An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 1_ *_Free pages_* ________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv _________________ A tsari da tarihin rayuwa ƘADDARA MADUBI ce. Domin tana sakaka kallon kanka a ɗan adam kuma bawan da rayuwarsa ba ikonsa bace. UBANGIJI ya halicci duniya da halittun dake rayuwa a cikinta daban-daban, wanda suke a zahiri, da wanda ya baiwa kansa ilimin sani shi kaɗai. Sai dai a dukkan halittunsa ya tabbatar mana ƊAN ADAM mai daraja ne. Musamman idan mukai dubi da ayoyi da suka zo cikin Alkur'ani mai girma.         Bawai hakan na nufin sauran halittunsa basu da muhimmanci ba, a'a kai dai DAN ADAM ya baka wannan darajar, ya kuma fifitaka, idan muka duba Suratul Baqarah. Yayin da ALLAH ya ce wa mala’iku zai halicci khalifa a ƙasa (wato Adam), kuma ya umurci su su yi masa sujada, abin da ya nuna fifikon mutum fiye da mala’iku (sujuda ta girmamawa ba ta ibada ba). Bai barmu a mutanen kawai ba, sai ya rabamu a jinsi guda biyu, NAMIJI da MACE. sannan ya yomu a BAƘIN FATA da FARAREN fata. Ya yomu a YANKUNA DABAN-DABAN. Ya kuma banbantamu a ADDINAI DABAN-DABAN. Ba iya nan kawai muke ba, yarukan bakunan mu ma daban-daban suke, ta yanda wani idan zai kwana magana wani bai san mi yake faɗi ba koda zaginsa yake kuwa. Ba'a nan kawai muka banbanta ba, yama wasu ARZIƘI, wasu DUKIYA, wasu ILIMI, wasu BAIWAR SARRAFA HARSHE ko yin AIKI tuƙuru daga gaɓɓansu da ƙarfin daya azurtasu da shi. Samun ɗaya daga cikin wannan bashi ke nuna maka kafi wane DARAJA ba. Dan zai iya yinka mai ARZIƘI a DUNIYA, ka tashi talaka a lahira, talauci irin na rasa ƙyawawan ayyuka da rashin samun ƙyaƙyƙyawar MAKOMA. Zai iya yinka TALAKA a DUNIYA a lahira ka tashi mai tarin arziƙi da AYYUKANKA da samun kyakkyawar makoma. Zai iya yinka mai ILIMI, a lahira ka tashi ILIMIN bai amfaneka da komai ba domin baka amfanar da kanka da shi ba bisa kyakkyawar hanyar data dace da iklasi a DUNIYA. Zai iya yinka JAHILI, amma ka tashi a ƙyaƙyƙyawar MAKOMA saboda baka cutar da kowa ba a duniya, baka kuma bi mummunar hanyar da zata RUGUZAKA ba wajen yin ayyuka saboda RIYA (Rahama ta ALLAH ce). Wannan kaɗan ne daga cikin RAHAMARSA ga bayinsa.       A yanda DUNIYA take kamar ƙwallon wasa a ido, haka RAYUWAR kowane ƊAN ADAM take a NASARA ko FAƊUWA. Yanda kwallon ke a hannunka kusa da idanunka babba, haka girman matsalolinka da damuwarka da nasararka suke a zahirin idanunka da ZUCIYARKA. Idan ka harbata nesa da kai takan koma ƙarama, haka idan ka yarda UBANGIJI shine mai ƙaddarawa da bada sakamako sai ka dinga kallon wannan damuwar taka da matsaloli da jarabawoyi ƘARAMA kamar yanda kwallon nan dake nesa da kai take ƙarama.      Banbancin kawai girma da ƙarantar kwallo a idanu muke ganinta ƙwaƙwalwa ta auna mana. Amma girman jarabawa da matsalolin rayuwa muna kallonsu ne a ZUKATANMU da KWAKWALWAR MU baki ɗaya.       Bara mu taƙaita domin ku fahimci inda ainahin shimfiɗar tamu ta dosa kai tsaye, dan karmu shagala lokaci na gudu ba kuma mu yake jira ba. Abinda kawai nake so mai karatu ya auna anan minene ainahin RAYUWA? WANENE SHI? MAI ZAI KOMA A WATARANA? MINENE ƘARSHENSA A ƘARSHEN RAYUWA?.      Ki yarda, ka yarda a cikin kowace RAYUWA akwai farin ciki, akwai jarabawa, akwai nasara, akwai faɗuwa, akwai ƙalubale, akwai mafari, akwai ƙarshe, akwai mina aikata mina bari a bayana?. Dukansu kuma suna ƙunshe ne a cikin wannan rayuwar taki ko taka guda ɗaya tak da ba'a hannunka take ba, yanda ba'ai shawara da kai yayin halittarka ba, sai da ka girma ma kasan wanene kai? Haka baza'ai shawara da kai wajen tabbatuwar waɗan can abubuwan na sama ba. Domin a dukkan ni'ima da rahamar da UBANGIJI ya baka babu wacce kake biyansa da KUƊI. Ibada ma idan kayi kai kakema kanka gata bazaka rageshi da komai ba, ba kuma zaka ƙareshi da komai ba. Dan haka mu tafi kai tsaye kawai a wannan labari mai suna KIƊA A RUWA! MAI MAGANIN DODO. da zaizo gareku a wannan lokacin, mu kuma hango darasin da yake mana hannunka mai sanda akai domin mu fahimta, mu ilimantu, mu nishaɗantu, mukuma wa'azantu idan hakan ta kama...... •>•>•>•>•>•>• .....17/5/20013.....       ......Motse-motse yake ɗan yi da surutai cikin barci, har takai wanda ke a kusa da shi yana iya jin komai. Gashi yayi sharkaf da zufa a goshinsa duk da ba yanayi ne na zafi ba. Hasalima wani ɗan karan sanyi ake zuwabawa irin mai hazo ɗin nan da iska mai kwaso ƙasa ta buɗe mutane.      Da mamaki wanda ke kusa da shi da littafi a hannunsa yana dubawa ya ɗan zuba masa ido, sai kuma ya kai hannu ya taɓa shi yana kiran sunansa amma ko motsi. Littafin hannun nashi ya ajiye, zuciyarsa na ƙara shiga ruɗani da tsoro. Ba wannan ne karo na farko da abokin nashi kuma amini ke shiga cikin wannan halin ba a cikin barci, wani lokacin har sai ka fara fassara al'amarin nashi kamar na mai aljanu, kuma sam ba aljanun bane ba, in dai har zai kwanta barci mai nauyi a ƴan shekarun nan da wahala ya tashi bai shiga wannan yanayin na mafarki ba, duk da bai taɓa faɗa masa irin mafarkin da yake yi ɗin ba shi ya fahimci mafarkine mai nauyi da ban tsoro....        Sosai ya girgizashi kam yanzu, bayan ya janye bargon da yake ciki kalar army green, tare da shafa masa ruwan gorar dake gefensa a fuska. Wani nannauyan numfashi ya kawo tamakar mai dawowa daga suma, sai kuma ya ɗan furzar ya sake jan wani kaɗan kafin ya buɗe idanunsa a hankali.       Masha ALLAH na ambata ganin wasu kyawawan idanu tamkar ba na namiji ba. Da farko abokin nashi da shima ke kallonsa ya zubama ido, sai kuma ya kauda gefe yana yunƙurawa ya tashi zaune yana jingina da jikin tantin da suke ciki. Riga ce armless data kama ginannen jikinsa kalar army green, sai wando 3-quater irin kakin sojoji. Duk da a zaune yake kallo ɗaya zai tabbatar maka da sojan ne na gaskiya kuma tsayayye, dan kuwa jikinsa irin na lafiyayyun tsayayyun jaruman sojoji ne da zasu iya tunkarar kowane harmutsi musamman na nuna ƙarfin ƙwanji.       Abokinsa da ya zuba masa ido ya ɗan girgiza kansa, sai kuma cike da kulawa ya ce, “Da ace ina da damar matse bakin nan naka da baya son motsawa yayi magana da nayi hakan dan sanin wane irin mafarki kakeyi a shekarun nan, dake saka ka a wannan yanayin, *_Zak-Shadow_* duba fa yanda kake zufa tamkar wanda yake a filin daga, amma kuma akan mafarki, wannan al'amari na bani mamaki da tsoro”.        Wani ɗan kallon fishaa yay masa slowly da idanunsa ya kuma janye, batare da yayi maganar da yake so yayi ɗin ba ya miƙe abinsa. Nace oh oh! Wato fa da gaske a sojojin ma akwai SOJA, akwai kuma SOJI. Kai daka kalla wannan kasan yaci sunansa na Zak-Shadow, har hamar ya dace a ƙara masa da ILIYA ƊAN MAI KARFI. Dan kuwa mazan faman ne fa a mazansu da kayar da su ƙasa sai an haɗa da babban shirin haɗin gwiwa. Cikin yanayinsa na rashin gaggawa da hayaniya ya saka tausasan slippers baƙaƙe dake a gaban gadon daya tashi, batare daya sake kallon abokin nashi da yay tagumi yana binsa da idanu ba ya nufi ƙofar tantin da suke ciki, sai da ya ɗan ranƙwafa sannan ya fice.     Babbar magana, jeji ne iya jeji da babu alamar wani gari ko motsin halittu na mutane a kusa. Idan ka cire ɗan sansanin da suka kafa nasu na sojojin mai Tanti biyar kacal. Uku manya ne sosai da zai iya cin sojoji da yawa. Guda biyun sune ƙananu madaidaita. Guda ukun manya da ɗanyan ƙaramin suna a kusa da juna ne, ɗayan da Zak-Shadow ya fito a ciki yana gefe guda ne a ware ƙarƙashin wata ƙyaƙyƙyawar bishiya ƙatuwar gaske. Sosai garin yayi hazo na yanayin sanyi har baka iya hango abinda ke ɗan nesa da kai da ƙyau koda bishiyoyi ne, a gurin yashine shimfiɗe mai ƙyau da ɗaukar idanun mai kallo, ga tsafta, dan gabansu kaɗan akwai ruwa kwance dake rayuwa a wajen, dan haka ya zama matattara dabbobin jeji dake zuwa shan ruwa, wani lokaci kuma harda masu haɗari amma suka zo suka kafa sansani a wajen saboda ƙarfin hali irin na soja.       (Sojojinmu ALLAH ya ƙara muku lafiya da nisan kwana a duk inda kuke🙏).      Babu yawan sojoji a waje, dan basufi a ƙirga ba dake ɗan kai-kawo da bindigu a hannu sai wasu a zaune, da alama ƴan jiran kota kwana ne.         Fitowar Zak-Shadow ya saka wanda ke jikin tantin daya fito nutsuwa da sauri, tare da ƙamewa yayi salute nashi cike da girmamawa yana sake risinar da kai ƙasa, dan da gaske Zak-Shadow zakine a wajen na sama da shi ma ba naƙasan kawai ba. Idanunsa kyawawa masha ALLAH ya zubama sojan na sakanni, sai kuma ya maida ga sauran da ƙamshinsa ya fargar da su, suma duk sun nutsu, wasu a cikinsu jikinsu har tsuma yake yi. Jin shakkar Zak-Shadow a jinin duk wani matashin soji daya sanshi yake, badan ya kasance azzalumi ba, sai dan kasancewarsa tsayayyen mutum da baya ɗaukar shirme akan aikinsa da gaskiyarsa, kana take doka ko gaskiya ya ɓallaka ya ɗora gaɓa-gaɓa wannan abu ne mai sauƙi a wajensa.      Sai da ya gama ƙare musu kallo tsaff batare da yace uffan ba yay wucewarsa cikin takun bajinta na ma'abota ƙarfin jiki. Numfashi suka shiga saki a hankali, dan tunda ya fito kowa ya riƙe nashi a maƙoshi gudun shiga tarko. Sai kuma suka shiga ɗan kallon juna suna gulma da idanu, dan buɗe baki dai ayi magana tamkar taro match ɗin da babu yawan ƴan wasa ne..........✍🏼      _(🤣To bana kuma wa muka kwaso ne? Nima fa masu karatun wannan Zak-Shadow ya fara razana ni🤭, kota yaya labarin ma zai rubutu oho🥱😆. Kudai kuyi addu'a kawai kar ku ji ana karya Bilyn ku gaɓa-gaɓa ana ɗorani🤥.)_     ________________👇 _Zaku samu wannan Littafi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA)_(VIP 1000 CFA)* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 2_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 ________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv __________________ ........A gaban ruwan nan da kowa yasan wajen zuwansa ne in har ba suna akan aiki ba ya iso, ya ɗan bi wajen da kallo cike da nazari, sai kuma a hankali ya furzar da huci mai ɗan nauyi da nuna damuwa. Dai-dai nan wani matashin soja ya iso wajen hannunsa ɗauke da roba cike da dawa. Ɗan kallonsa Zak-Shadow yayi, sai kuma ya miƙa hannu ya amshi roban dawar alamar baya buƙatar wata magana. Cikin girmamawa sojan ya bashi, ya juya yabar wajen. Tamkar tsuntsayen dake rayuwa a wajen sunji ƙamshin dawar ne, sai gasu suna sauka ɗaya bayan ɗaya a gabansa. Karo na farko yay wani ɗan murmushin gefen baki, tare da ɗibar dawar a hannunsa ya shiga watsa musu, ai kafin wani ɗan lokaci tsuntsaye kala-kala sun cika wajen, shiko yana cigaba da watsa musu dawar. Abin sha'awa harda masu sauka akan kafaɗarshi. Dan dai-dai nan ma wata ƙyaƙyƙyawa mai adon ja da blue a jikinta ta taso fiirrr ta sauka akan kafaɗarsa ta haggu. Juyawa yay a hankali ya zuba mata ido, kai da ganin kallon da yake mata kasan tunaninsa ya tafi wani waje ne kuma daban.         