kyakkyawar farar fuskarta kyau koyaushe. Sun shigowa dining room din akanta idanuwansa suka fara sauka Itama kusan akansa idonta ya sauka din. Murmushi tasake Wanda yasashi dauke Kai ahankali yana Dan gyara maqoshinsa dayaji Yana bushewa take.. Haj umma kallonta tayi tana Dan Kama kanta Dan maganarta datayi da majeed din akan Inayah dataga kaman Babu abinda yake ganewa idan akan lefin Inayah ne, Tarasa masifar datafi Inayah a rayuwarta sbd akanta 'danta ya zabi yabarta shekarun baya Kuma ko yanzu idanba bude Masa Ido yayi akan munafurcin maceba zai sake rufewa ne. Zama INAYAH tayi gefen Abbin tana satar kallonsa Shikuma gabaki daya indanuwansa nakan wayarsa dayake duba Sako saidai kusan hankalinsa baya kan wayar yanajin qamshinta na shiga hancinsa Wanda ya talasta Masa ajiye wayar gefe tareda juyowa ya kalleta da idanuwansa dasuka sata Jin tsikar jikinta tashi saidai takasa iya juyowa ta hada idon dashi sai kawai ta maida hankali kan serving dinsa tanajin idanuwansa akanta Wanda shikuma idanuwan Haj umma na kansa tana kallon ikon Allah dayafi karfin bawa. Har aka Gama cin abincin yau Babu Wanda yayi magana sai Inayah data bude Baki tabawa Haj umma hakurin abinda yafaru dazu cikin sanyi da son hajiyar ta hakuri. Shiru hajiyar tayi taqi amsawa... Aje spoon dinsa yayi tareda miqewa tsaye can qasan maqoshi yace musu saiya dawo. Yanayinsa kobai fadaba yasa Haj umma jikinta yasake sanyi da Al'amarin Dan kuwa tasan zuciyarsa ta sosu ne da shirun dataiwa Inayah. Inayah ma miqewa tayi ba damuwa a fuskarta tace" Umma yaganah na tafi Abbina zanbi ya ajiyeni, Haj umma bye... Handbag dinta ta sauka tareda wayarta tabi bayansa. Ko data fito harabar gidan motar data gani setin kofa tasan shine zaiyi tuqin da kansa Dan duk aka fiddota to shine zaiyi driving da kansa Dan haka ta nufo motar Kai tsaye ta shiga gaba. Zaune yake cikin motar da alama ita yake jira kenan ko Bata ambataba Abbinta yayi niyar kaita aikin da kansa. Tada motar yayi tareda juyowa ya kalleta Ya maida idanuwansa ya zuwa shigar jikinta Yana kalla.... Ahankali yace" Ina coat naki? Gefenta ta nuna Masa tana cewa" Gashinan tareda handbag Dina. Motan yaja suka fice Yana maida hankalinsa kan driving dayakeyi saidai qamshinta na neman rarraba hankalinsa Wanda ya rasa meyasa hancinsa yake daukan qamshinta komai kankantarsa tun ba yanzuba. Suna Isa asibitin ya ajiyeta tareda kallonta yayi Mata ta kula yaja motar ya wuce itama ta shige akan idon umma Hadiza data Kira umma yaganah tace Mata Inayah din na hanyar zuwa aiki. Inayah Bata qarasa shigaba Hadiza ta iso gurinta tana kallonta cikin kulawa ta Kira sunanta. Inayah na ganinta ta sake murmushi tana cewa" Good morning. Dariya Hadiza tayi tana kallon yanda farin ciki ke kwance kan fuskar Inayah din tace" Yaya jikin? Harkin warke wannan farin cikin na fuskarki fa? Nasan bazai wuce na Abbinki Daya kawoki bane. Kallon Hadizan tayi tareda sakin murmushin Daya qarawa fuskarta kyau tace" Harkin sanni haka da wuri? Dadin maganar Hadiza taji ta riqo hannun Inayah din tana sake murmushin farin ciki tace" Bakida wuyar fahimta Ayshatouh sbd bakida wahalalliyar zuciya da rayuwa halin mahaifinki kika dauko baida damuwa ko kadan duk yanda rayuwa tazo Masa karba yakeyi hannu babbiyu... Sanyi jikin Inayah yayi ta zame hannunta ahankali tana cewa" Allah yaji qansa" Amma zuciyarta har lokacin batajin Hadizan da mahaifinta data ambata kaman yanda takejin Abbi daya cike gurbindaya kamata su zauna a zuciyarta duk da ko ahakan yanzu tanajin kaunar Hadiza aranta. Bata shigaba daganan ta juya tabar Inayah itama Takoma gida. Inayah ma shigewa tayi tana waya da Neesah datake kiranta suna maganar wani abun dabam. Sai yamma tadawo gida a Dan gajiye Kuma Hadiza ce tadawo da ita gida batai Mata tayin shigowaba sbd haryanzu Abbinta baice komaiba akanta da Hadizan itama Hadizan Bata damu da shigarba sbd tanason bashi lokaci da kansa ya sauko ya Bata Daman kasancewa da yarta aduk lokacinda taso hakan. Tana shigowa ta taradda Dr farhat a gidan Bata wani damuba sbd Abbinta yace Mata ba auren zeyiba Dan haka Babu abinda ya shafeta da Dr farhat. Fuska ba laifi ta tsaya ta gaidata tunda sosai ta girmeta ba kusaba. Haj umma ta kalla itama cikin girmamawa ta gaidata kafin ta qarasa gurin umma yaganarta ta Dan rungumeta tareda Mata sannu da gida ta wucewarta zuwa bedroom dinta. Wanka tafara Yi ta sanya gajeran wando Mai Fadi blue da light vest ta fito bayan tayi sallar la'asar ta nufi kitchen gurinsu zubbi tasa Salimat ta dafa Mata noodles da kwai taci acan suna Dan Mata fira tana dariya sbd tanajin dadin firarsu Suma sunajin dadinta sbd ba ruwanta acikinsu sakewa take tana dariya idan suna Mata fira da labari masu ban dariya. Sai gab da magriba ta fito kitchen din sbd ta Dan saka hannu a aikin tace Zata fara koyan girki sosai sbd Abbinta tanason Nan gaba itace zatana Masa abinci. Koda ta fito har lokacin Dr farhat Bata tafiba Haj umma tace tunda magrib tayi ta tsaya tayi sallah anan suyi dinner da ita tukuna. Itama Bata wani musaba ta zauna din sbd tanason ganin MAJEED koba komai sbd gobe tafiya zatai zuwa Abuja daga can Kuma Zata koma Australia Amma duka daka bazata wuce wata dayaba zuwa biyu Zata dawo gida gaba daya tunda aurenta da MAJEED din yanata sake kankama. Wanka Inayah tafara Yi kafin tayi sallar magriba ta zauna tana yiwa Abbi txt din be dawoba. Tana tura sakon reply dinsa ya shigo Mata Ada alama wayar ba hannunsa sakon yashiga. Murmushi tasake tana karanta abinda ya turo, "Ina tareda cm" Love you my Abbi" kawai ta tura Masa tareda ajiye wayar ta miqe ta nufi dakin umma yaganah. A Palo ta taddasu har Haj umma da Dr farhat Dan haka gurin umma yaganah ta Isa ta zauna tareda kwantar da kanta a cinyarsa tana cewa" Umma kaina na ciwo kadan.. Dan fara massaging kan tai tana cewa" Rigimarkice datai yawa Ki rage sai kan ya Dena ciwo akai akai. Dr farhat ce ta saki murmushi cikin kulawa tace" Gaskiyar umma ne Inayah kullum cikin daga hankalinsu Haj umma kike da umma da rigimarki kaman ba likita ba... Dariya Mai kyau Inayah tayi tana cewa" Babyn Abbinta ce fa Ni, Idan na Dena Masa rigima waye zai masa? Kullum Ni zanyi tayi Ni kadai, Kuma haj umman ce take daga hankali akaina?.... Cikin raba Kai da wahala Haj umman itama tace" Daman Kam bazan iya daga hankali akankiba na na Hana kaina bacci a banza, Su dai dazasu iya suyita fama... Amma Kam maganar rashin ji da kema kike sane kike gashinan kina cewa zakici gaba dayi, Yana Tara qananun Yara Dole Zaki dawo hankalinki..... Shigowarsa batasa Inayah fasa maganaba tace" To ai Ni nayi Rigimar nawa 'yayanma idan sunzo suyi tasu, Mune zamuyita Masa rigima Yana rarrashinmu..... Dangwale bakinta umma yaganah tayi tana hanata karasa fadar sauran maganar. Yallaban kuwa yi yayi tamkar baiji abinda suke fadarba sbd zancen nasune dan ya lura Haj umma ita kesa Inayahn fadan wasu maganganun batareda taji nauyin fadarsuba. Kallonsa Inayah tayi daga kwancen datake tareda sakar Masa murmushi tana cewa" Abbi sannu da shigowa. Kallonta yayi tareda amsawa cikin kulawa. Su Haj umma ya gaidar shima tareda zaunawa a 2 seater Yana amsa gaisuwar Dr farhat batareda ya kalletaba sbd idanuwan Inayah dake kansa kaman ta taso ta rufe Masa Ido Dan kada ya kalla Dr farhat din Kuma yanajin idanuwan nata akansa. Kasa Haj umma ce ta kallesa cikin kulawa da murmushi kan fuskarta tace" Kaman gobe ne naji kace zakai tafiya Abuja right? Dr farhat ma goben Abuja Zata acan gidan juwairiyyah Zata zauna munyi magana da juwairiyyahn kafin jibi tabi flight dinta na wucewa gaba daya... Tunda kaima can din kayi inaga zaifi sauki ku wuce taren ka gaisa sosai da 'yan uwanka daga can.. Washe Baki Dr farhat tayi cikin Jin dadin maganar tana kallon MAJEED din a natse. Dan gyara murya yayi kadan kafin ya kalli Haj umman Kai tsaye yace" Flight din yamma zanbi ba buqatan ta tsaya jiran tafiya Dani. Miqewa yayi zai wuce ciki Umma yaganah tace" Angama shirya dining bazaka tsaya kaciba kafin ka shige?? Sai alokacin ya juyo Yana kallon Inayah yace" Ok. Inayah yake kalla ta hade fuskarta sosai idanuwanta ma kokarin cikowa da hawaye suke. INAYAH...."ya Kira sunanta a natse Wanda hakan yasa su Haj umma kallonta Umma yaganah Kuma miqewa tayi ta nufi dining Dan qarasa duba abinda aka jera kafin kowa yazo. Kasa dagowa tayi Saida yakuma Kiran sunanta cikin kulawa sbd yasan Zata iya rikicewa da rigima yanzu.. Dagowa tayi tareda miqewa tsaye batareda ta kalli kowaba ta nufi gurinsa ta tsaya gabansa ta dago ta kallesa da idanuwanta dasuke yagar zuciyarsa da dafinsu tace" Abbi Nima zanje abujan kaga bantaba zuwaba. Kallon Zaki kasheni yayi Mata ahankali kafin ya girgiza Mata Kai ahankali Yana cewa" No, Muje dinner is ready. Wucewa yayi gaba ta tsaya zuciyarta na shiga damuwa da rigima saidai wlh batajin Zata yarda yaje ba da itama saidai yafasa tunda Dr farhat bazata iya hanata tafiyarba suje can su qarata a gidan anty juwairiyyah din Amma Abbinta tunda Zata iya hanasa tafiya Koda rigimarta bazata Bari yajeba saidai yaje da ita. Haj umma ce ta kalleta tace" Karki yarda naji kin tada rigima akan tafiyar Nan ki dagawa bawan Allah hankali a banza ko tausayinsa bakyaji sai anyi magana kice Abbinki ne ke Babynsa ce.....ba baby ba wlh 'yar tsana. Kallon Dr farhat tayi tace muje kici abinci kafin ki tafi farhat kinji. Ajiyar zuciya Dr farhat ta ajiye kafin tace" Haj umma inaga Bari kawai na tafi basai na tsaya cin abincinba zanje na qarasa shirina kafin kigama magana dashi akan tafiyar idan ya amince. Ok shikenan Saida safen Inshallah Zan sake Masa magana yanzu. Kallon Inayah Dr farhat tayi tace" Bye Inayah. Batareda ta nuna bacin Rai ko wani abunba itama ta juyo bayan tafara tafiya tace" Allah ya tsare hanya Dr farhat. Tana fadar hakan ta juya ta nufi dining room Haj umma na bayanta tana kallon kayan jikinta cikin takaici. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/10, 10:03 PM] +234 703 623 7917: *_57_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Suna shigowa ya Dan dago ya kallesu Ya tsaida kallonsa kan kayan jikinta da masuda wani kauri leggings ne black Daya kwanta a siraran cinyoyinta sai vest me Dan Fadi Bata kwanta ajikinta ba.. Dauke kansa yayi tareda maidawa kan abincin da umma yaganah tagama zuba Masa ya dauki spoon a natse yafara ci. Itama gefensa ta qaraso ta zauna ta kallesa zatai magana ya dan lumshe fararen idanuwansa ya bude tareda girgiza Mata Kai yana cewa" Kici abinci tukuna kafin magana daga baya. Shiru tayi tareda gyara Zama tana zuba abincin. Ganin yakusa Gama cin abincinsa ya tashi yasa Haj umma kallonsa tace" MAJEED inason magana dakai zuwa anjima kafin kashige. Ok Inshallah" yace Yana daukan lemon juice Mara sanyi sosai yasha kadan ya ajiye tareda daukan tissue ya goge bakinsa tareda miqewa Yana cewa alhmdllh. Yana barin dining din ya fice daga gidan gabaki daya sbd akwai Inda zaije. Yana barin gurin Haj umma tafara gamawa itama ta tashi tabar Inayah da umma yaganah. Kallon umma yaganah Inayah tayi tana Dan Bata fuska tace" Umma bin Abbi zanyi abujan nidai bazan iya zaunawaba tunda Haj umma tafara maganan zaije tareda Dr farhat nasan takurasa zatayi Kuma Ni bazan yardaba. Numfashi umma ta sauke tana dagowa ta kalli Inayah tareda hango kishi me zafi dake cinta Kuma ita kanta tasan manufar Haj umma tayin hakan Dan haka bazata Hana Inayah binsaba indai shine yace zaije da ita Amma yanzu rigima kawai zasuyi tayi itada Haj umman su sakasa a damuwa sbd sun kasa gane sune mutum biyu dayafi so da kauna a rayuwarsa Kuma sunqi jituwa koyaushe rigimarsu neman sakasa damuwa take. Inayah kiyi hakuri karkice Zaki bisa tunda kinga wani aikin ne ze kaisa. Shiru tayi batareda zuciyarta tayi na'am da hakanba sedan Bata saba dogon musu da ummanba. Suna gamawa ta nufi dakinta tayi sallar ishai ta miqe kan sofa tana chatting da Neesah dake sake zugata akan tabi Abbin Kuma Dama itama batada niyar fasa binsa tana Nan tana jiran yadawo suyi magana. Sun jima suna chatting kafin ta aje ta tashi tayo wanka tayi Shirin kwanciyarta cikin Riga da wando guntu masu santsi sosai ta fesa turarenta ta nufi gadonta. Harta hau gadon ta tuna da maganar tafiyar Abbin Dan haka ta yaye bargonta ta sauko gadon tareda daukan wayarta ta fice zuwa gurinsa suyi magana. Ko data fito Kai tsaye palonsa ta nufa, Baya palonsa Dan haka Kai tsaye bedroom dinsa ta nufa ko knocking bataiba ta bude Qamshin Turarensa Mai dadi da sanyin AC ya daki fuskarta ta lumshe idanuwanta tana rufe kofar ta Isa kan couch dake dakin ta zauna tana cigaba da chatting sama sama tana jiransa. Koda yadawo Haj umma tariga tayi bacci Dan haka baije gurinta maganar datace zatai dashiba ya nufo dakinsa Kai tsaye Yana Kiran numbern Inayah dataita kiransa Yana driving bai luraba wayan na silent. Yasan tayi bacci Dan haka baiyi tunanin zuwa dakintaba ya tahowarsa. Wutar dakinsa yasama ba haske sosai so baiwani damuba ya tube Kai tsaye ya nufi toilet ya shige tareda sakarwa kansa ruwan dumi. Wanka yayo tareda brush ya fito ya nufi gaban mirror ya goge jikinsa Bai shafa maiba spray kawai ya fesa kadan ya saka dogon farin wandon bacci batareda ya sanya rigar wandonba ya nufi gadonsa tun kafin yahau Yana Isa hancinsa ya shaqo Masa qamshinta Daya Gama Zama kansa... Da mamaki ya kalli gadon da kyau Yana hawa gadon cikin sauke numfashi ya Dan yaye quilt dinsa sai gata kwance tana bacci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Rintse Ido yayi yabude ahankali Yana sauke numfashi a fili ya zauna Yana kallon fuskarta tareda tunanin meyasa tazo Nan Bayan yaqin dayake fama da kansa kan Hana qwaqwalwarsa dake din karfinsa dawo Masa da abinda yafaru Wanda kwata kwata yau din Babu abinda yake ganewa da kyau.... Kallon fuskarta yake yanda take baccin rungume da hannayenta da alama sanyi takeji, Kasa tashinta yayi Takoma dakinta sbd Zata iya ciwon Kai Idan ya tadata daga baccin Kwantawa yayi gefenta tareda gyara Mata rufarta ya lumshe ido yanajin qamshinta dake shiga hancinsa Yana halaka duk kuzarinsa. Ahakan yayi bacci wahalce yanajinta tana jujjuyawa cikin jikinsa cikin baccinta duk wata sauran mutunsa tagama yagawa acikin abin rufar hakanan ya riqe kansa suka kwana. Yana fita sallar asuba yauma ta tashi tayi Tata Tana gamawa taqi tafiya sbd jiran dawowarsa. Tana kwance cikin gadonsa ya dawo daga masallaci Yana shigowa ta tashi zaune tana kallonsa tace" Ina kwana Abbi? Kallonta yayi Yana zaunawa kan kujera yace" Kin tashi lfy? Saukowa gadon tayi ta miqe tsaye tareda nufosa Kai tsaye Ya dauke idanuwansa daga kallonta sbd Rabin fararen cinyoyinta dake bayyane cikin gajeran wandon kayan baccinta. Gefensa ta zauna tareda riqo hannunsa Kai tsaye tana Dan marairaice fuska tace" Abbi zanbika Abuja please Kaga bantaba zuwaba. Juyowa yayi ya kalleta Jin Qamshin mouthwash dinsa Mai Qamshin mint leaf na tashi a bakinta dake gaf da fuskarsa..... Wani Abu ya hadiye daga maqoshinsa tareda dauke Kai daga kallon nata ya Dan girgiza Kai kadan yanacewa" No. Sake matsowa tayi jikinsa sosai tana bayyanarda shagwabarta sosai tace" Abbi Dan Allah zanbika, To zanbi mijina idan Abbina bazaije saniba... Juyowa yayi Yana kallon bakinta dake wannan maganar lokaci daya Yana Sako Masa Qamshin cikinsa dayasashi aje wayarsa Dan baya gane abinda yake rubutawa Kuma. Yanda ya juyo fuskarsa Yana kallonta gaba Daya yasata yin qasa qasa da murya can kusan kunnensa ta sake cewa" Please Abbi, Baby Inayah dinkace fa.... A yanda dumin numfashinta da Qamshin bakinta suka saukar Masa a fuska yasashi matsota jikinsa da hannunsa daya batareda ya San yayi hakanba. Mannewa kirjinta yayi da nasa tsinin kirjinta ya sauka da kyau kan kirjinsa take bakinsa zuw maqoshinsa ya bushe Ita kanta tsikar jikinta tashi tayi sbd ba zato ya matseta da jikin nasa Dan haka ta dago tana kallon fuskarsa da shima ita ya zubawa idanuwansa dasuka sauya Yana kallonta jikinsu na sake mannuwa Dana juna. Wuyanta yakai fuskarsa yana shaqar qamshinta Daya Zama kaman wani jarabta agaresa... Cusa kansa sosai yayi cikin wuyan nata Yana lumshe ido tareda sake mannata da jikinsa yanajinta sosai jijiyoyin kansa na fitowa. Gangaro da kansa yayi zuwa gaban rigarta yasake shaqarta Yana rungume qugunta Dake hannuwansa dakyau. Jin yanda yake sauke numfashi masu dumi sosai a fatar wuyanta zuwa saman kirjinta yasata dago fuskarsa tana shafawa cikeda kulawa da kauna ta bude Baki Zata Kira sunansa ya rufe bakin da nasa yanda zakulo Qamshin bakin Daya Gama cushe kansa... Kissing dinta yakeyi sosai Yana shanye yawun dayake zukowa bakinta cikin wani irin Nishi Mai sanyi da zafi lokaci daya. Gaba Daya sakewa tayi ajikinsa sbd ita kanta zaqin harshensa takeji a nata bakin dayakesha, Hannuwansa dake safa wuyanta zuwa bayanta taji suna tada Mata tsikar jiki tareda kashe jikin Dan haka ko idanuwanta kasa budewa tayi abbin kawai takeyi tako Ina a gangar jiki da zuciyarta. Daqyar ya iya seta kansa ya saketa ahankali Yana kallon gashin kanta me santsi dake daure duk sun wargazashi, Kan rigarta Daya kusa farkawa ya maida kallonsa yana Dan miqewa tsaye sbd zai iya aikata abinda yafi hakan idan Bai tashi agurin ba. Toilet ya nufa Kai tsaye ya shige Yana Jan numfashinsa dake neman sarkewa da halinda yake ciki. Yadauki lokaci kafin yafito wanka sanyeda bathrobe fara. Bata dakin ta wuce dakinta sbd itama kwanyarta ta yamutsu sosai da sakon abbin nata. Itama tana Isa bedroom dinta toilet ta nufa ta shige tareda rufo kofa. Wanka tayo ta fito tana zaunawa gaban mirror cikin nutsuwa. Fuskarta ta kalla tareda qurawa bakinta Ido tana lumshe fararen idanuwanta sbd harshenta datake Jin dandanon harshen Abbinta akansa har lokacin. Wani qayataccen murmushi ta sake tareda miqewa ta dauko wayarta dake kan gado ta Nemo numbern anty Hafsat takira. Tana dauka tace" Good morning anty Hafsat. Morning babyn Abbi. Fara jero Mata bayanin tafiyar Abbi da Dr farhat tayi kafin ta Dora da cewan binsa zatai. Ba kunya anty Hafsat tace" Kibisa Kam idan ba hakaba dagacan zamuji mugun labari tunda kawunsa yanacan abujar Kuma itama kaman yayyun mahaifinta na abujan... Waro Ido Inayah tayi waje cikin tashin hankali da firgici tace" Anty Hafsat Dan Allah kice umma yaganah Tai Masa magana nidai zanje wlh bugawa zuciyata zatai idan yaje da Dr farhat. Kece dai Zaki Masa magana Karki yarda yaje badakeba Nima hankalina be kwanta atafiyarba shi kadai tsaf zakiji ankai karshen maganarsu acan..... Tashi hankalin Inayah yayi tafarajin wani nauyi na mamaye zuciyarta ba Shiri ta tashi daga ita sai bra din data saka fara tas sai towel ta fice zuwa dakinsa. Haj umma na zaune Palo tazo wuceta da bra da towel din Baki haj umma tasake tana cewa" Ke,ke,ke Inayah ke, Ina Zaki haka dawo Nan..... Ko ta kanta Inayah Bata tsaya bi ba ta nufi hanyar palon Abbin tana Isa ta shige ta nufi bedroom dinsa Kai tsaye ta Shiga. Tsaye yake gaban mirror har lokacin ba Kaya jikinsa Dan Bai Dade da fitowa wankaba shima mai yagama shafawa ya juyo Yana kallonta. Strapless bra din dake jikinta qyam ya idanuwansa suka sauka ya zuwa cikinta Dake bayyane Ya tsaida kallonsa kan qaramar cibiyarta data Sara kansa lokaci daya Ya dauke Kai Yana cigaba da abinda yakeyi yace" Meyasa Zaki fito haka? Karki dama kanki da rigiman tafiya Abuja Babu Inda Zaki.. Hawayen datake riqewane kawai suka fara sauko Mata ta zauna kan kujera tareda fashewa da kuka ahankali Mara sauti. Qaramin sutin kukanta yasashi ajiye Turaren dayake fesawa ya rintse Ido Yana sauke numfashi sbd kukanta wani babban weakness dinsane Kuma tasan hakan tuntuni shiyasa take hakan. Juyowa yayi zuwa Inda take ya tsaya cikin kulawa yace" Meye na kuka Kuma yanzu? Me zakiyi a abujan? Kai zanbi., Nidai kaje Dani Dan Allah Abbi. Bayason kukanta Dede da second daya, Hawayenta shine abinda yafi baqin ciki da tsanar gani.. Tayar da ita yayi tsaye Yana kallonta a natse yace" Shirya Zaki abujan Amma gidan anty juwairiyyah zaki zauna okay??? Gyada Kai tayi tareda kallonsa tana cewa" Na yarda. Ok shikenan jeki ki saka kaya kafin sanyi ya kamaki. Juyawa tayi tabar dakin ya sauke numfashi kadan tareda komaw Yana qarasa shirinsa. Tana komawa dakinta ta doguwar Riga kawai ta saka ta fito breakfast sbd yunwa takeji sosai. Dakin umma yaganah tafara zuwa ta gaidata kafin ta nufi gurin Haj umma ta gaidata cikin sakewa. Ko kallonta Haj umma bataiba tayi kaman Bata jitaba sbd tagano Inayah tagama renata. Suna zaunawa cin abincin saiga qamshinsa ya doso gurin take sukasan Yana hanyar shigowa daga Haj umma har Inayah kusan tare suka kalli kofar daidai shigowarsa cikin wata lafiyayyar navy blue filtex me shegiyar tsada sai qube kalar kayan nasa Fuskarsa kawai Inayah ta kalla taji zuciyarta da jikinta na mutuwa akansa a fili tace" I love you my Abbi,my husband,my....danne qafarta umma yaganah tayi da tata qafar... Rikicewa Haj umma tayi da tea din datake hadawa Jin Inayar. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/10, 10:04 PM] +234 703 623 7917: *_58_* *_Arewabook@Mamuhgee_* Cikin idon Inayah din ya kalla da qaramin bakinta Daya furta kalmar ya lumshe idanuwansa dasuka saka Inayah din sake Jin son Abbinta ya zauna Yana gaidasu Haj umma da umma yaganah kafin ya kalleta yace" Bakin Nan baya shiru ko gaban kowa ko? Murmushi tayi ba zato tasake cewa" I love you Abbi. Wannan karon wani qayataccen miskilin murmushi ne ya sauka a fuskarsa Wanda yasa umma yaganah Jin kanta gingirim Haj umma kuwa duk qarasa rudewa tayi tana lafta shuga a tea.. Umma yaganah ce tace" Haj umma sugan Nan bazai Miki yawaba kuwa? Sai alokacin Inayah ta juyo ta kalli Haj umman tana murmushi tace" Haj umma kema I love you. Wannan karon kasa hakuri Haj umma tayi tace" Gidanku Inayah, MAJEED kana gani yarinyar Nan Zata maidani abokiyar wasanta ko? Kallon Inayah yayi da idanuwansa dake kasa boye kaunarta wasu lokutan yace" Ki bawa Haj umma hakuri Kuma ki Dena Mata rashin ji Bana fada Miki hakanba? Abbi da gaske nake fa ina Sonta sbd itace mamanka. Kallon Haj umma tayi cikin kulawa tace" Kiyi hkr Haj umma bazan sake. Ciki ciki da murya ta amsa tana cewa" Zaki sake nama sani Allah dai ya kyauta yasa kugane ku duka. Amin" Umma yaganah ta amsa tana murmushi da cewa" Wasan Kaka da jikane take miki Haj umma Dan Bata dauki bangaren sirikaba. Shiru Haj umma tayi tanason cewa Bata fata saidai tana shakkar yanda MAJEED ze dauka yanayin sbd tafara gano da gaske dai baya hada Inayah da komai, 'yar datayi sanadin barinka gida, Ka rabu da uwarka da Yan uwanka da danginka da rayuwarka ta daula ka qare a yawon dako da gadi Amma memakon ka guje wannan 'yar jinta kake kaman kurjin zuciya da Baya ganuwa bare a taba. Inayah dai yau Satan kallon Abbita takeyi sbd kyan da yayi Mata hakama duk ya diba abinci yakai bakinsa saita kalla bakin cikin wani irin shauqi tana tuno dandanon lips din nasa da zaqi harshensa cikin bakinta. Jin idonta akansa tun dazu yasashi waiwayowa ya kalleta, Shima bakinta ya kalla tana tauna chips ahankali ga tomato ketchup ya Bata gefen lips din nata kadan. Tissue ya dauka tareda kallon bakin ya goge Mata batareda yasan yayiba shaf idonsa da kansa sun manta dasu Haj umma dake zaune taredasu.. Yana goge Mata ta riqe hannunsa agurin a sakalce tace" I love you Abbi. Duk lokacinda ta fada wannan kalmar duniyarsa gabaki daya take jijjjigawa, Neman rasa kansa yake saiya riqe da karfi sbd komai zai iya faruwa idan tana yawan fadar wannan kalmar me yamutsaba. Wannan karon Haj umma tafara tashi tabar gurin sbd zuciyarta bazata iya daukan ganin wannan rashin mutuncin na Inayah ba gashi Zata lalata Mata tsohon tuzurun 'da. Umma yaganah ma tashi tayi ta tafiyarta zuwa kitchen tabar gurin. Suna tashi Inayah ta kalli kofar dasuka fice Yana murmushi ta tashi tsaye tadawo kan cinyarsa ta zauna tana kallon fuskarsa datake Tona asirin zuciyarsa tace" Abbi na kayi kyau yau sosai, Nima sainayi adon dazan maka kyau Kuma saika yaba tunda Nima na yaba. Murmushi ya sake a hankali tareda shaqar qamshinta a boye Yace" Meyasa zakiyi rigiman zuwa Abuja? Sauyawa muryarsa tayi a shaqe yace" Kiyi zamanki karki bini... Hannuwanta ta rataya a wuyansa tareda matso da fuskarta kusa da tasa itama qasa qasa tace" Bazan iyaba Abbi, Zuciyata ciwo zatayita Yi idan katafi da Dr farhat.. Cikin idonta ya kalla Yana Jan boyayyan numfashi me Qamshin da dumin nata numfashin a kasalance yace" Waye Dr farhat? Wani irin Dadi da farin ciki maganarsa ta sakata Batasan lokacinda ta rungumesa ba tana dariyar farin ciki tace" She's no one. I love you Ab.......Bata qarasaba ya dago fuskarta yayi bakinta kyakkyawar kamawa da nasa sbd tundazu datake juya Masa Kai da kalmar.. Wani irin kiss yakewa bakinta Yana matseta jikinsa tana sake matsesa zuciyarta cikeda farin cikin abinda ya fada. Itace tafara Jin motsin zubbi Dan haka ta zame bakinta tareda dagowa ta kallesa gabaki daya ya juye da alama ma ya manta Inda suke... Murmushi ya saki tana boye dariyarta tace" Abbina nawa Ni daya, Kana lattin fita fa. Murmushi dabai San dashiba ne ya zuwar Masa. Tayar da ita zaiyi zubbi tashigo tattara gurin tagansu ahakan da sauri ya juya a rude tayo Palo Haj umma dake zaune tana gadin lokaci tace" Makanta zakiyi Nan gaba ma indai Inayah ce, Nema zauna ki nutsu tukuna ki koma aikinki. Cikin ranta ta qarasa da cewa" Tanacan tanawa bawan Allah iya shege. Shine yafara fitowa daga dining room din Yana Dan gyara wuyan rigarsa da hannu daya data yamutsa Dayan hannun Kuma Yana cikin na babyn nasa data riqe tanata sakin murmushin farin cikin Abbinta da maganar da yayi akan Dr farhat. Bai lurada Haj umma ba Saida Inayah taga yanda Haj umma ta daure fuska sosai tace" Haj umma mun fito...... Sai alokacin ya lura da Ido ya kalli Inayah da alaman"keep quite" Shiru tayi tana sakin hannunsa ta tsaya daga Nan ya wuce ta juya zuwa dakin umma yaganah. Acan dakin takira anty Hafsat ta sake sanar da ita maganar tafiyan da ita zaayi. Tana Gama waya da Anty Hafsat saiga Kiran umma Hadiza yashigo wayarta. Cikin sakewa ta dauka tana cewa" Good morning Umman Dr. Murmushi da dariyar farin cikin yarta data Zama free mutum ba ruwanta tayi kafin tace" Antashi lfy Dr INAYAH A MAJEED¿ Yasu umma yaganah da Abbin naki? Murmushi tayi tana dawowa gefen umma yaganah ta zauna tace" Lafiyansu kalau, Ya Dr Abdulsamad? Oh sorry kaman a asibiti zai kwana jiya right? Eh a can ya kwana gashi Zaki Kuma tulawa 'dan bawan Allahn yarona aiki ki gudu da Abbinki sbd gata ko tausayin 