Mafarkinsa ne ke dawo masa daki-daki tamkar Film da ake kallo zaune a cinema. Ba yau bane farko a garesa yin mafarkin, amma duk sanda yayi yana koma masa ne kamar sabo, kamar kuma a ranar ya fara yinsa, ga mafarkin a duk sanda zai yi shi cikin maimaita masa kansa yake abin kamar wani sihiri koma mi zai kirashi oho. Shekararsa bakwai da wasu watanni kenan da fara wannan mafarki, tun daga randa suka fara shigowa wannan jeji (2006) akan aikin da suke kai har zuwa yanzu lokacin yana ma a matsayin Major. Sun yo nisa sosai da jejin sukaci karo da wasu gayyar mata tafe da kayayyaki a kansu har da yara anata raira waƙar aure, ganin motocinsu da kayan jikinsu na kakin sojoji ga bindigu a hannu ya saka mutanen firgita suka shiga watsar da kayan kansu suka kwasa da gudu, masu ihu nayi masu kururuwa nayi. Sai mace ɗaya mai tsohon ciki data tsaya cak a hanyar, lallai itama a tsoracen take, sai dai da alama bazata iya gudun bane ba saboda ciki. Idanunta a rufe suke ga zufa ta gama wanke mata jikinta dake rawa. Duk abin nan dake faruwa kallo ɗaya yay musu ya maida kansa ga jaridar da yake dubawa, sai da abokinsa, koma ace amini da ya zama ɗan uwa na jini dake gefensa a motar da suke su biyu rak sai driver ya furta, “Ikon ALLAH irin wannan cin gudu kamar kunga dodanni! Ita kuma wannan halan cikin jikinta ne ya hanata gudun..?”       A karo na biyu ya ɗan ɗago a hankali jin furucin Imran ɗin, akan matar dake tsayen ya sauke kyawawan idanun nasa da kullum suke a juye da sirkin ja kamar wani mai afa ƙwaya, baya ganin fuskarta saboda ta juya musu baya, atamface a jikinta kalar blue da zanen barewa yallow. Zanen atamfar shine a matsayin gyale data lulluɓa, sai fanteka madaidaiciya a kanta dake haɗe kusan guda goma. Ƙafarta takalman danƙo ne da ake kira ɗan-madina suma blue. Tunaninsa ya katse sakamakon fitar wani yaron sojansu inda matar take yana mata tsawar data sakata daburcewa har tana neman zubar da kayan kan nata. Shi kansa baima san ya ɓalle murfin motar ba ya fita, sai ganinsa yay kawai a gabansu. Yaron sojan ya ƙame da sauri yana salute nashi, sai kuma ya nuna matar cike da takaicinta zai fara masa bayani kawai sai yaga ya ɗan duƙa a gaban matar. Ba shi dake tsaye inda suke ba har waɗan da ke mota sai da suka firgita, ai tuni suka shiga rige-rigen fitowa a motocin harda Imran, yo oga kwata-kwata ya fito su ubammi zasu jira yi kuma. Zak-Shadow dake a gaban matar cike da tsigunnon ƙasaita kaɗan ya motsa lips ɗinsa ya ce, “Kiyi haƙuri”. Da wani kalar sauri ta ɗago tana kallonshi, dan gaba ɗaya ta gama ƙarasa susucewa tunda ya duƙunnu gabanta, sai taji ma ai gara na farkon da wannan mai kama da mala'ikan ɗaukar ran. Kalmar ‘Kiyi haƙuri’ daya ambata ta matuƙar jijjiga mata zuciya kwarai da gaske, dan ba abinda tai zato ba kenan. Numfashi ta sauke mai nauyi, sai kuma cikin sanyin murya da rawar baki ta ce, “Ku su waye dan ALLAH? Dan bamu taɓa ganin irinku a wannan yankin ba shiyyasa sauran ƴan uwana suka firgita”.     Kallonta kawai yake baice komai ba, fin minti ɗaya kafin ya furta amsar da kowa baiyi zaton zai batan ba. “Mu sojoji ne, masu bada garkuwa ga al'umma da ƙarfin ikon ALLAH.”      A mamakinsa sai yaga tayi murmushi mai ƙayatarwa tana ƙara sauke ajiyar zuciya da sharce zufar data jiƙeta da mayafinta. Ta ce, “ALLAH sarki, lale marhabun da shigowarku wannan yankin namu, dama haka sojojin da muke ji ana faɗa a redion Tanimu suke?. Lallai yau na yarda SOJA MAZAN FAMA, SOJA GA WUTA GA YAƘI. ALLAH ya ƙara kareku bisa ƙyawawan aikin ku, ya baku nasara da kariya daga duk wasu mugaye. Tunda na fara jin labarin aikin ku nake fatan ALLAH yasa na haifi ɗa namiji idan Tanimu zai tafi birni yaje da shi ya saka shi a makarantar sojoji shima ya zama soja. Amma tunda yau har gaku a wannan yanki namu in sha ALLAHU in dai namijin na haifa zan nemoku a wannan jejin ko badaɗe ko ba jima na baka amanar yarona ka koya masa wannan aiki na jarumai. Dan daga ganinka kai mutumin kirki ne jarumin kwarai ɗan gaske”.       Karo na farko ya kai idanunsa akan cikin nata da yay girma sosai, sai kuma ya kauda kai batare daya ce komai ba, anutse ya miƙe gaba ɗaya yana mai tura hannayensa cikin aljihun wandon kakinsa na soji, daga sama kuwa riga ce baƙa t-shirt data kama ingarman jikinsa, yanda yay zanzaro da belt ya bama shafaffen cikinsa bayyana kwance a rigar luf. Tabbas suffarsa itace ta asalin Zaki da ake faɗa.       “ALLAH ya saukeki lafiya, mun gode da addu'ar ki garemu. Zan zo da kaina amsar amanarki! Ku bata ruwa, a ƙarbi address ɗinta”. Yay furicin ƙarshe da umarni yana barin wajen. Ba ƙaramin mamaki abin ya bama sauran sojojin ba, hatta da aminin nashi Imran kuwa. Duk da dai kowa yasan Zak-Shadow a kallon nesa ne zakai masa ganin mugu, dodo mai firgitarwa koda a kallo ne, amma yana da tausayin na ƙasa da shi da sassauci ga mata, dan ko macen soja ce tai masa laifi yanda yake mata hukunci ba daidai yake dana namiji ba. Kamar yanda ya bada umarni sun bata ruwan roba da aka ɗakko a mota, sun kuma tambayeta garin da take ta faɗa suna rubutawa. Sannan suka taimaka mata ta tashi daga faɗuwar da tayi na firgita. Sojan da yay rubutun address ɗin nata ya miƙawa Imran cike da girmamawa, amsar takardar Imran yayi ya saka a aljihu kawai, sannan yay ma yaran umarnin su koma motoci, dan tuni shi mai gayya da aikin ya koma ciki abinsa. Haka suka wuce suka cigaba da tafiyarsu suka bar wannan mata mai tsohon ciki nabin motocinsu da kallo har sai da suka ɓace mata. Tun daga ranar bai sake bi takan zancen ba, sai dai a daren kwana goma sha shida da haɗuwa da su yay mafarkin ta haihu tana miƙo masa jaririn. Abin kamar wasa ya cigaba da maimaita wannan mafarki akai-akai, kuma koda yaushe irinsa yake maimaitawar babu canji. Gashi a ƙalla yanzu shekara bakwai kenan da wata har biyu..... _______________ FAZANAMS MULTIPURPOSE PLC. *_Ina masu neman ayi musu souvenirs Na bukukuwan su dana shagalin bikin birthday da dukkan wasu taruka?_* *_Ina masu son ayi musu abinci Na gargajiya da abin sha Don farin cikin taronku?_* *_Maza ku garzayo to ga Dama ta Samu a FAZANAMS MULTIPURPOSE PLC_* _Muna yin abinci Kamar: Masa, Dambu, Alkubus, Dashishi, Dan wake, Alala, Biski da sauran su da Miya Kala Kala 🍝🍜🍲🍛🥗🥘🫕💃💃_ *Sannan Muna yin: kunun Aya, Zobo Mai flavour Kala Kala, Kunun tsamiya, Kunun gyaɗa, Tamarind drink, Kunun Zaki da sauran su🥤🧋🧃🍸🍹🍷🥂💃💃💃 _Sannan Muna yin party packs na Yara da manya haka zalika Muna yin snacks Kamar samosa, spring rolls, doughnuts, cincin Mai kwakwa, Mai flavour Kala Kala da sauran kayan makulashe irin Aya Mai sugar da Mai gishiri, Muna yin kwakumeti, Muna alawar Madara, iloka, ridi da sauran su.🧇🥪🥙🌮🫔🌯🥐🥯🌭💃💃💃_ *_Muna yin abincin sadaka ga Mai bukata muna nan a area 2 Abuja_* kuna iya tuntubata a wannan lambar👇 *08094186230* _Whatsapp Ko Kira._ _________________        Ɗan motsin da wayarsa tayi ne ya sashi sake furzar da huci, sai kuma ya sauke hannunsa dake cikin dawar nan ya cirota daga aljihu yana dubawa. Kallon wayar kawai yake babu wani yanayi dake nuna kirane ke shigo masa ya kamata ya ɗaga, harta gama ta yanke, sai kawai yay ƙoƙarin maidata aljihun, amma hanzarinsa ya katse saboda sake motsawar data shiga yi a karo na biyu. Yanzu kam hannu ya kai ya wani murza goshinsa, kafin ya sake ɗaure fuska babu alamar wasa sannan ya kai wayar kunne alamar dai da gaske kiran nashi akeyi..   “Hallo. My D!”. Wata zazzaƙar murya mai sanyi da kwantar da kai ta faɗa daga can. Shiru babu alamar zai tanka, da sauri ta ce, “Oh I'm sorry dear. Assalamu alaikum”.         “Wa'alaikissalam”.    Karo na farko jarumar muryarsa ta bayyana cikin buɗaɗɗen sauti da ƙarfin lafazi irin na maza marasa son wasa da lokaci. Itama sai ta ɗan ƙara kwantar da murya ta gaisheshi. Maimakon amsawa tambaya ya jeho mata a kausashe.       “Kiran na miye?”. Yanzu kam murya ta raunana kamar zatai kuka, ta ce, “Haba My D. Shike nan abu baya wucewa a wajenka, na baka haƙuri, na tura maka saƙo amma duk ka share ni. Dan ALLAH kayi haƙuri, nayi kuskure kuma na yarda nayi ina sake neman afuwa. Wlhy ni kewarka ma nake yi dan ALLAH kazo gareni, wata biyu fa ba sati biyu bace.”       Shiru yayi bashi da alamar tanka mata, har sai da ta fara kuka ƙasa-ƙasa tana cigaba da roƙonsa da ban haƙuri sannan ya motsa lips da ƙyar ya furta, “Naji”.        Baiwar ALLAH, dariya ta farayi cike da farin ciki, sai jera masa kalaman soyayya take masu zaƙi da taushi dake nuna tsananin kewa da begensa da take ciki. Shi ko yaƙi ya ƙara cewa komai. Cike da sake kwantar da kai ta ce, “Na faɗama Ummie?”.       “No!”.   “Ammafa itama tana kewanka D. Haka ma su Biebah kullum zancen ka ne a gidan nan, yau tunda na shiga hiranka kawai mukeyi”.        “Uhmm!”   Kawai yace. Bata damu ba ta cigaba da masa labarin ƙannen nasa, sai kuma ta koma na yaran dake tare da ita. Shi dai nashi saurare kawai, sai dai fuskarsa ta ɗan sassauta kaɗan ba kamar farko ba. Hakan na nufin koma wacece tana da muhimmanci a gareshi. Ya jima suna wayar kafin network ya fara rawa, kasancewar inda suke sai a hankali dama. Wayar ya maida aljihu, sai kuma ya ajiye robar dan dawar ta ƙare duka. Jejin ya shiga bi da kallo irin na nazari, kafin ya bar wajen gaba ɗaya ya koma cikin tantin da ya fito ɗazun..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 3_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 _____________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ____________________ ........Ɗagowa Imran dake zaune a study table yana duba wasu takardu yay yana kallonsa. Shi ko kallo ɗaya yay masa ya ɗauke kansa, zama yay a bakin gado ya jawo takalma daga ƙasan gadon, batare daya kalla Abbas dake cigaba da kallonsa ba har yanzu ya ce, “Zanje gida”.         “Gida kuma? Lafiya dai ko?”.    “Kawai zanje ne!”. Ya faɗa a taƙaice. Abbas yasan amsar ke nan, amma sai yay shiru yana kallonsa da nazari. Eh yasan in dai yace zai je gida akwai dalili, sannan sai ya tabbatar babu wani ƙalubale da zai bari mai girma a inda suken, amma haka kawai shi sai a yau sai yaji kamar tsoro ya tsarga masa akan tafiyar tasa, sai ya kasa cewa komai. Dai-dai Zak-Shadow dake haɗa bindiga shima ya ɗan ɗago ya kalla Imran ɗin, ganin yanda ya zuba masa idanu sai ya sake tsuƙe fuska ya ɗauke kansa. Imran yayi murmushi, dan yasan ya tsani kallo. Cike da tsokana ya ce, “Anya ba kewar Madam bace ke tsikarin ka?”.       Bai kula tsokanar da yake masa ba, kansa ya ɗan girgiza kawai yana zuwa gab da shi ya ciri ƙaramar takarda ya ɗauki pen yay gajeren rubutu. Batare da yayi magana ba kawai ya tura gabansa ya nufi barin wajen, sai kuma ya juyo yana kallonsa, cikin ɗage gira sama ya furta, “Ka rage sa ido Imran, idan nayi kewar laifi ne?”.     Imran yayi dariya da faɗin, “A'a bakai laifi ba MAZAJEN FAMA, maza jeka ka ɗabbaƙa sunna abinka”. “ALLAH ya shiryeka”. Cewar Zak-Shadow. Imran ya amsa da amin yana ɗaukar takardar ya fara dubawa.         _“Bana son kowa yasan na fita, kamar yanda na faɗa maka 2 days ne, Kar abar ƙofar yamma a buɗe, dan haɗarinta yafi na sauran ƙofofi ka sani. Imran idonka ya zama sosai akan yaran nan da dukkan Captains ɗin kowanne sansani, sannan duk motsin da bai muku ba na sani, komai ƙanƙantarsa._      Takardar Imran ya ajiye ya juya yana kallonsa da faɗin, “Babu damuwa in sha ALLAHU. Amma dan ALLAH ka biya ka sayo min kilishi da gyaɗa. Zan sa a kawo maka saƙo daga gida ka taho min da shi..”       Wani kallo ya ɗago ya zuba masa, Imran daya san ma'anar kallon sai ya kwashe da dariya. “Maida wuƙar, ba ɗan aike zan maidaka ba ai ALLAH nace”.        A karo na farko Zak-Shadow ya ɗan saki wani murmushi gefen baki yana ɗauke kansa da ɗan girgizawa. Shima Imran ɗin murmushin sa ƙara faɗaɗa yayi. Yana matuƙar son aminin nasa, kamar yanda kowa yasan shima Zak-Shadow na sonsa matuƙar so ma kuwa. Dan shi mutum ne mai ra'ayin riƙau, idan baya yinka, baya yinka kawai. Idan ya soka kuma, to da gaske son naka yake. Mutum ne tsayyaye akan ra'ayi, kuma ɗan kai tsaye, baya iya kawaici akan duk abinda bazaiyi ba kuma baya buƙata. Idan har yace maka (eh) to ‘eh’ ɗin ce koda za'a kashesa, idan kuma yace (a'a) tofa ‘a'a’ ɗin ce. Zak-Shadow yasha baƙar wahala a lokacin da suke yaran soji saboda wannan taurin kan nasa a hannun manyansu. Dan a shekararsu ta biyu da fara aiki har zaman prison na sojoji yayi na wata shida saboda wata tirjiya da yayi akan umarnin wani ogansu. An azabtar da shi matuƙar azabtarwa a lokacin, dan bayan ya fito ma mutane da yawa sunyi zaton bazai sake rayuwa mai tsaho ba, amma da yake rayuwa ta UBANGIJI ce sai gashi ya miƙe, miƙewar data zama sanadin jajircewarsa a yanzu. Dan azabar da suka bashi sai ta zama kamar sun sake busar masa da zuciya ne ta yanda bai jin shakkar tunkarar kowane irin haɗari na rayuwa, daga nan kuma nasarorinsa suka fara bayyana har zuwa matakin da yake a yau.          Shi Dodo ne a idon wanda bai san ainahin halinsa ba, saboda a kallon fuska kai tsaye zaka kirashi mugu ne. Baida fara'a, bai san wasa ba koda da aboki ne. Duk wanda kaga yace maka yaga yana dariya lallai ya kai ai masa barka. Yana magana idan yaso, idan kuma bai so ba zaku iya kwashe awanni tare koma sama da haka bakinsa bai furta komai ba na hira sai dai kaji yana karatun Alqur'ani. Dan kuwa yana da addini sosai, hakama ilimin addinin. Tabbas da ace bai zama soja ba sai dai a kirashi malami, a yana sojan ma yana koyar da sojoji ilimin addini, kuma yana musu majalisi, sannan yana cigaba da neman nashi ilimin shi kansa.       Sai dai sirrin da mutane basu sani a kansa ba sai shi amininsa da mahaifiyarsa shine haƙuri. Zak-Shadow mutum ne mai haƙuri kwarai da gaske. Sannan mutum ne mai adalci da son tsayawa akan gaskiya komai ɗacinta. Yana da tausayi matuƙa musamman akan mata da yara. Zai iya saida rayuwarsa akan su. Sannan yana da kishin addini da yankinsa. Dan shi kai tsaye ma zai ce maka yana fara jin kishin yankinsa ne kafin ƙasa gaba ɗaya....         “Ka dinga tunani kamar wani mace”.     Buɗaɗɗiyar muryarsa ta dawo da Imran daga doguwar tafiyar tunanin da yayi. Cikin ɗan sauke numfashi yace, “Ai tunaninka nake yi”.        “Rashin aikin yi ne yay maka yawa da har zaka zauna tunani na halan?”.     Cewar Zak-Shadow yana ficewa a tantin. Tashi Imran yay yabi bayansa. Kamar ɗazun yaran sojin suka shiga kamewa da sake nutsuwa waje guda. Yanzu kam sunfi ɗazun yawa. Da alama wasu dama suna a cikin tantunan ne shiyyasa. Inda yake zaman yin alwala ya nufa, hakan ya tabbatar musu lokacin la'asar yayi, ruwa aka kawo masa shi da Imran, suma suka shiga haramar yin tasu musulman ciki kenan. Wanda ba musulman ba kuma suka amshi duty ɗin zagaye wajan. Koda suka idar da sallar shi da Imran sansanin suka bari gaba ɗaya, sun jima kafin can su dawo suna hirarsu. Wajen wani ɗan bukkan kara dake gefe suka nufa, koda ya buɗe buhun da akayi labule a bukkar wasu irin garƙama-garƙaman karnuka ne marasa ƙyawun gani, sai dai kallo ɗaya kai musu dole ne hankalinka ya tashi, dan babu tantama waɗan nan idan suka kama mutum sai kufan jinin jikinsa amma ko ƙashi bazasu bari ba, dan marabarsu da zakuna ƙalilanne. Aiko suna ganinsa suka fara zallo da haushi kamar wanda suke gaishe shi.     A mamaki na sai naga ya ɗaga musu hannu yana faɗin, “Good Afternoon my Boys”.        Wani haushin suka ƙara yi a tare kamar masu amsa masa. Imran yay dariya da faɗin, “Kama yaran nan naka training mai wahalar gaske. Idan suna wani abun sai ka rantse mutane ne”.      Ƙaramin Murmushi Zak-Shadow yayi da ɗan taɓe baki. Idan yayi murmushi ƙyau yake masa, maybe shiyyasa baya son yi. Sun jima a wajen karnukan sannan suka fito, lokacin duhun magriba yayi. Yanzu kam sojoji ne sosai a camp ɗin, gaba ɗaya sun fito daga tantunansu, ashe a ɗazun wasu basa wajen shiyyasa, wasu kuma na barci, dan maimakon barcin dare su na rana sukeyi saboda tsaro. Tunda Imran da Zak-Shadow suka fito gaba ɗaya wajen yay tsitt kamar an musu tsawa, kowa ya nutsu. Kallo ya bisu da shi kaf ɗinsu, a ƙalla sun kai su ɗari, dan wasu basa a cikin sansanin a yanzu suna kan aiki a cikin jejin tako wace kusurwa. Wanda ke nan tare da shi bazasu wuce ɗari ba. Wucesu yay ya zauna kan dutsin da yake zaman yin alwala akoda yaushe, ai da sauri wani ya kawo masa ruwa dan in dai kaga ya zauna a wajen alwala zai yi. Daga nan kowa ne ya fara ƙoƙarin yin alwalar, sai wanda ba musulmai ba suka sake amsar dutyn zama garkuwa a yanzu ma kamar dai ɗazun. Sanin yau zai bar jejin kuma baya son su fahimta sai ya ce yanzu ma Imran ya jasu salla. Hakan baisa sun zargi wani abu ba suma, dan yana yin hakan a kowane lokaci, ba oga Imran ba har a cikinsu yaran masu addinin kan jasu salla, duk da dai duk wanda ke a ƙarƙashin Zak-Shadow duk iskancinka da sakacinka ga ibada wlhy sai ya saita maka haukan kanka. Dan in har kana cikin tawagarsa bakai ba wasa da salla, ba kai ba shaye-shaye koda na sigari ne kawai, bakai ba zama da jahilci dole ka cigaba da neman ilimin addini, shiyyasa ma ya saka musu ranakun karatu, bashi kuma kaɗai bane malamin harda wasu a cikin yaran masu ilimi na koyarwa suma, sai dai in ana kan matsannacin yaƙi ne. Hakan yasa Alhamdullah hatta wanda ba musulmai ba a cikinsu zaka gansu a nutse. Dan in ma kace zaka bijire kayi jikinka ne zai gaya maka a hannunsa..      Bayan sunyi sallar magriba Imran yay musu nasiha kamar yanda suka saba, har zuwa lokacin isha'i. Bayan an idar kowa ya miƙe suka kasu group-group dan kowa da abokansa da kuma abokan maganarsa suka kunna wuta suna hira, wasu na cin abinci. A lokacin ne Zak-Shadow ya sulale ya bar jejin, barin da da yasan sakamakon da zai so da shi da bazai yi ba. Dan kuwa tabbas wannan barin shine mafarin wata babbar ƙaddara da alkalami ya jima da rubutata a cikin rayuwarsa tun yana cikin Ummiensa.........✍🏼    *_Wace ƙaddara ce wannan? Mizai faru? Mike shirin faruwa ne da Zak-Shadow 😭. Ya labarin mace mai ciki kuma? Wace rawa zata taka mana a wannan labarin?. Amsar ku na cikin labarin KIƊA A RUWA MAI MAGANIN DODO. Kada ku bari a baku labari. Dan ni kaina Bilyn ku labarin nan tsumani yake yi💃💃💃._* _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 Fcfa)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 4_ *_Free page_* _______________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃. __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ____________________ .........Gaba ɗaya hankalin yaran sojojin ya raja'a akan taɗi da jin ɗumin wutar da suka kunna. Amma shi yana gefe a saman wata bishiya ko tsoron dare baya ji balle wasu halittu daka iya fakewa a bishiyar koma aljanu. Shi ɗin ɗaya ne daga cikin amintattun yaran Zak-Shadow, dan haka duk wani motsinsa na yau da kullum zuwa yanzu ya haddace shi. Yakan fahimci yaren idanu daga Zak-Shadow, ya kan fahimci na gangar jiki harna ɗabi'a. Tun lokacin daya kai masa dawar daya zubama tsuntsaye ya fahimci akwai damuwa a tare da shi, dan haka ya laɓe yana nazartar shi, sai kuma akai sa'a aka kira wayarsa a lokacin, dan haka duk wayar da yayi acikin kunnensa take, duk da ba wani surutu ya zuba ba, amma da yake yana ankare da sai ya saka ma komai alamar tambaya. Sai kuma gashi da za'ayi sallar magriba yaga Major Imran Abbas ne yaja sallar, dan haka zuciyarsa ta bashi Lieutenant Colonel na shirin barin jejin kamar yanda ya saba fitar ɓadda sawu da tunanin basa fahimta. Eh tabbas basa fahimtar, dan a duk sanda suka daina ganin gilmawarsa kawai abinda zuciyarsu ke basu yana zagayen sauran sansanin ne ko meeting da sauran jagororin sansanin wato Captains, dan yakan yi hakan akai-akai. Dan kuwa runduna guda ce a ƙarƙashinsa dake rarrabe a cikin jejin da suka kai a dadin dubu ɗaya da wani abu, kuma shine Boss gaba ɗaya da suke ƙarƙashin umarninsa, Major Imran Executive Officer, sai Captains da su na ƙasa, duk da dai suma yaran hawa-hawa ne, kamar shi yana cikin Lieutenants. Akwai Sergeants na ƙasansu, akwai kuma Soldiers (rank-and-file). Tun asali tun fari shi dama ya shiga aikin soja ne badan kishin ƙasa ba, dan kamar an ƙirƙireshi ne saboda manufar da yake akai a yanzu, kafin ma ya shigo aikin an bashi horo na musamman ta yanda yake iya duk wani aikin munafunci da leƙen asiri cike da wayo, musamman akan Zak-Shadow a yanzu, kuma yana da tabbacin akwai ire-iren sa ma dan bashi ɗaya bane kuma suna tare da Zak-Shadow ɗin kusa sosai dama wasu manyan jami'ai irin Zak-Shadow ko na sama da shi harma dana ƙasa da shi batare da su sun sani ba. Koda yake kwanaki an taɓa kama ire-iren nasu aka kuma hukunta shi da hukunci mai girma, dan amanar gidan soja ta wuce tunanin mai tunani, su kansu a lokuta da dama suna wannan sheɗancin ne a tsorace, matuƙar tsoron gudun randa zata tashi musu. Amma maƙudan kuɗin da ake biyansu da shi na tunzurasu da assasa gurɓataccen tunaninsu da jagorancin shaiɗan. Balle shi dake a ƙarƙashin babban ZAKI, dan bafa a banza aka saka ma *_ZAK-SHADOW_* ɗin wannan sunan ba a gidan Soja, Zakin ne na gasken gaske da ya ciyo sunan tunma a asalin sunan yankan sa. Maybe shiyasa ma sunan ke da tasiri sosai a rayuwarsa da ɗabi'arsa. (ALLAH ya ƙara kare ku jami'anmu a duk inda kuke🙏. Kai mutane na ku ba MAZAJEN FAMA jinjinar ban girma mana💪😄, a haɗa musu da kirari na musamman kuma, ƙarshe a sara musu👍🏼). Waya ya zaro daga jikinsa, ƙarama ƙirar nokia, ya dannama wata number kira. Ba'a ɗaga ba sai da ta kusa tsinkewa. Murya ƙasa-ƙasa ya furta, “Good evening Sir!”.      Amsa masa da akai daga can ya sashi cigaba da magana cikin tsantseni da risinar da kai tamkar yana a gaban wancan ɗin.       “Sir! Yau ɗin nan ya fita. Dan sanda na kai masa dawar da yake zubama tsuntsaye bayan nabar wajen sai na laɓe, naji yana waya da matarsa kamar.....”      Sai kuma yay ɗan jimm alamar saurare. Kafin cikin yaƙini da son a yarda da shi ya cigaba da faɗin, “Tabbas na tabbatar baya jejin nan, dan yau ba shine yaja sallar magriba da isha'i ba. Na duba inda ake ajiye mashin ɗinsa kuma babu shi, na leƙa tantinsu oga Imran ne kawai a ciki, kuma in dai ba ana kan aiki ba baka raba su. Duk da haka na bincika dukkan sauran sansanin kuma an tabbatar min bai je ba”.     Sai kuma yayi shiru. Zuwa can ya sake cewa, “Yes Sir!”. Daga haka ya cire wayar a kunensa yana murmurshi, yasan yau account ɗinsa sai yayi rawar girgiza kwankwaso saboda manyan kayan da zasu shigo cikinsa akan wannan albishir ɗin. Sakkowa yay a bishiyar ya koma cikin ƴan uwansa, koda abokinsa da bai san ainahin shi munafuki bane ya tambayesa daga ina yake sai ya nuna ya zagaya ne yin uzuri, dan haka babu wanda ya kula suka cigaba da hirar su......        _____________   A can ɓangaren wanda ya kira kuwa yana yanke kiran wata number ya lalubo ya danna mata kira shima. Ana ɗagawa ko gaisuwa bai tsaya yi ba ya fara magana kai tsaye.        “Congratulations Aboki, yau dai mun samu damar da muka daɗe muna fako tun a watan jiya, dan na samu tabbacin barin yaron nan jejin yanzun nan”.     Daga can aka furta, “Woow Zak-Shadow!, damar da aka daɗe ana jira kace ta samu. Lallai yau rana ce ta musamman a garemu, dan kuwa na tabbatar zamuja kaya iya kaya akan wannan albishir. Ba damuwa yanzu zan sanar da oga kuwa ai ba zancen wasa faka-faka kawai Aboki”.        