'dana bakwayi Yana aiki asibitinku. Dariya Inayah tayi tana cewa" Bazan dadeba Zan dawo Kuma ai namasa waya na sanar dashi tunda ai sune manya a asibitin. Wane time zaku wuce inason kawo sakon Anty iklimat ki wuce Mata dashi sbd idan kinje idan abbin naki ze Bari saiki Kai Mata ku gaisa tanata son ganinki kinji? Shiru ta Dan kafin tace" Sai Abbina idan ya yarda zanje. Ok ganinan zuwa gidan Banda mintuna Zan kiraki saiki fito. Ok Tom. Suna aje wayar umma yaganah tace" Idan ta iso tashigo Mana tunda dai ba cewa yayi kada ta Kuma shigowa gidanba, Koba komai ai anzama Daya Dole ko baa so tunda ita sirikarsa ce itama Kuma sirikinta ne uwa uba su biyun kaman sune asalinki. Acan Hadiza kuwa wasu kayan dataiwa Inayah siyayya tun kwanaki da Anty Hafsat tafada Mata aurenda ake tunanin Haj umma Zata saka MAJEED yaqara takeson Bata Amma tana dakatawa sbd batason batawa AA MAJEED din kokuma yaga tanason Bata Masa 'ya yasa Bata bawa Inayar ba Amma yanzu Kam Bata zatayi suje can su qarata ko zaa samu ya rage wannan kame kamen fuskar ya dawo mutum kaman kowa. Mintuna masu Dan yawa dauka kafin ta iso gidan sbd sunada Yar tazara Tana parking takira wayar Inayah saiga zubbi ta fito tashigo da ita har dakin umma yaganah. Zaunawa tayi suka gaisa a sake sbd zuwa yanzu sun saba sosai Musamman kullum sai Hadizan takira umma yaganah. Kallon Inayah dake kwance tana faman chatting take bayan sun sake gaisawa tace" Ga sakon Anty iklimat" wata qaramar envelope ce da takarda aciki. Karba tayi tana cewa" Iya sakon kenan? Na dauka Babba ne¿ No wannan dinma Babbane sbd yanada mahimmanci sosai agunta takardan Daya shafa aikinta ne. Fira suke sama sama ita Kuma tana chatting a waya sosai suke fira Neesah akan tafiyan nata da Abbi. Umma yaganah ce tace" Inayah tashi ki raka ummanki taje ta gaida Haj umma Basu gaisaba Dagacan kuje dakinki ta tayaki hada kayan tafiyar sbd idan aka biyeki sai abbin yadawo Baki hada komaiba. Tashi tayi suka fito tareda Hadizan tana cewa" Yanzu muna zuwa zanyi lefi agurin Haj umma. Suna shiga kuwa dakin ta zaune kan kujera Salimat na gasa Mata qafafunta ta kallesu da mamaki bayyane kan fuskarta tace" Baqi akai gidan kenan? Zaunawa Hadiza tayi tana gaidata cikin girmamawa da Yar sakewa... Inayah Kuma gadonta ta nufa Zata zauna sbd sun cike kujerun biyu dake sakin Cikin babban sauti tace" Maza karki haumun gado ki yamutsa kaman yanda kike mulke gadon yaganah sbd Bata Miki fada, Zo zauna gefen mamarki karki yamutsan gado. Kai Haj umma daga Zan Dan hau? Baga Salimat nanba saita gyara Miki. Banaso jeki kiyita yamutsa Wanda kika Saba na yaganah. Miqewa Hadiza tayi suka fito tare tana dariyar Rigimar Haj umman da Inayah. Suna Isa dakin Inayah Hadiza tafara kallon koina dakin cikin nutsuwa da kulawa tareda mamakin zuciya irinta MAJEED, Dakin Inayah yafi kowanne daki girma da tsaruwa tareda Jin dukiya a gidan bayan dakinsa Wanda Batasan Yaya yakeba, Komai na Inayah a gidan da rayuwarsa is different, Komai nata na Musamman ne sbd ya banbantata da kowa a rayuwarsa, Meyesa yake tsananin so da kaunarta irin haka Bayan qyamatarta yakamata yayi sbd rayuwarsa data lalace sanadinta Dana uwarta. Zama tayi kan sofa tana ajiye qaramar paper bag din hannunta me tambarin Alex Mill. Cikin kokarin sakewa da 'yarta tace" Ina luggage dinki? Zubbi ta qwalawa Kira a waya tazo tace ta dauko akwati Daya acikin akwatinanta dake sama jere kan closet dinta. Rimowa suitcase din da zubbi ta dauko Hadiza ta kalla tana kiyasta kudinsa a ranta sbd MJ Muhammed yanada irin set din cikin luggages dinsa. Da kanta tanufi closet din Inayah din tana zaban Mata kayan dazata saka Mata a akwatin.. Kaya kalilan ta daukan Mata marasa nauyi da wahala sai tsadaddun designer kayan baccin data siyo Mata tazo dasu. Undies de tasa Mata da yawa sbd lurada Inayahn nada tsafta sosai Dan ko undies dinta dake jere basa iya kirgiwa tun daga kan wainda aka fasa da wainda Bata taba amfani dasuba. Tana Gama hada Mata kayan ta tsayar da akwatin gefe ta dawo ta zauna gefenta tareda karban wayar hannunta ta ajiye gefe tana cewa" Inayah kin taba tafiya kuwa dagake se Abbinki? Girgiza Kai tayi tana kallonta tace" Baya zuwa damu koina koyaushe muna gida nida umma yaganah. Numfashi umma Hadizan ta sake tareda riqo hannunta tana Mata Yan maganganu irin na uwa da 'ya. Sun jima a dakin kafin suka fito taje tayi bankwana da Haj umma suka fito itada umma yaganah da Inayah har harabar gidan ta Shiga mota ta wuce suna shigewa Abbi na dawowa gidan. Bai Bata lokaci ba kawai dakinsa ya nufa Kai tsaye ya shiryo yafito janyeda qaramar givenchy luggage Mai shegiyar tsada da kyau Kai tsaye yacewa Inayah ta samesa mota sbd sun Dan Yi latti zuwa airport din. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/11, 9:11 PM] Ummulkhairi: *_59_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Haj umma Dole rasa bakin magana tayi sbd mamakin Daya Gama cikata ganin da Inayah zaayi tafiyar,, Tana kallo Inayah ta fito jayeda akwati ta wuce ta gabansu tana masu bye bye harda hawayen kewan umma yaganah da Basu taba tafiya Kota kwana daya bace ba tareba sai wainda tayi da abokan karatunta da suna Australia. Haj umma yau takaicin da mamakinta har akan umma yaganah datakega tamafi kowa Zama mutuniyar banza. Inayah na fita driver ya karba akwatinta yasa bayan boot ta bude baya Inda Abbinta yake zaune Yana waya tashiga driver yaja motar sai airport. Suna Isa kaman hadin Baki saiga Dr farhat qaninta ya kawota airport din. Cikin mamaki take kallon Inayah duk da tana tunanin ko kawosa airport kawai tayi dan ya wuce fuska a sake tace" Babyn Abbinta ce takawosa airport din da kanta yau. Murmushi itama tasake tana kallon ashraf qanin Dr farhat din tace" Yaya ashraf barka da yau. Gun Dr farhat ta dawo da kallonta har lokacin da murmushi kan fuskarta tace" Ba rakosa nayiba Dani zaije hankalina be kwantaba da tafiyan Abbina shi Daya. Dan waro Ido Dr farhat tayi cikin mamaki da dariyar rainin hankalin Inayah tace" Waini yaushe duk kika Zama hakane Inayah? Maganar Haj umma Gaskia ce gata na neman maidaki wata abin dabam, Abbin nakine kike cewa Zaki raka sbd hankalinki be kwantaba? Shima AA MAJEED Gaskia yakamata yarage Miki wannan gatan ya fara Zama wani iri. Dariya Inayah kawai tayi tareda wucewa gaba tabi Bayan Abbinta da Bai wani tsayaba tun fitowarsa mota ganin Dr farhat. Jirgi Daya suka Shiga Kuma dukansu a first class suke Dan haka Inayah ganin Yana tareda CM da wani babban mutum abokinsu Daya yasata zaunawa gurin Dr farhat tana Dan biyewa zancenta sama sama Danma umman Dr Abdul tasata Dena nunawa Dr farhat din shariya da wani abin shiyasa take daurewa tana basarwa a gabanta Kuma hakan yasata Jin dama Dama da yanzu rigima Zata fara. Shi kansa Abbin zaune yake dasu CM din Amma zuciyarsa na kan Inayah dake tareda Dr farhat Sam bayason ta dauki damuwar ganin farhat din suje ta daga hankalinta kawai. Maganar Dr farhat damunta takeyi Musamman muryarta jinta take tana toshe maqoshinta da kishi sbd har maganar Abbinta takeyi cikin nuna kulawarta da kaunarta garesa,. Rufe idanuwanta kawai tayi tareda yin baccin qarya sbd kawai tai Mata shiru da fadan sunan Abbinta a bakinta sbd hakurinta da juriyarta sun fara qarewa. Dayake tafiyar yamma sukai ana Isha suka sauka. Motoci biyune daga gidan Wanda suke tare sukazo daukansu CM dashi Alhj falalun suka shiga mota Daya suka wuce dayan motar kuwa shida Inayah da Dr farhat suka Shiga. Shine a gaba tareda driver sai ita da Dr farhat a baya. Kai tsaye gidan anty juwairiyyah suka nufa Dr farhat itace me bada address din da alama harsun Saba koma har ta taba zuwa gidan. Suna parking shine ya daga wayarsa yakira anty juwairiyyah din.. Tana dauka Kai tsaye yace mata" Gamu a gaban gidanku. Da Murna anty juwairiyyan ta tashi daga zaunen datake cikin babban palonta tareda 'yayanta da Anty safiyyah ma tana gidan tana jiran isowarsu taga MAJEED dataketa gani a hoto yazama babban mutum masu fada aji. Fitowa sukayi harabar gidan anty juwairiyyah tasa megadi ya bude musu gate suka shigo da motar. Ana parking Dr farhat ta fito cikin farin cikin ganinsu suka rungume itada anty juwairiyyah dasuka Saba sosai a waya. Inayah kuwa qin fitowa motar tayi ta kalli Abbinta dashima ita yake kalla ta mirror yace" Ya ya? Marairaice fuska tayi tareda ciko hawaye a idonta na kishin Dr farhat dake cinta sosai tana dannewa tun a Abuja zatai magana ya bude motar ya fito a natse kwarjininsa ya cikawa su Anty juwairiyyah da 'yayansu dasuka fito gaida uncle din nasu da Basu saniba sedai labari Ido, Anty safiyyah Neman daburcewa takeyi da zallar haiba da kamalar da Allah yacikasa da ita ga uwa uba dala data Kama ta zauna.... Gefen da Inayah take ya bude ahankali tareda kallonta cikin kulawa yace" Rigiman me zakiyi ba kince Zaki zauna anan ba kafin nagama mukoma? Fitowa motar tayi ahankali tareda tsayawa gefensa ta riqe hannunsa cikin shagwaba a hankali tace" Aa bazan iya zaunaba anan Kuma. Numfashi ya sauke tareda juyowa suka nufo gurinsu anty juwairiyyah dasuka ja poster duk su dukan suna kallon ikon Allah Baki sake. Anty juwairiyyah data 'dan San kadan daga halin Inayah da rayuwarta murmushi tasake tana kallon MAJEED din batareda ta damu da halin Inayah ba a sake cikin kulawa tace" MAJEED barka da isowa, bazaka shigo ko abinci kaciba anyi maka dinner Musamman domin zuwanka Naga ka tsaya daga Nan. Agogon Omega dake daure hannunsa ya kalla kafin ya dago kyakkyawar fuskarsa ya kallesu Yana Dan kokarin wadata fuskar da murmushi Mai nutsuwa yace" Inada baqin dazan gani 9 Dan haka ba time din tsayawa cin abinci May be next Inshallah. Anty safiyyah ya kalla fuskarsa har lokacin da sauran kyakkyawan murmushinsa yace" Barr Ina wuni? Ya family? A daburce tace" Lafiya kalau alhmdllh, MAJEED zance kokuwa AA MAJEED? Wani murmushi yasake Yana amsa gaisuwar 'yayansu dake gaidasa cikeda girmamawa da farin cikin ganinsa. Farin cikin ganin yaran yasashi kallon tasa babyn datake riqeda hannunsa daya har lokacin Kuma a hakan ta gaisar dasu duka itama ba laifi fuskarta asake. Cikin kulawa yace" Ok I have to go Inayah time na tafiya kije ku shiga ciki zandawo gobe sai a kaiki Inda kikace din gidan Dr waye??? Qin sakinsa tayi tana kallonsa a Dan marairaice tace" Abbi Zan bika please. Ni bazan iya bacci ba anan muje goben se nadawo Nan. Ganin yaransu anty juwairiyyah na kallon zuqeqiyar budurwa na Dan shagwaba yasashi yanke Rigimar da cewa shikenan. Da kulawa Anty juwairiyyah tace" Haba Inayah kiyi hakuri ki kwanar Mana zakiji dadin Nan dinma Zaki Saba dasu rumanah gasunan manyan Yan Mata kamarki. Dan murmushin yaqe ta saki ahankali tana gefensa tace" Gobe Zan dawo saimu Saba. Baki anty safiyyah ta bude zatai magana anty juwairiyyah datasan a banza zatayi ta hanata sbd MAJEED akan Inayah baya Gene zancendaba Wanda takeso ba. Ita anty safiyyah so tayi MAJEED dinma ya tsaya su zanta sosai na yaushe rabo Su Kuma fahimci juna tunda dai yanzu dukansu ba quruciya atare dasu bare shi Daya Zama babban mutum duk da sune yannan Amma ai yanzu Kuma shine ubansu. Hannunta cikin nasa suka juya zuwa Mota bayan driver ya mayar da akwatinta da aka fidda tare dana Dr farhat data shige tuni Batasan Rigimar da aka tsaya Yi a wajenba Dan ta dauka MAJEED din ze shigo cin abinci kaman yanda anty juwairiyyah ta fada. Suna fita gidan ya juyo ya kalli fuskarta dakeda sauran rigima Itama ta juyo ta kallesa tana sake Bata fuska tace" Abbi da gaske nake bazan iya bacci acanba. Hannunta dake riqeda nasa ya dago ahankali yayi kissing yace" I Know. Murmushi tasake tareda sake matsowa jikinsa tana lafewa. Transcorp Hilton dake maitama suka driver yakaisu sbd acan akai Masa reserving Lafiyayyan daki. Tunda suka fito motar hannunta na cikin nasa driver na janyeda akwatinansu a bayansu kafin ma'aikatan hotel din suka karba Kai tsaye suka nufi lift suka shige zuwa dakinsu. Suna Shiga dakin ta saki hannunsa tana nufar tsadaddun kujerun Dake dakin ta zauna tana ajiye handbag dinta da wayarta Dake hannunta. Kai tsaye toilet ya wuce yayo wanka yafito daureda sabon towel fil da aka jera masu a dakin. Bai tsaya Bata lokaciba ya shirya tareda zuwa zura jallabiya fara Sol yayi sayi sallolinsa Yana idarwa ya kalli agogon Daya sauya na Patel Philippe yaga time yaja Dan haka ya tashi ya shirya cikin ash luxury filtex Mai tsananin taushi da shegiyar tsada ya juyo ya kalleta tayi zuru tana kallonsa kaman Zata rusa kuka ganin yanda yake zuba qamshi da wani cika Ido da kyansa da kwarjininsa. Ahankali ya shafa fuskarta yace" Zanje nadawo kiyi ordern abincin da kike buqatan ci ok? Dafa hannunsa tayi Tana gyada Kai. Juyawa yayi ya fice. Ajiyar zuciya ta sauke tareda tashi na nufi toilet tayo alwala. Sallolin dake kanta tafara Yi kafin ta tube ta koma toilet tayo wanka tareda gaso jikinta da ruwan zafi ta fito daureda towel itama. Mai tashafa sama sama tareda turare kadan ta bude kayanta ta dauko kayan baccin dazata saka taga duka Babu masu wando sai Yan dogaye da umman Abdul ta siyo mata, Tafison kayan bacci masu wando sbd sunfi dadin bacci agurinta Amma haka ta saka Daya daga cikin na umman Abdul din batareda ta damu da fingilewar rigarba. Tea da snacks sai kebabs tayi order aka kawo suka jere kan dining dake qatoton dakin suka fice kafin tazo ta zauna ta Sha tea sosai taci snacks da kebabs din kadan ta tashi sbd bacci takeji. Brush takuma Yi tadawo ta zauna kan kujera tana jiran dawowar Abbin Amma har bacci ya dauketa Bai dawoba. Sai guraren 11:30 ya dawo... Gabaki daya qamshin turarenta ya Gama gauraya sanyin ACn dakin.. Qarasowa yayi a hankali cikin nutsuwa ya tsaya akanta Yana kallonta wayarta na rungume a kirjinta da alama kiransa taketayi har baccin ya dauketa. Hannu yakai ya zare wayar zai ajiye gefe hotonsa Dake wallpaper na lock screen ya fito baro baro, kallonta yayi yana sake kallon wayar, Shafa fuskarta yayi ahankali tareda Kai fuskarsa yayi kissing lips dinta ahankali Yana kallon cinyoyinta Dake bayyane afili suna sheqin lafiya da hutu, Rigar jikinta yabi da kallo tun daga saman har Inda ta tsaya daidai ko Rabin cinyarta Bata kaiba Tabi ta lafe kan jikinta tagama bayyanarta ni'iman da Allah yayi Mata. Hannuwansa yasa ya dauketa cak tareda nufar gado da ita zai kwantar ta bude idanuwanta ahankali ta kallesa cikin bacci tareda Kiran sunansa a shagwabe tana komawa baccinta. Gyara Mata kwanciyar yayi tareda rufeta ya tashi ya rage kayan jikinsa ya sake komawa toilet baijimaba ya fito daureda towel ya saka wandon kayan baccinsa batareda ya saka rigar kayanba sbd kusan hakan dabiarsa be. Kwantawa yayi tareda Shiga tattausan white quilt din dake gadon ko Gama gyara kwanciya baiyiba ta shige jikinsa tareda lafewa kaman mage jikinsa da Babu Kaya Yana haduwa da nata dake sanyeda rigarda gwara Babu da ita. Ajiyar zuciya ya sauke ahankali tareda rage musu wutar dakin Yana sake gyara Mata kwanciya jikinsa. Da asuba kusan tare suka tashi sukai sallah suna idarwa ta zare doguwar abayar jikinta Zata koma ta kwanta. Shima jallabiyar jikinsa ya zare ba zato yajita jikinsa ta Dan kwanto tana cewa" Barka da asuba Abbi. Rigar Dake hannunsa ya ajiye Yana kallon kirjinta data manna Masa suka sukar kirjinsa tareda kunce notikan kansa a kasalance yace" Kin tashi lfy? Sake shigewa jikinsa tayi tana cewa" Lafiya kalau tunda na kwana gurin Abbina. Bakinta ya kalla cikin jin zancenta har zuciyarsa Ya shafo wuyanta Dake bude har zuwa kirjinta yana kallon yanda take lumshe ido da shafawar dayake matan. Wani mayen light kiss ya sakar Mata a fatar wuyanta Daya sanya numfashinta katsewa tareda qanqamesa batareda tasan tayi hakanba... Shinshinar wuyanta yakeyi kaman Wanda numfashinsa yake maqale agurin Yana kissing fatarta me taushi... Sake qanqamesa takeyi tana mannuwa dashi sosai numfashinta na neman yankewa da abinda yake matan Shikuma gabaki daya tagama birkitasa da kirjinta datake manna Masa yanajin laushi da tsininsu har cikin kansa. #MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/12, 2:41 PM] Ummulkhairi: *_60_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Fatar wuyanta ya saka harshe ya lasa cikin sanyi da nutsuwa Yana sake Jan numfashi cikin wuyanta, Daqyar ta iya Kiran sunansa cikin sanyi da yankewar numfashin tana sake qanqamesa sbd abinda yake Mata yafara fin qarfinta...... Sunansa data ambata yasashi dagowa ya kalleta da jajayen idanuwansa ya tashi zaune dakyau tareda dagota ya zaunar da ita kan cinyarsa dakyau suna shaqar numfashin juna cikin yanayi na tsananin kauna da buqatan juna... Cikinta ya shafo zuwa cibiyarta da sauri taja numfashi tana yin baya ya tarota tareda dawo da ita jikinsa yana sake lasar wuyanta zuwa kirjinta da tuni rigar jikinta ta zame kusan saman tudun kirjinta duka a bayyane suke yasaka harshensa ya laso tsakiyar kirjinta take ta sake wata zautaccen numfashin tana kokarin Kiran sunansa ya dago ya zura harshensa cikin bakin Yana laso yawun Dake tsinkewa cikin bakin sbd hannunsa dake wani irin aiki a kirjinta Yana Jan numfashi da qarfi shima... Juyawa yayi dasu ahakan suka kwana Yana Sama tana karkashinsa ya zame rigarta yayi wurgi da ita qasa Yana zafafa wasan sbd sosai yakejinta ayau din, Suka fatar Dake jikinta Babu Inda Bai Gama lashewaba da harshensa Yana sakar Mata numfashi Mai zafi da tada tsigan jikinta take hankalinta ya tashi gabanta ya ringa faduwa ba kakkautawa sbd Jin yanda jikinta yagama daukan zafi da zafafan kisses dinsa uwa uba yanayinsa ya tabbatar Mata da bazata iya daukan wannan babbar maganar ba Dan haka tafara dawowa hayyacinta saidai Kuma kisses din dayake bin fatar kirjinta zuwa cibiyarta sungama kashe jikinta tareda tsananta Mata sonsa me qarfi da bazata iya hanasa ko bayyanarda tsoronta ba....... Wata kyakkyawar zuqa yayiwa kirjinta daya sanyata sakin wani marayan ihun Nishi a daidai cikin kunnensa Wanda hakan ya Kuma yamutsa kwanyarsa daqyar ya iya bude idanuwansa dasukai jajir ya kalleta zazzafan Sonta na kwantar da zuciyarsa.... Fuskarta ya shafo zuwa digon wuyanta tareda sauke numfashi a Dan wahalce Yakai bakinsa yayi kissing idonta data bude a matuqar kasalance ta kallesa., Ya sake kissing din kunnenta Yana Kuma kallonta ahankali cikin tattausan sauti dake nuna yanda yake tausar kansa qasa qasa yace" Baby Inayah you are too special da bazan iya yin hakan dakeba a hotel.. Wani irin boyayyan numfashi ta sake tareda lumshe ido tana budewa akansa da qyar ta iya bude Baki murya Bata fita sosai tace" I love you Abbi.. Cikin tsakiyar idonta ya kalla da nasa idanuwan aciki yace" I love you bai Kai matsayin babyn Abbi acikin ransa ba..... Dagowa tayi daga kwancen datake qarqashinsa takai bakinta kan nasa tayi kissing lips dinsa ta dawo tayi kissing idonsa Daya lumshe takuma cewa" I love you my Abbi... Murmushi kawai yayi Yana zamewa daga kanta ya kwanta gefe Yana sauke numfashi ahankali sbd yasan ita kanta kalmar data fada Masa sbd Batasan yazatayi da abinda yayi Mata yawa a zuciya bane akansa Amma nata me saukine tunda tana iya ragewa da kalman love din a fili. Rungume kansa tayi a kirjinsa yanajin bugun zuciyarta ahakan sukai shiru tsawon lokaci har bacci ya daukesa. zuba Masa idanu tayi tanajin zuciyarta kaman bazata iya daukan sonsaba dayayi Mata yawa hartakejin kaman tabi hanya tayita fadan tana sonsa kowa yaji ya sheda hakan ko Zata samu sasssauci, Amma ahakan duk abinda takeji akansa kaman Zata zauce tasan abinda yake ji ansa ran yafi hakan, Nasa son ya wuce duk tunanin kowa dasuke Batasan Yaya yake iya riqe kansansaba Yana iya controlling na kansa da zuciyarsa..... Allah sarki Abbina Kai na dabam ne... Kissing kansa tayi Ahankali tana shafawa kaman baby sbd Abbinta tasan ya cancanci yasamu duk wani farin ciki da Jin dadin rayuwa. Itama baccin ne ya dauketa Dan haka Basu farkaba sai guraren 11 Dan haka suna tashi itace tafara yin wanka ta fito daureda towel Babba tana kallonsa Yana amsa waya a natse cikin class da kamewa sai kawai taji abunta yasake kamata tayo gurinsa batace komaiba ta haye cinyarsa ta zauna tana kallonsa Yana wayar. Kumatunsa tayi kissing Yayi Dan gyaran murya sbd zancen dayake ya Dan kwace masa kadan... Murmushi tasaki ganin da gaske Zata iya fidda abbin Kan layi kenan kome kamewarsa.. Bakinta takai tayi kissing lips dinsa take zancen dayake ya qara qwace Masa gabaki daya da idon ya kalleta yana kallon towel dinta da Bai wani dauruba kaman ze kwance.... Dan sake gyaran murya yayi tareda sallama da CM yace Masa gashinan fitowa zai samesa. Yana kashe wayar ta kallesa tana shagwaba fuska tace" Abbi zamuje gidan Dr iklimat fa yau kace. Towel dinta dayaketa sake zamewa ya kalla da idonsa masu shegen kyau kafin ya kalli fuskarta yace" Gidan juwairiyyah Zan kaiki... No Abbi gidan anty juwairiyyah tare zamu ai muyi musu fira Amma gidan Dr iklimat bazaka zaunaba nasani. Ok naji jeki ki shirya akwai sanyi. Miqewa tayi ta nufi gaban mirror shikuma ya nufi toilet. Daureda towel yafito shima Babu Bata lokaci ya shirya cikin brown yadi me shegiyar tsada da hular qube itama ta shirya cikin Riga da skirt na lace Mara nauyi me tsada sai qaramin veil breakfast dinma bawani sosai sukaciba suka fito tana riqeda hannunsa cikin nata Chloē handbag dintama Dole shine ya riqo Mata a dayan hannunsa suna fitowa ya miqawa driver handbag din ya saka Mata a gaban motar sukuma suka Shiga baya suka wuce. Kai tsaye gidan Dr iklimat suka nufa Batada wani nisa sosai Dan itama a maitama take. Umman Dr Abdul tun acan Daman tabawa Inayah address dinta Dan haka drivern Kai tsaye yakaisu har kofar gidan. Suna Isa Dr iklimat da kanta ta fito ta tarbesu cikin wayewa da farin cikin ganin Ayshatouh me tsanani tamkar itace ta haifeta sbd kusan atare suka Sha wuyar rashin ganinta itada Hadiza wancan lokacin gashi itama batada 'ya mace ko daya 'yayanta biyu duka maza ne sun girma tuni basama qasar dukansu. Babu wani damuwa ko kame kame tasaki jiki ta gaisa da MAJEED shima ba laifi ya Dan sake Mata sbd Inayah dayaga hankalinta yafi kwanciya anan din da Bata saba ko taba zuwaba Akan gidan juwairiyyah ko safiyyah. Bai shiga gidanba ya juya da nufin dawowa anjima daukanta ya wuce. Suna Shiga gidan Dr iklimat ta ringa dawainiya da Inayah din tana nuna Mata farin cikinta sosai da ganinta da zuwanta gidan, Ko masu aikin gidan kusan duk sunsan Anty Hadiza nada 'yar data Bata ganin Inayah yasasu Mata hidima cikin kulawa da girmamawa sbd kowa Kam yasan yanda anty Hadiza ke tsananin Jin Ayshatouh a zuciyarta. Dr iklimat mace ce Mai sakewa da faran faran tareda kulawa Musamman tana gane gatan dayayiwa Inayah yawa ta ringa wani lallabata tana janta ajiki Inayah Kuma dayake dama gata tasaba dashi da tattali take ta saki jikinta ta sake da Dr iklimat din ganin sai wani gata da lallabata takeyi. Hadiza tayi waya da antyn tata Dr iklimat taqara Mata bayanin komai akan abinda ake ciki na dalilin tafiyar Inayahn Abuja ta biyo Abbinta. Fada Dr ta ringa Yi sosai tana ganin lefin Hadiza da bazata sake ta cusa 'yarta da gyarataba su qwaci yancinsu agun uwar MAJEED din, Ita kanta Inayah Saida Dr din Tai Mata fadan uban me take jira da Bata dauki cikiba kowa ya huta masu mutuwa su mutu masu bin duniya subi can su suka jiyo. Dayake dama Hadiza nada niyar zuwa Abujan yau tun jiya ta yanki ticket Koda suke waya tana airport daman Dan haka ba zato Inayah taganta driver yaje ya daukota da mamaki take kallonta tace" Umman Dr dazu Koda muke waya kina hanya kenan? Da farin ciki kan fuskarta tace" Eh ba Dole nazoba sbd inason na kwana Ina zantawa da 'yata tunda haryanzu Abbinki yaqi yafemun yaban cikakkiyar dama. Dan murmushi kawai Inayah tayi tana cewa" To ai ko yanzu ba anan Zan kwanaba anjima zai dawo tafiya zamuyi. Dariya Dr iklimat tayi tana cewa" To ai yau de Dole ku hakura anan Zaki kwana. Kallonta tayi zatai magana Hadiza ta hanata ta hanyar dafa hannunta cikin kulawa tace" Inayah, Ba kowace magana ake bada amsartaba, Ni mahaifiyarki ce wannan Kuma da kike gani yayatace dukanmu bazamu cutar dakeba Bakyason kema ki ringa bugun gaban kinada Yan uwan nunawa koyaushe daga Abbinki sai Abbinki kawai, Shima yanzu Yan uwansa sun dawo rayuwarsa muma ki bamu Dama mu dawo rayuwarki. Shiru tayi tana sauraronsu sunata Mata maganganun hikima da lurarwa, Dr iklimat Bata bartaba Saida tasa Mata ra'ayin son kwana gidan tagani yau abbin zai iya bacci kaman jiya batareda itaba. Murmushi tasake zancen na Mata Dadi da Dr tace" Daqyar yau zaiga safiyar gobe. Ba kunya ta nuna farin cikinta tana tunanin yanda zaiyi. Hadiza wanka tayi tai sallah kafin taci abinci ta zauna tana shiga firar Dr da Inayah. A cikin wunin suka fahimci yanda rayuwar Inayah take sosai ba kwabar magana gata yayi Mata yawa sosai hakama soyayyar abbinta tariga ta ginu cikin ranta sosai ta yanda Babu abinda zai girgiza hakan sai ubangijin Daya dasa Mata wannan so da kaunar, Ta bangare Daya sosai suka jinjinawa MAJEED da ganin girmasa Mai tsanani ya qaru a idonsu sbd yanda Inayah take fada musu yanda take rayuwarta dasuke qiyasta gata da girman son dayake Mata. Sanyi jikin Hadiza yakuma Yi sbd tasan Koda a hannunta Inayah ta taso bazata Bata irin girman gata da tarbiyar da MAJEED ya bataba. Dr iklimat kuwa cewa tayi to ai bamuga zamaba tunda 'yar Tamu tagama mutuwa a sonsa koina fada takeyi gaban kowa Dan haka Dole wannan kurman abbin naki ya magantu Dan Naga alaman bazaiga girmanmuba sai 'yarmu tagama da bude Masa Ido. Ba Bata lokaci suka fara dirka Mata wasu Hadi na natural Kaya na Musamman. Da farko bataso Amma haka Dr ta bude Mata Ido tasakata Shan abubuwan kala kala. Hadiza Kam farin ciki take ciki yau ta wuni Zata Kuma kwana da 'yarta ga MAJEED datasukeson saukewa duk wata kamewa ya samu farin ciki da Jin Dadi kaman kowa. Sai bayan sallar ishai har sunci abinci abbin yazo daukanta. Da farko marairaice fuska tayi tanajin son binsa Amma su Dr ta bude Mata Ido ta hanata Dan haka ta fasa tareda Dan Kama kanta. Shigowa dashi akai har Lafiyayyan palon gidan yana shigowa akanta idonsa ya sauka tana fitowa daga hanyar bedroom din Dr iklimat sanyeda wasu kayan dabam. Da kulawa yake kallonta da kayan data sauya na wata doguwar Riga Mara albarka Dan kuwa rigar robace doguwa har qasa ta lafe jikinta tun daga sama har qasa ta fidda duk wata albarkar shape din jikinta Musamman shafaffen cikinta dayasa kirjinta dake cikin padded push-up bra. Dan gyara muryarsa kadan yayi tateda dauke Ido daga kanta Yana sake gaisawa da Dr iklimat Dake rokonsa ya tsaya yaci abinci yace aa yariga yayi dinner tareda baqinsa. Hadiza ce itama ta fito fuskarta a Dan sake jiki ba kwari ta gaishesa. Yayi mamakin ganinta Amma Bai nunaba ya kalli Inayah dashi take kallo ya amsa gaisuwar Yana Dan kallonta da cewa" Ashe kina garin? Allah ya taimaka. Amin suka amsa ta juya ta shige tabarsu. Miqewa yayi Yana kallon Inayah yace" Kije ki shiryo mu tafi time na tafiya. Kallonsa tayi cikin marairaicewa tace" Abbi Zan kwana anan tunda gobe zamu koma please.. Kallonta ya juyo yayi da kyau Yana mamakinta sanin Bata iya kwana baqon gurinda batasan kowaba. Cikin kulawa Yana kallonta yace" Zaki iya kwana anan? Gyada Kai tayi tana kallonsa. Kin tabbata? Sake gyada Kai tayi tana kallon yanayinsa dayake sake nanata tambayar. Hannu ya miqa yace" Zo Nan. tahowa tayi ahankali tana kallonsa a shagwabe maimakon ta Kama hannunsa saita shige jikinsa ta Dan kwanta tana cewa" Abbi Zan iya kwana anan Ina sone. Dago kanta yayi ya kalli fuskarta cikeda kulawa yakuma cewa" Are you sure? Yes Abbi" tace ahankali tana kallon fuskarsa cikeda kauna da shagwaba. Numfashi ya sauke ahankali kafin yace" Ok shikenan Zan barki anan din Amma idan kin kwanta kinji bazaki iyaba ki kirani Zan dawo na daukeni ok?? Okay, I will miss you my Abbi. Lumshe fararen idanuwansa yayi tareda sakinta Yana cewa" Shikenan kije ki saka Kaya masu nauyi ki kwanta akwai sanyi. Gyada Masa Kai tayi tana sakin hannunsa. Sallama yayi da Dr iklimat Dake tsaye tana kallonsu cikeda shaawa da burgewa batareda ta damuwaba sbd tanada wayewarta sosai ba komai bane agurinta. Yana ficewa Inayah ta sauke ajiyan zuciya tana juyawa ciki itama. Shima Yana fita bayan ya shiga mota numfashi ya sauke me zafi tareda Dan rufe Ido ya bude Yana sake danne zuciyarsa kafin ahankali ya bude Baki yacewa driver sutafi kawai. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/12, 2:41 PM] Ummulkhairi: *_61_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Bedroom din Dr iklimat takoma ta qarasa gefen Hadiza dake zaune kan kujera ta zauna tana kokarin boye sanyin jikinta na rabuwa da Abbin sbd bude Mata idon da zasu iyayi da fada tunda since karta nuna ala Dole Jan aji zasu koya Mata basusan Batasan wannan ba idan akan Abbinta ne. Dr iklimat ce ta shigo daga baya itama daukeda ruwan kankana da Madara ta miqa Mata tana Zama bakin gado fuska asake tace" Hadiza lallai wannan sirikin namu yafimu idon yawon duniya. Murmushi Hadizan tayi tana kallon Inayah dake kurba drink din ahankali tanajin tsikar jikinta na tashi da abubuwan dasuketa Bata tun Rana tana Sha. Hanata tunani sukai da zantukansu na sabbin abubuwan dasuke koya Mata Wanda suka shafi hanata maganganu da yawan sangartarta. Sosai suka dage cikin dubara da lallabawa suka koyar da ita wasu abubuwan data rasa daga rashin Zama da mahaifiya. Sai dare sosai suka kwanta bayan tayita ganin sakon Abbi na tambayarta ta kwanta? Tayi bacci? Is she ok? Zata iya kwana a Nan ko yadawo ya dauketa? Wainnan sakonnin nasane sukaita shigowa tana gani ta kasa replying nasa ko so daya sbd jikinta dayake amatuqar mace da abubuwan datasha dakuma farin cikin kwana gado Daya da mahaifiyarta. Dan kusan ma akan cinyarta tafara bacci sai daga baya ta kwana kan gado tana Jin ranta fes duk da Kuma kewar Abbinta na cinta Amma Kuma shima yawan text din nasa yasata Jin sanyi aranta Dan tasan yakasa baccine Yana tunanin ko Yaya Zata iya bacci anan. Washe gari tana tashi Kiran abbinta ne yafara shigowa wayarta a kasalance ta dauka tana shagwaba murya tace" Aslm alkm, Good morning my Abbi. Ajiyar zuciya da numfashi yafara saukewa a boye kafin cikin nutsuwa da kulawa yace" Kintashi lfy? Lfy kalau Abbi kewanka kawai nakeyi.... Ahankali yace" Kinyi bacci kuwa? Tashi zaune tayi tana cewa" Yes Abbi, Abbi kayi missing nawa? Kayi bacci? Wani boyayyan numfashi ya sauke Mara sauti ahankali sbd gabaki daya zuciyarsa Bata samu nutsuwar dazai iya ko kwantawaba bare baccin Zaune yaga asuba kan kujera Yana jiran reply dinta Amma shiru shiyasa Kai tsaye yakira da safen. Yes" kawai yace Mata a taqaice Yana cewa" Ki shirya in time zamu wuce zuwa 2:30 Amma kafin can zamu tafi gidan juwairiyyah da safiyyah. Ok Abbi. Sallama sukai ya ajiye wayar tareda rufe idanuwansa dasukai nauyi Yana Dan dafe kansa. Tashi yayi tareda kashe wayarsa gabaki daya ya nufi gado ya hau a natse ya kwanta sbd yanzu zai iya samu ya Dan Yi baccin kafin anjima. Acan gidan Dr iklimat kuwa su umma Hadiza wasu mayun turaruka masu shegiyar tsada da mayen qamshi suka siya gurin wata qawar Hadizan Dake Nan Abuja tun daren jiyan sukai Mata waya sai gashi da safen driver yakawo. Harhada Mata su sukai tareda wasu sabbin fitinannun kayan baccin da Dr iklimat ta fita da kanta ta siyo Mata shima a gurin neighbor dinta me Saro designers daga waje. Sam Inayah Bata saka mini skirts sbd batadasu a kayanta Amma hardasu suka siyo Mata. Qarfe daya tagama shiryawa suka zauna jiran zuwan Abbi. Lafewa tayi jikin mahaifiyarta tanajin kaunarta sbd kwana dayan Nan dasukai duk sun sake saka Mata kaunarsu da Jin dadin dawowarsu rayuwarta gashi suma sunata lallabata kaman yanda Abbinta ya sabar Mata duk da suna Mata fadan wani abin Amma akwai kaunarta sosai ataredasu. Qarfe daya da rabi ya iso gidan Bai shigoba saidai suka fito. Fitowa yayi motar suka gaisa dasu a mutunce Yana kallon gefen datake a fisge sbd ganin kaman tasauya Masa sbd harda skin scrubbing sukai mata. Itama shi take kallo zuciyarta na cika da son kayanta suna hada Ido ta shagwabar da fuska tana sakin murmushin farin cikin ganinsa. Ahankali Yana Mata wani mayen kallo yace" Muje ko? Jikin umma Hadiza ta qarasa ta rungumeta tana cewa" Kidawo da wuri kema. Murmushi kawai tayi Tana cewa" Allah yakaiku lfy Ina gaida su umma yaganah da Haj. Dr iklimat ta runguma itama tana cewa" Mommy kince zakizo Ki cika alqawari kinji? Gyada Mata Kai tayi tana cewa" Zanzo Inshallah ki gaida mutan gidan Allah ya tsare, Kuma kindai ji abinda na fada Miki. Gyada Kai tayi tana cewa" Yes Mommy. Mota ta juya ta nufa Dan already Yana ciki Yana kallonta da idanuwansa dasuka kasa daukuwa daga kanta. Tana shiga motar driver yaja suka wuce. Bai juyoba sbd yawan kallonta matsala ne agurinsa Dan haka ya Dan maida hankalinsa kan waya Yana son Kiran safiyyah dasu juwairiyyah suna gidanta gabaki dayansu da Yara. Bayan ta dauki wayar da qyar ya riqe kansa tareda kamewa ya sanar da ita suna hanya ya kashe sbd wani mayen Qamshin dayakeji Yana tashi daga jikinta ahankali Yana Shiga hancinsa Yana neman buga kansa. Gashi taqi zuwa ta maqalesa kaman yanda ta saba tana zaune itama tana duba sakon Neesah data turo Mata ta WhatsApp. Hankalinta na kan Abbin nata tannuwanta da zuciyarta dasuka Saba zuwa garesa sai kokarin hanasu zuwan takeyi sbd fadan su umma Hadiza dake yawo cikin kanta na hanata zuwa koyaushe tabari yazo da kansa. Daqyar kowannensu ya iya riqe kansa harsuka Isa gidan anty safiyyah suna fitowa motar su Anty juwairiyyah da 'yayansu suka sake zuba idanuwansu kanta sbd Babu abinda yake jikinta Mara kyau da tsada tun daga kan kyakkyawar halittar da Allah yayi Mata har tsadaddiyar suturar jikinta da wasu matsiyatan designer handbag da takarmin Stuart W. Babbar 'yar anty juwairiyyah rumanah itace ta saki fuska sosai tareda rungume Inayah din tana cewa" Uncle sannu da zuwa, Welcome matan uncle. Murmushi Inayah tayi tana amsawa ahankali. Gaidasu anyu juwairiyyah tayi cikin girmamawa da sanyi. Amsawa sukai anty safiyyah na qarewa Inayah kallo tana yaba kyanta da komaima dan itakam take Inayah Tai Mata Dan shekaran jiya Basu ganta dakyauta sbd dare ne yanzu Kam taganta Kuma wlh tafi Dr farhat komai ta fada a fili tana cewa" Gskia Inayah is the perfect match wa MAJEED. Haj umma Dan Allah ta Dena maganar wata macen Kuma. Dadin maganar Inayah taji Amma Bata kalli Abbinba sukai ciki gabaki dayansu. Abinci sukaci a babban dining din palon gidan sunata fira da 'dan uwansu yaran Kuma sunatayi da Inayah wadda kusan hankalinta yafi kwanciya da yaran dasuka nuna Mata kauna sai Anty safiyyah Amma Kam anty juwairiyyah Dr farhat sukeyi wuta itada Haj umma. Sosai anty safiyyah ta sauke kanta tabawa 'dan uwanta hakurin abinda ya faru baya Bayason tada komai Dan haka ya dakatar da maganar yace abarta ya wuce kawai. Karfe biyu Saura suka baro gidan bayan yayiwa yaran dasu kansu uwayen yaran kyautar girma Data sake sasu jinjinawa MAJEED din sukaita godiya da Jin Dadi suka rakosu suka wuce. Kusan late suka Isa airport Dan hakan suna Isa ba Bata lokaci suka tashi. Ko a jirgi dai Babu wata doguwar Hira data shiga tsakaninsu sai mayen kallo dayake binta dashi Yana Jin sabon yanayi akanta. Itama yau jinsa take cikin ran nata sosai sbd tunda suka hadu ko hannunsu be haduba Dan haka takejin kaman zuciyarta Zata fashe da sonsa. Charles ne yazo daukansu airport da Daya daga cikin lafiyayyun motocin gidan. Saida suka kamo hanyar gida ya kasa hakuri ya juyo ahankali ya kalleta tareda kamo hannunta dake kan cinyarta ajiye tana kallonsa. Kama hannun nata da yayi kusan atare kowannensu ya saki ajiyar zuciya a boye. Cikin idonta ya kalli tareda bude Baki ahankali yace" Are you okay???? Gyada Kai tayi ahankali tana narkar da fuska. Jin yayi wani a feeling na fizgarsa akanta sbd galabaituwa kusan dayake tun jiya a zuciya, Tunda take baitaba barinta taje wani gurinba ta kwana sai jiyan, Duk tafiye tafiyensa hankalinsa yafi kwanciya dayaje duk Inda zashi yabarta gida tareda umma yaganah shiyasa jiyan hankalinsa yakasa nutsuwa. Bude motar tayi kafin yasake wata maganar ta fice tana satar kallonsa Tana ganin umma yaganah ta qarasa da gudu tayi kanta ta rungumeta sbd Basu taba rabuwaba duk tafiyansu tare sukeyi sai yanzu. Ajiyar zuciya yayi tareda sauke numfashi ya dedeta kansa ya fito motar shima yayo ciki su umma dake palon duka suka fara Masa sannu da dawowa cikin farin ciki. Ana Gama gaisawa ya wuce hanyar palonsa dake gyare tsaf Salimat ta gyara koina Yana fidda sanyin AC da qamshi me Dadi. Itama Bayan angama murnar ganinsu umma dakinta ta wuce zubbi na biye da ita da kayanta ta ajiye tareda bude akwatin ta fidda komai dake ciki ta kaisa Inda zai zauna ta maida akwatin ta fice daga dakin lokacin Inayah na toilet tini. Alwalar sallar la'asar da basuyiba tayo ta fito tazo ta sauya kayan jikinta zuwa jallabiya tayi sallar. Tana gamawa ta saka wayarta caji tareda fitowa ta nufi dakin umma yaganah ta kwanta jikinta tana Bata labarin tareda umma Hadiza ta kwana. Palo suka dawo gurin Haj umma suka qarasa firarsu itadai Haj umman Bata wani saka Baki sbd bacin ran datake ciki tun ranarda MAJEED yatafi da Inayah abujan batareda sun saniba sai data fito da akwati suka San da ita zaiyi tafiyar Kuma kiri kiri ya dauke 'yar cikinsa zuwa hotel din daya sauka suka kwana acan. Abin ya Bata mamaki tareda Bata ranta sbd duka tsarinsu na iyayen farhat dazai gani a abujan ya wargaje da damuwa Dr farhat tabar Nigeria duk tashiga damuwa sosai. Dole lallabata tayi da Bata tabbacin taje kafin tadawo komai ya kankama aure ba fashi. Sallar magriba tasa kowannensu tashi ya nufi dakinsa yayi sallar. Tana gamawa Bata fitoba Saida lokacin cin abinci yayi zubbi tazo kiranta tace ta koshi zubbin ta hado Mata cornflakes kawai shi zatasha. Koda zubbi tazo ta sanar da cewan Inayah tace ta koshi shiru kawai yayi Yana cigaba dacin abincinsa Amma hankalinsa baya gurin Kuma. Bai wani ci abincinba yaji ya ishesa yasha juice da ruwa kadan ya tashi ya fice zuwa sallar ishai da lokaci yayi. Yana tashi Haj umma tabisa da kallo sbd Sarai tasan sbd Inayah Bata fitoba yaji abincin ya ishesa. Numfashi ta sauke tana tunanin tabbas Hadiza da yarta qaddara ce rayuwar 'danta duk sunbi sun firgitar Mata da Natsatsen yaronta. Inayah tana sane taqi fitowar saidai duk batajin dadin hakan itadai ba lallai Zata iya wannan salon nasu umma Hadiza da Dr iklimat ba Sallar ishai tayi ta miqe ya nufi dakin umma yaganah tareda qarasa chats dinta a kwance tanajin Nishadi Amma idan Abbinta ya fado ranta saitaji kaman taje ta samesa. Sai guraren 11 ta tashi ta nufi bedroom dinta ta tube tafada toilet tayo wanka da ruwan zafi ta fito ta shafa Mai tareda shafa normal turarenta na black opium tana kokarin saka kayan bacci Kiran Abbi yashigo wayarta. Kallon wayar tayi tareda Jin wani sanyi cikin ranta ta saki murmushi tareda daukan wayar ta zauna bakin gado cikin shagwaba tace" Abbi... Ajiyar zuciya ya sake a boye sbd tunanin kwananta gidansu Hadiza ya sauya Masa ita shiyasa baya barinta zuwa koina bare kwana sbd sauya Masa tarbiyarta gashi daga kwana daya ta sauya. Ahankali takuma Kiran sunansa Ya bude Baki a natse yace" Meyasa kike Wasa da abinci? Kici wani abin ne? Murmushi tasake ahankali kafin tace" Nasha cornflakes Kuma ya isheni Abbi. Kaci abincin Kai Abbi? Alhmdllh" kawai yace Mata a taqaice zaiyi magana saikuma ya fasa kawai ya aje wayar. Murmushi tasake zuciyarta na cika da farin ciki sbd tasan Abbin saiya sake Kiran wayarta. Kayan data fidda na bacci zata saka ta maida tareda dauko wata fitinanniyar rigar bacci Mara albarka ko kadan ta kalla taga banbancinta da Babu kawai kala ne, Hot red ce rigar Dan haka ta saka batareda ta saka bra ba sai wani qaramin red pant data saka ta nufi gaban mirror ta dauki Turaren dasu umma Hadiza suka siya Mata ta bude tareda Ciro abin shafawar taringa shafawa wuyanta zuwa tsakiyar kirjinta. Jin itama yafara tada tsikar jikinta da Qamshin yasata ajiyewa da sauri tana Dan rage Wanda ta shafa... Juyawa tayi Zata nufi toilet ta debo tissue ta sake ragewa saiga kofar bedroom din nata an bude Kai tsaye cikin nutsuwa tareda shigowa. Da sauri ta juyo cikin tsoro sukai Ido biyu da Abbinta Dake kallon rigar jikinta cikin wani gigitaccen yanayi. ##MAMUH# #HOTLOVE/HOT ROMANCE #MAJEED/ INAYAH. _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/12, 2:41 PM] Ummulkhairi: *_62_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Kasa motsawa tayi daga Inda take sbd take kunyar rigar jikinta ta kamata a Karo na farko dataji kunyar, Dauke idonta tayi daga kansa tana Dan fasa qarasawa kofar toilet datai niyar zuwa debo tissue, Idanuwansa takeji ajikinta suna yawo Dan haka ta Dan motsa kadan tana dagowa ta kallesa... Wani mayen kallo ya qare Mata cikin sakanni kafin ya dauke kansa ya qaraso Kai tsaye ya nufi 2 seater sofa dake gefen gadonta ya zauna ahankali tareda ajiye wayarsa Dake hannunsa gefensa ya Dan sake dedeta kansa ya dago cikin nutsuwa ya kalleta tana gurin tsaye Bata motsaba Kuma takasa dagowa ta kallesa yanda ta saba. Nazarinta yadan yi na minti Daya kafin yasake daidaita kansa daketa kuncewa da wata shaqaqqiyar murya me shegen laushi na nutsuwa da kasala duk aciki yace" Zo Nan. Juyowa tayi ta kallesa jiki a mace Jin abinda yace. Fuskarsa ta kalla taga mayen sanyayyan kallon dayake binta dashi ta marairaice fuska zatai magana ya miqa Mata hannu ahankali Yana sake cewa" Zo. Ahankali ta dago qafafunta tafara tahowa jikinta na sake bayyana acikin idanuwansa ga hasken wutar dakin fes kaman Rana.... Wasu mugayen yawu suka wuce maqoshinsa a wahale sbd bushewar da maqoshin yayi take Yana hada Ido da asalin kalan siffarta Data bayyanar Masa cikin rigar da baima Gama sanin rigace ko qyalle ne kawai ta daura. Tafiyarta kawai Mai sanyi juya kansa take tana sake yamutsasa Dan duk takunta sai kirjinta dayake gani fresh acikin rigar me kaman Babu sun motsa.. Tana isowa gabansa hannunsa ta Kama ahankali atareda Zaunar da ita kan cinyarsa dake sanye da pyjamas na bacci masu santsi. Zamanta akan cinyarsa yabashi damar jin wata sabuwar fitinanniyar kamshin Dake tashi jikinta a wahale ya kalleta da idanuwansa dasukai wani iri yakai fuskarsa cikin wuyanta ahankali Yana shinshinawa kaman sabon maye cikin maqoshinsa yace" Me su Dr suka fada Miki take cewa karki manta kike cewa eh????? Ajiyar zuciya tasake tareda sakin murmushin tsikar jikinta suna tashi koina da irin shinshinar dayake Mata cikin wuyanta zuwa kirjinta Yana sakar Mata numfashi Mai dumi. A kasalance ta bude Ido ta kallesa shima Dan bude idon ita yake kalla Yana sake shaqar qamshinta Daya Gama dashi daqyar ya furta" Uhummm,Ina jinki me suka fada Miki? Wani murmushin takuma saki tana sake shigewa jikinsa ta saqalo wuyansa tareda fuskantarsa da kyau Yayiwa kirjinta data manna Masa a kirji wani mayen kallo Yana Jin yanda take motsawa suna sake shafarsa dakyau har tsininsu na sukarsa Kai tsaye.... Fuskarsa ta shafa ahankali tana murmushi kafin takai bakinta kan kunnensa ahankali tace" Sirri ne..... Dan bude Ido yayi a wargaje sbd tagama wargasa da numfashin data sauke cikin kunnensa kafin maganar tata, Qugunta ya Kama tareda matseta jikinsa shima cikin qaramin sautin dayafi nata shiga wani hali yace" Yaushe kika fara boyemin sirri? Wane sirrinki ne bansaniba??? Dariya me qaramin sauti tasake Yana lumshe ido sbd Jin hannunsa cikin rigarta Yana shafa cibiyarta da qyar ta furta" Wannan dai sirri ne Abbin baby Inayah bazaijiba...... Maganarta tasake kashesa yayi sama da hannunsa a kasalance ya shafo kirjinta dasuke kashesa tun dasu..taja wani marayan numfashi tanayi baya ya tarota tareda dawo da ita suka Mannu sosai ya cusa kansa wuyanta yaja wani mayen numfashi Yana sake bin jikinta da wata irin fitinanniyar shafar dake saka jikinta daukan zafi kaman ana gasata a dumi... Ahankali cikin fita hayyaci yace" Wannan Qamshin shine sirri, Kinason ki kashe Abbinki ne baby Inayah? Wani zazzafan numfashi taja tanajin wata masifaffiyar abinda Bata taba jiba...... Daqyar ta iya bude idanuwanta dasuka sauya ta kallesa shima ita ya kalla da idanuwansa dasuka Gama tabbatar mata da wannan ba Abbi bane AA MAJEED ne... Harshensa yasa ahankali yafara lasan wuyanta Yana sakar Mata numfashi masu dumi dasuka rikitata take qaramar kwakwalwarta tafara watsewa tana bin iska... Lasar dayake Mata da harshensa tafi qanqara sanyi da Santsi, Arikice ta riko kansa tana kasa Jan numfashi sbd fita hayyacinta datai tana kiran sunansa batareda tasan tana hakanba... Kuma Kiran sunansa tayi cikin wani buwayayyan sauti dayasashi dagowa ya Kama bakinta ya riqo harshenta da nasa yafara zuqan duk yawun bakinta daketa Qamshin cool mint Listerine mouth wash. Yau sosai takejinsa da zafinsa sbd ko kirjinta sun fara shedan hakan, Kissing din dayake Mata Yana yamutsa gashin kanta daya fizge band din dake daureda gashinta tuni ya jefar, Dagashi har ita sunkai gabar da Babu Mai iya hakurin Dan uwansa duka da ita tana cikin fargaba da tsoro Amma Kuma kisses dinsa da yanda yake lasar fatar jikinta yasa tsoron da Jin dadin ke kokawa da juna. Yana Shan bakinta ya miqe da ita a jikinsa zuwa Lafiyayyan gadonta Daya Gama Kama Qamshin jikinta ya kwantar da ita Yana kallon rigarta dake sake kashesa har kwanya Kai tsaye ya balle batiran rigar jikinsa ya zame ya jefar qasa Yana kallon kirjinta dake sama Yana qasa sbd numfashin datake fitarwa me qarfi..... Hawowa gadon yayi ahankali tareda daga rigar tata ahankali ya zura kansa Yana shaqan Qamshin cibiyarta da har anan Qamshin yake ya lumshe ido a hawale Yana Dora lips dinsa kan cibiyarta da sauri taja numfashi tana tsikar jikinta suka miqe ta qanqame tattausan pilon da kanta yake kai... Tun daga kan cibiyarta ya fidda harshe yafara lasheta Yana kissing zuwa saman kirjinta kansa na cikin rigar.... Ba zato taji hawaye na bin fuskarta jikinta yafara rawa sosai daqyar take iya furta sunansa sedai Sam baya gane yaren komai a lokacin... Irin yanda yakewa kirjinta taji kukanta na tsananta sbd taji abinda yafi karfinta ba kadanba, Kwakwalwarta neman bugawa takeyi bazata iya daukaba Al'amarin yayi Mata zafi ga numfashinta na neman siqewa sbd fita da sauri cikin yanayi. Ta cikin rigar ya bullo da fuskarsa ta wuyan yasake hade bakinsa da nata Yana Bata sabon kiss dayasa Kuma kanta sake daburcewa..... Rigar kasa daukansu su biyu tayi acikinta ta farke biyu daidai dama tamkar net take..... Farkewar rigar yasashi bude Ido daqyar ya kalli asalin komai nata dake gabansa zahiran...... Daga wannan lokacin baisake sanin me kansa yake cikiba kuma sbd take kunnuwansa da idonsa suka dif bayani baya gani baya fahimtar komai sai abinda yake gabansa. Abinda taji Yana Shirin faruwa ne yasa ta shiga gigitar gaske tagara janyewa tana Kiran sunansa a tsorace sbd tabbas tasan taji abinda yafi karfinta saidai a lokacin Babu tsira Dan kuwa Abbinta yagama kaiwa sama a Inda Bata tunani duk girman Sonta Dake cikin Rai da ruhinsa bazai iya riqe kansaba alokacin Dan kuwa komai yazo Masa a gabar da Babu abinda zai iyaji. Ihun Kiran sunansa tafara tana son janyewa Amma yayiwa qugunta kyakkyawan riqonta Babu abinda zai karbeta a gun..... Kukan masifa da azabata tafara saki tana turesa Amma babu alamarma yasan metake Yi ko fada.... Wasu manyan balain dabaisan dasuba a duniya yaji suna kunce kansa daya bayan Daya suna farfashewa..... Akaron farko rayuwarsa dayaji kansa cikin shock din dabaita tsammanin jiba Koda a wutar lantarki ne Dan wanna yafi wutan lantarkin...... Abinda yakeji yafi karfin kansa da kansa Dan haka yake abinda kawai ke gabansa bayajin komai na duniyar... Tun tana ihun Kiran sunansa cikin kuka da turesa harta Kai Bata iya kukan hannuntama sanyi sukai tafara hawaye kawai tana Kiran sunansa cikin wuya. Wani sabon abinda dayaji ya buga kwanyarsa da karfi baisan lokacinda ya daga hannunsa ya daki kan gadon dasuke kaiba da qarfin gaske take gadon ya balle bat lokaci daya duk shegiyar tsadarsa kuwa sbd dukane na masifar gaske yayi Masa batareda yasan yayi hakanba sbd karon farko dayasan mace a rayuwarsa... zufa da wani sanyine yaji suna keto Masa tako Ina lokaci daya ya qanqameta Yana Kira sunayenta duka ukun, AYSHATOUH, INAYAH, BABYN ABBI.... alokacin itace batajin abinda yake fada sbd tayi nisanda suma ne kawai Bata qarasa yiba Amma ko idonta Bata iya budewa sbd tsananin azaba da mawuyacin halinda take ciki. A gefenta ya mirgina da qyar sbd sanyi da rawar da jikinsa ya dauka take Yana qarasa sauke numfashin abinda yagama.... Ahankali ya daga hannunsa ya janyota jikinsa ya qanqameta Yana Kiran sunanta can qasa daqyar sbd zazzabin gaske ya rufesa shima take sbd shikam zumar tayiwa kwanyarsa da gangar jikin babbar illar dabai San haka abun yakeba. Ajikin juna suke sauke numfashi akan gadon Daya rizga dasu rugugu ya balle. Sum jima tsawon lokaci ahakan harya samu yadawo Yar nutsuwarsa ya shafa bayanta zuwa wuyanta tareda Kiran sunanta ahankali Jin Bata wani iya motsawa. Ahankali ya tashi ya sauko gadon tareda nufar toilet dinta ya sakarwa kansa ruwan zafi Yana lumshe idanuwansa da Basu Gama dawowa daidaiba. Wani Abu yakeji jikinsa yana yawo cikin jininsa Yana birkita kansa Wanda yasan tsananin son Babynsa ne ke basa wannan yanayin, Jinta yakeyi a koina na kansa da jininsa Musamman ayau din tagama kaisa Inda bazai taba dawowaba mutuwama zaiyi acan akanta. Yana Gama wankan ya fito daureda towel dinta dabai Gama rufesa ba ya dawo sakin a lokacin karfe uku da kusan wata na dare ya durqusa kan gadon ya Dan janye kan gadon Daya balle rabi ya Fadi Rabin ya rankwafo gadon ya saka hannu biyu ya daukota a hankali kaman bayason jijjigata ta wahala ya nufi toilet din da ita. Saida ya sakar musu ruwan zafi tana rungume jikinsan yaga Bata motsaba ya fahimci a some take Dan haka hankalinsa ya tashi take ya tara ruwan zafi a bathtub ya sakata ahankali tareda shiga cikin ruwan ya rungumeta jikin Yana lumshe ido tareda kokarin Hana kansa shiga sabon yanayi akanta. Zafin ruwan dakuma yanda suka fara ratsa jikinta yasata farfadowa ta bude idanuwanta da har sun kumbura sbd kuka. Ganinta jikinsa yasata sakar Masa wani kasalallen kuka tana qarasa sake Masa jikinta gabaki daya. Kasa cewa komai yayi sai shafa kanta dayakeyi Yana Kiran sunanta cikin galabaitacciyar sonta da batasan yariga yai Masa illaba tuni. Rigimar kukanta yasashi fita da ita daga ruwan ya sake hada wainda basiyu zafinsuba ya maidata ciki. Kukan taci gaba dayi sbd azabar da jikinta ke Mata koina tanajin radadin gurzan datasha ciki da wajenta har kirjinta zafi suke Mata da radadin gurzan dasuka Sha. Daqyar suka gamo toilet din suka fito ya daukar Mata wasu kayan da nasa ya dauketa sukai dakinsa. Suna Isa ya saka Mata kayan baccin shima ya saka wasu dogon wando da Riga na baccin suka kwanta sbd dagashi har ita zazzabi me qarfine ya rufesu atake daurewa kawai yakeyi Yana lallabata ganin tanajin jikin sosai sbd kakkarwa takeyi sosai ga jikinta ya dauka zafi take ko bude idanuwanta takasa Yi. Ajikinsa ya sakata ya rungumeta Yana shafar bayanta cikin tsananin so me girma Daya Gama gauraya jininsa da komai nasa. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/12, 2:41 PM] Ummulkhairi: *_63_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ko da akai asuba jikinta yayi tsanani sosai shi kansa yanajin jikin Amma ta Babynsa yakeyi Dan haka sallah ya tashi yayi ko masallaci Bai iya fita ba Yana idarwa yaga ko sallar bazata iyaba ya janyo qatuwar Fendi hoodie jacket dinsa ya saka Mata akan kayanta ya saka Mata hular sanyi da safa a qafa shima ya sauya kayansa zuwa Riga da wandon Balenciaga masu kauri da hula a hade ya dauketa tareda rungumeta cikin jikinsa da kyau ya fita da ita batareda ma Yan gidan kowa ya tashi sallar asubaba Dan akwai duhu sosai lokacin wasu masalllatanma ko Sallar asuban Basu idarba. A mota ya kwantar da ita a set din gaba ya Shiga ya tada ya fice gidan. Asibitinsu ya nufa da ita Kai tsaye Bayan ya Kira Dr Anna Daya daga cikin manyan asibitin tace tana can anan ta kwana asibitin.... Suna Isa Kai tsaye shine ya dauketa zuwa office din Dr Anna batareda yajira anzo da abun daukaba an dauketa. Kwantar da ita yayi kan gadon patients dake office din Dr Anna na gyara Mata kwanciya cikeda kulawa da damuwa tace" Oh my God,meya sameta? Temperature dinta is too high. Bai Bata amsar tamnayartaba cikin kulawa yana kallon Inayar yace" Zafin jikinta yayi yawa please do sumtin about it kafin komai... Daqyar Inayah ta iya bude idanuwanta dasuka kumbura ta kalli Dr Anna cikin murya mata sauti a kasalance tace" Dr Anna koina jikina ciwo... Hawayenta ne suka gangaro yasa lallausan hannunsa ya tare tareda share Mata hawayen Yana Jin kaman ya Ciro ciwon daga jikinta ya dawo dashi nasa. Jinta yakeyi kaman wani jaririn kwai Yana yawo a zuciyarsa bayason ya fashe ko ya bugu ko kadan. Kallonsa Dr Anna tayi tace yaje ya zauna zataji da Inayah din. Kallon Inayah tayi cikin kulawa da tausayawa tace" Kunyi having sex ne? A wahale Inayah ta rintse Ido hawayen ciki suka gangaro ta gyada Mata Kai. Cikeda mamaki takuma cewa" Wannan shine first time dinki? Yes,Dr please ki rage min radadin Nan I'm in alot of pain please" ta fada cikin kosawa da azabar ciwon jikinta da zazzabi. Sosai Dr Anna tashiga mamakin Inayah da Abbin duka lokaci daya Ashe see yanzu suka Zama intimate da juna Bayan tsawon lokacin dasuke tare. Qafafunta ta ware ahankali tareda zare Mata wandon Dake jikinta ta kunna qaramar fitilarsu ta likitoci ta haska gurin da kyau. Oh my God" ta fada cikin sabon tausayin Inayah sbd gurin Kam Sir AA MAJEED yagama gurjesa ba sauki.. Ba qaramar gurza da farka yayiwa gurinba Dan haka take takira nurse Daya takawo Mata abubuwan dazata buqata gurin duba yanayin na Inayah daketa hawaye tana kasa ko daga hannunta. Yana office din zaune suka jata zuwa labour room Dinsu Dan sake dubata da kyau idan ba buqatan dinki. Suna fita Dr Abdul daya kwana asibitin shima ya gansu da Inayah zaa wuce da ita hankaki tashe yake kallonsu ya tambayi Dr Anna meya sameta Kuma yaushe aka kawota? Ba kwana kwana Dr Anna ta sanar Masa first sex dinta tayi ayau din shine abin yazo Mata da wahala. Wuta ya dauke cak agurin batareda ya sake daga qafa ya bisu ba har suka shige. Addua yayita karantowa Yana korar shedan dakeson sakasa qunci haka kawai Ya rufe Ido ya bude Yana tsananta adduarsa ya juya yabar gurin zuwa office dinsa da sauri. Acan ciki kuwa Babu wani dinki da akai Mata duk da ta gurzu iya gurzuwa kawai dai sun Dan gogge Maya gurin da Cotton me sanyi sai allurai da pain killers sai na zazzabin jikinta me qarfi. Ruwan zafi sosai Dr Anna ta taimakata Mata tashiga a office dinta bayan sun dawo kafin ta taimaka Mata ta kimtsa suka fito sbd zazzabin ya rage sosai ta Dan dawo hayyacinta yanda ya kamata tana tafiya da qyar ahankali suka dawo gurinsa Yana kallonta kaman zuciyarsa Zata bude agabanta sbd yanda yake jinta. Hannunsa ya miqa ahankali ya kamota zuwa jikinsa yana kallon fuskarta dataqi kallonsa tasake narkewa jikinsa tana sako hawayen sauran ciwon da jikinta keyi koina. Godiya yayiwa Dr Anna suka fito ta karasu har mota suka wuce lokacin garin yayi haske sosai. Hannunsa daya na riqe da nata hannun yake driving da hannu daya sbd har lokacin jikinta da sauran zafi. Koda suka Isa har lokacin Babu Wanda ya tashi a gidan Dan haka Kai tsaye dakinsa suka koma ya taimaka Mata da qyar tayi sallah ya kwantar da ita a jikinsa Takoma bacci kan gadonsa..... Yanajin yanda numfashinta ke fita ahankali cikin sanyi da kasalar ciwo ya lumshe idanuwansa Yana Jin komai na duniyar daren jiyan Yana Neman dawo Masa cikin qwaqwalwa Yin hakan matsala ne garesa Dan zai iya sake buqatarta Bayan tana cikin wannan halin Kuma yasan qarasa rikice Masa zatai Dan haka ya sake lumshe ido tareda kissing kanta ahankali Yana rufe Ido ko zai samu baccin shima. Bacci sosai sukayi sai guraren 10 ya tashi yayi wanka ya taimaka Mata tayi wanka sbd zazzabin ya Dan tafi ba lefi Amma gabaki daya jikinta yayi tsami sosai bata wani iya dogayen motsi. Dakinta yakaita suka saka doguwar Riga Mara nauyi sbd tace batason kaya masu wando zafi Zata ringa ji agun ga pant ga wani wandon. Suna Gama shiryawa suka fito dakin sbd ba gurin kwanciyarta a gadon dan ba qaramin ballewa yayiba. Bakowa Palo anan tace Zata zauna dan haka ajiyeta yayi zubbi dasuke aiki kitchen ta fito kenan yace taje ta hado Mata tea me zafi takewo Mata. Kissing din gashinta yayi ahankali Yana kallon fuskarta da duk ta narke cikin kulawa kaman zai iya cire Mata ciwon yace" Zanje na shirya okay???? Kasa magana tayi Dan har bakinta ciwo yake Mata sbd jikinta da Babu qwari koina Kai ta daga Masa hankali tana ciko idanuwanta da Hawaye. Idon da hawayen suka ciko yayi kissing ahankali tareda miqewa ya nufi dakinsa. Yana barin palon Haj umma na fitowa yau kusan duka lattin tashi sukai gidan kaman hadin Baki, Kallon Inayah dake cikin kujera ta wani lafe kaman Mara lafiya sosai tayi tana qarasowa ta kalleta. Mamaki ne ya Dan Kamata ganin fuskar Inayah din kaman a Dan kumbure alamar kuka ko rashin lafiya. Cikin sauti taqaitacce tace" Lafiyarki kuwa yau kika lafe anan? Zubbi data kawo Mata tea me zafi da kauri sosai tareda zallar liver sauce me zafi ta jiye cikin tray tayiwa Haj umma Ina kwana tace" Zazzabi Inayah din keyi" kaman yanda dai ta fahimta ita. Allah ya sawwaqa kawai hajiyar tace tana barin gurin. Umma yaganah ce kawai tayi breakfast a gidan Takoma tayi kwanciyarta Dan haka haj umma ita kadai tayi nata itama yau din tana gamawa tazo palon ta zauna tana wayoyinta hankali kwance. Suna zaune umma yaganah tafito itama shirye cikin atampar cotton satin me tsada. Ganin Inayah lafe fustarta wani iri yasata qarasowa ta zauna gefenta cikeda mamaki da damuwa da kulawa tace" Lafiyanki kuwa? Yaya naganki haka? Ba bakin magana sai hawaye data saki kawai tana kwantawa jikin umman. Kallon Haj umma tayi suka gaisa tace" Meya sameta ne? Kallon Inayar Haj umma takuma Yi tace" Sai wani Abu ya sameta ne take wannan Rigimar? Ai Kun Saba ku dukan karma ki daga hankalinki indai itace bazai wuce zazzabi ba take Neman dagawa jama'ar gida hankali. Kafin umma yaganah takuma magana saigashi ya fito a shirya cikin wasu black Balmain full zip hoodie set  masu kauri kadan sbd hoodie wears na cikin kayan dayafi sakawa sbd ko kadan bayason sanyi tsadaddun slippers din Mk. Qamshinsa Daya gauraya palon yasa Inayah bude idonta kadan ta kallesa tana sake cigaba da tsiyayar hawaye ajikin umma yaganah. Cikin girmamawa ya gaida su Haj umma idonsa na kan Inayah din Ya maida kallonsa kan abincin dake gabanta kan table aje Bata ci komaiba Kai tsaye cikin nutsuwa da kulawa yace" Bakici komaiba har yanzu? Umma yaganah ya kalla yace" Abata taci wani abun. Tea din Umma ta dauka tana Bata a Baki tana cewa" Ni bansanma meke damuntaba wannna hawayen kin kasa denawa to tayaya za'a san meke damunki a Kira likita kinqi yiwa kowa magana. Zuba Mata Ido yayi yanajin zuciyarsa na kasa samun sukuni da rashin cin abincin nata gashi yanason Jin ya zafin jikin nata yanzu sbd hawayen nata duk sun dagula Masa lissafi fitowarsa gashi baiyi zaton su umman duk sun fitoba. Kallonsa Haj umma tayi tana gundura da wannan kallon duk kamewarsa tana neman zubewa agaban 'yar cikinsa Dan haka ta kwalawa zubbi Kira tace a shirya Masa breakfast a dining. Saida zubbi tagama tsara komai a dining din tazo ta sanar masa Kai tsaye ya Dan gyara Zama Yana ajiye wayar hannunsa dayake dubawa Amma hankalinsa baya Kai Yana kan Inayah da umma keta lallabawa Tana Shan tea din daqyar, yace" No abani tea kawai. Kallonsa Haj umma tayi cikin kulawa tace" Zaka fita aiki bakaci wani abincin kirkiba MAJEED, Please ka Dena Wasa da lafiyanka Rashin cin abinci yanda ya kamata zai iya baka matsala. Kallon Inayah da aketa fama da ita yayi a hankali yace" Kinaji right? Ki daure kici abincin kafin wani damuwan yashiga sbd rashin cin abinci. Sake Baki Haj umma tayi tana kallonsa Tana magana akansa yanayi akan Inayah tsabar rashin tausayi irin na Inayah din data daga hankalin kowa akan Dan zazzabin dama taqi fadar meke Mata ciwo. Tea dinsa aka kawo Masa cikin wani kyakkyawan farin cup yafara Sha ahankali Yana karanta sakonnin wayarsa Amma kwata kwata hankalinsa ko Rani bayakan wayar bare tea din dayake Shan Yana kan baby Inayah data Gama Shan tea din daqyar umma yaganah tana shafa kanta tanata sake tambayarta abinda yake damunta. Amma yau bakinta budesa ma takasa sbd nauyin da komai jikinta yayi Mata Dan haka shiru kawai tayi tana sake yamutsasa daga Inda yake zaune da qananun rigima da hawayenta. Haj umma da itama abin ya isheta gashi majeed din taga baida niyar fita Kuma ta tabbatar sbd Rigimar Inayah dinne a siqe tace" Wai bazaki fada abinda yake damunki ba Akira likita ya dubaki ki dena Mana wannan koke koken? Wayarsace tayi ringin Yana dubawa yaga kamfanin furnitures din dayayiwa magana ne tun kafin yafito yaso suzo da wuri su sauya gadon dakinta kafin kowa ya fito.. Kamewa yayi tareda Basu damar shigowa su biyu ne maza matasa sai manager din kamfanin na uku suka shigo Kai tsaye ta kofar kitchen zuwa bedroom dinta suka fara fiddo da pieces na gado Daya bayan Daya suna fita waje dashi su umma yaganah na kallo cikeda mamaki. Umma yaganah tashi hankalinta yayi sbd tananin gadon ne ya balle yajiwa Inayah ciwo har take cikin wannan halin Dan haka cikeda kulawa ta kalleta tana kallon jikinta tace" Kinji ciwone Inayah? Meya sameki ne wai? Haj umma kuwa da kusan tafi umma yaganah shiga dibbin mamaki baki a sake tace" Uban me kika ringa yiwa gado me qarfi haka harya balle rugugu? Kinsan abinda kikai kenan kika jawowa kanki ciwo shine kike Neman daga hankalin mutane, Daqyar Naga safiyar yau din ta waye sbd tashin hankalin da naita ji tsakar sililun dare na dauka iskokai ne wlh a kitchen suna barin Kaya shiru kawai nayi sbd kada na daga hankalin jama'a Ashe kece kika tashi saka Jinina kaiwa dari biyu na mace abanza.. Wannan abin naki yafara wuce hakurin kowa Da girmanki shine Zaki hau gado kiyita tsalle ko rawa harkika Karya gado me tsada irin wannan.... magana fa ake Miki......cikin sauti Mai kosarwa a tausashe yace" Umma please..... Batada lafiya tambayan yayi Mata tsauri please.. sauran qarashen gadin da aka fito dashine yasasu kallon shatin Inda da alama buga gadon akai agurin yasa ya roshe take Haj umma takuma shiga mamaki me girma ta bude Baki zatai magana....... ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 0913484810764 BABU SO Chapter: 64 Share: Report BABU SO View: 167 Words: 2K Chapter 64 64 ........Dariya take tana masa gwallo. Fuska ya ɓata, da harɗe hannayensa a ƙirji irin yayi fushin nan. Yanda yay ɗin sai ya saka Anaam shiga ƙyalƙyala dariya da faɗin. “Kai Yaya shagwaɓa kuma?! ALLAH kamafi ƙyau a haka fuskanka so cute”. Ta ƙare maganar da kashe masa ido dariyarta mai ƙaramin sauti na bayyana fararen haƙoranta. Ta nuna lips ɗinta da kaɗa masa idanunta dake cikin gilashi. “Indai lipstick ɗin nan ne Yaya ba shansa zakai ba garama ka haƙura”. “Oh oh haba princess kiji tausayina mana”. Yaya maganar da matsar da fuskarsa gab da tata. Baya taja dasa hanunta ta kare bakinta, “Babu wani princess na daɗin baki fa Yaya, barima kaga na shanye abuna, idan baka ganiba ai dole ka haƙura”. Yana ƙoƙarin riƙota ta tura lips ɗinta cikin baki da sauri.. Idanunsa ya waro sosai yana kallonta cikin langaɓe wuya. Ta fito da lips ɗin tana dariya da masa gwalo. “Sai kaci abinci yanzu babu”. “Ni ko? Yarinya zan rama ne”. Dariyarta ta cigaba dayi ƙasa-ƙasa, shiko ya ɗauka spoon ɗin ya cigaba da cin aincinsa fuskarsa da ɗan murmushi. “Nifa yaya karka cinye min abinci na”. Idanunsa ya ɗago yana kallonta, sai kuma ya ɗibo abinci ya nufi bakinta, “Ba marowaci bane irinki ai hahh”. Bakin ta buɗe ba musu ya zuba mata, a hankali ta shiga taunawa da faɗin, “Nima ai bana rowa”. “Kika min yanzun?”. “Baga abincina kana ci ba”. Murmushi kawai yayi batare da yace komai ba. Itama bata sake magana ba, ya cigaba da bata abincin shima yana ci. Suna gab da kammalawa wayarsa tai ring, ɗauka yay ya duba, ganin Khaleel sai kawai ya ɗaga. Bata san mi'akace masa a wayarba, sai gani tai ya miƙe da kama hanunta.... Da mamaki take kallonsa zatai magana ya girgiza mata kansa. Baki ta ɗan tura dan ita dai bata ƙoshi da abincin ba, sai dai babu yanda zatai dole ta bisa. Hango Khaleel jikin wata mota mai ƙyau fara tas jingine ya sata zare hanunta cikin nasa, bai ce komai ba har suka ƙaraso. Ita ta fara gaida Khaleel ɗin, ya amsa mata fuska da murmushi sannan ya maida hankalinsa ga Yayansa. Gaisheshi yay da girmamawa. Ya amsa masa da kulawa. “Daga ina haka mazan fama?”. Murmushin Khaleel ya faɗaɗa dan yana son Yayan nasa ya kirasa da sunan nan. Wani ɗan ƙaramin gi! ya ɗakko a gaban motar, ya dubi Anaam dake kallon motar da ita kanta an naɗeta da zaren gi!. Sai kuma ya sake maida kallonsa ga Share" ɗin da shima dai motar yake kallo. “Saƙone daga Abie. Abawa Granny”. Idanu ta waro matuƙa da kai hannunta duk biyu saman bakinta, sai kuma ta dubi Share" da shima murmushi ke shimfiɗe akan fuskarsa. Shine ya amsa ya buɗe key na mota ya bayyana. Ai batama san sanda ta rungume Share" da faɗin, “Wayyo Yaya daɗi zai kasheni”. Rungumeta yay shina da sakin dariya kamar yanda Khaleel shina ke dariyar. Ɗagowa tai ta amsa key ɗin tana kallo, sai kuma ta ɗagasa a saitin fuskar Share" tana kaɗa masa. Murmushi ya sake saki mai faɗi da faɗin, “ALLAH ya sakama Abie da alkairi Congratulations dear”. Da amin ta amsa, Khaleel ma ya amsa da kallonta. “Congratulations Granny. Saura kuma tukuyci na, k ko Yaya wazai bani?”. “Karka damu Yaya Khaleel, saika zaɓa”. Ta bashi amsa da shigewa motar da Share" ya buɗe mata, daidai nan Fadwa ta fito hakama Aysha. A tare suka ƙaraso wajen, Fadwa da gaba ɗaya ranta ke'a jagule tun maganganun da Share" ya yaɓa mata ta dubi Khaleel fuska a tsuke. Kafinma tai magana ya nuna musu motar ita da Aysha yana murmushi. “Ƙyautace daga Abie aka kawoma Anaam”. “Woow!!” Aysha ta faɗa cikin zaro ido da shafa motar tana kallo, Fadwa kam mutuwar tsaye tai. Dai-dai nan Share" da Anaam dake cikin motar suka fito kowanne fuskarsa har yanzu da murmushi. Khaleel ya miƙa mata hannu, “Nifa a tafamin tukuycina”. Kafin tace komai Share" dake danna wayarsa ya miƙa masa, saka details ɗinka”. “Woow da kyau babban yaya da gudu kuwa”. Yanda Yay ɗin ya saka Anaam da Aysha kwashewa da dariya. Shigar saƙo a wayarsa yasa bai tankasu ba, ya buɗe da sauri, “What!”. Ya faɗa yana ɗago kai da sauri ya kalli Share". “Yaya duk tukuyci?”. Murmushi Share" yay da kallon Anaam, “Idan tace a ƙara maka ma sai a ƙara maka ai”. A salon da yay maganar da ɗage mata gira ya sakata rufe fuskarta da dukkan tafin hanunta dan taji kunya. Matsota yay tare da ranƙwafawa saitin kunenta. “Nima ina jiran nawa tukuycin yanzun nan, inba hakaba a gaban Khaleel zanyi.....” Da sauri ta buɗe idanunta... “Kayi mi?”. Maimakon amsa sai ya nuna mata lips ɗinsa cikin kashe ido. Sarai tasan zaiyi ɗin, amma sai ta kauda ido da nufin cewa a'a. Akan Fadwa da sam bata san da wanzuwarta a wajen ba ta saukesu. Sukaima juna kallon ido cikin ido, ita ta fara kauda idonta da sakin wani tattausan murmushi mai ma'anoni da yawa ta maido dubanta ga Share". Murmushi ta sakar masa shima ta ɗan saci kallon Aysha dake a mota hankalinta baya kansu, ta maida ga Khaleel, ganin shi ɗin dai zaiga komai sai ta ɗanyi jimm na tunani. “Yaya Khaleel kalla can”. Ta faɗa da sauri tana mai ɗane Share" a bazata ta manne tausasan lips ɗinta kan nasa lips ɗin. Numfashinsa neman shiɗewa yay saboda rashin zaton hakan daga gareta. Baya ta nema janyewa ya ƙara cafkesu da saka hannu biyu saman ƙugunta ta zuba masa mintsini a gefen ciki da janye jikinta kunya kamar ta nutse.. Khaleel daya waiga baiga komai ba ya juyo da nufin hararar Anaam, ai babu shiri ya sake maida kansa gefe da sauri yana dafe bakinsa da sakin siririyar dariya. Aysha da bata san mike faruwa ba ta fito a motar tana rungume Anaam da faɗin, “Wayyo blood motar nan ta haɗu wlhy ALLAH yasa a kashe da kai”. Wani bahagon tari ya sarƙe Fadwa, cikin sassarfa kamar zata kife ƙasa dan sauri tabar wajen hawaye masu azabar zafi na kufce mata. Gaba ɗayansu kallonsu suka maida gareta, dan sai yanzu ma shi Share" yasan Fadwar na'a wajen. Cike da son basarwa itakam Anaam ta rungume Ayshar. “Thanks you blood, thanks you”. Shima dai gogan ya basar a binsa kamar komai bai faru ba, ya nunama Khaleel hanya alamar su shiga ciki idonsa akan Anaam. Anyi sa'a itama ta ɗago suka haɗa ido. Baki ta ɗan murguɗa masa. Ya taune lips dinsa da sakin murmushi alamar azakizo hannu. Kafaɗa ta ɗage masa da labe baki irin na i don't care taja hanun Aysha suka koma motar... Da ƙyar Fadwa ta iya kai kanta sashenta saboda jiri dake ɗibarta da lulluɓe ganinta gaba ɗaya. “Subahanalillhi. Hajiya lafiya?”. Mmn Abu ta faɗa da nufo Fadwa da sauri dake neman zubewa ta tareta. Kuka ta sakar mata kamar wata karamar yarinya, maman Abu duk sai ta rikice. Kamata tai har bedroom. Tana son tambayarta mike faruwa tana jin tsoro, dole ta fito ta barta cikin damuwa. Tadai san labarin kitse baya wuce ƙoƙi dan ta jima da fahimtar Fadwa na cikin jerin mata masu tsananin kishi. Gata da hali irin na ɓoye abu a rai da idan bakai dogon nazari akanta ba saika ɗauka kishiya cutarta take musamman irin Anaam da bata iya ɓoye abinda ke ranta. “ALLAH ya ƙyauta”. Ta faɗa da komawa kitchen ta cigaba da aikinta..... Anaam kam da tuni sun koma ciki tana can cikin farin ciki tana waya da Mamie da Abie ta video call. Addu'a take zubama iyayen nata harda hawaye, yayinda suma suke kallonta murmushi shimfiɗe a fuskokinsu da tsananin ƙaunarta da tausayinta harma da alfahari da ita na kai mutuncinta gidan aurenta. Dan aunty mimi ta sanarma Mamie komai, hakama Mamie ta sanarma Abie, shiyyasa ya danƙara mata mota najin alfahari da ita akan riƙe tarbiyyar da sukai mata. Sai dai su kansu sun san sun kaita wani filin gwagwarmayar rayuwane na yankin kaddararta, amma sukanji sassauci da tunawa zumincin ALLAH suke son karfafawa insha ALLAHU sadaukarwarsu bazata taɓa zama a banza da wofi ba.. ______________________________ Tafiyar dai Aysha bata yuwu a yau ba, dan tuni Share" ya fice gidan tare da Khaleel yin godiya ga Abie, Anaam kuma sai ta ƙara samun sauƙin jikinta insha ALLAH zai kaita. Sai da suka fara biyawa ta o"ice yin wasu muhimman baƙi, ba wani dogon zama sukai ba sai zuwa monday idan ya dawo aiki. Takardar da zai basu suje su duba kafin zaman ya nema ya rasa, cikin ɗan dafe kai ya dubu Khaleel da Fharhan. “Inaga fa nama bar file ɗin nan a gida wlhy, Khaleel saika koma kenan dan dole ne mu basu suje su duba.” “Okay bara naje ai bawani nisa bane”. “Okay ba damuwa, kafin ka isa zan kira su ɗakko maka kawai”. Kansa ya jinjina masa ya fice. Shi kuma ya shiga ƙoƙarin kiran layin Fadwa. Harta tsinke ba'a ɗagaba, yay mata uzirin ko bata kusa ya sake kira, amma nan ma dai hakan, ya ƙara kira har sau uku sai aka koma danna masa number busy. Ransa ya sosu matuƙa, dan ya gane tana kan sani. Amma sai ya shanye kodan baƙin dake tare da shi ya maida akalar kiran ga Anaam. Gama wayarta da su Abie kenan kiran nashi ya shigo, bugu biyu ta ɗauka har yanzu muryarta cike da farin ciki tai masa sallama. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, ya amsa mata. “Har yanzu murnar motar ce?”. “Humm Yaya bazaka ganeba”. Murmushi yayi, “Okay idan na dawo ai sai ki ganar dani, yanzu nidai nutsu na saki aiki”. “Okay” ta faɗa kanta tsaye. “Ki duba a study table ɗina, akwai wani file green a wajen ki ɗaukama Khaleel zai zo ya amsa yanzun”. “Tom”. Ta duba a kurkusa inda yace amma bataga file ɗin ba, sai dai kuma hankalinta ne kawai bai kaiba saboda ya dannesa da wani book. Ta shiga bin komai daki-daki da kallo tana ɗan ɗagawa harda buɗe drawers ɗin wajen. Saukar idonta akan wani ɗan akwati ya sata nutsuwa tana kallonsa, harta maida drawer ɗin ta rufe sai kuma ta sake buɗewa ta ciro akwatin. “Uhhm su Alhaji Yaya mm mi kuma ake ɓoyewa anan? Koma dai miye zuciyata na son gani”. Tana ƙoƙarin buɗewa kira ya shigo wayarta, shine dan haka ta ɗaga. Kafinma yay magana tace “Yaya ban ganiba fa, inata nema kuma tun ɗazun”. “Kamarya? Bayan nasan yana nan akusa- kusa. Ki ɗan ɗaga kayan wajen Khaleel na waje yana jiranki amfani zanyi da shi”. “Oh sorry kamarma gashi anan ka ɗaura littafi akai”. “Ok ki kai masa yana jiranki”. Koda ta kaima Khaleel littafin sashen ta sake dawowa. Dan zuciyarta naga akwatin nan haka kawai batare data san dalili ba. Kiciniyar buɗewa ta shigayi, da ƙyar ta dace ya buɗu bayan ta haɗa da ƴan dabaru. Da littafi ta fara cin karo, ta ɗan jujjuyashi tana taɓe baki ta ajiye. Sai envelope brown babba. buɗeta tai ta zaro albom na hotuna mai tudu sosai sai dai bai cika girma ba a tsaho. “Hotunan sirri ne kenan su Yaya aka ɓoy....” ta kasa ƙarasa abinda ta faro. Ko'a magagin barci aka tasheta babu gilashi a idonta aka nuna mata hoton babu gargada zata bada amsar itace. Hotone da taga irinsa yafi guda ashirin a gidansu. Hoton ne da aka ɗauketa a ranar haihuwarta tun a asibiti. Tana rungume a hanun Yaya Share" Abie da aunty Mimi sun sakashi tsakkiya suna leƙenta a hannunsa ya babbake ya hanasu gani. Da sauri ta koma na ƙasa, shi kuma a ranar sunanta ne ita da shi, na gaba itace da shi da Mamie da Abie da aunty Mimi. Ta cigaba da buɗe albom ɗin mamaki fal ranta dan ta kasa fahimtar ma'anarsa. Hotuna na gaba sun kasance a gurare daban-daban. Wani wajen ita kaɗai, wani ita da shi, wani har da su Abie. Ranar birthday ɗinta na cika shekara ɗaya. “Ya ALLAH” ta faɗa tana cigaba da kallonsu daki- daki. Jikinta ya ɗan fara rawa ganin hotunan da har tana a shekarar shiga primary, secondray, kai har jami'a ma akwai, bayan zuwa lokacin Share" baya tare da su. Duk wani hoton birthday ɗinta akwaisa, hakama hotunan bikin salla kona wani taron makaranta kona islamiyya duk akwai. Hoton ƙarshe da yay matuƙar bata mamaki shine na ranar ɗaurin aurensa da Fadwa, itama kuma ranar nata ɗaurin auren da bata sani ba. Rubutun da yay a jikin hoton ya matuƙar firgitata.......... End of book Leave a comment C Post omments No Comments posted yet Contact Us Arewa Books Publishers WhatsApp: 09031774742 Email: arewabookspublishers@gmail.com Navigation Home About FAQ's Social Facebook Instagram Legal Privacy Policy Terms of Service Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.ioAssalamualaikum NAFISAT K ABDULLAHI Is an actress in the kannywood industry She's a singer and can sing all types of songs You can't afford to miss her newly released song named *KADDARATA* part 1-4 on her YouTube channel *OFFICIAL FEENAT* You can only click on this link and stand a chance to listen and watch her amazing video https://youtu.be/t__84EwU7Fo Dont only enjoy the emotional video but also *SUBSCRIBE* to anable you to be notified when ever she upload another video Like and drop your comment under the video to encourage her do more of that . The only way you can support and encourage her is by *SUBSCRIBING* to her YouTube channel below https://youtu.be/t__84EwU7Fo She is used to noticing those following and commenting on her videos . *GUESS WHAT*? https://youtu.be/t__84EwU7Fo Click and see for yourself Thank you so much *_64_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Innalillahi wai meya faru a gidan Nan ne bamu saniba? Barayi sun shigo gidan ne? Me sukai Mata? Menene wai kunqi fada kowa yayi shiru idan akwai abinda kuka sani bamu saniba ku fada Mana Dan tabbas nikam nasan naji motsi Babba a gidan Nan daren jiya. Maida kallonta tayi kan MAJEED Wanda ya miqe tsaye batareda yace komaiba yayi gurin manager din dazasuyi magana. Dawo da kallonta tayi kan Inayah hankalinta na Neman tashi tace" Yaganah ki tambayeta abinda yake faruwa ke idan Zata fada miki. Kallon Inayah umma yaganah tayi cikin kulawa da Dan tausasa murya tace" Inayah meyake faruwa ne? Fadamun kinji. Kuka Inayah ta fashe dashi a hankali tana sake lafewa jikin umma yaganah ta bude Baki daqyar tace" Ni ku Dena tambayata Banda lafiya koina jikina ciwo yakeyi ku tambaya Abbi. Kuma Ni Haj umma ki Dena tambayata na balla gado bani bace. Umma yaganah kallonta ta tsaya tanayi dakyau kaman tanason gane abinda ya faru saidai Bata Gama tabbatarda hakanba ahankali ta tayar da ita daga jikinta tace" Kukan ya Isa haka muje dakina ki kwanta to tunda yanzu daura Miki sabon gadon. Baki haj umma ta bude tana Neman ma'aunin dazata Dora kalmar Inayah na cewa a tambaya Abbin Bata Gama samun abin fadaba umma yaganah ta tayarda Inayah din tsaye su tafi daki taja ta tsaya tana sakin sabon kuka tace" Umma yaganah Ni bazan iya tafiyaba. A rude Haj umma ta hadiye zancenda dah Zata fada tana sauyawa da cewa" Ke bamason shashanci fa tafiyarma bazaki iyaba? Ahankali umma yaganah ta kalleta tace" Inayah meya sameki ne? Kasa kallon umman tayi tana komawa ta zauna sbd gurin yayi Mata tsami zafi takeji sosai. Zuwa lokacin umma tafara zargin komai Amma sbd kaman uwa take Kuma ba wani boyo tsakaninta da Inayarta Dan haka cikin kulawa da dan rage sauti tace" Wani Abu yafaru ne dake? Gyada Kai tayi tana sake tsiyayo hawaye tace" Umma yaganah zafi nakeji a jikinsa sosai, Abbi........ Hanata fada tayi tana Jin wani irin sanyi da nauyin maganar lokaci daya Dan haka ta juyo ta kalli Haj umma data sake Baki da hanci tana kallonsu tana jiran Jin abinda Inayah din Zata fada Amma Bata gane komaiba saidai kaman taso ta gane abinda umma yaganah ta hanata fadan.... Jin tayi hankalinta yayi mummunan tashi idan har wani abun ne datake zargi ya faru a gidan nasu shine aka karyo gado..... Qalu innalillahi wainnan ilaihrrjiun" tafada a zuciyarta zufa na Neman keto Mata, Me MAJEED zaiji agun wannan yarinyar dabazai Bari ayi Masa auren kece reniba da babbar mace dazai morewa rayuwarsa abasa Jin dadi da kulawa yanda ya kamata. Tunani me zurfi tashiga tana lissafin da batamasan tanayiba. Umma yaganah kuwa lallaba Inayah tayi akan su tafi daki Amma takasa tafiya gashi ita Kuma bazata iya daukantaba.. Rigima sosai Inayahn ta ringa zubawa Wanda yake sake dama lissafin Haj umma harta kasa hakura a fusace tace" Kinfa ishemu da kukan banzan Nan waye ya aikeki wasan banza da girmanki har kika jiwa kanki ciwo kikaja hasarar gado Babba irin wannan... Shigowar MAJEED dinne yasa Inayah maida kallonta kansa tasake Bata fuska tana sako sabbin hawaye tace" Abbi bazan iya tafiyaba Ni ka kaini dakin umma yaganah Haj umma tanata min fada na Karya gado saikace nice na Karya din. Haj umma ya kalla a natse cikin bayyanarda damuwa yace" Umma batada lafiya Ina Zata tsaya wani iya barna, Nufar Inayah din yayi ya kalleta cikin kulawa yace" Kema ki Dane wannan kukan ze sakaki ciwon Kai da zazzabi. Umma yaganah ya kalla yace" Kuje gurinki din tunda can takeso. Kin tafiya Inayah tayi Umma yaganah dataga dai Neman sanin komai zasuyi gaban MAJEED kunyar tayi Masa yawa tayi musu yawa Suma saita wucewarta tana cewa" Bari naje kitchen inada aikin Yi ni tunda bazakiba ki zauna idan kin tashi kinje. Tana barin gurin ya kalli Inayah fuskarsa a marairaice kaman zai Ciro ciwon daga jikinta ya mayar nasa ahankali yace" Na kaiki da kaina? Gyada Masa Kai tayi tana cewa" Bazan iya tafiyanba zafi nakeji. Shikenan ya Isa Dena hawayen Zan kaiki Amma ki daure ki Dena kuka idan ba hakaba kowa zesan meyake damunki. Haj umma datai zuru kaman jinta ya dauke Inayah ta kalla sbd abbin ya dauka itama ta wuce su kadaine a palon.. Juyowa yayi ganin tana kallon bayansa yaga Haj umma na zaune idonta baya kansu Amma dai baiyi zaton tajisa ba Dan haka ya Dan matsa daga jikin Inayah din zaiyi magana Haj umma ta tashi kaman Bata gani sosai tayi dakinta.... Tana shigewa ya janyota jikinsa ahankali Yana kallon shagwabbiyan fuskarta data kumbura sbd kuka da rigima ya shafa fuskarta Yana share Mata hawayen da tafin hannunsa yace" Dakin umma yaganah Zan kaiki ki kwanta ko nakaiki nawa? Lafewa tayi jikinsa tana girgiza Kai tace" Dakin umma yaganah zani. Ok to hawayen ya Isa muje na kaiki. Daukanta yayi cak kaman bayason jijjigata ya rungume jikinsa ta lafe tanajin sonsa na yawo zuciyarta Amma Kuma Bata marmarin zuwa dakinsa tayi baccin. Fitsari tace maza zatayi dan haka bedroom dinsa ya nufa da ita acan tayi fitsarin tana kuka tana komai duk tabi ta yamutsa Masa kayan jikinsa haka dai tagama suka fito yakaita dakin umma yaganah. Dayake yasan umman na kitchen dan haka har kan gado ya kwantar da ita tareda Dan rufeta tana sake narke Masa ga Kuma zabbinta da kaman zai dawo. Haka ya lallabata yabarta tayi bacci yakoma palonsa hankalinsa na rabuwa biyu. Baccine ya dauketa Koda umma yaganah tashigo zaunawa tayi tana kallonta cikin kulawa da tausayawa sbd ba shakka taci wuya a hannun abbin nata. Anty Hafsat takira tace tazo ta kula da Inayah din Dan itakam Batasan ya Zata lallabata ta iya kulawa da itama tunda dai da alama kulawa take buqata sbd yaji rauni sosai kila. Anty Hafsat kuwa ba Bata lokaci sai gata dasu ruwan bagaruwanta masu zafin gaske a qaton flask data dafa tazo dasu. Inayah na tashi bacci kuwa ta zuba matasu a roba suka shiga toilet din umman tana ihu da kuka da komai tasata Zama acikinsu... Ihunta da kukanta tana Kiran sunan Abbinta yasa Haj umma data Kama kanta a daki tun dazu tana shiga zurfin tunani fitowa tazo dakin tana tambayar lafiya hankali tashe. Umma yaganah dai kasa cewa komai tayi sbd Jin nauyi Anty Hafsat ce ta iya cewa" Ruwan zafi ne akasata Shiga sbd likita Dana Kira tace asata ciki sosai. Son tambaya Haj umma keyi na menene dalilin shigar ruwan zafin Amma gudun abinda zai iya hanata bacci yasata hadiye tambayar ta juya ta fice Tana cewa" Allah ya sauwaka" sbd ta lura gidan kowa na neman Zama abinda ya Zama kuma. Dakinta Takoma Yana jiyo irin draman da aketa Yi da Inayah din wadda tasaka zuciyarta kasa nutsuwa Dan kuwa wannan tabarar tata tasaka MAJEED dinta duk yabi ya susuce akan qanqanuwar yarinya. Bayan anty Hafsat tagama gasata da kyau sai gashi kuwa jikinta ya sake sosai tasamu Dan qarfin jiki da kuzari.. Umma Hadiza ma datasan halinda Inayah din take ciki sakamakon wayar data bugo Mata tajita sai rigima take ta daga hankalinta Dole anty Hafsat tafada Mata abinda yasamu Inayah din Karban waya Dr iklimat tayi ta fadawa anty Hafsat ta dafa Mata Naman rago kokuma gasa Mata abata taci tareda tea me kauri. Aikuwa hakan anty Hafsat ta dafo Mata wani Dan lafiyayyan farfesun nama da tea me kauri taci ba wani sosaiba tasha maganin da Abbinta ya aiko dashi na Dr Anna data Basu tun asubar. Tana Shan maganin tasake samun jikinta yaqara Dan sakewa Amma tana lafe ko wani dogon motsi Batayi sosai sai narke musu takeyi. Sai Bayan sallar ishai anty Hafsat ta tafi gida Bayan tasake sakata shiga ruwan zafi dakyau dakyau. Duk wunin tunda ta shiga dakin umma yaganah din Bata fitoba Dan haka Bata sake ganin Abbinta ba duk da kusan massages dinsa sun fi kusan goma Sha biyar a wayarta Bata budeba fushi takeyi dashi Amma qasan zuciyarta tanajin kewan rashin ganin nasa Koda daga nesa ne. Shi kansa gabaki daya a palonsa ya wuni batareda ya fitaba kusan duka ayyukansa sama sama yayi su iPad da laptop Nan gida batareda yaje office ba duk masu son ganinsa hakuri aka Basu Dan kuwa Koda ya fitan nutsuwarsa Bata tare dashi Dan ko acikin gidan kamewa kawai yayi Amma nutsuwarsa nakan halinda babyn Abbi take ciki. Sai guraren 10 ta nufi dakinta Dan yin wanka sbd zatafi Jin dadin wanka toilet dinta sbd idan ba towel din Abbi ba batajin ta taba iya daura towel din kowa a rayuwarta tanada damuwar hakan sosai barema umma yaganah da Bata daura towel se zani Dan haka ta tafi dakinta. Sabon gadon da aka daura Mata a dakin ta kalla Mai kyau da tsada kaman wancan duk saitaji abinda yafaru jiyan Yana dawo Mata Take tsikar jikinta ya tashi na tuno zazzafan Al'amarin da wasu daga abubuwan dasuka faru masu dadin da masu wahalar. Tubewa tayi ta daura qaramin towel dinta ta nufi toilet tashige. Ruwan zafi tasake shiga mintuna sosai kafin tayi wanka da ruwan zafin ta fito hannunta a kirji dafe da towel dinta sbd Bata daureba. Batasan da mutum a dakinba Saida takai tsakiyar dakin kafin qamshinsa yafara ankarar da ita ta tsaya cak tareda juyawa ta kalli Inda sofa take.... Fararen Lululemon ne masu tsadar ajikinsa Riga da wando na bacci masu kauri fuskarsa datai wani fresh kaman baby Yana kallonta da idanuwansa dasuka Gama galabaituwa a wunin na rashin ganinta da jinta... Ajiyar zuciya ya sauke ahankali tareda miqa Mata hannu ahankali yace" Come here babyn Abbi. Kallonsa tayi a marairaice tareda qin tahowar tana sake Dan riqe towel dinta Daya sake sauka kadan daga kirjinta tudun kirjinta farare tas suna sake Dan bayyana daga saman. Tasowa yayi ahankali ya iso Inda take tsaye tareda tayata dafe towel din nata Yana kallon gashin kanta da gaba gaban ya San jiqe gurin wanka ya kwanta Mata a gefen fuska. Kasa cewa komai yayi ya dago hannunsa daya ya taba wuyanta zuwa kirjinta yaji ba zafi Dan haka ya saki ajiyar zuciya tareda shigar da ita jikinsa ya rungume tsam Yana rufe Ido nutsuwarsa Da Bata jikinsa Wuni guda tana dawowa jikinsa ahankali. Saida yaji yasamu nutsuwa sosai kafin ya dago da ita daga jikinsa Yana kallon fuskarta da wata tattausan murya da bayason damunta yace" Yaya?kinci abinci? Jikin ya Dena Miki ciwo? Ko zamu koma gurin Dr Anna ne? Lafewa tayi jikinsa tareda narke fuska da murya tace" Aa Zata sakemun allura banaso Kuma. Shafa bakinta da yayi maganar a shagwabe yayi da hannunsa Yana kallon cikin fararen idanuwanta dake bayyanarda kasalar data wuni ciki da rashin kuzari shikuma yanayin idon yaji yasashi jin wani dumi ya Dan taso Masa. Hannunta ya Kama ahankali suka Isa gaban mirror ya zauna tareda zaunar da ita kan cinyarsa yace" Akwai sanyi ki shafa Mai sai ki saka Kaya kada sanyi ya kamaki.. Kasa dauke hannunta tayi daga kan towel dinta sbd ba daure yakeba Kuma Bata dauki Babba ba qaramine Dan Bata dauka zaizo dakin nataba a lokacin. Ganin taqi dauke hannunta akai kuma taqi motsawa yasashi bin towel din da kallo yaga gabaki daya Bai rufetaba cinyoyinta Dake zaune kan cinyarsa sai sheqi suke na lafiyar fata da hutu... Akan Inda hannunta yake ya tsaida idonsa Yana kallon saman kirjinta dasuka tsole idonsa,. Oil din Neutrogena ya Kai hannu ya dauka da kansa a gaban mirror din ya zuba kadan a hannunsa Yana cewa" A Ina zaa shafa man? A kan cinyarta yafara shafawa ahankali Yana bin cinyoyin da wani irin shafan mai Yana kallon fuskarta.. Wani irin shafan mai yake Mata Wanda yasata kallonsa da sauri Tana marairaice fuska Jin shafar na tada tsikar jikinta alokaci daya... Bata firgita ba Saida taji hannunsa cikin towel din shafarsa takai kan cibiyarta zuwa cikinta da sauri taja numfashinta dayaso daukewa tana rufe idonta da qarfi. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/15, 2:26 PM] Hajiya Qarama: *_65_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Ahankali da qyar ta iya cewa" Abbi" cikin qaramar murya tana riqe hannunsa daya Isa saman towel dinta daga ciki. Tsoro takeji sosai Saidai yanda yake matan Yana saka jikinta mutuwa tareda kasala sosai.. Juyo da ita yayi akan qafafun nasa Yana cigaba da shafa Mata Mai a wuyanta zuwa kirjinta tasake qanqame towel dinta ya kalli hannunta tareda yimata wata shafan man a gaskiyar bayanta a kidime ta saki towel din tana sargafo wuyansa sbd baya datayi Zata zube Dan kuwa yafin hannunsa a tsakiyar bayanta da Babu Kaya yayi mata wani irin shafa shock ya sakar Mata Shikuma Yana sarkafo wuyansa ya mannata da kirjinsa Yana lumshe ido cikin wani shauqi me dadin gaske. Bayanta yafara bi da shafa zuwa wuyanta Yana sauke wata wasu numfashi masu dumi Yana shaqar asalin qamshi fatar jikinta Dake Dan Qamshin shower gel dinta me tsada data gamo wanka dashi.... Dumin zafafan numfashinsa dayake sakar Mata a wuya suka sake gigitar da ita tsigan jikinta na tashi ta janye daga jikinsa tana fidda numfashin tsoro.... Janyewar datai yabasa Daman ganin kirjinta da kyau ya zuba musu ido yanajin kansa na qarasa birkicewa Dan kuwa har wani zillo kwanyarsa keyi acikin kansa.... Hannu yakai akansu ya Kama Yana lumshe ido tareda Kai Baki akai yafara yanda yakeso dasu kaman zai rasa ransa.... Hawaye tafara tana Kiran sunansa cikin tsoro dakuma rawar jikin abinda yake Mata din Dan kuwa Babu Inda baya mazari ajikinta da irin abinda yake Mata din.... Sake Kiran sunansa tayi murya a kakkarye bata gama Kiran sunanba ya dago fuskarsa ya Kama bakin da nasa Yana zuqo yawunta dasuka fara tsinkewa sbd Shiga yanayi na tsoro Dana zazzafan abinda ke tasowa daga jikinta.... Kissing dinsa yafi komai kashe jikinta sbd Babu Inda harshensa Baya shiga cikin bakinta ya zaqulo komai Dan haka take jikinta ya saki Yana ganin hakan ya tashi da ita ajikinsa suka nufi sabon gadon ya kwantar da ita Yana qarasa jefar da towel dinta Daya Dade da sauka.... Ganinsu kan gado yasata dawowa hayyacinta ta bude Ido da sauri hawaye na fara gangarowa ta girgiza Masa Kai tanason yin magana Amma ya kasa barinta ya sake jone bakinsu guri Daya Yana cusa hannunsa daya cikin gashinta Mai santsi da tsayi. Kuka tafara sosai Jin komai na jiyan na Shirin sake maimaituwa ga wani irin rawa da gurnani da Abbin keyi Daya sake rikitata tafa Kiran sunansa tana turesa Amma Sam Baya wani ganewa Bayan sunayenta Babu abinda yake fada.... Masifar datake ji yau din kusan irin ta jiyance sbd radadin ma na yau yaqaru sbd fami ne yayi Mata agurin... Kuka takeyi sosai shima kusan kukan yakeyi tana rokonsa Yana rokonta ahaka ya ringa yawo a duniyar Babynsa daqyar ya iya kwatar kansa ya zube gefe tareda shigewa jikinta ya qanqameta sbd idan baiyi da gaskeba ya qwaci kansaba babyn tasa bazata iya daukaba ta galabaita sosai. Kuka takeyi har lokacin Mara sauti sosai Dan haka Yana samun qarasa dawowa daidai ya dauketa suka nufi toilet, Yauma tare suka Shiga ruwan zafin Kuma har lokacin kuka take Masa tana qin kallonsa sbd kunya da zafi Dama fushi dashi. Sbd ita tasamu taji ruwan zafin yasa ya ringa shiga ruwan tareda ita sbd kukan Rigimar datake ya Hana ko tsayuwa da kanta ta iya Yi ga jikinta yayi zafi sosai da alama zazzabinta yakuma dawowa. Saida jikinta ya Dan sake sbd ruwan zafin kafin suka fito ko yau dinma Kaya kawai ya saka Mata suka wuce dakinsa ya suka kwanta ta dasa sabuwar rigamar jikinta na ciwo koina duk hankalinsa yabi ya tashi yafara rarrashinta Yana tambayarta Ina da Ina ne yake ciwon Amma takasa fada sai qananun kuka da hawaye take masa qarshe dai zaunawa yayi tsakiyar gadon ya janyota jikinsa ta kwanta yanda zataji Dadi da saukin jikin datace koina Yana ciwo ahaka bacci ya dauketa daqyar Bayan duk tagama dama Masa lissafi da rigimarta. Saida ya tabbatarda ta jima da baccin kafin ya zame ya kwanta da ita a jikin nasa yaja musu tattausan quilt dinsa suka shige Yana sauke ajiyar zuciya tareda kissing goshinta ahankali yana cewa" Babyn Abbi rigima. Sallar asuba ma latti sukai Amma ba sosaiba sunayi suka koma suka kwanta bayan yabata magani Tasha da rigima da komai haka ya lallabata suka koma baccin. Har guraren 10 Babu Wanda yaga Inayah Kuma daga Haj umma har umma yaganah suna shakkar tambaya sbd gudun abinda akai wancan karon kada ran MAJEED ya baci, Hakama ko umma yaganah dake shiga dakinta yau din ta Kama kanta taqi zuwa dubota sbd batasaniba ko MAJEED din Yana ciki, Bare su zubbi da dama yanzu ko aikin gyaran dakin Inayah zataje saita tabbatarda ko Inayah Bata dakin tunda akai auren Inayah din da Abbinta. Haj umma dai tayi tsit takasa magana itama gashi ko MAJEED din basuji motsinsaba bare ganinsa. Yau ko breakfast dai kusan kowa nasa yayi tsakaninsu biyun daganan kowacce tayi zamanta a dakinta. Inayah kuwa sai 10:12 ta farka daga baccinta ta Dan motsa tana sake gyara kwanciyar a jikinsa kafin ta bude idanuwanta ta dago ta kallesa ahankali shima ita din ya kalla sbd ya Dan Dade da tashi Amma Bai saukaba sbd baccin datake a jikinsa kaman baby bare dama shi Babyn tasa ce. Ahankali cikin Yar shagwaba tace" Abbi Ina kwana?¿ Shafa fuskarta yayi da bakin da yayi maganar tareda sakin kyakkyawan murmushi yace" Kin tashi lfy? Yaya jikin? Ya Dena ciwo koina? Girgiza Kai tayi tana tashi zaune ahankali daga jikinsa a shagwabe tace" Aa haryanzu yanayi. Zamu koma gurin Dr Anna ne? Girgiza Masa Kai takuma Yi duk da wata irin sabuwar azaba takeji agurin Dan kuwa yayi Mata tsami ma gurin ko tashi zaunen datayi cikin azaba tayisa. Saukowa yayi kan gadon tareda miqa Mata hannu ta Kama saidai bazata iya dogon motsiba take tafara hawaye tana cewa" Abbi bazan iyaba zafi.... Dawowa yayi kan gadon cikin tsananin kulawa ya shafa fuskarta Yana cewa" Ok,ok basai kinyi kukan ba Zan daukeki da kaina. Rungumota jikinsa yayi tareda daukanta ya sauko gadon da ita suka nufi toilet, Brush ma tana jingine jikinsa ya Dan rungumeta tayisa da rigima da komai sbd wai har qafafunta sunyi nauyi Bata iya tsayuwa sosai. Suna Gama brush agurin fitsari ta dinga zuba Masa kuka tana qanqamesa qarshe dai azabar datai yawa suna fitowa baida zabin Daya wuce Kiran Dr Anna. Wankama kasayi tayi haka suka fito daqyar ta iya Zama shima akan cinyarsa sbd zaman anan yafi sauki sauki. Kafin Dr Anna ta iso yanason tafara cin wani abin Amma taqi saima kaman sabon zazzabi dayake taso Mata. Daqyar yaga isowar Dr Anna Dan haka ya kamata da tata suka fito palon saidai maimakon tabiyo ta kofar dazata kawota palonsa direct daga harabar gidan saita biyo ta palon cikin gidan. Dole acan suka sameta tana ganin fitowarsu ta taso tana Dan murmushi takama Inayah din suka zauna tafara tambayarta. Guri yabasu yakoma palonsa, Tashi daga palon sukai suka koma bedroom din Inayah acan ta dubata daqyar sbd gurin Kam an qarasa gogesa Dan harda dinki Kam Dole sai anyi yau gashi kaman tasani tazo da kayan dinkin. Inayah na Jin abinda Dr Anna zatai Mata jikinta yafara rawa hankalinta yatashi tafara kuka. Daqyar Dr Anna ta iya farawa sbd kasa tsayawar da Inayahn tayi aikuwa tana farawa Inayah ta qwala ihun kuka tana cewa abarshi bataso... Ihunta yasa Haj umma dake zaune ta rasa abin Yi abin duniya ya isheta ta fito a gigice tana rarraba idon lafiya? Wane balain ne yasamu Kuma. Umma yaganah ma hankali tashe ta fito tana son qarasawa dakin Amma Kuma saita fasa ta tsaya tana tunanin taje kokuma kartaje sbd Batasan meke faruwaba. Wani Gigitaccen ihun kuka Inayah takuma saki tana Kiran sunan Abbi da umma yaganah tana cewa bataso Dr Anna ta barta. Ihun nata ya sanyashi fitowa daga palonsa zuciyarsa kaman Zata Fado waya yakeyi Amma Baima kasheba ya ajiye wayar ya fito. Ganinsu Haj umma na rarraba Ido Musamman ma ita tana tsoron kada MAJEED ya kashe 'yar mutane sai ganinsa sukai ya fito daga palonsa Yana kallonsu zuciyarsa na tsalle Take haj umma tasaki ajiyar zuciya a boye kafin tasamu karfin halin cewa" To meya samu yarinyar Nan kuma da safiyar Nan? Bai tsaya jinsuba ya wuce dakin Kai tsaye tareda bude kofar yashiga yana ganin abinda Dr Anna ke Mata ya dakata agurin tareda juyar da Kai Dan bazai iya ganin baby Inayah cikin wannan azabar ba.. Ya Salam" yafada cikin tsananin damuwa da kaunar Babynsa Hankali tashe yace" Dr ba wani abinda ya kamata ne se wannan? Dan dakatawa Dr Anna tayi sbd Inayah din Tama kasa tsayawar ayi abinda ya kamata ta dago ta kallesa tace" Dole sai anyi Mata dinkin Gaskia, Amma takasa tsayawa ko zaka Dan rarrasheta ta tsaya. Qarasowa yayi ahankali batareda ya iya kallonsuba ta gefenta ya zauna tareda daukan tissue Yana goge Mata zufa cikin kulawa yace" Baby Inayah ki Dena kukan Zata Miki ahankali.... Kuka takeyi sosai tace" Baayi ahankali Abbi azaba ne dashi sosai nidai banaso abarni haka bazan Karaba, Abbi bazan Karaba wlh ko dakinka Ni bazan Kuma zuwaba..Dan Allah abarni haka. Hawayenta yake sharewa Yana rarrashinta Amma takasa denawa duk tabi ta rikice. Kasa riqeta yayi sbd bazai iya ganinta cikin wannan halinba yace abar dinkin kawai shima bayaso. Dr Anna kuwa tace aa wannan Dinkin shine daidai dole se anyisa. Bazai iya ganinta cikin azaba ba Dan haka ya fito Dole umma yaganah ce ta riqeta akai Mata dinkin, tayi ihu,tayi kuka,tayi mutsu mutsu da barin zance kala kala na cewa bazata sake yarda da Abbin ba,bazata sake barinsa yazo dakinta ba nasa dakinma bazata sake zuwaba. Sulalewa Haj umma tayi Takoma daki sbd kunnuwanta Dake Neman kurumcewa kala Bata samu Daman fadaba ga MAJEED din da alama ko kansa baya ganewa sbd halinda take ciki. Kallon umma yaganah Dr Anna tayi Bayan tagama Tai Mata wasu alluran bayan na farko tace" Kada tashiga ruwa masu zafi sosai sai dinkin ya warke Kuma please kada ta koma gurinsa saita warke gabaki daya. Maganunguna ta bawa umman ta fito tana kallonsa Yana zaune palon a lame saidai a zahirinsa kaman zai cire kansa yakeji tsabar Neman bugawar dayake da halinda Babynsa ke ciki. Murmushi ta sakar Masa tareda sake fada Masa abinda ta fadawa umma yaganah ta wuce. Bayan tafiyar Dr Anna ta jima jikin umma yaganah tana kuka da ajiye zuciya kafin akasa zubbi ta hado Mata tea da Dan chips shima daqyar taci Tasha magani ta kwanta sai bacci. Tana yin bacci umma yaganah ta sauke ajiyar zuciya tana miqewa tsaye tareda kallon curtains din dakin dasuke qasa kaman fizgesu akai kokuma riqewa akai da qarfi suka balle. Bata tsaya wani dogon kalle kalleba a dakin ta fice Bayan ta rufe Inayah din da bargo. Tana fita ba jimawa yashigo dakin ganin tasamu bacci yayi kissing idanuwanta dasuka kumbura ya sake gyara Mata rufarta ya fice. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/15, 2:26 PM] Hajiya Qarama: *_66_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Yana barin dakin Bai samu nutsuwa sosaiba Saida ya koma dakinsa ya daga waya ya Kira babban Likitan Daya sani mutuminsa ne sosai a Australia yayi Masa bayanin halinda Inayah din ke ciki Dr Aron yayi Masa bayanin ba komai bane cikin qanqanin lokaci Zata warke sumul idan tanashan magani da kulawa. Umma yaganah kuwa kitchen Takoma da kanta ta dorawa Inayah din farfesun qoda da hanta Mara ruwa ko sai veggies kawai. Kafin tagama tana kitchen anty Hafsat suka iso itada Safnah da mimi dubiya duk da Mimi da Hafsat basusan menene ciwon na Inayah ba anty Hafsat ce kawai tasani Kuma itama hankalinta tashi yayi da umma yaganah ta sanar Mata anyiwa Inayah din dinkine. Sai bayan azahar ta farka jikinta a sanyaye ba qwari sbd tsamin da jikin yayi, Tashi zaune tayi ahankali tana Dan rintse Ido sbd ciwon dake jikin nata. Mimi ce cikin kulawa ta ringa Mata sannu tana tambayarta Yaya jikin nata, Safnah ma cikeda kulawa tayi Mata ya jiki itadai ba bakin magana saidai Kai kawai datake dagawa ahankali.. Anty Hafsat kuwa tanason yimata magana da dama Amma ganin su Mimi yasa batai dinba ta Bari sai Inayah din da ita suna  su Daya. Kallon anty Hafsat tayi fuskarta a Dan marairaice ta bude Baki tace" Anty Hafsat zanje toilet ki taimakamun. Jin hakan yasa Mimi ficewa daga dakin ta nufi dakin Haj umma Dan su gaisa tunda Koda suka shigo sun tsaya su gaisa Amma tana toilet gurin wanka, Safnah ma bin bayan Mimi tayi Dan gaida Haj umman su dawo. Suna fita anty Hafsat ta Kama Inayah dake tafiya ahankali kaman me koya suka nufi toilet. Fitsarin datai shima kusan Jin take kamar tayita kuka tana dorawa Abbi laifin. Ruwan dumi tashiga na Yan mintuna kafin tayi alwala ta fito tana tafiyar ahankali batareda an taimaka mataba sbd ruwan data Dan Shiga din ya rage Mata radadi kadan Kuma taji Dan sauki saukin radadin. Sallah tafara Yi tana idarwa ta gyara zamanta ahankali tana daukan wayarta da kusan massages dinsa ne suka shigo duk a jere gasunan Yana tambayarta Yaya jikin nata tareda kalmar "I'm sorry babyn Abbi" Karanta sakonnin kawai tayi batareda ta maida Masa amsaba zubbi takawo Mata farin cous cous da farfesun da umma yaganah tayi Mata sai ruwa Mara sanyi. Ta 'dan ci abincin sosai sbd rabonta da cin abincin arziki tun shekaran jiya da wainnan abubuwan suka fara samunta. Tana gamawa anty Hafsat ta Bata magani Tasha daga Nan tasake Dan sakewa su Safnah na dawowa daga gaiso Haj umma suka fara Yar fira sama sama Mimi na sake tambayarta meke damunta shiru kawai Inayahn tayi sbd Batasan me zatace ba kokuma ta fada wani ciwon daban Wanda zaisa zancensu ya Zama biyu itada anty Hafsat Dan Batasan me tacewa su Mimin na damunta ba. Fira sukayi ringa yimata dukkaninsu a dakin umma yaganah suka koma sbd umma yaganah din datace su koma can cikin dubara sbd dakin na Inayah yanzu kaman na mijinta ne tunda Yana kwana ciki ga curtains din dakin da Safnah ta nace da tambayar meya samesu suka katse da qarfi haka¿ Babu Wanda ya sani bare ya bada amsa amsa Inayah data sani amsar Bata faduwa daga bakinta jiya Abbinta ya balla gado yau Kuma tace damqi curtains ne sun balle¿ Suna dakin umma yaganah sunata fira Haj umma na Palo zaune masu sauya curtains sukazo suka wuce bedroom din Inayah din aka gyara ballewar da akaiwa can Inda suke daga saman aka maida curtains din suka fita suka wuce yau dai Bata ce ko kalma daya ba Ido tabisu dashi harsuka Gama suka fice, Ko MAJEED Dake gidan, shima yashigo dasu Bata tambaya ba sbd gudun jin abinda zai bata ruwa. Su Mimi a Nan suka wuni se magriba suka wuce aka bar anty Hafsat ita Saida tayi Isha a gidan ta wuce Bayan tasake tattaimakawa Inayar tasake shiga ruwan dumi da sauran abubuwan dazasu taimaka Mata gurin warkewa da wuri. Neesah da Anty Hafsat sunyi dariyar Inayah din harsun gaji Amma dai anty Hafsat Bata nunaba Neesah kuwa zagewa tayi tayi abarta a vidcall dasukai tana cewa" Babes, stitches fa? Are you for real???? Wlh Nima inason hakan idan time Dina yayi....ihun dariya takeyi tana sake mamakin Inayah data kasa magana sai Bata fuska da cewa" Abinda yafi stitches dinma Zaki samu idan dai bakinki bazai rokarwa kanki Alkhairi ba, Anfada Miki ba stitches dinma da sauki ne bare anyi? Ni bani ba sake yin sex na rufe bazan qaraba. Dariya Neesah keyi tana sake mamakin yanzu Abbinsu ne da wannan aikin. Suna Gama waya bayan tafiyar anty Hafsat tanason komawa dakinta tayi wanka ta kwanta Amma takasa sbd fargabar yauma Abbi zai iya zuwa Kuma tasan sauran azabar dazata biyo bayanta Dan hakan ta qi tafiya Dole toilet din Umma yaganah tayi wanka bayan tasaka zubbi taje ta dauko Mata towel da kayan baccinta. Ta gasa jikinta sosai tareda shiga ruwan dumi tagama ta shirya cikin kayan baccinta masu kauri ta haye gadon umma yaganah ta kwanta abincin dare dama tun anty Hafsat na Nan sukaci. Umma yaganah data gamo firarta a dakin Haj umma tadawo ta tadda Inayah kwance kan gadonta ta lafe tayi bacci abinta Kallo ta bita dashi tana sakin murmushi tace" Dama waya fada Miki barno gabas take¿ Ai hakan yamun daidai daga yanzu Zaki rage rawar kan tunda kinsan asalin menene auren yanzu sauran haihuwa itama ki sani saimu samu lafiyar bakin Nan naki. Toilet ta wuce bayan ta kashewa Inayah din wutar dakin tayo duk sauran abinda zatayi tayo alwala ta fito Dan sun saba basa kwanciya sai sunyi alwala Kuma wannan din duka MAJEED ne ya koyar dasu ya sabar musu da hakan. Kan gadon ta kwanta tareda Inayah din dayake gadon Gabba ne Addua kawai tayi ta shafawa kanta da Inayah Tai baccinta itama. Da asuba umma yaganah da fada da komai suka Shiga ruwan zafin sbd Inayah dake maqalewan bataso Haka ta bude Mata Ido batari suka shiga ruwan ta Dan jima ciki kafin tayi alwala ta fito tayi sallah. Tana idarwa komawa tayi ta kwanta batareda ta kunna wayarta data kasheba Dan tasan Abbinta Kira zaiyitayi itakuma ko muryarsa shakkar ji takeyi batareda ta warkeba sbd tasan muryarsa na shiga kunnenta zuwa gurinsa zatayi sbd tayi kewan ganin Abbin nata. Sai qarfe goma ta tashi Kuma a Nan takuma wanka ta saka wata qaramar Riga Mara nauyi da tsayi sosai A daki aka kawo Mata breakfast dinta tayi tana gamawa ta koma gadon ta haye tanason kunna waya Amma ta daure taqi. A nasa bangaren a zaune yaga safiyar ranar tayi sbd ko rufe Ido yayi idan ba ganinta zaiyiba radadin budesu yakeji, Wayarta Bata Shiga, Massages dinsa ba reply, Yayi yawon dakinta a cikin daren yakai so biyar Kuma Haj umma na jinsa duk zagayen yawon dayake Amma tayi shiru tana mamakin ikon Allah ikon Gaskia. Qarfe goma yasan tana tashi yawanci Dan haka karfe goman ya fito a shirye cikin ash brioni suit da black Christian louboutin fullcover shoes yafito Yana fidda wani sahirtaccen qamshi me sanyi da Dadi fuskarsa a natse saidai zuciyarsa a hargitse take rashin ji ko ganin Babynsa. A dining sukai breakfast shi dasu umma Amma Babu Inayah Ya kasa daurewa ya Dan dago a natse ya kalli umma yaganah yace" Yaya Inayah? Ya jikinta? Nauyi ne ya rufe umma yaganah da Haj umma data saki Baki tana kallonsa har zai iya tambayar jikin Inayah a gaban idonsu bayan kowannensu yasan menene matsalar Inayah din. Cikin Jin nauyi umma yaganah tace" Taji sauki alhmdllh Tayi breakfast dinta Takoma bacci ma. Baiji komaiba yace" Ok Allah yaqara Bata lafiya. Amin" ta amsa kafin tadan gyara zamanta da kallonsa tace" MAJEED Nima inason zanje maiduguri sbd anyi rashe rashe da bikukuwa duk bansamu najeba yanzu tunda ga Haj umma Nan saina samu naje nadawo. Dan tea dinsa ya kurba ahankali tareda ajiye cup din, Bayason tafiyan umma yaganah koina ko Ada can sbd kada Inayah ta shiga kadaici ko kadan Amma Kuma tafiyan nata yanzu baida doguwar damuwa sbd baby Inayah Zata dawo karkashin kulawansa idan umman Bata Nan zai zamu kulawa da ita da kyau ko yasamu nutsuwa. Ahankali ya kalli umman yace" Ba damuwa Allah ya tsare, Muna gaida familyn Idan nafita yanzu za'a siya Miki ticket din jirgi.. Yaushe ne zakiyi tafiyan? Ni yauma idan ansamu ticket din zanje. Dagowa yayi ya kalleta a natse ganin kaman son take tayi tafiyar da sauri itama. A natse cikin kulawa yace" Badai wani matsalan komai umma? Murmushi tasaki tana qarasa cinye yamball din bakinta tace" Bakomai MAJEED kawai dai nason tafiyar ne. Ok" kawai yace Yana sake Mata fatan sauka lfy. Tun Bai fita ba anan yakira yace asiya Mata ticket. Kudi ya saka Mata a account dinta saidai kawai taga alert bayan Kuma akwai kudi hannunta masu Dan yawa. Bayan fitar MAJEED Haj umma dataga tafiyar umma yaganah dai ta tabbata sai taji kewan gida itama na kamata koba komai zamanta daga ita sai Inayah rigima zasuta Yi tasani. Ita Kam umma yaganah tafiya takeson Yi tabasu guri sbd ganin sun takurawa majeed din a gurin kulawa da matarsa gwara abari su samu yanda suke so na kwana biyu tukuna. Da yamma umma yaganah driver yakaita airport ta wuce Inayah Babu kalan kuka da Rigimar da bataiba akan umman kada ta tafi koina Amma umma ta lallabata ta wuce. Bayan tafiyar umma yaganah Rigimar Inayah yasa ba girma ba arziki Dole Haj umma ta dawo rarrashinta ganin Babu kowa ko MAJEED dinma bai dawoba har lokacin sbd baqin turawan dasukeda taro dasu tun safe. Rigimarta tasa zazzabi Dan saukar Mata haka Haj umman ta lalace gurin lallabata har dare Sai gasu har ruwan zafin ma data Shiga Haj umman ce ta taimaka Mata a wunin. Tsabar rikitarda ita da Inayah tayi har ciwon Kai takeyi itama take tafara tunanin tafiyarta wlh sbd bazata iya wahalar Inayah ba kafin umma yaganah ta dawo Dan tasan rikitata Inayah zatayi 'yayanta su rasa gane kanta. A dakin Haj umman ta kwanta bayan zazzabinta ya sauka ta dawo daidai. A jigace Haj umma tayi Shirin kwanciya tayo alwala tayi sallar ishai tana idarwa akai knocking kofar dakin Kai tsaye tasan MAJEED ne sai alokacin ya dawo kenan. Basa damar shigowa tayi ya bude ahankali cikin nutsuwa ya shigo sanye cikin hoodie fendis Riga da wando milk dasukai Masa kyau sosai kaman ba bacci zaiyiba sbd komai yasaka kyau yakeyi Masa. Idonsa akan Inayah dake kwance suka fara sauka itama idonta fes akansa ta sauke tana kallonsa take idonta ya ciko da hawayen tsananin kewarsa datai ta tashi zaune ahankali tana kallonsa a narke. Da qyar ya iya kama kansa ya dauke idonsa daga gurinta ya qaraso ya zauna kan Kujera Yana gaida Haj umma datake kallon Inayah data tashi zaune tana kallonsa shima Sarai taga kallon Daya ringa yiwa Inayar. Amsa gaisuwarsa tayi tareda yimasa sannu da kokarin aikinsa Dan kuwa yau Kam ya wuni zur har dare gurin aikin. Miqewa yayi tareda kallon Inayah da itama shi take kallo a natse yace" Yaya jikin? Gyada Masa Kai tayi ahankali tana sake narke fuska sbd itadai tafison gurinsa akan gurin Haj umma tasan kwana zasuyi suna fada da Haj umma yauma haka suka ringa wahalda juna. Ganin yanda ta marairaice fuska tana Neman yin kuka yasashi mantawa da Inda yake gabaki daya gashi Daman tun jiya a Rikice hargitse zuciyarsa take da rashin babyn tasa Dan haka a natse yace" Zo, Taso naji menene kike Bata fuska, Me akayi? Gaba yayi ta kuwa fara kokarin saukowa Zata bisa Haj umma data rikice daga adhkar din datakeyi a Rikice tace" Binsa zakiyi? Ba Jin komai Inayah tace" Fada Masa zanyi yace umma yaganah tadawo kada ta dade.. Baki Haj umman tasake saki gaba Daya tana cewa" Wuce ficemun daga daki, Allah yasa gobe kizo kinamun kuka akan wlh saina fasa bakinki. Wucewa Inayah tayi tana cewa" Dawowa zanyi fa Haj umma Kuma shine yace nazo. Bazaki wuce daga gabana ba kenan. Wucewa tayi ta nufi kofa ta fice Haj umma nabin siraran cinyoyinta dake cikin three-quarter wandon baccinta da Riga. Tana fitowa Yana palon Bata ankaraba ya rungumota ta bayanta tareda sake ajiyar zuciya me sanyi Yana sake kwantar da kansa a bayanta Itama ajiyar zuciyan ta sauke tareda juyowa ta kallesa a marairaice Zata Kira sunansa ya Dora bakinsa akan nata yayi kissing ya dago ya kalleta ahankali yace" Kinsan me kikayi min jiya kuwa? Kinsan yanda nayi wunin yau kuwa? ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/16, 9:22 AM] +234 806 494 4178: *_67_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Kasa janye jikinta tayi sbd tayi missing ganin abbin nata sosai duk da akwai tsoronsa aranta na kebawansu su kadai. Dan zamewa tayi ahankali ta juyo ta kallesa a marairaice tana narkewa kafin tayi magana ya shafa lips dinta ahankali cikin kulawa Yana kallon cikin fararen idonta ahankali yace" Yaya ne? Babyn Abbi tasamu lafiya? Yaya jikin? Sake narke Masa tayi ganin yanda yake tambayar cikin kulawa sosai da bayyanarda tarin sonta Dake rinjayarsa tace" Abbi shine yau ka wuni baka gida kilama ko abinci bakaci. Wani qayataccen murmushi yasaki Yana Kama hannunta suka nufi dakinsa ta gabanta na faduwa Amma haka ta daure suka tafin. A palonsa suka zauna ya dorata kan cinyarsa Yana kallonta yace" Naci abinci Amma banji daidaiba ko nutsuwar komaiba sai yanzu danaga Babyn Abbi. Sai alokacin cikin Yar shagwaba tace" Naji sauki to Amma haryanzu da sauran rashin lafiyan. Murmushi yayi Yana gyara Mata qaramar hular kanta me kauri sosai ta sanyi yace" Zaki samu lafiyan duka sosai sbd inata adduan baby Inayahn Abbi tasamu sauki sosai. Lumshe ido tayi tareda Dan juyar dasu hakan yasa ya dauki hankalinsa tareda Burgesa sosai Dan haka ya shafa idon yana cewa" Wannan juya idon shima koya kikayi sbd ki qarasa jagwala ni? Dariya ce ta kubuce Mata Mara sauti sosai ta dora hannunsa dake kan idon nata Yana shafawa a shagwabe tace" Abbi juya idon ne zaa koyamun? Nice nayi abuna Kuma ai ba komai bane. Matso da fuskarta yayi ya hade da tasa suna shaqan Qamshi da numfashin juna direct ahankali cikin qaramin sauti yace" Karkimun irin wanna juya idon a gaban mutane sbd bansan mezai iya biyowa bayaba. Kallonsa tayi da mamakin zancensa ta Dan motsa Baki zatayi magana sai Kuma ya fasa tana Dan zamewa daga jikinsa ya dawo da ita sosai Yana sake matseta suka manne sosai Yana shaqar qamshin Dake tashi cikin wuyanta zuwa cikin rigarta.. Ahankali cikin wani qaramin sauti tace" Abbina.... Kasa qarasawa tayi sbd Jin hannunsa cikin rigarta Yana shafa cibiyarta zuwa saman kirjinta Taja numfashinta dake Neman sarkewa da qyar sbd yananin yanda yake shafar kaman Yana janye numfashinta... Daqyar ta iya bude bakinta dake daidai kunnunsa ta sake Kiran sunansa a hankali Wanda shikuma numfashinta da maganar datai cikin kunnensa a hankalin ya sake zugo kaunarta da buqatarsa akanta duk da hakan Bai nuna komaiba ya juyo kadan da fuskarsa bakinsu ya hadu ya Kama nata bakin tareda tura harshensa ciki Yana shanyo duk yawun Daya katse bakinta na fargaba data shiga. Kiss din nasa baigama juyar da qaramin kantaba hannunsa ya fincike hular kanta ya jefar tareda dago kansa ya shige dashi cikin rigarta ya fara lasar cikinta zuwa saman kirjinta dasukai tsamin jiran sabuwar gwamutsa. Fara mantawa tayi da azabar datasha dakuma dinkin Dake jikinta ta sakar Masa jiki yaringa lasarta Yana binta da kisses da komai. Rigarta da kansa yake ciki qarshe maballan rigar kasa dauka sukayi suka fincike Dan kansu suka watse a gurin..... Rigar na rabuwa da kanta ya bude idanuwansa ahankali ya kalli fuskarta ya kalli abubuwan dake sake buga kwanyarsa yace" Babyn Abbi Zaki buga kan Abbinki.. Bata iya cewa komaiba sbd abubuwan dayake Mata sun gama kashe Baki da jikinta. Wasa yayi sosai da ita suka jagwalgwala juna tareda watsar da kayansu anan batareda yayi komai da itaba ya dauketa sukai bedroom dinsa sukai wanka kawai suka kwanta. Ba Bata lokaci kuwa bacci me Dadi ya daukesu su dukan a take yau shinema lafe cikin jikinta itace ya rungumesa kansa a kirjinta Kaman wani babyn. Asubar fari bayan sungama sallah Inayah ta silale Takoma dakin Haj umma tana toilet ta haye gadonta ta kwanta ko Gama gyara rufarta bataiba Haj umman ta fito toilet taganta tanata kokarin kwantawa sbd kada haj umman tace komai" Shiru dau Haj umman tayi batace komaiba sbd ganin safiyar fari kada su fara tallan hali...Amma Banda sun Gama Rena Mata wayo yarinya ta kwana acan bayan uwar wahalar data Bata gurin gasata jiyan Amma shine gabanta zai Mata wani Kiran munafurci cu tsallaketa subarta se yanzu yarinya Zata dawo tana Neman nuna kaman ba acan ta kwanaba. Sallarta ta tada tayi tareda lazimi tukuna tazo ta kwanta lokacin Inayah tayi bacci tuni. Guraren 10 wayar inayar ta isha Haj umma da vibrating Dan haka Dole ta tada ita ta miqa Mata wayar tana ganin sunan majeed ne akai Kuma. Inayah na karba ta dauki wayar ta Dora a kunne tanajin abinda yace ta tashi tareda saukowa gadon baccinta Bai wani ishetaba ta nufi kofa ta fice. Bedroom dinta ta nufa tana Shiga ta tube tareda daura qaramin towel tana kokarin juyawa yashigo dakin sanye cikin kayan asalin Adidas farare Riga da wando yafito daga exercise.. Qwandarsa masu nuni da qaqqarfarsa ta kalla kafin ta kalli fuskarsa tana shagwabar da tata tace" Abbi Ina zamu? Janyo towel dinta datek riqe dashi yayi ta matso jikinsa batareda towel dinta ya saukaba Yana kallon farar fatar kirjinta tas kaman ta baby Saida yakai bakinsa yayi kissing ahankali kafin yace" Good morning baby Inayah. Sai lokacin ta tuna Bata gaidasaba gashi shi Yana gaidata,. A shagwabe tace" Ina kwana Abbi? Sai Daya lakaci hancinta kafin ya amsa Yana gyara Mata daurin towel dinta da kansa yace" Jeki kiyi wanka ki shirya Zan fito cikin mintuna qalilan Nima. Sakinta yayi ta wuce toilet tashige shima ya juya ya fice daga dakin ya nufi hanyar nasa ya shige. Wanka tayo na Musamman sbd fita zasuyi da Abbinta duk da batasan Ina zasuba. Tana fitowa ta zauna gaban mirror tashafa oil sbd kaman koyaushe tafi amfani dashi. Turarukanta kadan ta shafa sai B opium dinta dashima ba wani sosaiba ta fesa a iya Indies dinta. Doguwar rigar lace tasaka fari tas Mai shegiyar tsada da rashin golden acikinsa ta dauko medium gyalen chantley ta yafa. Daga ita se wayarta da flat takalmin Chanel ta fito tayi kyau very simple abunta. Ko qarasawa tsakiyar Palo bataiba saigashi ya fito cikin brown Kaftan masu laushi da tsada take qamshinsa ya doke nata sbd ita Bata sakaba a kayanta iya na jikintane saina kabbasa dake kayan nata. Kyau yayi Mata sosai taji sonsa na ninkuwar Mata ta marairaice fuska Zata Masa shgawaba shikuma da Yana ganinta yaji zuciyarsa ta sake rufewa ruf da ita Dan dama Babu wani space ko Dan qanqanin fili Daya rage a zuciyarsa da rayuwarsa da Bata Gama cikesaba shiyasa har Koda yaushe yasan Babu kalman dazata fassara matsayinta a rayuwarsa kowama dasuke ganin abbi na tsananin so da kaunar Inayah fada kawai sukeyi Dan basusan asalin girman matsayintaba da girmansa Wanda shima baisan adadinsaba. Ganin tana kallonsa Bata kamasaba kaman yanda ta saba yasashi miqa Mata hannu Yana isowa ta Kama abunta kuwa suka nufi dakin Haj umma. Ko a dakin Haj umman Bata saki hannunsaba tabarsa da 'yan kame kame gaban Haj umman Itadai Haj umma kasa kallonsu ma tayi sama sama ta amsa gaisuwar suka fice. Breakfast sukai Basu wani Bata lokaciba suka Gama suka fice. Hanyar asibiti taga ya nufa take tasan gurin Dr Anna zasu Dan dama jiyan yanata maimaita tambayar warkewarta. Suna Isa kuwa Dr Anna da murmushi ta tarbesu shine ya zauna ita Saida sukai kuryar office din ta dubata. Babu wani Bata lokaci tayi musu duk abinda yakamata suka Gama da asibitin suka dawo gida. Ajiyeta kawai yayi ya juya zuwa office da aketa jiransa suna kiransa. Tana shigowa gida itakuma ta tadda momynta Dr iklimat da umma Hadiza a gidan Da wani irin tsananin farin ciki da murna ta rungume Dr iklimat tana cewa" Mommy yaushe kukazo? Bayan na fita??? Umma Hadiza ta kalla cikin kauna irin ta uwa da 'ya ta rungumeta tanajin nutsuwa dakuma dumin uwarta tsawon lokaci kafin ta saketa tana cewa" Shine Baku fadamun zakuzo ba? Haj umma dake zaune dasu a Palo suna Yar firar Dole sbd Babu me tarbansu dole se itan tunda itace kadai a gidan sai masu aiki. Farin cikin ganinsu yasa duk tasake narkewa tanata lafewa kaman Bata warke ba. Dakinta suka nufa acan suka zauna Dr iklimat na kallon tafiyarta cikin kulawa da murmushi akan fuskarta tace" Baby Inayah menene haryanzu Naga tafiyan kaman be dawo daidaiba? Baku koma asibiti bane? Zama tayi daga drinks da snacks dataje da kanta ta hado musu daga kitchen tace" Daga asibitin nake yanzu. Daga hakan sukabar zancen sbd ganin Inayah tanajin nauyin zancen Kuma nuna Jin nauyin yayiwa umma Hadiza Dadi sosai. Fira sukeyi abinsu hankali kwance saiga anty Hafsat tazo gidan itama aikuwa Nan suka sake sakata gaba da maganganu kala kala tun tabajin nauyin wasu hartafara Jin nauyi karshe dai Kitchen ta gudu tabarsu. A gidan suka wuni se magriba suka wuce dukkaninsu Haj umma tayita magana ita kadai da mamakin yanda iyayen Mata zasuzo gidanta su zauna su sake Baki da zantuka kala kala hardana banza, Wannan Dr iklimat da dogon bakinta tasani idan ba ganin sukayi sunsaka Inayah ta rabata da MAJEED dinta kwata kwataba ya qare a bautan Inayah hankalinsu ba kwanciya zaiyiba, Tasan zuwan Nan nasu se abinda Allah yayi yau. Bayan tafiyarsu dayake sunci abinci sunyi sallah Dan haka Kai tsaye dakinta Takoma ta tadda zubbi na gyarawa Dan hakan ta dauki wayarta ta fito Palo ta zauna tareda saka Kiran Abbinta. Har Zata tsinke tukuna ya dauka cikin nutsuwa yace" Yes Inayah¿ Abbi haryanzu baka dawoba aikine? Kana lfy? Dan gyara murya yayi kadan Yana dauke Ido daga kallon su CM dake taredashi da baqinsu sbd muryarta kawai sanyi take saka jikinsa Yi Shiyasa aduk lokacinda Zata kirasa tun acan idan ze dauka saiya Dan fita daga Mutane sbd kada a Gane rauninsa, ahankali yace" Zandawo gida Nan da time kadan" Yana fadar hakan suka kashe wayar kusan atare shi da ita. Itama tana ajiye wayar anan palon tayi zamanta Saida zubbi tagama gyara koina har palo dasu dining room aka sake kunna abubuwan qamshi tukuna ta miqe ta nufi dakinta. Tubewa tayi ta nufi toilet tashiga ruwan zafin bagaruwan da Anty Hafsat yauma tazo Mata dashi acikin roba ta shiga sbd Yana Bata toilet Dan haka tana Gama shigarsu a robar takira zubbi ta fice da qatuwar robar itakuma ta zare towel dinta tafara wanka. Tana gamo wankan Mai kadan ta shafa da turare ta saka kayan bacci ta Dora abaya akai tayi sallar ishai Tana idarwa ta haye gadonta ta zauna tareda rufe qafafunta ta dauki wayarta tafara duba chats dinsa da Bata samu damar bi ba yau sbd zuwansu umma Hadiza. Tana cikin chatting sama sama bacci yafara daukanta ta sake Nemo numbern Abbinta tasaka kiransa ganin har time din be dawoba. Wayar Bata shigaba Dan hakan ta sauko da qafafunta kan gado tareda miqewa ta zira slippers ta nufi dakinsa. Haj umma tashige tuni Dan haka tsit ba kowa ta nufi palonsa ta bude tashiga Kai tsaye ta nufi bedroom dinsa. Tana budewa Yana fitowa wanka daureda towel brown. Fuskarsa ta kalla ko Bai fadaba taga alamar gajiya ataredashi Dan haka ta matso gurinsa tana cewa" Abbi kaci abinci kuwa? Lumshe fararen idanuwansa yayi tareda budesu akanta baice komaiba ya janyota jikinsa ahankali ya rungumeta tareda sauke ajiyar zuciya mara sauti dukkaninsu sukai shiru basuce komaiba suka jima ahakan Saida ya samu nutsuwa da Jin gajiyarsa ta rage sosai kafin ya saketa suka kalli juna Ya maida kallonsa kan rigar jikinta Daya jiqa da ruwan wankan jikinsa Daya fito dasu. Murmushi yasake Yana Kama hannunta suka nufi gaban mirror. Mai ya Bata a hannunta Ta kallesa ta cikin mirror kafin ta karba ta fara shafa Masa ahankali hannun na Dan rawa Wanda shikuma yanda takeyi ahankali kaman tana shafa baby dakuma Dan rawar da hannunta keyi yasashi jin jikinsa na sake mutuwa gabaki daya hakama zuciyarsa na sake raunana da tafiyar Nan data taso Masa wadda zaiyi gobe Inshallah. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107 [11/16, 9:23 AM] +234 806 494 4178: *_68_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Tana Gama shafa masa man ya Jata ta tayasa saka kayan baccinsa Babu me doguwar magana acikinsu sbd gajiya dakuma lura datayi bayajin maganar kwata kwata da alama akwai abinda yake cizon ransa. Kwantawa sukai yauma shine ya shige jikinta ta rungumesa tana shafa bayansa ahankali har bacci ya dauketa. Jin bacci ya dauketa ya sanyashi zamewa ahankali ya gyara Mata kwanciyarta tareda shigar da ita jikinsa ya rungume bayan yayi kissing goshinta ahankali. Bacci sukayi sosai har yaso lattin sallar asuba, Tada ita yayi sukai sallar Suna idarwa ta matso jikinsa ta kwanta tana kallon fuskarsa ahankali cikin kulawa tace" Abbi akwai abinda yake damunka ne? Murmushi ya sake Mai kyau tareda saka hannuwansa cikin hijabinta Yana yawo dasu cikin rigarta yace" Bakomai kawai tafiyane ya kamani tsawon sati biyu Ina tunanin ko Zan iya ne. Kallonsa tayi fuskarta na narkewa tace" Sati biyu Abbi? Nidai bazan iya sati biyu baka Nan umma yaganah Bata nanba. Wani murmushin ya sake Yana zare hijabinta yace" Zaki iya ga Haj umma Nan Zata kula dake tunda taga bama Nan. Shiru tayi sbd kada ta fada abinda zai Sosa ransa Amma ai kowa yasan basa jituwa da Haj umma. Jin tayi shiru ya sake matseta jikinsa tareda daukanta suka koma kan gado suka koma bacci Yana cewa" Bazan sati biyun ba Zan dawo sbd nasan nabar patient ai. Murmushi tayi tana sake lafewa tace" Nidai kada kayi sati biyu Abbina kaji?? Bakinta ya Kama ya tsotsa sosai cikin nutsuwa kafin ya gyada Mata Kai. Bacci suka koma har sai karfe goma kaman yanda suka Saba fitowa suka fito abbin Yana shirye tsaf cikin ash Armani's fuskarsa a natse cikin sahirtaccen marmushin Dayake sake bayyanarda kyansa da kwarjininsa. Hannunta cikin nasa suka nufi dakin Haj umma data fito dakin dan zuwa Kiran Salimat tazo tai Mata gashin qafafunta data kwana suna Mata ciwo sbd ciwon bayan da Inayah ta sakar Mata tun shekaran jiya gurin dawainiya da yaqin kulawa da ita ba masifar da basuyiba gurin shigar ruwan zafinta Wanda duk tabi ta jijjigata gashinan ta taso Mata ciwon baya da qafafu. Kallon fuskar MAJEED dinta tayi taga kwanciyar hankaki da nutsuwa tareda kyakkyawan sahirtaccen marmushi akan fuskarsa Wanda ke bayyanarda nutsuwar zuciyar Daya samu. Wani sanyi jikinta yayi tareda da farin cikin ganin 'danta yafara komawa ABDULMAJEED dinta data sani ba AA MAJEED ba Wanda zuciyarsa take a kulle Babu farin ciki ko walwala acikinta ko kadan. Inayah data wani narke a gefensa ta kalla a karon farko dataji Dan sanyin Inayar fuska a sake ta amsa gaisuwar MAJEED din tana kallon Inayah tace" Lafiya kike yamutsa fuska kaman zakiyi kuka? Sake riqe hannun Abbinta tayi tana sake Bata fuska tace" Haj umma Abbi fa tafiya zaiyi har sati biyu abarki Dani Bazaki iyaba kema ko? Haj umma ko taso Jin sanyin Inayah iya shegenta kesawa suna watsewa da wuri, Cikin gatse tace" To idan bazan iyaba saiki bisa kokuma nace Karya tafi ko? To yatafi Allah ya kiyaye Zan iya Dake din ai. Kai Haj umma wato sbd kada aje Dani kokuma yadawo da wuri shine zakice Zaki iya Dani? Abbi cewa fa tayi duka Zataiwa bakina idan Ina maganar da bataso tun a gabanka ma Idan ka tafi kuwa kilama Koda zaka dawo Haj umma ta sauya maka kamannin baby Inayah dinka. Wani kyakkyawan murmushi yasaki Yana kallon Haj umma data sake Baki tana kallon shegen bakinta da sai yanzu tasan me umma yaganah keji datake buge Mata bakin.. Inayah ta maidata gabaki daya kakarta ko alamar nuna a uwar miji ta dauketa batayiba, Haqiqanin kakarta ta dauketa.. Cikin kulawa Yana sake fadada murmushinsa gaban Mata biyu dayafi so a rayuwarsa fiyeda komai da kowa, Matan dazai iya komai akansa Banda sabon ubangiji Amma Babu abinda bazai iya badawaba akansu ciki harda tasa rayuwar, Farin ciki da zuciyarsa ne tsaye a gabansa tsaye suna Rigimar tafiyar tasa, Hakan yasake saka zuciyarsa farin ciki ya sake kallon Haj umma yakai hannunsa yakama hannunta cikin kulawa yace" Haj umma karki biyewa Inayah so take tasaki kiyita magana, Ki kula da ita tunda yanzu ke kadai take da ita umma... Inayah ya kalla yace" Ki lallaba Haj umma karkiyita sakata magana, Idan kinsan Zaki fada abinda zai sakata fada ki dena fada kiyi shiru okay???? Gyada Masa Kai tayi tana sake janyo hannunsa daga na Haj umman ta riqe cikin nata tana cewa" Haj batason ana riqe hannunta tace Idan na rike cewa takeyi bataso damunta hakan keyi bataso. Haj umma da Inayah tagama cika kanta ta janyota daga hannun Abbin tana cewa" To ki barsa kema ya wuce kada yayi latti. Mamaki suka fara basa Dan haka ya juya Yana cewa" Muje breakfast zanyi tukuna kafin na fita. Sbd tafiyar dazaiyi yasa Haj umma yin breakfast din tare dasu zuciyarta na sanyi da kaunar 'danta sbd rabonta dataga farin ciki ko walwala a fuskar MAJEED tun kafin haduwarsa da Hadiza. A natse sukai breakfast din Inayah na maqale gefensa duk tabi ta narke da rigima kala kala akan tafiyar sbd ba zato fa kawai tafiyar tazo Masa. Haj umma ala Dole ta kwankwade sauran tea dinta ta tashi tabar gurin sbd Inayah na gap da saka MAJEED yin abinda baiyi niyaba a gaban Haj umman. Haj umma na fita ya janyota kan cinyarsa ya zaunar Yana shinshinawa kaman maye, Hannunsa daya ya saka cikin rigarta da batada komai aciki ko bra Dayan hannunsa Kuma fuskarta ya kamo ya hade fuskarsu ya Kama bakinta yana zuqe zaqin tea din datake sha. Wani mayen numfashi sukaja a tare Yana sake yin sama da hannunsa cikin rigar tata Yana Mata wata irin yamutsa.. Kissing dinsa yafi komai rikitata Dan haka Batasan lokacinda ta sake kamo kansaba tana basa daman shanye zaqin bakinta tas.. Duk wata muguwar wasan romance Saida suka Gama yinta a dining din kafin yabarta suka koma dakinsa ya sauyo Kaya sbd gabaki daya sun yamutsa wainnan. Ganinsa da waje kayan dazai wuce yasa Haj umma Yi Masa sallama daga kofar dakinta Takoma suka wuce waje Inayah har lokacin tana maqale da hannunsa tana Neman Masa kuka duk tabi tasake yamutsa nutsuwarsa haka ya rarrasheta yasamu ya wuce. Tana dawowa Bata dire koinaba sai dakin Haj umma ta haye gadonta tana kukan da Haj umma takira da kukan iya shege. Banza tayi Mata harta Gama kukan batarar ta tashi taje dakinta tayi wanka ta koma ta kwanta tana chat da Neesah. Tana gamawa umma yaganah ta Kira suka jima suna waya daganan Kuma dakin Haj umma Takoma sbd ta Saba dakin umma yaganarta take zuwa to yanzu batanan batada zabin Daya wuce zuwa na Haj umma. Ko data je Haj umma nata waya dasu anty safiyyah har tace Bata Inayah din su gaisa Haj umma ta miqa Mata wayar tana hararar kayan dake jikinta na wasu Riga da wandon Nike masu kauri Amma basuda tsayi sosai. Gaisawa sukayi da Anty safiyyah har take Mata ya jiki sbd takira MAJEED shekaran jiya ta tambaya Inayah din yace batajin Dadi. Cikin zolaya tace" INAYAH kodai laulayin ciki ne kikeyi mufara Shirin tarbon yayan MAJEED din Haj umma?? Haj umma ta kalla tace" Aa anty safiyyah Amma nakusa samu ai tunda Haj umma tace Dr farhat Zata aurawa Abbi ta Haifa Masa 'yaya......... Pillon kujerar dake kusada Haj umma ta dauka ta jefawa Inayah tana cewa" Wannan yarinya Allah ya rufa Mana asiri Dake, Ke wai haryanzu bakiyi hankaliba kenan bakinki yafara nutsuwa ko?? Ban wayata kafin na fasa bakinki kisan na yaganah Wasa ne. Wata muguwar dariya anty safiyyah take saki cikin wayar sbd Allah ya hada Haj umma da sirikar da dolenta Zata biye Mata su Zama daidai... Koba komai ta wani bangaren Inayah jikartace da baayi aurenba. Kin Bata wayar Inayah tayi ta tashi ta gudu bakin kofa sai data Gama magana da anty safiyyah dake sake cewa" Inayah takurawa Haj umma saita karbeki complete dinki matar MAJEED uwar jikokinta Kuma jikarta. Haj umma ganin Inayah na Neman Cinna Mata hauka ko bacci ranar da wuri tayi bayan Tasha maganin hawan jininta Dan idan ta biyewa Inayah da wuri Zata aikata lahira Mata shiryaba. Sbd tsananin kewar Abbinta a dakinsa ta kwana da safe ta gyara koina da kanta ta tsaftacesa ta fito. Bedroom dinta Takoma tayi wanka tayi shirin tafiya asibiti sbd kadaicin yayi Mata yawa gashi taji sauki. Ko data Isa asibiti aiki sosai tayi sbd hanawa kanta tunaninsa sbd koina jikinta tafara tunaninsa karbawa yakeyi. Sai yamma sosai tadawo sbd ta dade bataje asibitinba yasata tsayawa tayi aiki sosai. Wanka tayi ta fito taci abinci ta nufi gurin Haj umma, Kwance ta taddata batajin Dadi kaman BP dinta ya Dan hau. Da kanta ta dubata taga tabbas bp din ya hau Dan hakan takira asibiti aka aiko Mata da wani maganin da allura tayiwa Haj umman take bacci ya dauketa sbd hadda baccin da Bata samu tayiba yasa jinin nata hawa. A dakin Haj umman ta kwana sbd jikin nata, Kwana tayi tana duba BP din nata akai akai ko baccin arziki Bata samuba itama karshe da ciwon Kai ta tashi me tsanani Amma ganin jikin Haj umman itama ba wani sauki sai ta daure ta Kira Dr Abdul yazo gidan shi Daya fita qwarewa ya tayata duba hajiyar Dole suka dauketa suka tafi asibiti da ita. Kasa fadawa Abbi tayi sbd kada ya Shiga damuwa Dan hakan ta dage sosai tana kulawa Haj umman har sukai kwana biyunsu suka Gama a asibitin Babu Wanda yasani Saida suka dawo gida tukuna su Anty safiyyah suka sani hankalinsu yayi mummunan tashi suka fara Shirin tahowa Lagos din. Dawainiyar da Inayah tayita Yi kwana biyun da Bata saba ba yasata itama zazzabi kamata Haj umma data warke sumul tadawo jinyarta ga Inayah ta iya narkewa a ciwo kaman jinjira. Da fada da komai suke jinyar sbd basa fasa Dena halinsu na rigima tsakaninsu. Kwana biyu tafara warwarewa su Anty safiyyah suka iso tayi farin ciki sosai da ganinsu Dan haka gidan ya Dan Yi musu Dadi daga ita har Haj umman, Kuma duk wannan ciwon dasukai saga ita har Haj umma Basu Bari abbin yasaniba kullum sukai waya Bata Bari yagane ta ringa narkemasa a wayar tana Masa shgawaba kala kala shiyasa duk yabi yakoma wani iri agurin aikin kamewarsa ta qaru yakoma AA MAJEED dinsa sbd yasake tabbatarda Inayah itace abinda kawai ke haskaka rayuwarsa da zuciyarsa tareda faranta rayuwar. Zuwansu anty safiyyah gidan da rumanah yasa tasake warwarewa sbd da gaske suka ringa kulawa da ita sunata lallabata sbd zuwansu suka sake tabbatarda matsayin Inayah a gidan da rayuwar MAJEED sbd duk abinda yake gidan na Inayah ya banbanta da kowa.. Komai nata special ne a gidan ko masu aikin zubbi zaman Inayah takeyi a gidan Salimat ce ta kowa da kowa. Taji sauki sosai Amma Bata sake fita aikiba sbd kasalar da Bata saketaba ta Dan zazzabin datai. Ranar da Abbin yakirata vidcall ta manta ta dauka da magani agabanta data Gama Sha, Kallon maganin yayi batareda yace komaiba ya zubawa fuskarta Ido Yana Mata kallon tsaf yasan ba haka yabar kayarsaba Dan hakan Bai wani ja zancenba sukai sallama. Washe gari Dr iklimat da umma Hadiza sukazo gidan dubiyarta data Haj umma duk da duk sun warke. Daki suka shige da 'yarsu sukasha maganganunsu sai yamma suka fito zasu tafi su Haj umma duka suna zaune Palo suka tsaya suna bankwana bayan tun shigarsu Haj ke complain suna can suna koyawa 'yarsu shegantaka da rashin kunya. Fuska asake suke bankwanan kafin Haj umman ta amsa aka bude kofar palon suka waiwaya duka Banda Inayah data bawa kofar baya. Dr iklimat ce tasake fadada murmushinta da farin ciki da ido ta nunawa Inayah kofa. Tun kafin momynta ta nuna Mata kofar taji qamshinsa yashiga hancinta dan haka da sauri ta juyo aikuwa sukai Ido biyu dashi shima idonsa akanta suke gabaki daya yakasa hana kansa kallonta......ba zato batareda ta damu da kowaba taje da gudu ta maqalesa tana Kiran sunansa cikin farin cikin ganinsa. Su umma Hadiza murmushi sukeyi hankali kwance batareda damuwar komaiba ita kuma Haj umma su take bi da kallo ganin ko ajikinsu suna saima murmushi sukeyi aranta tace" Danginsu kaf marasa kunya ne da alama tunda gashi 'yarsu na rungumar Miji agabansu Amma murmushi sukeyi shiyasa take tsoron zuwansu gidan duk sun qarasa fitsarar da 'yar Dama gata ga yanda take. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_69_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* Da hannu daya ya riqe Dan qaramin qugunta zuwa bayanta Yana Dan sauke ajiyar zuciya a boye yasamu nutsuwa ko ahakan Dan hakan ya janyeta daga jikinsa Yana Dan wadata fuskarsa da kamilallan murmushi Yana kallon Dr iklimat da umma Hadiza dasuka gaidasa tareda Masa barka da dawowa. Fuska asake cikin mutuntawa ya amsa Yana tambayar Ashe Bata koma Abuja ba tana Lagos har lokacin. Suna Gama gaisawa dashi suka fito Inayah tabiyo bayansu tabarsa yasamu Daman Gaisawa dasu Haj umma a natse Dan idan tana gurin tana maqalqalesa ba tsayawa zaiyi sosai su Gama gaisawa zai sulale yabar gurin tun kafin mutuncinsa yagama watsewa agurin. Har jikin motar umma Hadiza ta rakasu suka sake tsayawa magana Dr iklimat tasake nanata Mata zancen girkin datai Mata dazu sbd haryanzu su basuga ta Kama gidanta da kyau ta qarasa Zama cikakkiyar matar gidan koyaushe kaman 'yar lelen gidan takeyi gwara dai tazama cikakkiyar matar gidan me iko da megidan da duk Wanda ke karshin gidan. Suna wucewa tadawo ciki sai ta tadda har abbin ya shige baya palon. Rasa abinyi tayi sbd taso binsa dakinsa Amma Kuma sai ta tuna da zancensu ummanta dasuka Bata tabbacin idan Bata karba har ragamar abincinsaba zaa iya samun damuwa Dan hakan saita wuce Kai tsaye duk da batasan me zatayi ba. Zubbi tasa ta wanke Mata fresh veggies ta yanka Mata ita Kuma ta Dora spaghetti sbd ita tafi iyawa Kuma tafi sauki a lokacin tunda dare ne. Brown vegetable spaghetti ta dafa Masa wadda kusan Naman kazar data zazzarewa qashi tafi veggies din yawa aciki. Sosai abincin yayi Dadi sai qamshi kitchen din keyi Yana samma Palo Dan dama umma yaganah tayita koyar da ita girke girke itace kawai Bata maida hankali sakalcinta kawai tasaka agaba shiyasa girkin Bai wani kamata ba Amma idan ta dage taso tsaf zatayi abinci Mai Dadi da tsari. Saida zubbi ta jera komai a dining kafin ta fito kitchen din ta wuce dakinta ta kwabe kayanta ta fada toilet. Ta jima tana wanka sbd duk gajiyar aikin datayi takeji qafafunsa har ciwo taji sun Mata sbd tsayuwa a aikin. Wankan tayi tana fitowa sai datayi sallar ishai tagama kafin ta shafa Mai kadan ta saka doguwar free wide neck English gown. Qaramar hula kawai ta sako akanta ta fito ta nufi hanyar palonsa kenan sai gashi ya fito sanye cikin milk jallabiya me maiqo datai Masa kyau sosai yafito kaman balaraben uztaz. Kallonta yayi a natse kafin ya miqa mata hannun damarsa yana cewa" Zo Nan.. Tahowa tayi fuskarta na bayyanarda tsananin son datakewa halittar Dake gabanta ta Kama hannunsa tareda rungume hannun tana cewa" Abbina harka Gama hutawan? Muje yau nice nayiwa mijina girki me Dadi. Dakin Haj umma suka nufa sbd ganin Salimat ta fito daukeda manyan kulas ta nufi dakinta. Suna zuwa yaga alaman a daki zasuci abincin yace Salimat ta maida dining su fito duka suci acan tare kaman yanda aka Saba. Inayah dake gefensa ta qaraso tana cewa" Haj umma yau fa nice nayiwa Abbina girkin Amarya Gwara kifito kici kiji dadinsa gskia sbd kada gaba nayi lefi kice ban iya abinciba Ina barin Abbina da yunwa adawo da maganar Dr farhat.. Wani mugun kallon takaicin rashin tsarkin bakin Inayah Haj umman tayi Mata tana cewa" Ko yanzu ce miki akayi anfasa maganar Dr farhat dinne? Zaro ido waje tayi a Rikice ta kalli Abbinta cikin mamaki da rikici..kafin tayi magana ya kamo hannunta ahankali yane cewa" Muje naci abincin naji. Dawowa tayi gefen Haj umma tana cewa" Yanzu Haj umma duk wannan biyayar danake Miki da girki gashinan nayima Harma da 'yayan Abbi da kikace nace duk zanyi Haifa shine Baki yafe maganar Dr farhat ba. Hawaye ne ke Neman cikowa idonta abbin ya kalli Haj umman da alaman roko kafin yayi magana tace" Naji to muje naci abincin naje idan yayi Dadi sai abar maganar Dr farhat din yanzu Amma dai bakinki idan Bai fara koyan maganaba akwai maganar a gaba Dan bazaa ringa Shiga mutane dakeba kina wannan sakarcin. Wucewarta tayi gaba tanajinma ta Dena Jin yunwa da dokin cin abincin. Tana ficewa Abbinta yabi bayanta sbd yasan rigima Zata fara Zata iya hautsinewa ta rikitasa. Riqota yayi tareda dawowa da ita ta baya bayanta ya hadu da kirjinsa ya rungumeta Yana goga Mata fuskarsa ahankali Yana cewa" Keda Haj Kun Zama kaman jika da Kaka ko? Menene na tado maganan wata agaban mijin da kikasan Babu gurin kowa a zuciyarsa... Uhumm????? Shiru tayi tana danne abinda takeji din harya fada Mata ta sauke ajiyar zuciya ahankali itama kafin ta zame kadan ta juyo ta kallesa taga yanda shima yake kallonta tace" Shikenan muje kaci abincin Amaryarka kaji. Jan hannunsa tayi zuwa dining din da harsu Haj umma sun fito Ashe sun wucesu sun Isa dining din Basu luraba. Zaunawa yayi ta janyo abincin tayi serving dinsa tana kallon yanda shima yake kallon abincin cikin bayyanarda Jin dadinsa na cin girkin Amaryarsa kaman yanda tafada. Haj umma ta zubawa bayan tagama zuba Masa kafin ta zauna tana kallon fuskarsa data Haj umma tana cewa" Kome kukaji ku fadamun Dan Allah kaji Abbi? Murmushi kawai yayi tareda daukan fork ya fara cin abincin cikin nutsuwa hankali kwance da alaman abincin yayi Masa komai da komai. Haj umma ce dai takasa shiru tace" To ba laifi da Dan sauki tunda kin iya girkin...sauran iya Kama bakinki. Dariya Inayah tayi tana Jin dadin Yana abincin da Haj umman tayi ta maida kallonta kan Anty safiyyah tace" Anty safiyyah kefa? Yayi Miki Dadi? Sosaima Inayah"" tace sbd itakam babu abinda Inayah zatai yayi Mata ba daidaiba sbd son samun Shiga sosai agurin 'dan uwanta Dan itakam bakin fama so take su daidaita fiyeda dah to kuma ta lura ka so Inayah na kaunaceta shine abinda zai baka samun shiga agun MAJEED. Sosai yaci abincin daidai cikinsa yasha ruwa ya zari tissue ya goge bakinsa ya miqe yabar gurin. Saida kowa ya kammala ta taya zubbi tattare gurin suka kai kitchen. Tana baro kitchen a Palo ta taddasa zaune tareda anty safiyyah da Haj umma suna magana ko rumanah data girmeta Bata gurin Dan haka itama Bata zaunaba ta nufi hanyar bedroom dinta ta wuce tanajin idonsa akanta Yana binta da kallo harta bace daga palon. Zaunawa tayi ta dauki wayarta taga misscalls din Umma yaganah tasaki murmushi tana bin bayan Kiran da nata Kiran.. Basu jimaba suna wayar suka Gama ta ajiye wayar ta miqe ta nufi toilet ta tayo brush da alwalar bacci data Saba ta saka kayan bacci masu santsi Riga da wando farare tas ta shafa turare ta haye gadonta tashige bargo ta lafe sbd Abbinta har lokacin magana sukeyi dasu Haj umma a Palo basuda lokacin gamawa.. Baccintane ya dauketa me Dadi bayan ta kashe wutar dakin.... cikin baccin taji mutum na kwanciya a bayanta tareda rungumeta sosai jikinsa Bata wani motsaba sbd baccin dayayi Mata qarfi shikuma sbd kada ya takura Mata tana baccin yasa Bai tashetaba kokuma yimata abinda Zata tashin ya rungumeta kawai sukai baccinsu cikin nutsuwa da kewan dumin juna. Washe gari 10 tafito daga dakinta sanyeda kayan baccinta ta nufi kitchen tasaka hannu a aikin breakfast dinsa Dan kusan angama komai Amma Saida tayi Masa Honey pancakes da kanta ta dafa Masa tea dinsa suka jere a dining Amma nasa pancakes din bayan ta zuba Masa zuma a wani farin kyakkyawan tray ta jera tareda qaramin cup din tea dinsa ta nufi bedroom dinta da tray din. Tana shiga taga har lokacin bacci yakeyi cikin tattausan duvet din gadon hankalinsa kwance. Ajiye tray din tayi gefen gado kan bedside tana murmushi tana kallon kyakkyawar fuskarsa ta Kai hannu ta shafa fuskar ahankali kafin takai bakinta kan kunnansa ahankali cikin qaramin sauti ta furta" I love you my Abbi. Cikin bacci yaji saukar kalmar cikin kunnuwansa Dan haka ya Dan motsa kadan Yana Jin wani sanyi na ratsa gangar jikinsa. Zuman pancakes din ta lakato da tsaftatacciyar yatsarta ta nufa bakinsa sai data fara kissing dinsa ahankali shima cikin baccin ya bude Baki zai kama bakin nata ta janye tana dariya tareda saka Masa yatsarta cikin bakin nasa zaqin zumar yasasa bude idanuwansa dake wani irin lumshewan bacci sai hakan yayi Mata kyau sosai itama tana rage dariyarta ta matso tayi kissing idonsa tana cewa" Good morning Babyn baby Inayah. Wani kasalalliyar dariya yasake mara sauti Yana motsawa tareda tashi  zaune Yana jingina da gadon ya zura hannu Daya ya hawo da ita kan gadon tareda janyota jikinsa yana tsotsan yatsarta cikin bakinsa ahankali kaman sweet da ido ta nuna Masa abinda takawo Masa tana murmushi. Shima da Ido ya nuna Mata ta basa a bakinsa. Zanje hannunta dake bakinsa tayi tana dariya tace" Abbin ka yarda kenan Kaine babyn baby Inayah ko??¿ Gyada Mata Kai yayi Yana karban pancakes din cikin bakinsa datake sakawa ahankali. Taunawa yafara Yana kallonta da mayun idanuwansa da Basu Gama wartsakewaba da baccin. Cikin taushin murya yace" Baby Inayah yanzu ai ta girma tazama Amarya tunda gashi tana kulawa da miji. Hannunta dakeda zuman pancakes din ya riqe Yana kallonta yakai hannun bakinsa ya ringa tsotse zuman cikin nutsuwa. Mutuwa jikin yafara Yi sbd yanda yake tsotsar yatsun nata cikin sanyi da wani yanayi ga dumin cikin bakinsa take tafara Jin kaman sanyi na kamata tana. Dayan hannunta takai ta sosa saman kunnenta dataji kaman ana mata tafiyan tsutsa take zumar Dake dayan hannun data sosai ta shafu a kunnen... Murmushi yasake Yana kallon kunnen yasaki yatsarta tareda janyota suka matse sosai yakai harshensa ya laso kunnenta Yana kashe zuman batasan lokacinda taja wani wahalalliyar numfashiba tana qanqamesa da qarfi sbd kusan Suma tayi da yanayin. Yana yake lashe kunnenta yasata binsa tana qanqamewa da qyar ta iya hada kalmar sunansa takira a rarrabe tana sakin numfashi. Sakinta yayi ahankali Yana kallon yanayinta Daya Gama bayyanarda mutuwar da jikinta yayi... Kasalallen murmushi yasake Yana juyawa gefensu ya sake debo zuman ya saka cikin bakinta ya Dora bakinsa akai ya rufe suka tsotse zuman tare cikin harshen junansu suka shanyeta tas. Basu Gama barnatar da zumanba da pancakes din sai kusan bayan awa Daya suka Gama tsotse tsotsensu saida sukai wanka suka fito Dole shima a dakin nata yayi wanka sbd gabaki daya bakinsa da fuskarsa har wuyansa dankon zumane dasuka Gama lashewa ajikinsu. Itace taje dakinsa ta dauko Masa kayanda yasakata suka fito lokacin tuni kowa yaci abinsa Basu tsaya jiransuba tunda basusan yaushe zasu fitoba. Su kadai sukaci abincinsu a dining tana kan cinyarsa sukai breakfast din Suna gamawa ya fita sbd akwai Inda zashi kafin yakoma Dan tafiyar tasa bawai ya gamo abinda yaje Yi bane ita yadawo dubawa. Bayan fitarsu itama shiryawa tayi ta nufi asibiti Amma Bata dadebe tadawo sbd ranar su Anty safiyyah zasu wuce Amma Abbi yace Subari se gobe. Ko yau da ita dasu zubbi sukai aikin abincin dare suna gamawa ta wuce dakinta tayi wanka tayi zamanta daki tana wani aikin karanta wasu abubuwan dasuka shafa aikinta qarshe see data hada da Kiran Neesah suka tattauna akan matsalar. Bata fita Cin abincin darenba a daki Tasha tea da cake kawai taci gaba da abinda takeyi shima abbin Bai dawo gidan da wuriba. Tana gamawa a gajiye ta miqe tayo wanka tazo ta shirya ta nufi dakin Abbinta ta haye gadonsa tayi kwanciyarta. Koda yadawo yasan ta Isa yin bacci Dan haka Saida yaci abinci kadan kafin yashigo da niyar yin wanka ya sameta dakinta tunda shine me zuwan sai gashi yayi mamakin ganinta dakinsa tana bacci a takure kaman baby. Kissing din kanta yayi tareda gyara Mata rufarta ya ajiye wayarsa da key din motar Daya dawo da ita ya nufi toilet bathroom Yana tubewa. Wanka yayo sbd shima ya Dan gaji sosai sbd komawan dazaiyi gobe daqyar ya Gama Samar da komai na tafiyarsa da ita tun yanacan dama ya fara Mata Shirin tafiyar dayazo zasu Koma tare. Kayan bacci yasaka masu budadden gaban Riga ya hau gadon tareda janta jikinsa ahankali ya shigar suka sauke ajiyar zuciya atare shima take bacci Mai Dadi da nauyi ya daukesa. Washe gari suna tashi bayan sunyi sallah da adhkar har gari yayi haske sosai ta matso daga Inda take zaune tadawo gabansa tareda hawa kan qafafunsa Dake lanqwashe ta zauna tana Masa wani kallon love tace" Abbi, good morning. Gyara Mata Zama yayi a qafafun nasa Yana amsawa ya zare Mata hijab yace" Yau zankoma..... Bata Bari ya qarasaba ta Dan zaro Ido da mamaki tana cewa" Wat? No Gaskia Abbi nidai karka sake komawa yau, Baka gamaba dama kadawo?nidai to karka koma yanzu,. Murmushi yayi Mata Yana shafa gefen fuskarta yace" To Yaya kenan??? A marairaice tace" Yaushe zaka dawo idan katafi??? Jin Bata furta cewa Zata bisaba kaman yanda takeyi yasashi cewa" Watanni zanyi.... Mene???? Tafada cikin fito da idanuwa tana narkewa jikinsa tace" To nidai zanbika Abbi Gaskia. Wani qayataccen murmushin dadin abinda ya furta Dan kanta yace" Shikenan Banda damuwa ki shirya muwuce yau da yamma ne tashin jirgin. Yanda yayi maganar Yana Wasa da siririn hannun rigarta ta bacci yasata kallonsa da alamar tambaya tace" To Ina zamu?? Australia, Amma idan nagama Maldives zamu canma wani abin zanyi..... Kamo fuskarsa tayi da tafin hannuwanta biyu tana murmushi tace" Maldives? Abbi Honeymoon zaka daukeni muje???? Fadamun.. Dariya zancenta yabasa dakuma yanda take yiwa fuskarsa kaman wani cartoon.. Wata shafa yayi Mata a wuyanta data sanyata saurin sakinsa tana dariya tace" Abbi Dan Allah ka dena.... Qarasa saka hannunsa yayi cikin rigarta tanajin haka ta miqe da gudu tana dariya. Fitowa tayi ta nufi dakinta Dan hada kayan dazata dasu sbd Abuja zasu wuce dagacan zasu tashi da yamma. Shima Saida yayi wanka yafito ya nufi dakin Haj umma acan ya tadda su Anty safiyyah nasake shiryawa. Cikin nutsuwa Kai tsaye ya sanarwa Haj umma tafiyarsa da Inayah din akan wani karatu zatai da abokan karatunta a wani asibiti Dake can. Jinsa kawai Haj umma tayi Yana gamawa tace" Siyamun tickets din mu wuce abujan tare Dan bansan zamanda zanyi anan dinba ba kowa. ##MAMUH## _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107*_70_* *_Arewabooks@Mamuhgee_* cikin kulawa ya kalli Haj umman yace" Umma kiyi zamanki umma yaganah Zata dawo jibi Inshallah sbd kada abar masu aikin Babu kowa. Numfashi ta sauke tana cewa" Bari naje dasu zubbi din sbd Dama can duka masu aikin an sallamesu bakowa sbd bana Nan so Bari naje dasu can idan yaso yaganah na samemu a abujan tunda itama ba dadin zaman zatajiba bakowa idan Kun dawo da dawo kawai. Batareda Jan zancenba yace shikenan atafi dasu zubbin Abuja. Wannan tsayayyar shawaran yasa Dole aka daga tafiyarsu anty safiyyah dasu Haj umman a ranar sbd asamu damar gyara komai a natse a San yanda zaayi da abubuwan cikin fridge da sauransu. Inayah ce ta sanar musu da maganar tafiyar dan haka suka fara ayyukan dasukasan zaayi kafin barin gidan bakowa. Dakinta ta wuce Dan hada kayanta Dan sukam aranar zasu wuce, tana Shiga wayarta tafara dauka tasaka Kiran umma yaganah sukai magana kafin takirasu ummanta. Maganar dasukai yasata Dole shiryawa sharp sharp taje gidan da mota ta karbo turaruka masu shegen qamshi da wasu abuwan kafin ta fito.. Ganin yanda take sauri yasa Dole Dr Abdulsamad yace tabari yajata ya maidata gida sbd kada garin sauri matsala ta biyo baya. Sama sama suke fira dashi sbd yadan fara sakewa da ita sbd yanzu Yana iya danne komai dayake ji aransa gameda ita sabanin farko farko dayake nesanta kansa da ita sbd shedan baya Bari Yana iya danne zuciyarsa akanta. Har gidan anty Hafsat Saida suka biya kafin suka dawo gida. Yanayin parking ta suka fito ya miqa Mata key suna sake tattaunawa akan mahaifiyarsu kafin tayi Masa godia sukai bankwana ya wuce. Tana shigowa har Saida tayi wanka taci abinci kafin Abbi yadawo suka fito suka nufi airport jirginsu ya daga zuwa Abuja. Suna sauka Abuja ko airport Basu Bari ba Sako kawai aka kawo Masa daga gidan kamfanin dasuke aiki tare sbd sun iso latti Dan haka time dinda zaije yadawo jirginsu be tashiba shiyasa sukai zamansu a airport din aka kawo musu sakon ko mintuna arbain da karban sakon basiyiba aka Kira jirginsu suka wuce. Sai asuba suka Isa Dan haka Kai tsaye mota suka dauka daga airport din zuwa gidansu Komai na Nan fes sai qamshi da sanyin AC daya cike koina sbd tun suna Lagos yakira kamfanin cleansing aka aiko masu aiki suka tsaftace gidan tareda gyarasa tsaf. Amatuqar gajiye Inayah take Dan haka ko doguwar magana Batayi bedroom dinta ta nufa komai fes harsu bedsheets da curtains ana sauya kusanma an sauya abubuwa da dama a gidan. A kasalance ta tube kayanta ta nufi bathroom ta shige shima duka kayan wankanta dasu toothpaste din datake amfani dasu komai ansake zuba sabbi. Sabon brush ta fasa tayi brush tareda Shiga ruwan zafi ta kwanta acikin tsawon mintuna gajiyarta ta Dan sake tukuna tayi wanka ta dauro alwala ta fito. Sallah tayi ta lallaba tana kokarin miqewa Abbinta yashigo dakin sanyeda Riga da wando marasa nauyi da alama shima yayi wankan yayi sallar gajiyace take cinsa da bacci Amma yafison yayisu a jikinta Dan haka da kansa ya cire Mata jallabaiyar datayi sallah ya dauketa suka nufi bedroom dinsa dayafi nata Fadi da girma. Akan Lafiyayyan gadonsa suka kwanta tareda shige quilt Mai tsananin laushi tasake gyara kwanciyarta cikin jikinsa take bacci yayi gaba dasu. Bacci sukayi sosai Basu farkaba sai guraren 1 na Rana.. Itace tafara tashi tashiga bathroom dinsa tasake fasa sabon brush tana cikin Yi sai gashi yashigo dagashi sai dogon wandon kayan baccinsa dama Bai kwanta da rigarba. Ta cikin madubi take kallon kyakkyawar siffarsa ta masu qarfi da lafiyar fata sbd sheqin hutu da lafiya da fatarsa keyi. Rungumota yayi ta bayanta Yana kallonta ta cikin madubin itama ya shaqi Qamshin wuyanta Yana sake rungumeta dakyau yace" Good morning Babyb Abbi. Da brush a bakinta tace" Morning babyn baby. Murmushi yayi Yana sake rungumeta yace" Yaya dai? Wanke bakinta tayi tareda ajiye brush din ta dauko wani sabo ta fasa Masa tareda saka Masa toothpaste akai ta juyo suna fuskantar juna a matse Ta Kai brush din bakinsa ya bude ya karba Yana sake matseta Jikin mirror din. Murmushi tayi tareda zamewa ta qasa ta fice toilet din tana cewa" Yunwa nakeji sosai Abbi. Palo ta nufa ta Isa kitchen taga har siyayyar abinci da komai anyi an saka duk abinda zasu buqata a fridge. Toasted bread da kwai ta soya musu sai tea. Shi sukai breakfast dashi tana kan cinyarsa Suna gamawa yaje yayi wanka ya shirya ya fita zuwa aikin dasukeyi. Itama wankan tafara Yi tasaka mini skirt da vest qarama data lafe skin dinta Ba masu aiki daga ita sai Abbi Dan haka dole tashiga kitchen tai musu brown rice da salad sai soup din fresh vegetables Mai Dadi. Tana gamawa takoma ta gyara bedroom dinsa da baiyi komaibama tadawo tsaftace nata da kitchen da Palo ta kunna humidifier tareda qara turaruka masu shegen qamshi aciki Takoma dakinta tasake wanka tayi sallar la'asar tana idarwa Neesah na isowa gidan daga gurin aiki Cikin ihu da farin cikin ganin juna suka rungume juna kowacce na kallon Yar uwarta Neesah ta ajiye handbag dinta kan kujera tana cewa" Babes??¿¿ Oh my God banmasan yazance kin sauyamin ba, Kai I miss you babes. Bedroom dinta suka nufa suna sake baje shafin fira kaman basa waya kullum da juna. Abinci sukaci a dakin suna sake nisa a firarrakinsu har lokaci yaja sosai kafin Neesah din ta fito ta tafi gida lokacin har 6 ta wuce. Bayan tafiyar Neesah ko cikin gida Bata komaba saiga shigowar motarsa Dan haka ta dakata tareda folding hannuwanta tana kallonsa cikin yanayi na daukan hankali harya fito motar ya nufota Yana isowa ya miqa Mata hannunsa daya Yana cewa" Baby Inayah me takeyi waje cikin sanyi? Shigewa jikinsa tayi suka nufi ciki tare tana cewa" Neesah ce ta tafi yanzu Nan Nayi kewanta munyi fira sosai shine na rakota motarta ta tafi. Suna shigowa Palo ta zame daga jikinsa ta nufi kitchen din warming abincin dazaici shikuma ya wuce dakinsa Dan yin wanka da sallar magriba. Sanin bayason abinci me zafi sosai yasata warming abincin sama sama saita dafa Masa tea dashima tasan yanasha da dare. A dining tasake jerasu kafin Takoma kitchen tasake tsaftace komai tafito ta nufi dakinta Tai alwala tayi sallar magriba tana idarwa Yana shigowa dakin sanyeda Fendi wears masu Dan kauri dasuka maidasa kaman sabon matashin saurayi fuskarsa sai kwarjini take tana cika Ido. Abayar sallarta ta zare ta ajiye Yana qarasowa gurinta ya Kama hannunta ahankali Yana cewa" Yauma abincin Amaryarta zanci kokuwa order zamuyi??? Murmushi tasaki tana kama dayan hannunsa ta jasa suka nufi kofa tana cewa" Nifa Abbi a gabansu Haj umma ne kawai nake Amarya Amma gurinka ai Ni baby Inayah dinka ce, Muje kaci abincin babynka na yau ma kaji yanda yayi. Murmushi kawai yayi suka Isa dining din Yana kallon abincin dasuke jere da mamaki kan fuskarsa yace" Duk babyn Abbi ne tayi wannan aikin? Hannunsa yakai ya janyota jikinsa yana sake cewa" Oh oh,yau baby Inayah tayi aiki sosai Dole kin gaji ko? Zaunawa yayi kan Daya daga kujerun dining din tareda zaunar da ita kan qafarsa Yana cigaba da cewa" Sannu, Gobe zansa a kawo cook dame tsaftace gidan Karki sake aiki irin haka ba Zaki iyaba,girkinma na yafe Zan ringa cin na cook. Dan bata fuska tayi tana Dan shagwaba fuska tace" Abbi nidai zanyi inson na iya sosai ne idan na Gama qwarew sai akawo masu aikin. Shaf dogon hancinta yayi da yatsarsa kafin yace" Ok, Amma dai anan bazakiyiba kibari saimun koma gida tukuna... Saimun koma gida Kuma? Meyasa bazanyi ananba? Hutawa nakeso kiyi anan. Kumatunsa ta Kama da tafukan hannunta tabawa tana murmushi tace" Dagaske kenan honeymoon kazo muyi anan ko Abbi? Cikin idonta ya kalla yace" Honeymoon yashiga bakinki meyasa? Eh nidai Abbi kace Honeymoon mukazo... Zaunar da ita yayi gefe Yana daukan spoon zaifara cin abincin yace" Me kika Dani gameda honeymoon dinne? Dariya Mai kyau tayi tana cewa" Inason kaman kowa Nima mijina yaje honeymoon Dani muje gurare... Abincin bakinsa ya hadiye ahankali yace" Shine Honeymoon kenen? Eh Abbi nidai kace eh kawai. Abincinsa yakeci Yana sauraron bayananta akan honeymoon Wanda duk bayanin ya qare akan yawon guraren shaqatawa shine Honeymoon batareda ta ambaci yafi komai mahimmanci a honeymoon dinba. Bataci abincin ba sbd batajin yunwa Tea dinsa kadai kadai sukasha atare shima Saida ya ringa Bata abaki da kansa. Suna gamawa dakinta suka nufa acan sukai sallar ishai yafito Palo ya zauna Yana amsa wayar gurin aikinsa. Wanka tayi ta saka Riga da wando na bacci gajeru dasuka lafe jikinta sbd yanayin Dan sanyi da akeyi. Kanta ko hula Babu ta fito dashi daure agefen kanta da black hairband sai slippers dinsa dasukaiwa qafafunta girma. Tunda tafito ta dosa Inda yake ya Dena gane me ake fada Masa a wayar shi kansa rasa Gane meyake fada yayi ya dauke kai daga kallon Inda take Amma qamshintama yafi rudar dashi.. Tana zuwa ta zauna kan cinyarsa sbd yafara sabar Mata da hakan. Dan gyara murya yayi Yana riqe kansa cikin kamewa yayi sallama da Wanda yake wayar yace zai Kira daga baya. Yana kashewa jefar da wayar yayi gefensa Yana juyowa ya kalleta da idanuwansa dasukai dan ciki ciki. Murmushi ta sakar Masa tana gyara zamanta kan qafafun nasa ta Dora hannuwanta kan kafadunsa tana cewa" Bacci kakeji ne Abbi?? Girgiza Mata Kai yayi Yana saka hancinsa kan wuyanta Yana shaqar qamshinta tareda zagayeta da hannuwansa biyu Yana sake shigar da ita tsakiyarsa. Shiru tayi tana basa Daman shaqarta dakyau iya yanda yakeso idanuwanta a lumshe sbd duk lokacinda take shaqan Qamshinta dumin numfashinsa kashe Mata jiki yakeyi. Hannuwansa taji sun gangara zuwa cikin rigarta ya tsafa cikinta zuwa cibiyarta... Daurewa tayi tana Hana kanta shiga fargaba ta sauke numfashi Mai sanyi ahankali cikin kunnensa tana sake rungumesa. Idanuwansa dasuka Dan shige ciki ya bude ya kalleta cikin qanqantacciyar murya yace" Kin shirya fara honeymoon din da kiketa fadan nace wani Abu akai??? Batareda tasan me yake nufiba ta gyada Kai tana Dan kallonsa a kasalance sbd har lokacin hannunsa na yawo cikin rigarta. Lumshe fararen idanuwansa yayi tareda sakin wani malalacin murmushi yakai bakinsa kan botiran rigarta Yana fizgewa da hakorinsa sbd har lokacin hannunsa na cikin rigarta Yana wata shafar dake yanke numfashinta Yana daukewa Yana dawowa daidai.... Botiran farko daya Ciro da bakinsa itace tasaka hannu suna kallon juna cikin wani irin yanayi na kauna Mai zafi tacire daga bakinsa ta jefar , Na biyu ma yana Cirowa ta karba ta Yar ahaka yagama fizge botiran rigar duka suka watsar ya qurawa asalin lafiyayyar fatar kirjinta Ido yana hadiye wani busashen yawu. Aikin Daya faro da bakinsa shi ya Dora daganan Yana sake manneta da jikinsa sbd bayan datakeyi cikin wani shagaltaccen yanayi. Daqyar ta iya bude Baki ta Kira sunansa batareda tasan tayi hakanba sbd wasan yafara qarfinta. A Rikice ta bude Baki Zata Kuma Kiran sunansa ya miqa Mata bakinsa kan nata take ta karba da kanta tafara missing din bakinsa tana qanqamesa. Yanda take kissing dinsa yasashi qarasa daukan dumi ya qarasa zare rigarta ya jefar Yana Kama wuyanta cikin sanyi ya karbi ragamar kissing din yafara Mata wani qazamin kiss Wanda yawun juna ne kawai suke zuqowa suna shanyewa cikin tsananin so da kaunar junansu. Duk abinda yake jikinta Saida suka fincikesa a palon kafin ya tashi da ita a jikinsa suka nufi bedroom dinsa suna Shiga kan Lafiyayyan gadonsa Daya Gama Kama qamshinsa suka zube Yana cigaba da lasarta koina kafin yayi hanyar sakata Shiga tsoro da firgici saidai batada wani kuzarin janyewa. Bathroom ya kawota kansa ya fice yabarta cikin ruwan dumi Wanda suka sanyata lumshe ido sbd taji dadin shigarsu jikinta. Wannan karon zafin kadan ne