Dariya yayi irin ta nasara shima, sai kuma ya ce, “Okay hakan yayi,  amma abokina kadai tabbar babu matsala ko? Karfa mutanen nan su ci amanar mu. Bayan mun saida ƙasarmu sun sami biyan butarsu su zubar damu a banza batare da mun mori komai ba sai dukiya. Kasan fa halin ɗan Adam na wannan zamanin da wayo da iya cin amana, sannan mutanen nan a ankare suke komai nasu a tsare yake. Yaron nan yaron ƙasarmu ne na amana da kowa ke da hope a kan jarumtarsa, ba gidan soji da shugabanni kaɗai ba hatta al'ummar ƙasar nan ɗaukarsa suke kamar wani WALIYYIN SOJA”.         “Mtsoww!! Wato abokina wataran sai naji kana bani haushi. Wai miye damuwarka da batun wata ƙasa can, ƙasar data kasa gamsar da kai koda da albashin wahalar aikinka, su su minene ma kace duk basu suka so mu kasance a wannan hanyar ba, eh su suka so mana, tunda ai basai sunce muje mu aikata ba, sun gama tattare komai daga su sai ƴaƴansu da matansu dake ƙasashen waje. Muko an barmu da ɗumama kujera basir duk ya gama cinyemu”.        Dariya sosai wancan ya kwashe da ita, tare da faɗin, “Wlhy baka da dama, aiko bamace muna cikin masu ɗumama kujerar nan ba, dan mumafa tun farko karka manta munja kayan nan gwargwadon iko a gwamnati ta hanyar fakewa da ayyukan mu, kai dai a rufe rufau kawai. Ba lokaci faka-faka ka sanar dasu, kasan Yaron nan shegen kansa ne akwai wayo, komai a ankare yake yinsa”.       “Tabbas hakane. Ka bani 5minuts kawai, aikinka ya kammala a wannan gaɓar zakaji alert tare dana yaron shima”. “Okay yayi, byeee!”. Ya faɗa yana ajiye wayar fuskarsa cike da murmushi, sai dai can ƙasan zuciyarsa wani kalar luguden daka take yi. Tabbas yasan wannan halayyar tasu mummunar halayya ce kuma abar ƙyama da duk wani ɗan ƙasa na gari bazai aikata ba koda a wanne addini yake kuwa. Sun rufe jinsu da ganinsu saboda dukiya, sun manta da basu da inda yafi ƙasar a wajensu, anan aka haifi kakaninsu, haka iyayensu, suma haka, sun kuma haifi ƴaƴansu. Amma sam basa tunanin makomar ƴaƴan nasu da ƴaƴan ƴaƴansu, su dai kawai su tara kuɗi a kirasu masu dukiya. (Lallai UBANGIJI mai rufin asiri ne, dan tabbas da wani zai san wanene ai nahin kai a take zai danneka ya maka yankan rago koda da wuƙar yankan albasar gidansa ce. Amma wata hikima ta ALLAH sai kaita warkajaminka cikin al'umma ana girmamaka batare da ansan girman na riga bane kawai. Anya waɗan nan sunma kansu adalci kuwa?, summa shugabanninsu adalci da a kullum talaka ke ƙalubalanta da gazawa batare daya san ba laifinsa bane shi kaɗai, dan da yawan tsiyatakun da irinsu da ba'a tunanin zasu iya dasu ake haɗa kai ayi ba shugabannin da kullum ake kallo da zargi kawai ba. Yanzu kamar dai shi da abokinsa, ba shugabannin komai bane na siyasa, kawai ma'aikata ne a ƙasa da suka samu dama ake kuma amfani da damar tasu ake dama ƙasar saboda suna son suma su dama da kuɗaɗe. Anya kuwa bai kamata ace su zauna suma kansu faɗa ba, su tuna zuri'arsu dake rayuwa a ƙasar, dan duk iya ƙoƙarin su na su su barta ai iyaka dai su kwashe iyalansu ba wai zuri'arsu gaba ɗaya ba ko🤔? Wani lokaci irin waɗan nan sai kaga kamar kansu ya toshe. Basa tuna dukiyar a duk ma yanda ka tara sai duniyar daka nema dan ita ta maka tsirara tikk sannan ta turaka cikin ƙasa ta rufe ruf ta barka da azabar girbar abinda ka shuka. Dan UBANGIJI baya zaluntar kowa sai bawan daya zalunci kansa......) (Hummm kai dai ka sani zulwa, ni nayi nan🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️😏) >•<>•<>•<>•<>•<>•<             A ɓangaren abokinsa shima dai yana yanke kiran ya isar da nasa saƙon ne inda ya dace. Dan kuwa a cikin harkar gaba da gabanta ne. Buƙatar ganinsa da ogan nasu ya bashi ya sakashi shiga canja kayan jikinsa. Sauri-sauri ya kammala ya fice dan yana buƙatar ficewa karma matarsa ta ganshi. Aiko bata ganshi ɗin ba sai tashin motarsa taji. Cikin takaici taja tsaki, dan ita tunanin ta da manufarta daban ce kamar dai yanda kukasan mu mafi akasarin mata muke, kullum zargin baya wuce namiji na yawon banza ko huɗɗa da matan banza a waje kai tsaye idan yana fitar dare, sai dai abinda bamu sani ba wasu mazan ba hakan bane, wasu ɓarnar tasu ma tafi ta neman matan, ALLAH dai ya rufa mana asiri ya ƙara tsare mana mazajenmu. (😄👍🏼 Wannan jinjinar taku ce MAZANMU nagartattu, MAZAN ƘWARI kenan kuma MAZAN FAMA a wajenmu, ALLAH ya ƙara baku kariya da tarin ladar ƙoƙarin sauke hakkokinmu da kukeyi. ALLAH yasa mu da ku duk mu shiga aljanna. Ƴammata da zawarawa ALLAH ya baku mazaje na gari mazan fama a gidajen ku kuma. Kai a bama MAZA jinjina tare damu ma MATAN ƘWARAI RABIN ADDINI😘😘😀👍🏼❤️❤️💃)...........✍🏼                     _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 Fcfa) (VIp 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 5_ *_Last free page_* __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 ___________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .......Falo ne babban gaske, sai dai gaba ɗaya an kashe fitulun cikinsa sai wasu candles da basufi uku ba kacal aka bari suna ci, suma a cikin kwalba suke dan haka haskensu baida tasiri mai yawa sosai. Yanayin duhun wajen ya ɓoye ainahin fuskokin mutanen dake zaune a cikin falon harma da sirrin tsarinsa, koda yake fuskokinsun ma a rufe suke da facemask ta yanda koda ace akwai hasken wutar baka isa tantance su wanene ba. Cikin wani ɓoyayyen harshe suke magana, harshen da babu makamncinsa a ƙasarmu. Sai ɗan ƙarar kofuna alamar akwai abinda ake sha, sai ko room hitter dake basu ɗumi saboda yanayin sanyi da ake ciki. (Waɗan nan sune manyan munafukan shaiɗanci, kowannen su nada laƙabin suna, dan babu mai amfani da sunansa na yanka balle kasan ainahinsa a addini ko yanki balle harshen yare. Hasalima gamayyace daga ɓangarori ta waje da cikin gida).           Ɗaya daga cikinsu ne ya ajiye kofin shayin hannunsa, tare da yin gyaran murya. Lokaci ɗaya abokan zaman nashi duk suka nutsu, tare da maida dukkan hankalinsu garesa. Cikin harshen da suke maganar ya furta, “Ya kamata muyi abinda ya tara mu, dan bamu da lokaci isashshe”.        “Tabbas haka ne Black Spider. Yanzu minene a teburin mu?”.      Zama Black Spider ya gyara, tare da nutsuwa sosai ya ɗauki remote yana dannawa. Hoton Zak-Shadow ne ya bayyana a jikin ƙaton majigin daya cinye kusan rabin bango, tsayayyen jarumin soja, da ko'a hoton kasan eh da gaske Gwarzan maza ne, dan kuwa a cikin uniform ɗin aiki yake, alamu kuma sun tabbatar yana kan aiki akai masa hoton batare daya sani ba, hakan kuma bai hanashi fita da ƙyau ba kuma tartar har kwarjininsa na dukan zukatan maƙiya koda basu bayyana a fili ba. Amma yanda duk suka ja numfashi a lokaci guda zai baka tabbacin hakan.       Black Spider ya fara jawabi kamar haka, “Wannan mutumin ya lalata shirye-shiryemu a gabashi da yammaci da yawan gaske da bazasu ƙididdigu ba koda a kintace. Mun ƙyaleshi badan yafi ƙarfinmu ba, sai dan bashi dama ya gama taka irin tashi rawar kafin mu canja masa salon kiɗa. Lokacin mu ya yi a wannan gaɓar. Duk da a baya Target ɗinmu Zak-Shadow ya ci gaba da zama cikas a shirye-shiryenmu. Dabarun mu da yawa sun durƙushe a gabansa. Amma yanzu, lokacin da muke jira ya iso garemu, wato dama ta dawo hannunmu.”       Cikin wata ƴar iskar dariya Viper ya amshe zancen da murya mai taushi amma cike da shaiɗanci irin ta shaiɗanun azzalumai, “Kamar yanda Black Spider ya faɗa a yanzun nan babu jimawa mun tabbatar da bayanin sirri ta hanyar yaran Dagger. Zak-Shadow ya bar sansaninsa na tsaro domin wata tafiya ta sirri a jejin, sai dai bamu san inda ya nufa ba, amma hakan mu ba damuwarmu bace kai tsaye, duk da dolene mu sani dan aikinmu ya tafi yanda ya dace akansa. Wannan shi ne gibin da ba zai taɓa tsammani ya bari ba a gaɓar da zai fuskanci illarmu mai muni, dan zamu zuba masa dafinmu mai ƙarfi da har abada babu makarin warkewarsa a zuciyarsa”.       Dariya suka kece da ita a tare, sai kuma suka koma tsitt kowa ya nutsu. Dagger da sam bai dara ba sanda ake dariyar, sai ma danna hannunsa da yake a kan tebur da ƙarfi cike da fusata, dan shi kaɗai yasan adadi tsanar da yayma Zak-Shadow a duniyar nan, saboda shine ya kashe masa ƙaninsa a wani hari na bayanan sirri da basu san yaya akai Zak-Shadow ɗin ya bankaɗo ba a kansu. Cikin kaushin harshe ya fara faɗin, “Sirs! Nayi muku alƙawari gamu mayaƙanku ba za mu bari wannan dama ta sulale ba! Dole mu kafa tarkon da zai karya ƙarfinsa gaba ɗaya. Zan jagoranci ɓangarena da ƙyau kuma da tabbatar cikar buri fiye da baya! Dan ina son da hannuna na gurfanar da shi a ƙasan ƙafafu na cike da ƙasƙanci da wulaƙantarwa. Dolene ya ɗanɗani fiye da abinda na ɗanɗana a wancan karon, da ace zaku bani dama bashi ba kaf ahalinsa sai na shafe babinsu a doron wannan ƙasar, na kuma........”      Mr Specter ya katse shi cikin jan girma, dan kuwa dukansu Dagger matsayin yaronsu yake, matsayinsa kawai shine shugaban mayaƙansu, hakan na nufin amfani ake da shi domin cimma manufa, kawai dai ita tunkunyar sharri ba'a banbance farfesun kayan ciki a cikinta, haɗawa ake har kashin dabbar da ruwan fitsari a dafe, shiyasa suka jawo Dagger ɗin jikinsu har haka, ahakan ma abinda suke buƙatar ya sani kawai suke tattaunawa da shi, sauran sirrinsu kuwa nasu ne..        “Ya isa haka mana Dagger. Abin da ya kawo nasarar Target Zak-Shadow a wancan lokacin har zuwa yanzu ba ƙarfin bindiga bane dabarunsa ne kawai da iya salon yaƙi, dan haka muma fusatarmu ba itace zata bamu nasara ba wayonmu ne da iya taku, ƙarfin makaman mu kariya kawai sunansu. Dan haka kai da yaranka zaku raba sojojin nasa da yankunan da yake tsarewa ne farko, rarrabuwa zai zama rauni a garesu ƙwarai da gaske musamman da shi ne dama ya fisu idon hangen nesa yanzu kuma baya kusa”.        Raven dake kusa da shi ya ƙyalƙyale da dariyar mugunta , “Hakane kuma fa Mr Specter! Dagger zaku tura labari na ƙarya a gabashi cewa za a kai hari. Captains ɗinsa za su tattara sojoji su nufi can. A lokaci guda, ku kuma ku tarwatsa yammacin ƙasa da ƙarfin ƙwanjin ku da dabaru.”        “Yesss! Tsarin Raven yayi shima, Dagger ruɗanin da zaku sakasu a ciki shine zai zama nasarar mu. Lokacin da jama’a suka ga sojojin Zak-Shadow sun kasa tsare yankuna, tsoro zai cika zukatansu. Kunga abin da tsoro ya fara lalatawa, baku da buƙatar harbi mai yawa akan yaransa, dan target ɗinmu ba'a kansu bane kawai, koma muce ba'a kansu bane, akan yankunan wajen ne da shi Ogan nasu”. Cewar Iron Fang kenan yana jingina da kujera cike da jin kai da ƙasaita, dan muryar tasa ma da nauyi take fita da isa, gashi ɗan tsirit kamar kazar mayu hegen.      Miƙewa tsaye Scythe yayi yana wani watsa hannaye da ɗagasu sama kamar sabon boka, gashi ƙaton gaske ɗan taran kamar buhun geron kakana. Cikin wagegiyar muryarsa mara daɗin ji ya ce, “Duhu zai mamaye su ƙwarai da gaske, Zamu haifar da tashin hankali daga gabashi zuwa Yammaci, daga dukanin karkarar dake zagaye da jejin da su. Lokacin da saƙo zai isarma Target yay tunanin dawowa daga tafiyarsa, zai tarar da ragowar ƙungiyarsa a cikin ƙura da jini, shi kuma zai faɗa ainahin tarkonmu. Dan a dai-dai gaɓar zai ɗaura ƙawance na gaskiya da handcuffs”.        Rafff! Raf!! Rafff!!! Kake ji tafi na tashi.      Oga kwata da baice uffan ba tun fara meeting ɗin sai a yanzu ya buɗe baki cike da isa ya furta “…Babu wanda zai tsira daga wannan shiri. Duk wanda ya tsaya a kan hanyar mu dama, zai bace cikin inuwar duhunmu ne, dan haka wannan ƙalubalen naka ne Dagger, kasani idan muka rasa nasara koda ɗaya ce kaima zaka rasa kanka, dan bamu shigo wannan ƙasar taku domin rera muku waƙoƙin yabo ko tatsuniya kuyita nishaɗi ba. Mune iyayen gidanku a jiya, a yau da gobe dole ku cigaba da zama ƙarƙashin zartarwar mu dan arziƙinku shine ƙarfinmu”.         Sosai zantukan oga suka soki Dagger, ashe dai duk da yake shege akwai ɓurɓushin kishin ƙasar a can ƙasan zuciyarsa. Amma saboda kuɗi da son duniya sai ya shiga jinjina kai irin na girmamawa.       Shiru sukayi na ɗan lokaci a karo na farko gaba ɗaya, sannan Eclipse ya miƙe cike da gadarar masu jin su sune manyan shegun duniya. Kai tsaye ya furta “An gama yanke hukunci. Operation Shattershield ya fara daga wannan dare. Duk ku shirya. Lokacin da Zak-Shadow ya sulale daga jeji, mu kuma za mu sulale da mulkinsa. Dagger zaka wuce ka fara aikinka, kaida duk yaranka zakuji alert”.         A tare suka ɗora hannayensu a kan tebur ɗin tsakkiyar falon, kowanne yana kiran laƙabinsa kamar alwashin ƙaddarar nasara da suke jin ta tabbata dole (Mahaukata)  “Eclipse! Specter! Dagger! Raven! Black Spider! Scythe! Viper! Iron Fang! Ashen! muna cikin duhu, kuma duhu ne zai mamaye Target ɗinmu Zak-Shadow!”.         Hummmm!! Zakuga duhu kuwa a lahira😭, kai tun anan duniya ma zaku cigaba da zama a duhun🙄. _______________           A lokacin da masu makirci ke shirya zalunci acan , anan Mazan fama ne ke isa gida gabannin asubahi. Ƙarfe huɗu da wasu mintuna ya tsaida ƙaton mashin ɗinsa ɓaki wulik ƙatoton gaske da a kallo ɗaya zaka san ba siyen yara bane sai dai manya, dan kuwa ƙirace ta musamman, sannan yana kiransa da suna na musamm *(Black Phantom)* shi da kansa.        A ƙofar wani baƙin gate ya tsaida shi, kasancewar anguwar da akwai wuta ko'ina da haskensa, hakan ya bashi damar bin street ɗin da kallo ta cikin hular matsin ɗin da gilashin ta daya sakaya idonsa. Sai da ya gama nazartar komai yanda yake buƙata kafin ya ciro wayarsa ya daddana ya kai kunnensa, cikin buɗaɗɗiyar muryarsa da ta ɗan shaƙe alamar iskar mashin da ya sha ya furta, “Taso ka buɗe min ƙofa”. Daga haka bai jira komai ba ya sauke wayar.      Cikakken mintuna huɗu ba'ayi ba wani ɗan saurayi da bazai wuce shekaru goma sha takwas ba ya buɗe ƙofar gate ɗin, cike da girmamawa ya ce, “Sannu da zuwa Dada”.      Maimakon amsa mishi mashin ɗin ya tayar, haskashi da yay da fitilar mashin ɗin ya bayyana yanda ya sako jallabiyar jikinsa a baibai alamar sauri. Ciki ya shige, shi kuma ya maida gate ɗin ya rufe. Duk da akwai haske na security light ya haska ko'ina na gidan babu abinda zan iya ƙararwa game da gidan face ganin flat biyu jere da juna. Sai motoci biyu dake fake a gefe inda yake ƙoƙarin faka mashin ɗin nasa, da mashin roba-roba guda biyu suma. Yana ƙoƙarin sauka a mashan ɗin bayan ya kafesa matashin saurayin ya ƙaraso inda yake, sannu da zuwa ya sake masa cike da nutsuwa da girmamawa, yanzun ma bai amsa masa ba sai da ya cire hular mashin ɗin kansa ya ɗan jujjuya kan sannan ya furta, “Ya kake?”. A taƙaice.      “Alhamdullahi Dada, ya hanya?”. Saurayin ya faɗa yana amsar hular, sai kuma ya sake miƙa hannu zai amshi bag ɗin dake goye a bayansa.       “Karka damu jeka kwanta zan shiga da ita”. Ya faɗa batare daya bashi jakar ba. Shima baiyi musu ba dan tsakaninsu babu wannan. Flat ɗin hannun dama ya nufa, saurayin ya wuce wanda ke gefen haggu ɗauke da hular mashin ɗin yana binsa da kallo da ɗan murmushi. A hankali ya furta, “Dodon gidanmu ya zo, gobe zakaji gidan nan kamar anyi mutuwa kowa yayi nutsuwar dole barema ƴan iskan yaran can da suka cika mana gida”.       Shi kam da bai san ƙanin nasa na gulmarsa a zuciya ba ɗaya daga cikin keys ɗin dake tare dana mashin ɗinsa dama wasu da yawa a jiki ya saka a ƙofar sashen ya buɗe, kai tsaye ya shige tare da maida ƙofar ya rufe. Fitilar falon a kunne suke haske fayau, dan tun kan ma ya shigo daga can waje ya fahimci hakan, sai tv da itama take a kunne tanata aiki. Kansa ya ɗan girgiza tare da jan ƙaramin tsaki, sai kuma ya shiga bin falon da kallo. Babba ne ba laifi, akwai kujeru masu ƙyau kalar ruwan toka ƙirar ƙasar waje. Hakama carpet ɗin tsakkiyarsu mai ƙyau ne, sai tvn bango, falo dai na dai-dai mai wadata ba masu arnan kuɗi ba. Centre table ɗin kujerun cike yake da plates da ledojin ruwa da aka sha, sai kwalaben lemon kwalba guda huɗu wasu ma ba'a gama shanyewa ba. A yanda fuskarsa ta sake tsukewa lokaci guda zai baka tabbacin baya son ƙazanta sam. Duk da kuwa bayan kwanikan babu wani datti da falon ke da shi mai nuni da rashin gyarawa ko ƙazatar. Da yake manya su manyanne ko fitilar bai kashe ba yay gaba abinsa zuwa wata ƙofar gilashi dake tacan ƙarshen falon. Hannu yasa ya tura gefe ɗaya suka haɗe a waje guda, kai daga ganin yanda gilashin yake ƙal-ƙal kasan ana kula da tsaftarsa sosai, koda ya shiga corridor ne mai tsaho ƙaɗan da ƙofa ɗaya tal a cikinsa, yaja ƙofar gilashin ya rufe sannan ya nufi ƙofar dake tabbatar da bedroom ɗinsa ne. Ilai kuwa hakan ne, dan yana buɗeta ƙaton bedroom ya bayyana sakamakon kunna fitilar ɗakin da yay, gado ne mai ƙyau 6-by-6, sai wadrobe ɗinsa da mirror, gefe kaɗan shiryayyun kujeru ne tamkar falo harda tv suma dai irin gadon sak. Komai dake ɗakin fari ne tas, in ka cire carpet ɗin dake malale a ɗakin gaba ɗaya kalar blue, suma labulaye fafare ne. Kaida kaga ɗakin kasan ana kula da tsaftarsa akai-akai, dan duk da babu kowa cikinsa ko ina tsaff ga ƙamshi mai daɗi na tashi, sai dai gadon babu bedsheed a kansa.       Kujerun kawai ya nufa ya zube a cikin 1sitter yana mai sauke  numfashi da ɗan dafe kansa, sai kuma ya jingina bayansa da kan gaba ɗaya a jikin kujerar ya rufe idanu ruff. Yafi mintuna biyar a hakan kafin ya buɗesu ya ɗago ya fara kunce zaren takalminsa, safar ciki ma ya cire sannan ya tashi yana cire maɓallan rigarsa da fara takawa a cike da nauyin jiki irin na mai doguwar tafiya zuwa ƙofar dake tabbatar da toilet ce. Ya jima a ciki sai gashi ya fito ɗaure da towel, da wani a hannunsa yana faman goge jiki, agogo ya kalla, sai kuma ya nufi wadrobe ya ciro doguwar riga. Babu ɓata lokaci ya shirya a cikinta ya saka sallaya a ɗan lungun gadon ya kabbara salla. Da alama yana son ƙarasa abinda ya rage na daren ne da ibadar daya sabarma kansa akowane dare, dan yana a wajen har akai kiran sallar farko, sannan ya miƙe zuwa wajen mirror ɗin ɗakin ya ɗauka turare ya saka ya fice a ɗakin gaba ɗaya.         Ana idar da sallar asuba daya fita yi massalaci ko ƙannensa bai bari sun ganshi ba ya dawo gidan, sashen dai ɗazun ya shiga, komai kuma na a yanda ya barshi babu alamar wani ya tashi yin salla ma. Haka ya sake wucewarsa ɗakin ɗazun, koda ya shiga saida ya sakama ƙofar key sannan ya wuce wadrobe ya fiddo wata leda babba mai ɗauke da zanen gado, fiddoshi yay da kansa ya shinfiɗa fari tas, ya saka rigar filo ɗaya ya cire jallabiyar jikinsa ya haye gadon daga shi sai boxer ya kwanta. Sai lokacin ya kai hannu ya kashe fitilar ɗakin duhu ya mamaye ko'ina............✍🏼      Hummm masu karatu, ga Zak-Shadow anan zai sha barci. Ga maƙiya can idonsu biyu suna shirya babbar ɓarnar tarwatsa komai harda shi kansa mai gayya da aikin😭. Su waye iyalan Zak-Shadow? Minene ainahin sunan Zak-Shadow? Su waye zuri'ar Zak-Shadow?. Wacece mace mai ciki da suka haɗu da su Zak-Shadow a shekarun baya har ta kasance cikin mafarkinsa saboda nauyin amana? Yaya su Major Imran Abbas babban amini kuma ɗan uwan Zak-Shadow zasu ƙare a jeji? Shin ƙungiyar DUHU zasu samu nasara kuwa?     Rigiji gabji, abubuwan fa da yawa suke, dan wannan labarin da kuke gani cakwakiyar cikinsa ta musamman ce. Akwai ɗan karan: ƙulli, makirci, gwagwarmaya, rikici, kitumurmura, nagartaccen zumunci, jajircewar wata JARUMAR UWA, JARUMTAR MAZAJEN FAMA, tsaftatacciyar soyayya mai narka zuciya da gaɓɓai, (kai ku kanku ko kun daina soyayya sai kun dawo ruwa a wannan gaɓar😂). Nasarorin masu gaskiya da sakamakon da zasu ɗauka.. Hoho abinfa ba'a cewa komai, dan ba lallai ku gane mi nake son sanar muku ba sai kun karanta KIƊA A RUWA MAI MAGANIN DODONNI💪. Wato labarin nan ko, hummm ni kaina fa..... To bari dai nayi shiru kawai🤭. Amma ku sani takowane fanni yazo da wani irin sabon salo ne da sai ka karanta kawai zaka gane. Ba cika muku baki nake ba, in sha ALLAHU da ƙarfin ikon ALLAH zakuga tabbacin fiye da abinda na faɗa muku. Ku dai ku kasance kawai a wannan tafiyar dan ta musamman ce😉🤤☺️☺️😋😋😀👍🏼. Free pages sun ƙare, masu buƙatar wannan labari sai ku garzayo.💃💃💃💃 ☺️Mutane na kuma masoyana ƴan bati dan ALLAH bana kar aci batin nan, kun san kuda Bilyn Abdull akwai amana soyayya take muku irin ta musamman ɗin nan. To kada ku bani kunya 500 ba komai bace ba, idan ka sauke haƙƙin wahalar wani kaima ALLAH bazai bar kowa ya cutar da kasuwancinka ba. Maza kuzo ku sayi naku, kuma in sha ALLAHU kasuwancinku zai yi albarka, ba kuma zaiba ƴan bashi damar riƙe muku kuɗaɗe ba da izinin UBANGIJI. Dan wannan kuɗin kaɗan da muke rainawa na littafi sai su zame mana ƙarfen ƙafa idan bamu sani ba. Babu wani hakki da yake mai sauƙi ga bawa koda na harar wani ne. Rubutu akwai wahala, bazaku gane bane, sannan muma business mukeyi kamar yanda kuke fitowa tallata hajojinku a media, dan ALLAH mutanena a daure kar a ci batin nan babu amfani🥰🥰🥰🥰❤️👍🏼. 😀Masoya abokan tafiya akoda yaushe jinjinarku ta musamman ne👍🏼, dan kuwa kuɗin na musamman ne a wajen bilyn Abdull, babu abinda zance sai godiya da fatan ALLAH ya haɗamu a aljannarsa muyita zumunci muna farin ciki. Yanda kuke ƙoƙarin sauke nauyi kuma ALLAH ya bama wanda suka ɗauki nauyin sayen kayanku damar sauke nauyi ta hanyar biyanku, ya sakama kasuwancinku albarka da kasuwa tako ina❤️❤️❤️❤️🥰🙏.           🙄Masu sauke mana littafi a arewa. Masu saka mana Littafi a website ɗinku bada izini ba, masu kai mana littafi YouTube bada izini ba su canja masa suna. Masu sayar mana da littafi a facebook ko WhatsApp su buɗe groups ko WhatsApp Channels suna amsar kuɗaɗen mutane kuzo ku saya a wajenmu da munyi posting ku ɗauka ku tura musu ku kuma alhalin bada izninmu ba, kuji TSORON ALLAH! KUJI TSORON ALLAH!! KUJI TSORON ALLAH!!!. Ku tuna zaku biya wannan hakkin da abu mai darajane a ranar da kuɗi basu da tasiri, a lokacin da ya ƙure na neman yafiyarmu, a lokacin da aikin lada keda muhimmanci a gareku, kuke gudun ƙarin zunuban wanda kuka zalunta. Bance ku daina ba, ba kuma zan roƙeku ku daina ba, amma ku shirya da shiri mai girman gaske, domin akwai ranar DANA SANI, zata zo ko ka yarda ko baka yarda ba, ƙilama tun a nan duniya zaka fara girba daga naka sakamakon. Idan kukazo garemu zamu iya tsara yanda zaku amshi lirtatanmu cikin mutunta juna ku saka a duk inda kuke so batare da kunci hakkin kowa ba. Dan haka shawara ta ƙarshe. Masu Website, masu kai books Facebook, masu buɗe group a WhatsApp suna saidawa. Dama masu bi da shi tako wace hanya kuna da damar zuwa garemu, in ba haka ba kuma zamu cigaba da kwana kan buzu😂 muna kaima ALLAH kukanmu a kanku🥲, abinda baku sani ba kowanne irin mugunta bata hana nasara, sannan baya hana mai nema samu daga abinda UBANGIJI ya ƙaddara masa, kuna ɗorama kanku nauyi ne batare da mu kun ragemu da komai daga abinda ALLAH ya ƙaddara garemu ba, dan nasara ma kuke ƙara mana kune baku sani ba wlhy, dan ALLAH karku bari hakan ta faru. Yanda bana fatan komawa ga ALLAH da hakkin kowa, haka bana fatan kowa ya koga ga UBANGIJI da hakkina, mu zama masoya na gaskiya musulman ƙwarai kuma ƴan uwan juna masu son cigaban kansu dana ƴan uwansu. Fatan alkairi a gareku a duk inda kuke😀🥰🥰❤️❤️❤️🙏👍🏼. _______________ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 Fcfa)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 6_ _Barkanmu da dawowa filin daga. UBANGIJI ka bani ikon rubuta abinda bazai cutar da kowa ba 🙏, yanda na fara lafiya kasa mu kammala tare daku lafiya cikin aminci da kwanciyar hankali._ *_Labarin nan gaba ɗayansa ƙirƙirarrene, babu abinda yake gaskiya ko rayuwar wani, idan kaci karo da abinda ba haka yake ba ka sani ni ƴar adam ce mai kuskure, tara nake ban cika goma ba, iya abinda UBANGIJI yaso na sani kawai nake iya sani da fahimta harna kwatanta rubutashi a labari batare da sanin zahirin wani abun ba. Wanda yaci karo da rayuwarsa ta zahiri kuwa ba dakai ake ba, anyi ne don nishaɗi da faɗakarwa kawai irin ta marubuci, bamma sanki ko sanka ba_*. *_Ƴan bati azo a saya 500 kunfi karfinta mutane na kada ku bani kunya dan ALLAH bayan na gama yabonku salla ku kasa alwala😂._* __________________ *_NACE ina kuke ne?!!. Al'ummar Gombawa nake magana 💃 fulanin asali ke nan 😘._* *Shin kuna da labarin cewa kuma nesa ta matso kusa gare ku?