Babu raunin komai bare azaba duk da tayi mugun Jin jiki a hannunsa, Koina jikinta tsamin gajiya yakeyi. Ta Dan jima cikin ruwan kafin tayi wanka ta fito daureda towel dinsa kanta na tsiyayar ruwa., Sallar asuba ya idar Yana adhkar ta fito ya waiwayo Yana kallonta Ya tsayar da idanuwansa kan gashinta dayake digar da ruwa ya kwanta luf har gaban kanta Daman ita Sam na ma'abociya yin kitso bace tayi sabo da zaman Turan shiyasa Bata samun yin kitso. ##MAMUH# _ZAFAFA BIYAR_ *_INAYAH_* _MamuhGee_ *_GURBIN IDO_* _Safiya Huguma_ *_SANADIN LABARINA_* _Hafsat Rano_ *_FARHATAL QALB_* _(Miss Xoxo)_ *_BABU SO_* _Billyn Abdul_ _*Littafi daya 300*_ *_Littafi biyu 400_* *_Littafi uku 500_* *_Littafi hudu 700_* *_Littafi biyar 1k_* ZENITH BANK HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Shedar biya👇 07040727902 MTN card👇 09134848107[11/21, 5:33 PM] Hajiya Qarama: *_72_* _LAST CHAPTER_ Isarsu gida wata fitinanniyar soyaya suka watsar a Palo Saida kowannensu ya sake tabbatarda bazai iya rayuwa Babu dayansa ba. Sai washe gari familynsu suka San da maganar cikin shima sbd Neesah ce data Kira umma yaganah ta fada Mata Daman Kuma umman na Abuja gurin Haj umma, Su Anty Hafsat ma Neesah ce ta sanar mata itakuma ta sanarwa su umma Hadiza... Haj umma Bayan kwana biyu angama Murna da farin ciki tafara zuga umma yaganah akan tayiwa MAJEED magana tace yadawo da Inayah din kada suje suyita shirme su barar da cikin tunda Inayah din ba Zama kurum takeyiba da sauran kuruciya atareda ita. Murmushi kawai umma yaganah tayi sbd ta fahimci abinda Haj umman ke nufi to Kuma itama nauyin fadawa MAJEED hakan takeyi. *****Bayan sanin cikin ko sati biyu Basu rufaba a Australia suka wuce Maldives Acan suka bude sabuwar rayuwar shaqatawa da Jin Dadi Dan kuwa kuwa duk sauran wani abin da Basu Gama qwarewaba akai sun qware a Maldives, Gashi gabaki daya cikinta baizo Mata da kowane irin ciwoba ko laulayiba Dan haka ta sake Masa jiki suka Gama lalacewa da soyayya Mai Dadi da kwanciyar hankali. Saida suka share kusan wata biyu acan kafin suka dawo Australia. Dawowarsu da wata uku lokacin cikinta yakai wata shida Haj umma ta rufe Ido tace yadawo da Inayah gida. Kai tsaye ya sanar Mata acan yakeson Inayah din ta haihu saita Haihu su dawo gida.. Itama rufe Ido tayi Kai tsaye tace Bai isaba dolensa yadawo da ita gida acikin dangi Zata Haihu. Baiso hakanba Amma yanda Haj umman ta daga Masa hankali kwana biyu hakama umma Hadiza da Dr iklimat suka nace da rokonsa akan Inayah din tadawo shiyasa kawai akan dole ya hakura zai turata gidan shikuma zai iso daga baya sbd akwai abinda Bai qarasaba Kuma akwai Dan lokaci Dan haka zai taho daga bayan shi gashi cikin lokacin harya fita wata na bakwai ma. A daren dazata wuce kaman zasu hadiye juna sbd so da kewan juna da zasuyi gashi tanata fargaban yanda Zata ringa bacci yanzu ba ajikin Abbinta ba data Gama sabo da hakan yanzu. Haka ya lallabata har airport suka wuce itada Neesah da Zata koma da aiki Nigeria kafin iyayenta su taho Suma sbd Suma zaman qasar ya ishesu qasarsu zasu koma. Bayan dawowarta ma kaman zaayi rigima sbd rokon duniya su Dr iklimat da ummanta sunyiwa Haj umma data Basu Inayah ta Haihu gida Amma Haj ko sauraron zancen ma Bata qaraba Dan tace suyi hakuri kawai. Ko Lagos da Abbin Inayah su koma dasu umma yaganah Haj umma taqi Bari tace abari saita Haihu. Inayah kuwa ganin yanda Haj umma ta cikin so da kauna yasata maqalewa tana zuba rigima tsiya iri iri duk tabi ta narkewa Haj umman Wanda itama tasan shegantaka take Mata Amma Kuma takasa qin biye Mata suyi Dadi, suyi fada, suyi rigima, suyi tsiya ahakan suke zaman renon. Ummanta da momynta kuwa kusan duk bayan kwana biyu suna gidan dubata sbd Dr iklimat din da Neesah ne likitocinta Dr farhat data kwana biyu da dawowa Nigeria itama tazo gidan gaida Haj umma...,hajiyar ta dakatar da ita sbd rikicin da Inayah ta ringa musu ta dagawa hajiyar hankali da Rigimar qarya Daga ranar Haj umma ta dakatar da zuwan Dr farhat gidan, Anty juwairiyyah dataso kawo Mata wani qabli da ba'adi taka Mata birki itama tayi tana cewa ko sunan MAJEED karta Kuma hadawa Dan Dr farhat idan ba hakanba zataga bacin ranta. A kunyace anty juwairiyyan ta Kama kanta ganin Haj da safiyyah sunyi nisa akan MAJEED da 'yar tsanar matarsa Gashi ya manyanta yayi kudinda ko agurin kowa ya wuce reni bare wulaqanci dan hka tasake Kama kanta taringa lallaba Inayah din itama ko Zata lakaci arziki tunda ga safiyyah Nan ita tanata cin arzikinsa ba shamaki. Kullum wuni takeyi waya da Abbinta Videocall da normal call Duk yabi ya fice hayyacinsa sbd rashnta Allah ya taimakesa daf yake da kammalawa kwata kwata ya dawo. ******cikinta yashiga wata Tara harda sati biyu ba zato suna zaune a palo dasu Haj umma Zubbi na Danna Mata qafafunta saiga drivern gidan anty safiyyah ya daukosa daga airport. Cikin farin ciki kowa ke Masa barka da zuwa Yana amsawa idanuwansa akan Babynsa da tsohon cikinta da yayi Mata kyau sosai. Itama shi take kallo zuciyarta na cika sosai da farin ciki ta janye qafafunta daga hannun zubbi ta miqe ta nufesa farin cikinta baya boyuwa. Da sauri ya qaraso ya tareta cikin tsananin kulawa Yana cewa" Easy Mana.. Bata damu dasu Haj umma ba ta rungumesa tana fadan yanda tayi kewarsa sosai. Wani boyayyan numfashi ya sauke ahankali Yana dagota daga jikinsa fuskarsa cikeda da boyayyan farin cikinsa na ganinta yace" Thank you, Amma ki Dena sauri irin hakan sbd yanayinki. Harara Haj umma ta ringa binta dashi Amma ta fuskewarta tayi kaman Bata ganiba tana dariyarta. Baida daki a gidan Dan haka suna Gama gaggaisawa ya fita masallacin kofar gida yayi sallar yadawo sukaci abinci dukkaninsu atare ya wuce masaukinsa yayi wanka yayi sallar ishai Bai koma gidanba sai washe gari da safe dasu yayi breakfast ya zauna da babynsa a dakinsa na dah Dake sama shikadai Dan shima bangaren mahaifinsa ne bayan rasuwarsa aka bar masa yanzu Kuma itace aciki Bayan angyara an sauya komai tareda zuba Mata sabbin furnitures. Narkewa tayi a jikinsa tana zuba Masa shgawaba Yana biye Mata kaman qaramara baby Dan Nan gabama San itada babyn dazata Haifa waye zai barwa wani shagwaba da rigimana agurin Abbin. A palon sama aka Kai musu abincin Rana sukaci tare yabata maganinta Tasha. Sai qarfe uku yabar gidan masaukinsa yayi wanka ya kwanta yayi bacci Dan ya sake hutawa. Bai dawo gidanba sai bayan sallar ishai sbd zaiyi bankwana dasu gobe zai wuce Lagos kafin yadawo daga baya. Ya jima Yana magana da Haj umma har kusan goman dare tukuna ya fito lokacin kowa ya shige ya kwanta Dan har hasken koina an kashe. Wayarsa ya daga ya kirata ta sauko suka nufi dining sbd yaci abinci Baici komaiba tun abincin Rana. Zama sukai a dining da kansa ya zuba cous cous din dasuka dafa Mai Dadi dayaji qoda dasu carrot. Kadan yaci sbd bayason abinci me nauyi da dare. Tea ta hada Masa ya karba tareda zaunar da ita akan table din dining din suna fuskantar juna yafara kurban tea din ahankali Yana Bata itama tanasha Yana kallon yanda take narke Masa sbd batason yakoma Lagos Duk tagama kunce Masa notikan Kai Aje cup din yayi bayan sun Gama shanyewa ya zari tissue yana goge Mata bakinta ahankali yace" Yaya dai? Kun koshi keda babyn abbin daya? Daukan tissue tayi itama tareda Dan matsowa tana goge Masa Baki ta gyada Masa Kai. Tana Gama goge Masa ta Kama fuskarsa ahankali ta matso da tata tayi kissing lips dinsa masu taushi cikeda kaunarsa. Rintse idanuwansa yayi Yana danne numfashinsa dake daukan dumi sbd yanda yaketa riqe kansa akanta sbd yanayinta dakuma gidan dasuke. Bude idanuwansa yayi suna sauyawa ya kalleta a kasalance yace" Kinsan me kikayi??? Kinsan bazan iya riqe kainaba Kuma kika...... Kama fuskarsa takuma Yi ya sake maida bakinta akan NASA tayi Masa wani rikitaccen kiss ta sakesa ta dago tana kallonsa fuskarta daukeda da murmushi.. Jajayen idanuwansa ya saukar Mata Yana matso da ita suna sake hadewa ya Kama bakin yayi Mata Gigitaccen kiss din dayake rikitata kafin ya dago suna kallon juna ya kalli rigar jikinta datasan ciki yayi yanzu. Da kanta ta daga Masa rigar ahankali cikin wani salo... Saka kansa yayi cikin rigar tata Cibiyarta yafara sakarwa kiss me sanyi kafin yayi kissing cikinta Yana shafawa cikeda kauna me qarfi da shauqi.... Sama yayo da kansa ya lashi kirjinta da harshensa take tasaki wani zararran numfashi tana barar da cup din dasuka Gama Shan tea dashi ya Fadi qasa ya fashe Yana bada sauti Mai qara Wanda ya sauka kan kunnen Haj umma Amma zargin ko aikin su waye yasata qin fitowa tana saka kanta baccin dole tana cewa" Aikuwa Dole gobe ya qara gaba Dan bazasu zo su hanani zaman wali a gidanaba da shegen rashin hakurinsu, Shi kwadayi ita rawar Kai. Abubuwan dayake Maya yasata rikicewa tana ambatar sunansa cikin yanayin Jan rudewa Dan haka ya dauketa cak sukai sama dakinta. A gado ya zaunar na ita Yana qarasa zare Mata rigarta dasuka fincike tun acan..... Wata zazzafar romance suke gudanarwa cikin sanyi kafin daga qarshe suka shiga duniyarsu..... Wata rayuwar da Abbi yasamu kansa aciki ya gigice Yana fita hayyacinsa da maganganu kala kala daga karshe gadon ya sauke nauyi Wanda yasashi fashewa Amma Bai balleba. Bayan sun nutsu wanka sukayo Dole anan ya kwana rungume da babynsa... Daqyar ya fita sallar asuba daga can Bai dawoba Dan daga masallacin zai wuce batareda kowa yasan gidan ya kwanaba. Bayan fitarsa daqyar ta iya sallar asuba sbd sabon yanayin ciwo ciwo datakeji Yana taso Mata ahankali. Tana idarwa taji ciwon yafara tsananta Taso daurewa Amma sai tsoro yafara shigarta ta silalo ta sauko qasa. Haj umma da tunda ta idar da sallar asuban take zaune tana lazimi kaman daga sama taji salatin Inayah a Palo Ta ajiye carbin hannunta tareda tashi ta fito hankalinta na Dan tashi. Umma yaganah ma taji Dan haka kusan atare suka fito palon. Tsayawa sukai kallonta cikin mamaki da Yar fargaba, Haj umma kallonta tace" Lafiya kuwa? Menene kike salati da safiyar fari??? Shiru tayi tana kokarin danne yanayinta tace" Bakomai. Binta suka Kuma Yi da kallo ganin hakan taso silalewa Takoma sai dai ta daga qafarta takasa Ta kalli umma yaganah cikin tsananin abinda takeji tanason tayi magana Amma takasa.. Cikin damuwa da kulawa sosai umma yaganah tace" Inayah kodai kinajin wani abun ne? Zata girgiza Kai wani azababben ciwon Mara ya taso Mata a Rikice ta Dora hannu akan marar tana cewa" Wallahi ciwo da azaba nakeji ku taimakeni,nnalillahi.... Cikin damuwa da takaici da rashin sanin abin fada Haj umma tace" Kinje Kun tadowa kanki naquda ko?? Ai gashinan yanzu zakisan abinda ake nufi da nutsuwa guri Daya. Kuka ta fashe dashi cikin tsananin azabar datakeji tana Neman durqushewa agun sukai saurin riqota sbd gadan gadan nakuda ce ta taso mata sosai. Ruwan haihuwa ne suka fashe Mata agurin Take hankalinsu ya tashi Haj umma ta tafi daki da sauri ta dauko wayarta takira Dr iklimat ta sanar Mata, Tana kashewa takira MAJEED din Wanda har lokacin Yana masallacin kofar gidan Bai wuceba tukana. Asibitin Dr iklimat suka nufa da ita Neesah da aka Kira daga baya harta rigasu Isa Dan haka suna Isa a gaggauce aka shiga labor room da ita. Azabar data ringa ji me gigita qwaqwalwa da hankali yasata ringa fadar bazata sake zuwa dakin Abbi ba.... Daga tayi salati da addua saita maimaita hakan,.... Momynta Dr iklimat da Neesah ne suka karba haihuwar Allah yasa ta Haihu lafiya daqyar bayan taci wuya sosai. Lafiyayyar baby girl aka samu Mai Kama da Abbinsu sak...su umma yaganah Kuma sunce Haj umma ta biyo. Bayan sun dawo gidama su umma Hadiza sukaita fama da Haj umma da Abbi akan Inayah taje gida zaman haihuwa Amma daga Haj umman har abbin Basu amintaba haka suka hakura akan daga baya Zata dawo gidan kafin Takoma gidanta Lagos. Ita kanta Inayah taso binsu ummanta gida Amma Abbi yace aa Sam Dole ya hakura. Duk yanda zaa fasalta farin ciki da nutsuwar da AA MAJEED yasamu bazata misaltu ba sbd tamkar wani bangaren ne na rayuwarsa ya qarasa cika da samun 'dan kansa. Da sunan Haj umma yayiwa babyn huduba Nana Fatima. Kwana biyar da haihuwa anty Hafsat ta iso Abuja itada Safnah dasu Siyama Mimi ce kawai Bata samu Daman zuwaba sbd wani uzurin. Ganin Baby Fatima Yar Inayah da Abbi Saida anty Hafsat tayiwa ubangiji sujjada tana gode Masa da ganin wannan tabbatacciyar alaqar da Allah ya hada. Ranar suna basiyi wani taroba sbd iya yawan taran familys din kawai ya wadatar Musamman kusan duka danginsu MAJEED na nesa Dana kusa sun halarto sbd son samun shiga agurinsa tunda yanada abin duniya. Su kansu su Anty juwairiyyah dukiyar dasuka karba a kan siyayyan baby Fatima da Inayah sun samu nasu Rabon sosai. Su Yaya kabiru ma takanas suka taho daga Adamawa da matansu sunata rawar qafa da Neman Shiga agurin MAJEED. Bayan suna da kwana biyu su Anty Hafsat suka Neesah Kuma zancen aurenta ya tabbata da Dr Abdul sbd Dr iklimat dataji Babu Wanda takewa Abdul din shaawa kaman Neesah Dan haka Babu Bata lokaci tun kafin su Yaya kabiru su koma suka fara zuwa gidan kakar Neesah din suka shigar da maganar Neman aurenta agurin Uncle dinta qanin dadynta Kuma akai musu na'am. Inayah da baby Fatima kuwa daqyar Abbinsu yabarsu sukai 40 days a gidan Haj umma suka koma gurin ummanta sukai Mata sati biyu kafin suka tattara suka komawarsu Lagos Daga ita sai masu aikinta zubbi da Salimat umma yaganah tayi zamanta gurin Haj umma bace ba yanzuba ba ranar dawowarta... Koda suka dawo kusan komai na gidan an sauya anzuba komai sabo an warewa baby Fatima dakinta Babu abinda baa saka Bata ba na babies Itama kusan hatta sabbin sitira Saida aka cika Mata wardrobe dasu kaman dai yanda takeyi kaman babyn itama. Dawowarsu suka bude sabon shafin rayuwar Jin Dadi da kwanciyar hankali tareda ibadar aure Dan kuwa yanzu bayan nauyin kula da miji data gida ga nauyin zamtowa uwa ya hau kanta Amma bashi yasa ta sauyaba agurin Abbinta Dan kuwa har gobe rigima da shagwaba kala kala takewa Masa Yana biye Mata. Bata fara dawo hankalinta ta nutsuba kaman yanda Haj umma tace Saida ta ganta da ciki ajikinta gashi baby Fatima ko shekara biyu bataiba Dole aka yayeta Wata Tara nayi ta haifa Namiji aka sanya Masa sunan mahaifinta salis suna kiransa da Adeel. ##MAMUH## ALHMDLLH YA ALLAH. ANAN MUKAZO KARSHEN LITTAFIN LABARIN INAYAH WATO RIBA BIYU.. INA FATAN YA NISHADANTAR YAKUMA ILMANTAR, ALLAH YA YAFE MANA KURA KUREN DAKE CIKI YABAMU LADAR GADAKARWAR DATAKE CIKI. KARKUCE YAYI SAURIN KAREWA PLEASE SBD BAYAN HAKAN BANSAN ABINDA KUMA AKESON NAYITA RUBUTAWABA. ABINDA KUMA NA MANTA BANSAKABA AYI HAKURI A DAUKI HAKAN AJIZANCI IRIN NA DAN ADAM DA MANTUWA NAGODE ALLAH YA SAKAWA KOWA DA KHAIRAN.. SAI MUN HADE A SABON LITTAFINA MAI SUNA................ [11/21, 5:33 PM] Hajiya Qarama: *_71_* Ganin irin kallon dayake Mata yasakata jikinta mutuwa Takumasan abinda zai iya biyowa Baya Dan haka ta qarasa gaban mirror ta goge kan da wani qaramin towel Bata tsaya busar dashiba sbd handdryer na dakinta Ta zira jallabiyarsa da mayafi tayi sallah. Tana idarwa ta tashi ta nufi dakinta Dan busar da kan tun sanyinsa Bai fara damuntaba. Tare suka tafi dakin nata Yana rungume da ita ta baya Yau ko doguwar magana bayayi sbd rayuwarsa da zuciyarsa dayakejin sun Gama kammaluwa da samun macen dayake tsananin so wadda itace gudan zuciyarsa. Gaban madubi suka tsaya Yana kallonta ta cikin madubin ta Ciro handdryer ta jona Zata kunna ya riqo hannunta tareda juyo da ita suna fuskantar juna Ya dauketa sama ya zaunar kan gaban madubin Yana sake kallon jiqaqqen gashinta cikin yanayi na Burgesa da yayi a jiqen. Tabawa yayi Yana shafawa Qasa qasa yace" Banason sanyi ya kamaki baby Inayah Amma inson ganin gashin Nan a jiqe....kansa yakai Yana cusa hancinsa cikin gashin ya shaqo Qamshin ruwa Daya hadu Dana Qamshin tsadaddan man gashin datake amfani dashi Ya lumshe ido Yana sake shaqarsa. Komai dayake jikinta kaunar qamshinsa yakeyi sbd qamshinta yazama kaman shine nasa mayen qarfen dayake fizgarsa zuwa gareta. Ko baya tareda ita hancinsa kamshinta kawai yake karba tun kafin yanzu. Dagowa tayi ta kallesa tana Dora hannunta kan hannunsa dake cikin gashinta cikin shagwaba tace" Na fasa busarwa to tunda kanaso Abbi. Girgiza Kai yayi Yana sake lumshe ido cikin jikinta a kasalance yace" No, banason sanyi ko kadan Yana tabaki. Cikin son Jin abinda yasa Sam Baya Wasa da sanyi akanta tunda ta girma tasan kanta tace" Abbi meyasa bakason sanyi atareda Ni? Kallonta yayi na tsawon minti Daya cikeda kulawa da so me qarfi Yana tuno baya zuciyarsa tayi nauyi na tuno abinda yake tsananin baqin cikin tunawa...ya janyo hannunta dake kan fuskarsa yayi kissing ahankali kafin cikin sanyi yace" Sbd sanyi yaso yimiki illa sosai da kina baby, Ya kamaki Wanda da Allah Bai taimakeni a lokacinna bansan ya rayuwata zataiba idan wani abin ya sameki alokacin... Ganin yanda ya qarasa zancen Yana janyewa daga gareta da alama Sam bayason tuno abubuwa da yawa na baya.. Saurin riqosa tayi tana rungumesa tsawon mintuna biyu kafin ya dago ta kallesa shima ita yaje kallo ta sakar Masa wani qayataccen murmushi tace" I love you Abbi. Lumshe Ido yayi kalmar na ratsasa ya bude idon ahankali zaiyi magana ta Dora bakinta akan NASA tafara kissing dinsa irin yanda koyar da ita tana zuqo yawunsa tana shanyewa.. Riqo wuyanta yayinyana sake Bata damar tayi kissing din yanda takeso dakyau. Akan madubin suka fara komai kafin ya dauketa suka koma akan gadonta bayan duk sungama jeho pillows da bargo a qasa Kansu kawai suka Bari akan gadon Amma komai an jeho qasa. Bayan sun Gama komai sun nutsu wanka sukai Ganin har 8 ta wuce yasashi shirin fita aikin Daya dawo Yi sbd daman 9 suke fita. Tea da fries kawai tayi Masa sukai breakfast ya fice Bayan ta sanar Masa itama Zata fita da Neesah. Yana fita bedroom dinsa da nata dasuka Gama haukatarwa tafara gyarawa kafin ta tsaftace gidan duka ta sake wanka ta shirya cikin off-white Palazzo trouser da white Vneck top sai black luxury chiffon kimono ta sanya black Chanel wedges da qaramar chain bag dinsu... Ko Gama rolling qaramin veil dinta bataiba Neesah ta iso suka fice. Asibitin da Neesah ke aiki suka fara biyawa ta miqa sako suka fito... Gurare da dama suka tattafi sai yamma suka koma gidansu Neesah Mum na ganin Inayah ta rungumeta cikin tsananin farin ciki da murnar ganinta. Sallah sukai sukaci abinci kafin suka koma daki suna firarrakinsu sai after 8 Abbi yazo daukanta suka wuce gida. Suna zuwa gida wanka kawai sukai su dukan suka shige dakinsa tana zuba Masa da rigima iri iri Yana biye Mata har sukai abubuwansu sukai bacci. Washe gari ma tare suka fita ya ajiyeta gidansu Neesah ya wuce Ko mintuna Ashirin basiyiba Suma suka fice.. Kwanaki takwas yayi Yana fita aikinsa aikinsa Su Kuma ya sakar musu katikansa na Banki suna yawon shoppings da sauran abubuwan dasukeso Dan haka Koda yagama aikinsa kwata kwata sungama siyayyan duk wani fititannan kayan zaman gidan dazai hanasa Gane kansa, Cikin qanqanin lokaci ta qarasa zarar dashi da shegun mini skirts dasu bmshort, Su kayan baccin data siyo masu tsananin kyau da tsada yagama tadasu aiki ta hanyar saka kansa cikin Riga sukuma basa dauka suna fincikewa. Watansu Daya harda sati biyu cm yazo qasar sbd kawo sauran takardin nasu kamfanin da zasuyiwa babbar Register a qasar. Sunyi kwanaki masu tsayi basa fita koina dagasu sai kansu a gida sbd sun sake samun wata sabuwar shaquwa da sabo da juna Koyaushe tana maqale a jikinsa ko fita sukai Yana riqe da ita Babu ruwan kowa dasu haka Suma Babu ruwansu da ita. Yau yafita tareda CM zuwa gurin processing abinda abinda ya kawo CM., Itama Neesah takira suka fita sbd kadaicin ya dameta yasata har tanajin kaman zazzabi zai kamata. Gidansu Neesah sukaje acan suka wuni sai yamma suka fito Neesah ta biya wani babban pharmacy Zata siya wani alluran dazata Shiga asibiti dashi anjima da dare idan Zata. Suna shiga Inayah ta tsaya dakata bakin kofar shiga tana Dan yamutsa fuska sbd Qamshin magunguna yayi Mata qarfi a hanci taji. Juyawa tayi Takoma mota tana Zama zuciyarta ta Dan ringa tashi Neesah na shigowa Motan ta kalleta zatai magana ta tareta da cewa" Sorry sorry,na dade ko? Fasa maganar datai niya tayi tana cewa" Kaini gida please, am feeling uneasy. Tada motar Neesah tayi tana cewa" Haryanzu kin kasa sabawa da warin magani ne? Kina aikin asibiti? Kokuwa dai wani matsalan ne daban? Kasa magana Inayah tayi sbd sosai takejin zuciyarta na tashi har kanta yafara juyawa da jiri jiri. Suna Isa parking kawai Neesah tayi Inayahn ta bude motar ta fito saidai ko taku biyu bataiba jiri ya debeta tayi baya Da gudu sosai Neesah data fito motar ta tareta tana kallonta cikin mamaki da Yar damuwa tace" Lafiya kuwa? Meya sameki yanzu yanzu?..... Kafin tasake jefa mata Mata tambayar jiri yakuma dibanta ajikin Neesah din idanuwanta sukai wani irin lumewa ta zube jikin Neesah din. Hankali tashe ta Jata ta saka a mota daqyar ta rufe ta zagaya ta Shiga ta tada taja tabar gidan tana Kiran wayar Abbi Amma baya dagawa a hargitse ta rubuta Masa text ta tura tareda ajiye wayar tana Dan qarawa motar speed. Asibitin datake aiki ta kawota Suna isowa da kanta takuma Kama Inayah data Dan hawo hayyacinta sbd sosai warin Inda sukaje din ya tana zuciyarta. Office din Dr farhat ta nufa da ita sbd tana cikin manyan asibitin Gashi tanata kokarin harhada sauran takardunta tabar qasar Takoma qasarta taci gaba da aiki tunda acan zatai aure. Suna Shiga office din tana tareda patient dinta da yawan abortion yasata kasa daukan wani cikin.... Da mamaki da Kuma firgici take kallon Inayah da Bata taba sanin tana qasarba kokuma tace Batasan suna qasarba sbd tasan Abbinta bazai taba barinta tazo qasar ita dayaba Dole tareda umma yaganah, Idan Kuma sun Inayah da umma yaganah suna qasar su dukan to tabbas kenan shima Yana qasar.. Ba lafiyarta tafara tambayaba tsabar rudewa yaushe sukezo take tambaya. Basu tsaya amsataba Ta kalli patient dinta Dake zaune tana kallonsu cikeda mamaki itama Tace" Sorry Amal Ina zuwa zuwa. Kwantar da Inayah sukai gadon duba patients dinta dake office din nata Tafara taba pulse dinta Dan taji Sai kawai taji alaman ciki a cikin yanayin nata. Faduwa gabanta yayi da sauri ta kalli Inayah wadda itama ita take kallo Dan batada wani qarfin kwacewa ne yasa tabarta tadubata dukuma qarin sanin Abbinta yagama Zama nata batajin Zata daga hankalinta akan Dr farhat din Kuma. Sake Jin pulse din tayi ta tabbarda abinda take zargi saidai duk wannan ba tabbaci bane cikin sake shiga rudani ta kalli Neesah ta kalli Inayah. Ganin hakan Neesah ta qurawa Inayah Ido tana karantar yanayinta cikin rashin tabbatarwa tace" I think you are pregnant Inayah.. Da sauri Dr farhat ta kalli Neesah tana cewa" Eh Nima abinda nake tunani kenan saidai ai bazai yiyu bane tana budurwa ace ciki Kuma? Tashi Inayah tayi zaune tana son gasgata zancen Neesah Dan itama sai yanzu da Neesah din Tai magana tafara hasaso hakan amatsayinta na likita. Cikin kasala tace" Kumin scanning nakeso na tabbatar banason wani test. Kamata Neesah tayi ta tashi tsaye da kyau suka nufi office dinta sbd na office din Dr farhat ya samu matsala. Kwantar da ita tayi a nata consulting office din tafara Mata scanning.... Dr farhat datai suman tsaye da mamaki da firgici bin bayansu tayi Itama Amal da Inayah da Neesah da basuma lura da itaba bare su ganet tashi tayi tabi bayan Dr farhat cikin nata tashin hankalin sbd tana cikin tsananin damuwa da tashin hankalin son samun ciki kafin Zaid ya rabu da ita akan hakan sbd yanzu da hakan yake Mata barazana da sakinta, Tunda sukai aure no Bari bata taba yiba bayan uban cikin dasuka ringa zubarwa kafin aure gashi sunaso yanzu dasukai auren Amma Babu cikin. 6 weeks pregnant suka gani.... Cikin tsananin farin ciki Neesah ta rungumeta tana cewa" A big congratulations to you babes, Finally Zamu Zama mummies.. Ita kanta Inayah kasa cewa komai tayi sbd wani sanyi Daya mamaye zuciyarta lokaci Daya Kaunar cikin sosai sbd shi din jinin Abbinta ne, Daga qarshe dai jininsu ya gauraya. Shigowar Dr farhat yayi daidai da AA MAJEED din idonsa akan Inayah dake kwance da ciki a bude da aka Gama scanning din Bata tashiba. Dr farhat bayanan Dake rubuce a screen ta karanta tana sake shiga babban rudu da firgici tace" Inayah ciki fa ake magana a jikinki??? Abbinki idan yasani kinsan abinda zai iya biyowa Baya kuwa? Langabar dakai Inayah tayi tana kallon bayan Dr farhat din cikin Yar narke fuska tace" Abbi wai idan kaji inada ciki ya zakayi Inji Dr farhat?? Da Ido yayi alaman" wat??? Cikin kasa fahimta ko yarda Kai tsaye da abinda tafada din zuciyarasa na dakuwa da zancen. Cikin farin ciki Mara boyuwa Neesah tai Masa nuni da screen din scanning dasuka Gama lokacin Ya saukar da idanuwansa akai yana dubawa. Bai qarasaba ya waiwayo da sauri ya kalleta cikin wani irin yanayi Daya Gama tona asirin zuciyarsa yau din Dan kuwa idanuwansa Yi sukai Kaman zasu zubo da kwallan farin ciki Mara misaltuwa. Takowa yayi Yana kallon cikin tsakiyar idanuwanta da itama shi take kallo a marairaice baice komaiba sai kawai ya rankwafo ya Kama fuskarta yakai bakinsa kan nata yayi Mata wani fitsararren kiss ya dago ya kalleta cikin wata ratsatsiyar murya yace" I love you baby Inayah. Daga Dr farhat har Amal da zaid da Babu Wanda yasan da isowarsa yabiyo matarsa dayaga tayo Nan duk mutuwar tsaye sukayi, Dr farhat da Zaid na rige rigen sauko da hawayen tashin hankali da baqin ciki akan fuskokinsu, Dukkaninsu sunji labarin cewan angano bashine ya haifeta tsintarta yayi Amma Basu taba hango wata alaqa bayan ta uba da 'yaba a tsakaninsu sai yau dasukai mugun gani, Gashi dai batareda anmusu bayaniba sun tabbatarda cikin jikinta nasane Kuma na aurene bana shegeba ko daga yanayin farin cikin fuskokinsu Dana Neesah. Neesah ce tafara lura da Zaid da matarsa a kofar Ta juyo ta kalli Dr farhat dake hawaye ba boyewa a fili... Tadan dauke Kai daga kallonsu Zaid tace" Dr farhat patients dinki kaman suna jiranki kila emergency ne Naga harda kuka sukeyi Ki taimaka ki dubusu kada ciwon yayi musu tsanani. Kasa aiki kwakwalwar Dr farhat tayi ta juya kamar wata zararra qafafunta kawai taji suna janta suka fitarda ita daga office din Suma su Zaid sukabi bayanta kowanne qafafu a mace. Bayan fitarsu Suma su abbin da baima lura da mutane ba tun shigowarsa sbd hankalinsa akan Babynsa kadai yake Suka fito suka nufi gida yanajin kaman zai hadiyeta sbd jinta a zuciyarsa. ##MAMUH# Downloaded From https://tknovels.com.ng