* _Maza kuzo ku sha labari da ɗumi-ɗuminsa, domin kuma fa NAKUN ya buɗe muku gidan gyara da ƙalƙale jikin mata ƴan kwalisa a kusa da ku gabb._ *_Idan kunji ana kiran maida tsohuwa yarinya to wannan katafaren shagon ne na👇_* *ALIYU HAIDAR COSMETICS PLAZA* _ADDRESS SHOP D80 WOMAN LINE GOMBE MAIN MARKET_ *_Zaku same mu a wannan numbers ɗin kamar haka👇_* *07068210505* *09133081313* _DEALER IN all kind of skin care products such as:_ moisturizer Sun screen Face Toner Eye cream Face serum Face wash Face scrub Face cream Face marsk Body lotion Body cream Shower gel Body scrub Tube Body oil Body spray Perfume Hair crm Hair spray and many more *_Harma da abinda bamu lissafo ba anan. Ku dai kawai karku bari a yi babu ku. Domin kayanmu garanti ne kuma dahir ne 💃_* *_Ku duba status ɗina yanzun nan ni bilyn Abdull zakuga kaɗan daga cikinsu in sha ALLAHU 💃😘😘😘_* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ TUSHIYA MAFARIN DAWA       >>>>>1940s<<<<<       Abdul-rasheed Shehu Isa ɗan asalin jihar Bauchi ne, an haifesa cikin anguwar Kobi. Mahaifinsu malam Shehu baban hadimi ne a masarautar Bauchi ƙarƙashin mulkin Sarkin Bauchi Alhaji Yakubun Bauchi. Amintaccen hadimi ne kwarai da gaske, dan yana kusa da sarki saboda mutum ne mai aminci da gaskiya da amana. Gashi dai talaka amma akwai dattako da dattijantaka irin ta mutanen kirki. Matan Malam Shehu biyu ne, yaransa kuwa tara cif. Matarsa ta farko nada yara biyar, uku maza biyu mata. Yaran na kiranta da suna Inna. Matarsa ta biyu nada yara huɗu, biyu mata, biyu maza. Yara na kiranta da Iya. Malam Shehu nada sha'awar yaransa maza suyi karatun boko, sai dai kasancewar sa talaka da yanda tsarin karatu yake a lokacin sai ƴaƴan sarakuna yasa bai fidda burin nasa a fili ba. Amma kullum yaga ƴaƴan sarki zasu makaranta sai ya tsaya yayta kallonsu yana murmushi abinsa da jera musu addu'ar nasara.       Yau da gobe sai mai-martaba ya fahimci kamar Malam Shehu nada sha'awar hakan, dan haka ya tuntuɓesa. Babu ko musu Malam Shehu ya amsa da zumuɗinsa. Abun ya burge sarki a lokacin, domin kuwa da yawan talakawa babu abinda sukafi ƙyama kamar batun bokon a wannan lokaci. Saboda kowa na tsoron a ɓata masa al'adar iyalinsa da addininsa. Cike da zumuɗi Malam Shehu ya nufi gida, ya tara yaransa da matansa biyu ya gaya musu ƙudirinsa da albishir ɗin da Sarki ya masa. Ya kuma tabbatar musu zai kai yaransa manya duka uku a sakasu boko. Wato ƴaƴan Inna kenan uwargida. Amma sai su yaran suka saka masa kuka dan basu da sha'awar hakan. Hakama mahaifiyarsu Inna ta nuna bata so, dan kuka ta saka masa ita bata so akai mata ƴaƴa su koyi kafirci, lallashin duniya da bayanin gamsuwa Malam Shehu yama Inna amma taƙi saurarensa bare ta fahimceshi. Har takai ransa ya ɓaci ma ya fita ya bar musu gidan.         Abdul-rasheed yana cikin yaran tsakkiya, dan a wajen mahaifinsu shine na uku, a ɗakinsu kuwa shine na fari da Iya ta haifa. Yana da ƙanne uku, mata biyu a tsakkiya sai autansu.  Ɓacin ran da Malam Shehu ya nuna ya dami Iya, duk da kuwa bai ambaci Abdul-rasheed a cikin wanda zai saka makaranta ba, tasan kuma saboda yana ganin shekarunsa basu kai bane. Dan a lokacin shekarar Abdul-rasheed 5 ne kawai. Haka ta yini tana saƙe-saƙe, sai dai batace da kowa komai ba har washe gari Malam Shehu ya dawo ɗakinta. (Ranar kwananta kenan).        Bata tada zancen ba ko a ranar sai dare, bayan ta bashi abinci yaci ya gode ALLAH ta kwashe akushin daga gabansa sannan ta dawo ta zauna gefensa cike da ladabi. Da yake lokacin ɗari ne kowa ya shige ɗakinsa, baka jin motsin kowa sam. Cikin nutsuwa da girmamawa tace, “Malam niko in zaka bani dama ina da shawara”.       Kallonta yayi da dukkan hankalinsa, kafin ya amsa mata da, “Ina jinki Halimatu, wace shawara ce? Kuma akan minene?”.         Iya ta ƙara duƙar da kai irin na girmamawa. “Malam akan maganar jiyane na batun makaranta. Naga ranka ya ɓaci daga kai har Yaya. Dan ALLAH kayi haƙuri ka fahimceta, kasan batun bokon nan yana bama kowa tsoro, ba kuma kowa ke fahimta ba kai tsaye. Amma tunda kana so, kuma kaji ka gamsu da saka ƴaƴanka, mizai hana kafin Yaya ta sakko itama ta fahimta ka ɗauki shi wannan yaron (haka take kiran Abdul-rasheed saboda karar kasancewarsa ɗan fari) ka saka kawai. Daga baya itama nasan idan ta fahimta zata bari a saka su Bilyaminu ɗin”.      Shiru Malam Shehu yay cike da nazarin maganar Iya. Kafin ya nisa tare da sakin murmushi irin nasu na manya. “Nagode sosai Halimatu, ALLAH yayi miki albarka. Tabbas naji daɗi matuƙa akan wannan shawara taki. Duk da da farko ina duba ƙanƙantar Abdul-rasheed ne shiyyasa ban sakashi a lissafi ba, dama sai gaba nake son kaishi shi bayan su sun fara. To amma maganarki sai ta min daɗi, kuma ya bani mafita dan dama a cikin tunanin yanda zan fuskanci mai martaba nake akan hakan. Kinga yanzu dai kawai na kai Abdul-rasheed a sakashi, su kuma tunda basa so bazan matsa musu ba, su cigaba da karatunsu na mahammadiya da noma. ALLAH ya sanya musu albarka gaba ɗayansu”.        “Amin malam. Idan hakan kayi ma dai-dai ne. Amma zuwa nan gaba ɗin dai suma a sake tuntuɓarsu ko zasu canja shawara bayan sunga shi wannan yaron ɗin ya fara”.     Bai musa mata ba akan hakan. Washe gari cike da farin ciki ya kama hannun Abdul-rasheed suka nufi gidan sarki. Wannan shine mafarin fara karatun bokon Abdul-rasheed. A lokacin yana da shekara 5 a duniya, dan an haifesa a 1947 ne. A shekara ta 1953 aka saka shi a makarantar Bauchi Native Authority Primary School (wacce daga baya ta zama Kobi Primary School). Kuma Alhamdullahi sai ya kasance shima yana son karatun kuma yana maida hankali. Malama Shehu yaji matuƙar farin cikin ganin Abdul-rasheed yana da himma akan karatun, dan haka ya ƙara tsayawa a kansa sosai. Ba'a boko Abdul-rasheed ya tsaya kawai ba, har ilimin addinin ma yana ƙoƙari akai dan suna zuwa malarantar allo kamar sauran yan uwansa, saɓanin ƴan uwan nasa da sunfi maida hankali dai akan ƴan abubuwansu na yara na yau da kullum, sai kuma makarantar allo da suma suna zuwa kamar shi.        Makarantar tana kusa da ƙofar gidan sarki, cikin unguwar da ke cike da yara masu sanya riga doguwa da rawani ƙarami, wasu kuma ke tafe da allo. Malamai suna koyar da aji da harshen Hausa a farko, amma daga baya aka fara musu harshen turanci a matsayin harshen karatu. Ya koyi rubutu da karatu, ya kuma fara sha’awar duniyar da ta wuce yankinsu. A kwana a tashi ba wuya wajen UBANGIJI. Abdul-rasheed ya kammala primary ɗinsa aji shida (Standard 6) a 1959, yana ɗauke da babban burin samun ilimin da zai sa ya taimaka wa garinsu. A Shekarar 1960 ta kawo masa sabon babi. An tafi da shi Zaria tare da sauran ƴaƴan manyan Arewa, inda ya shiga Government College Zaria (Barewa College), makarantar da aka san ta fi kowace a Arewa. Ya tafi yana kuka Iya nayi. Yayinda Inna ke dariyar ƙeta ita da ƴan uwansa, a ganinsu dai ya saka kansa a wani bala'i ne shi da uwarsa. Amma ita Iya addu'a tabishi da shi kawai, sai kewar rashinsa a kusa da ita matsayinsa na babba dake taimaka mata da aike da abubuwa na yau da kullum dake tsakanin uwa da ɗa. Zama a boarding school ya koya masa nisa da iyaye da wahalar rabuwa da gida. Ya saba da rana da safiya da bugun ƙaho, shiga aji da sautin turanci daga bakin malamai na Ingila, da kuma yin motsa jiki da yamma a filin kwallo. A can ne ya haɗu da wasu ƙananan jaruman Arewa, waɗanda daga baya za su iya zama manyan shugabanni idan UBANGIJI ya ƙaddara hakan a littafinsu. Tun a zuwa hutunsa na farko ƴan uwansa suka fara hango canji a tare da rayuwarsa, sai dai hakan baisa sunji suna son yin karatun boko ba, hasalima babban su ana shirin masa aure ne wato Bilyaminu. Shekaru sun miƙa a rayuwar karatu ta Abdul-rasheed, yana zuwa hutu a duk lokacin da aka basu, yayi kwanaki ya koma cike da kewar gida da ƴan uwansa da iyaye. A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI sai gashi ya kammala a 1966, yana da shaidar Cambridge School Certificate, wadda aka fi darajawa sosai a lokacin. Ya dawo gida Bauchi cike da farin ciki da nasarori, nasarorin da suka saka iyayensa a farin ciki mara misalin kwatance. Abdul-rasheed ya kammala Secondary school cike da nasarori da suka sake faranta ran mahaifinsa, dan haka ya sake tsaya masa akan cigaba da karatun nasa. Bayan kai kawo da taimakon wani malamin su na Boarding ya samu gurbin shiga jami'a a Kano. A wannan gaɓar ma dai kowa ya bishi da addu'a musamman mahaifinsa da mahaifiyarsa. Yayinda sauran ƴan uwansa ke masa dariya da kallonsa a matsayin wahalalle mara aikin yi, hakama Inna mahaifiyarsu kallon abin ta dinga yi kamar wani rashin aikin yi ne, sai dai duk habaicin da take da dariya iya bata kulata ba. Haka akai masa shiri ya taho Kano karatu a shekara ta 1967, ya shiga Ahmadu Bello College a Kano, wanda daga baya aka fi sani da Abdullahi Bayero College, har ya zama Bayero University Kano (BUK) a cikin 1975. Yana karantar History and Political Science, yana ƙara fahimtar tarihin mulkin mallaka da rawar da Arewa ke ciki a Nigeria data samu nasarar ƴanci kai a 1962. Cikin makaranta yake zaune, dan basu da kowa da suka sani na dangi a cikin Kano ɗin sam, hasali ma a cikin gidansu kaf babu wanda ya taɓa zuwa garin Kano sai shi yau da ALLAH ya kawo matsayin ɗalibin ilimi. Zaman Kano ya buɗe masa ido, ya kuma sake koya masa iya zama da mutane, ya kuma haɗashi da abokai na ƙwarai na amana... Rayuwar Abdul-rasheed a Kano wata irin rayuwa ce mai cike da ƙalubale da darasin rayuwa. Domin kuwa ba karatu kawai ya maida hankali ayi ba harda koyon ɗinki. Ya fara koyon ɗinki ne a dalilin abokinsa Nasiru. Wanda suka haɗu acikin makarantar department ɗinsu ɗaya. Da farko dai babu wata abota a tsakaninsu sai gaisuwa, sai da Abdul-rasheed ya fahimci Nasiru ƙuru ne dan akwai fahimtar karatu sai dai bashi da hayaniya sam sannan suka fara abota, dan kuwa Abdul-rasheed bashi da girman kai, duk abinda bai iya ba idan ya fahimci wanda ya iya koda mace ce sai ya nema taimakon a nuna masa, ta haka ne ya samu kusanci da Nasiru, a hankali suka zama abokai dan shima dai rashin girman kan Abdul-rasheed ɗin ya burge Nasiru sosai. Kamar wasa ya jashi suka je gidansu wani weekend, dan kuwa Nasiru ɗan garin Kano ne a anguwar ƙofar mata. A ƙofar gidan su Nasiru kuwa akwai shago da ake ɗinki kasancewar a bakin titi suke kusa da kasuwa, shagon kuma na yayansa ne. Tunda Abdul-rasheed ya ƙyalla ido yaga shagon sai abin ya bashi sha'awa, baiyi ƙauron baki ba da suka shiga gaida yayan Nasiru yay ta yaba abin, shi ko Yayan Nasiru yaji daɗi ya kuma fahimci kamar Abdul-rasheed na son harkar, sai yay masa tayi. Babu musu yace aiko yana son koyar kuma ya gode. Daga haka suka saita zai dinga zuwa duk weekend koyon ɗinki...........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 7_ _Amin afuwa wlhy gaba ɗaya banda nutsuwa ne an mana haihu bana yini a gida, jiya ma shaf na manta da batun posting ALLAH 😂. Kuyi haƙuri ayi suna gobe idan ALLAH ya kaimu sai na dawo gaba ɗaya hankali kwance, ga pages babu nutsuwar editing. Ina ƙara neman afuwa😀🙏._ __________________ *_NACE ina kuke ne?!!. Al'ummar Gombawa nake magana 💃 fulanin asali ke nan 😘._* *Shin kuna da labarin cewa kuma nesa ta matso kusa gare ku?* _Maza kuzo ku sha labari da ɗumi-ɗuminsa, domin kuma fa NAKUN ya buɗe muku gidan gyara da ƙalƙale jikin mata ƴan kwalisa a kusa da ku gabb._ *_Idan kunji ana kiran maida tsohuwa yarinya to wannan katafaren shagon ne na👇_* *ALIYU HAIDAR COSMETICS PLAZA* _ADDRESS SHOP D80 WOMAN LINE GOMBE MAIN MARKET_ *_Zaku same mu a wannan numbers ɗin kamar haka👇_* *07068210505* *09133081313* _DEALER IN all kind of skin care products such as:_ moisturizer Sun screen Face Toner Eye cream Face serum Face wash Face scrub Face cream Face marsk Body lotion Body cream Shower gel Body scrub Tube Body oil Body spray Perfume Hair crm Hair spray and many more *_Harma da abinda bamu lissafo ba anan. Ku dai kawai karku bari a yi babu ku. Domin kayanmu garanti ne kuma dahir ne 💃_* Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/HCLn6awOrmP5WJmO9jPrgK?mode=ems_wa_t __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Haka kuwa akayi, kamar wasa Abdul-rasheed ya fara zuwa koyon ɗinki, kasancewar yana son abun dan danan sai ga sakamako ya fara bayyana. Baya gajiya duk asabar da Lahadi sai yazo. Da Nasiru yaga yana wahala da kashe kuɗaɗensa ga ɗan makaranta komai nasa a ƙa'ide yake, ga nisa Abdul-rasheed yana jimawa baije gida Bauchi ba sai yace mizai hana duk juma'a ya dinga biyoshi sai Monday su dinga shiga makaranta tare, ya dinga weekend dai a gidansu. Da farko Abdul-rasheed yaso turjewa, sai da Nasiru ya nuna masa fushinsa sannan ya amince amma yana ɗar-ɗar dai, duk da kuwa kowa ya sanshi a gidan su Nasiru zuwa yanzu, kuma suna nuna masa so da kulawa. Amma shi dai baya son takura musu, yana kuma tsoron kar mahaifinsa yay faɗan barinsa makaranta harna kwana uku a kowane mako batare da saninsu ba. Tun dai yana ɗari-ɗari har ya saki jikinsa.          Tun a farko fara koyon ɗinkin Abdul-rasheed akwai wata yarinya a maƙwaftan su Nasiru da kullum takan wuce da safe da allo zata makaranta. Takan gaishesu idan zata wuce, hakama idan ta dawo da takan gaishesu ta shige gida. Shi dai bai taɓa tambayar sunanta ba, bai kuma taɓa magana da ita ba bayan gaisuwar nan da take musu a tare. Sai dai a kwana a tashi har ya haddace muryarta mai cike da nutsuwa da rashin hayaniya.         Ranar wata Lahadi da yamma yana a shagon shi kaɗai yana ɗinki ogansa Yaya Zubair yaje sayen kayan ɗinki zazzaƙar muryar yarinyar nan ta ratsa kunnensa. Ɗagowa yay da sauri tare da take keke ya tsayar daga takun da yake masa. Tana tsaye daga wajen shagon ta rissina ta gaisheshi kanta a ƙasa. Amsa mata yay da kulawa, kafin ya furta, “Kina son wani abu ne ƙanwata?”.      Kanta a ƙasa ta ce, “Eh Yaya, dama kayan ɗinki na kawo ma Yaya Zubairu, naga kuma baya nan ma kamar”.      Cike da zolaya ya ce, “Oh dan Yaya Zubairu baya nan kin fasa ɗinkin?”.      Da sauri ta ce, “A'a zan baka ka ajiye masa daman”.      Murmushi yayi a karo na farko, ya ce, “To shike nan”. Yay maganar yana tasowa yazo bakin ƙofar dan ita tana daga waje har yanzu. Miƙa masa ledar tayi kanta a ƙasa. Karo na farko a rayuwarsa ya zubama hannunta ido. Fara ce sol, hannunta da ƙunshin jan lalli da yay mata shegen ƙyau. Harga ALLAH sai da gabansa ya faɗi, mazantakar ta motsa amma sai ya kauda kansa kawai ya amsa yana ɗan murmushi da duba kayan ledar. Yadi ne irin nasu na maza. Ɗagowa yay ya sake ɗan kallonta. “A ajiye kawai kenan zaki dawo ki masa bayani?”.        “A'a basai na dawo ba. Ɗinkin Bashir da Tasi'u ne daman. Inna tace dan ALLAH idan bata takura masa ba zuwa jibi a ɗinka. Dan zamuyi tafiya ne biki”.       “In sha ALLAHU za'a ɗinka, nima zan ɗinka musu da kaina. Idan kin shiga ki turo min su yanzu naga girmansu a daren nan zan yishi dan da safe zan wuce makaranta”.      Godiya tai masa cike da girmamawa, sannan ya wuce kanta a ƙasa. Samun kansa yay da binta da kallo. Doguwa ce sosai masha ALLAH, shekarunta bazasu wuce 14 ba, tana da ɗan jiki, hakan ya nuna ne kuwa sakamakon kayan dake jikinta, zani da riga t-shirt sai kallabi disko, Tayi ɗammara da gyale a ƙugunta, kasa ɗauke idonsa yay harta shige gidansu, a mamakinsa ya ɗan juya zai koma yana sauke ajiyar zuciyar da tazo masa a bazata kamar ance sake waigawa sai ya ganta tana leƙensa. Wuff ta shige kamar walƙiya kuwa, tana turo ƙyauren zauren gidansu na katako burum. Ɗan tsai yay yana kallon ƙofar kamar mai tunani, sai kuma yay murmushi ya juya ya koma cikin shagon.       Yana zama su Tasi'u ƙannenta sukai sallama. Yara ne matasa da bazasu wuce 9/7years ba. Sun gaishesa da girmamawa, ya amsa musu da kulawa yana musu murmushi. Dan sun sanshi ya sansu tunda yanzu ya zama ɗan anguwar duk da kwana 3 kawai yake a duk sati. Amma sauƙin kansa da son kula yara yasa duk suka sanshi. A karo na farko a rayuwarsa ya tambaye su miye sunan yayarsu?. Caraf Bashir dake matsayin ƙarami ya ce, “Indo”.         Samun kansa yay da faɗin, “Masha ALLAH A'ishatu kenan. Wace makarantar kuke zuwa?”.       Yanzu kam Tasi'u ne ya ce, “Muna zuwa makarantar Malam Sallau. Yaya Indo nada ƙoƙari sosai, dan duk wata tana wanke allon ta sau biyu, yanzu haka tana izu kusan ashirin.          “Kai kai kuce dai yayarku Malama ce kawai?”.     Wannan kalma ta saka Bashir da Tasi'u tsuge masa da surutu akan yayarsu Indo. Abu kamar wasa hirar yaran ta dinga masa tasiri a zuciya, yana tare da su har akai kiran magriba, shi ya jasu suka je massalaci.  An idar da salla sun dawo sai ga Indo tana nemansu. Karo na farko da Abdul-rasheed ya samu kansa da yima Indo kallon ƙurulla sosai. Ƙyaƙyƙyawar yarinya mai cikar zatin fuska da hasken fata. Suna haɗa ido tai saurin juyawa zata shige gida. Amma sai ya dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta.        “A'ishah!”.    Cak ta tsaya amma ta kasa juyowa, dan haka ya ƙarasa inda take riƙe da hannun su Bashir. Sai da ya ɗan ƙara kallon fuskarta sannan ya furta, “Amin afuwa nine na riƙesu a shago suna tayani taɗi, Inna ma ki bata haƙuri”.      Batare data ɗago ba ta jinjina masa kai tana kama hannunsu suka shige. Yanzu ma sai ta juyo da tunanin yabar wajan zata saci kallonsa suka haɗa ido. Da sauri ta shige. Murmushi yayi yana girgiza kansa ya koma shago yana yaba halittar UBANGIJI a ransa, dan tabbas A'isha kyakkyawar yarinya ce kam. Kyawunta a bayyane yake ga mai kallonta kuma.     ★Tun daga wannan rana al'amarin Indo ya fara saƙar zare a zuciyar Abdul-rasheed, har takai Nasiru ya fara harbo jirginsa. Haka ma Yaya Zubairu ya fara fahimta halin da Abdul-rasheed yake ciki akan Indo da yanda itama in zata wuce yanzu takan saci kallon cikin shagon bakamar da da zata wuce kanta a ƙasa ba koda zata gaishesu. Ƙannent kuwa koda yaushe suna manne da Abdul-rasheed, tun mahaifiyarsu na jin sunansa a labarinsu ko idan ya saya musu abu irin na yara sun kai gida har dai ranar ta nema sanin wanene shi, dan bai kamata ta saki jiki da wannan shaƙuwa dake tsakaninsa da yaranta ba batare da tasan wanene shi da halayyarsa ba. Yaranta marayu ne mahaifinsu ya rasu shekara biyu data wuce. Kasancewar sun gaya mata a shagon Yaya Zubairu yake yasa ta nema Zubairu kai tsaye, aiko yay mata bayani na gamsuwa har ma ya ɗora da batun Indo daya shin-shino. Inna mace ce ba mai damuwa ba, sai kawai tai fatan alkairi cikin al'amarin.       Nasiru da Yaya Zubairu sune suka fito fili suka fara kwaɗaitawa Abdul-rasheed batun karfa yayi sake akan Indo in dai sonta yake da gaske, idan ko ya tsaya kallon ruwa lallai kwaɗo zai iya masa ƙafa. Tun yana dojewa har shima dai ya fahimci gaskiya suke faɗa masa, dan haka ya fito fili ya nema shawarar Nasiru akan ta ina ya kamata ya fara ne?. Tsaf Nasiru ya tsara masa komai kuwa. Dan haka a cikin satin suka je ga Inna domin basu damar fara zuwa hira.       Sosai Inna tayi farin ciki da hakan, domin ta fahimci wasu ƙyawawan halayya daga Abdul-rasheed ɗin a sanin data fara masa na watanni, taji kuma hankalinta ya kwanta da shi akan ƴarta Hadiza. Sannan yanda Abdul-rasheed ya gaya mata komai daya shafesa babu wani ɓoye-ɓoye nan ma taji daɗi. Ta tabbatar musu ita dai uwa ce, kuma taji ta gamsu da shi, amma suje ga ƙanin mahaifin su Indo matsayinsa na namiji shima. Suma sun gamsu da shawarar tata, sunyi godiya sosai kuma.         A wajen ƙanin mahaifin Indo ma dai bata canja zani ba, dan shima dai a anguwar yake basu ma da nisa da su, yasan Abdul-rasheed ɗin fiye ma da sanin da Inna tai masa matsayinta na mace. Bai wani jasu da nisa ba shima ya basu damar da suke buƙata tare da addu'a da fatan alkairi. Wannan shine sanadin fara tarayyar A'isha da Abdul-rasheed. Duk da tarayya ce mai tsafta da mutunta juna cikin ƙanƙanin lokaci shaƙuwa ta shiga tsakaninsu. Yana zuwa hira wajenta duk ranar juma'a da yamma idan ya shigo anguwar, dan kuwa ranar take da lokacin hutun makaranta. A cikin soron gidansu suke zama kuma. Wani lokacin da Nasiru, wani lokacin shi kaɗai, ita kuma tana tare da rakkiyar ƙaninta Bashir. Dan haka hirar take kasancewa mai tsafta sosai a ciki da nagarta, wani lokacin ma ɓigewa suke da ƙarin karatun islamiyya. Dan tunda ta fahimci yana da sani sosai akan ilimin addini duk wani tambaya ko neman sani takan rubuta da ajami ta bashi ko tayi da baki. A haka Abdul-rasheed yaje gida wani hutu, tafiyar da yaje ya yi ta ya dawo zuciya babu daɗi dan kuwa ALLAH yay ma mahaifiyarsu Iya rasuwa. Yaje ya sameta cikin jiyya ashe ta daɗe a hakan batare daya sani ba, kwanansa huɗu a daren juma'a ALLAH ya amshi abarsa. Yayi kuka sosai dan yana son mahaifiyarsu matuƙa, mace ce mai abubuwan mamaki sosai, sannan mahaifiya ce abar alfaharin kowane ɗa na kwarai.       Tana da sati uku da rasuwa hutunsu ya ƙare, haka ya tattaro ya dawo zuciya babu daɗi, sai dai nasihar mahaifinsu ta ɗan ƙarfafa shi. Amma ransa fal yake da tausayin ƙannensa uku daya tsallako ya baro. Duk da A'isha bata san mahaifiyarsa ba daya gaya mata tasha kuka, ta mata addu'a kuma sosai hakama duk wani wanda suke huɗɗa ta arziƙi ya masa gaisuwa da ban haƙuri. Yaso a zuwan da yay gida hutu yayma iyayensa batun A'isha da alaƙarsu da damar daya samu daga iyayenta, sai dai kuma ALLAH bai ƙaddara ba rasuwa ta gitta, dan haka ya haƙura har sai nan gaba kuma idan ALLAH ya bashi ikon komawa wani hutun...........✍🏼       _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 8_ __________________ *_NACE ina kuke ne?!!. Al'ummar Gombawa nake magana 💃 fulanin asali ke nan 😘._* *Shin kuna da labarin cewa kuma nesa ta matso kusa gare ku?* _Maza kuzo ku sha labari da ɗumi-ɗuminsa, domin kuma fa NAKUN ya buɗe muku gidan gyara da ƙalƙale jikin mata ƴan kwalisa a kusa da ku gabb._ *_Idan kunji ana kiran maida tsohuwa yarinya to wannan katafaren shagon ne na👇_* *ALIYU HAIDAR COSMETICS PLAZA* _ADDRESS SHOP D80 WOMAN LINE GOMBE MAIN MARKET_ *_Zaku same mu a wannan numbers ɗin kamar haka👇_* *07068210505* *09133081313* _DEALER IN all kind of skin care products such as:_ moisturizer Sun screen Face Toner Eye cream Face serum Face wash Face scrub Face cream Face marsk Body lotion Body cream Shower gel Body scrub Tube Body oil Body spray Perfume Hair crm Hair spray and many more *_Harma da abinda bamu lissafo ba anan. Ku dai kawai karku bari a yi babu ku. Domin kayanmu garanti ne kuma dahir ne 💃_* Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/HCLn6awOrmP5WJmO9jPrgK?mode=ems_wa_t __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ......... Abdul-rasheed ya cigaba da karatunsa, yana kuma koyon ɗinki da zuwa yanzu ma zamu ce ya iya tunda yana yi ya samu taronsa da kwabo, yana iya ɗinka kowane ɗinki da hannu da kuma yi da keken ɗinki, tsakaninsa da A'isha kuwa sai Alhamdullah, dan zuwa yanzu mutane da yawa a layin sun san alaƙar tasu. Har ma takai ana kiransa da suna Abdul-rasheed ɗin A'isha, dan ko baka ganesa ba da ance maka haka kuwa zaka gane shi ake nufi. Sun sake samun hutu yay shirin zuwa gida Bauchi, zuwan daya samu rakkiyar Nasiru abokinsa, shima zaije yaga tushen Abdul-rasheed a wannan karon yay sati guda sai ya dawo. Hutun nashi kuwa ya haɗa da bikin ƴan uwansa mata biyu da suke uba ɗaya da za'ayi, da ƙanwarsa ɗaya da suke ɗaki ɗaya, sai ɗaya namiji da suke uba ɗaya shima. Hakanne ma yasa Nasirun zai bishi.          Nasiru ya samu tarba ta mutuntawa a wajen mahaifin Abdul-rasheed dama ƙannensa, dan sun san sunanshi a bakin Abdul-rasheed. Kai hatta da abokan Abdul-rasheed tunna ƙuruciya dake anguwar kowa iya ƙoƙarin sa yake na ganin ya ƙyautatama Nasiru.         Yanda gidan ya cika da mutane da dangi sai Abdul-rasheed ya samu kanshi da share hawaye, ga dai dangin mahaifiyarsu cike taf da gida amma ita babu ita a wannan duniyar. Asalin mahaifiyarsa ƴar Maiduguri ce, dan haka danginta duk daga can suka zo, ƙanwar tasa ma da zatai aure can za'a kaita auren zuminci ne. Bayan ɗaura aurarrakin maza suka fara shirin wucewa, dan sai zuwa gobe matan zasu tafi da amarya itama. Abdul-rasheed yana cikinsu yana godiya akan ƙoƙarin su duk da shima goben da shi za'aima ƙanwarsa rakkiya Maidugurin. Cike da kulawa wani dattijo da suke kira Baba Kalla ya dubi Abdul-rasheed ɗin tare da faɗin, “Kaima kuwa kaga da zaka zo cikinmu ai sai ka ɗauki mata. Hakan zai ƙara dawwamar da hankalinmu a kanku muma batare da mun shagaltu akan yin wani abu babu ku ba. Kasan dai shaiɗan ba rago bane, yanzu yanda babu mahaifiyar nan taku a raye sai gaka muna shagaltuwa da yin sakaci akan lamarinku, balle ma gashi ba gari ɗaya ba. Amma kaga idan ka aura a cikinmu, kamar yanda shima Gana ya auri Khadijah ai kaga koda yaushe babu batun manta juna. Dan lokacin rasuwar mahaifiyarku shima kamar wasa mukai irin wannan zaman da shi ikon ALLAH ashe ma suna tare da ita tuni. Bazamu so ku zauna a ware a cikinmu ba dan mahaifiyarku sanda tana raye mai ƙoƙarin bibiyar al'amarin dangi ce da don ƙyautata musu a kowane motsinta.”       Karaf wani a ciki yace, “Ai Baba bama sai an kaita da nisa ba, dan da zasu dai-daita da Yakura ni dai al'amarin su na min kamanni, itama yarinya ce mai sanyin hali da nutsuwa kamar shi. Gashi tana kama da mahaifiyarsu kamar ita ta haife ta. Abdul-rasheed ka fara gwadawa ka gani akan Yakura duk da nasan itama dai bazata ƙika ba.”      Tunfa da aka fara maganar nan gaban Abdul-rasheed sai faman faɗuwa yake da dukan uku-uku, dan haka yay shiru na tsawon lokaci har sai da mahaifinsa dake wajen yana lure da yanayinsa ya kira yi sunansa. Ɗan firgigit ya kallesa, sai kuma ya amsa kiran da yay masan. Baba ya zuba masa ido na sakanni, kafin ya furta, “Bakaji abinda ake gaya maka bane?”.       Ajiyar zuciya mai nauyi Abdul-rasheed ya sauke, kafin ya ce, “Baba duk naji”.         “Shine kuma kai shiru Abdul-rasheed. Sufa shawara suka baka bawai sunce dole bane. Kuma tun a ɗazun nima suka sameni da batun amma nace su maimaita a gabanka saboda gudun halin ɗan yau dana sani”.         “Kayi haƙuri Baba, ni mai karɓa ne ga dukkanin umarnin ku. Kawai dama......”      Yayi shiru ya kasa ci-gaba. “Dama mi? Kayi magana mana. Dare keyi su suna son su ɗauki hanya ne ka sani”.       Yawu Abdul-rasheed ya sake haɗiyewa, ya muskuta zamansa kansa a ƙasa. “Baba dama akwai zancen wata yarinya ne da muka haɗu acan Kano kusan shekara ɗaya da rabi kenan, tun wancan zuwan naso samunka da batun sai rasuwar Inna ta gitta. Amma zan haƙura da batunta ɗin kawai. Sai dai damuwata ta yanda zan ma iyayenta bayani ne bayan su kuma sun riga sun bani yarda da aminci. Ban fara neman ta ba kuma sai da naje garesu suka amince min. Wannan ne kawai damuwata amma ba ƙin karɓar umarnin ku ba”.       Sosai zauren yay shiru. Baba ya zubama Abdul-rasheed ido kawai kamar mai nazari. Baba Kalla ne ya katse shirun da faɗin, “Tabbas maganarka abar a kalleta ne Abdul-rasheed, kuma bazamu saka ka zama ƙaramin mutum ba tunda har magana ta gitta haka. Zamu baka goyon baya kuma idan har ta kasance irin yarinyar da muke maka fata. ALLAH yasa haka shi yafi alkairi.”      Gaba ɗaya aka amsa da amin. Daga haka kuwa babu wanda ya sake motsa wannan zance har akai biki aka tashi lafiya. Koda yaje Maiduguri shi da Nasiru ma babu wanda yay masa maganar. Yaga kuma Yakura da akai masa magana a kanta. Itama dai yarinya ce ƙarama kamar Ai'sha, ko muce ma A'isha ta girmeta dan ita bazata ma wuce 12 ba da wasu watanni. Kwanansu biyu suka dawo, Nasiru ya koma Kano da shatara ta arziƙi daga dangin Abdul-rasheed, sai wasiƙa daya bashi ya kaima A'isha da kayan biki aba Inna da Gwaggon su Nasiru da Babansu da Yaya Zubairu suma.        Abdul-rasheed ya cigaba da shan hutunsa daya rage harna sati biyu kafin ya fara shirin komawa Kano. Ana gobe zai wuce bayan sallar isha'i baba yasa aka kirashi. Dama dai yana da shirin zuwa wajensa, yana jira ne ya gama cin abinci, sai kuma ga kiranshi. Daga tsugunne ya gaishe da Baba, ya amsa masa yana masa nunin ya zauna. Inda ya nuna masan ya zauna.       “Gobe ne tafiya ko?”.   “Eh Baba in sha ALLAHU”. “To ALLAH ya taimaka, ya kuma bada sa'a, sai a ƙara dagewa da karatu, bani da haufi akan ka Abdul-rasheed, sannan na yarda da tarbiyyar dana baku ku dukanku. A kowane motsina kuma ina bin ku da addu'a ne musamman kai dake nesa da ni a yanzu. Dan duk sauran ƴan uwanka ina tare da su idan ka cire Hadiza da aure ya ɗauke min yanzu itama. Nasa an min bincike akan batun yarinyar dakai magana....”         Karo na farko Abdul-rasheed ya ɗago a firgice yana kallon Baba. Cike da rawar murya yace, “Baba A'isha!?”.        Murmushi Baba yayi kaɗan shima yana kallonsa, sai Abdul-rasheed yay saurin yin ƙasa da kansa.     “Kwarai kuwa A'ishatu Abdul-rasheed, dan na fahimci kana sonta sosai. Shiyyasa banyi ƙasa a gwiwa ba na tada ɗan aike takanas yayo min bincike. Kuma Alhamdullah dukkan abinda ka faɗa min shi aka dawo aka sanar min babu ƙarya a ciki. Harma da wanda baka sani ba game da halayyar mahaifinta da mahaifiyarta da ita kanta. Abdul-rasheed na amince ka auri A'isha. ALLAH ya sanya albarka a cikin tarayyarku. Idan kaje sai ka sanar musu nan da sabon wata idan yayi kwana biyu iyayenka zasuzo garesu. Babanka Kalla zaizo su haɗu da iyayenku na nan su Nuhu sai suje, tunda karatunka saura shekara ɗaya kaga sai a tsaida magana kawai su tabbatar da gaske muke ko”.      Sosai wani irin farin ciki mai girma ya baibaiye rayuwa da zuciyar Abdul-rasheed, sai dai kunya ta hanashi bayyanawa, murmushi dai yake ta faman yi haƙoransa a buɗe. A zuciyarsa kuwa ji yake kamar ya tashi yayta rawa dan daɗi. Baba ne ya katse masa murmushin da faɗin, “Sai dai ina da wata shawara a gareka guda ɗaya”.       Cikin nutsuwarsa ya koma sosai. Ya ce, “To Baba”.     “A kan maganar da su Babanku Kalla sukayi ranar auren ƴan uwanka. Mizai hana ka auri itama tasun ka haɗa biyu tunda namiji na mata huɗu ne. Koba komai ka sake samun kusanci da ƴan uwan mahaifiyarku, ka kuma samu abinda kake so. Yarinyar da suke faɗa yarinya ce nutsatstsiya sosai, dan kasan da ita akai jiyyar mahaifiyarku gaba ɗaya da uwarta. Nidai a ɗan zaman da tayi na kusan watanni biyar damu banga wani abin ashsha a tare da ita ba sam. Ga yarinyar kasan itama mahaifinta ya rasu tun tana ƙarama, inda uwar ke aure yanzu sam mijin bashi da halin kwarai, nuna mata yake kullum ya gaji da yarinyar bayan kuma kafin ya aureta yay alƙawarin riƙeta shiyyasa ma su Kallan suka barta taje da ita. Kaga idan akai hakan itama an taimaketa ai ko? Amma shawara ce dai kamar yanda na faɗa maka ba tilastawa ko umarni ba. Dan ko ƴaƴana mata bazan ma auren dole ba balle ku maza. Kaje kayi tunani ka yanke hukunci da kanka. Duk kuma wanda ka zaɓa ni mai goya maka bayane a ciki”.      Daga haka Baba yay masa doguwar addu'a tare da ɗaukar kuɗi ya bashi. Amma sai yaƙi amsa, ya sanar masa yanzu ɗinkin da yake yi na kawo masa kuɗin amfani harma dana asusu da yake yi. Ko gudunmawar daya bama ƴan uwansa ta aure duk da kuɗin ɗinkin ne. Baba ya ƙara jin daɗi sosai, ya ƙara saka masa albarka. Ya bashi kuɗin kuma yace yaje dai dasu, dan wannan hakkine a kansa. Dole badan Abdul-rasheed yaso ba ya amsa yay godiya tare da addu'a sosai shima. Washe gari ya ɗauki kuma hanyar Kanon dabo, mai mata mai mota, mai dala da gwauron ɗutse, garin da ba Kano ba dajin ALLAH, hankaka maida ɗan wani naka, duk wanda ya shigo ƙasar kanon mu ya zama namu, jalla babbar Hausa yaro ko dami kazo an fika. ★Alhamdullahi Abdul-rasheed dai ya dawo Kano, ya kuma isar da saƙon Baba ga mahaifin su Nasiru, shi kuma ya samu Inna da kawun A'isha da maganar. Sunyi farin ciki sosai dan har zuci suke son Abdul-rasheed. Kamar yanda kuma baba yasa akai masa bincike akansu suma batare da sun sani ba sun aika har garin Bauchi an yi musu bincike akan Abdul-rasheed da ahalinsa. Kuma Alhamdullahi suma basu sami wani abin ashsha ko aibu ba sai nagarta. Ba iyayen A'isha kawai ba, hatta itama A'isha tayi farin ciki sosai, dan tunda ya gaya mata take ta faman murmushi tana ɓoye fuska..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 9_ __________________ *_Kowace mace na matuƙar son taga ta gyara kitchen ɗinta kodan ta kalla itama taji daɗi 💃_* *_Dunƙule kuɗin ki saya ne ke miki wahala hajiyata?_* *_Ko tarasu a hannunki ke baki wahala saboda kokin fara sai ki kasa ki kashe?_* *_To kwantar min da hankalinka ƙawata, IMZEED VENTURE ta gama shirya miki komai ta yanda kema zaki mallaki naki cikin sauƙi da rahusa._* _Ta buɗe adashin gata wanda yafi bashi kwanciyar hankali da daɗi, akan farashi mai sauƙi, kaya ƴan zamani, gasu ingattatu. Za'a kai miki a duk inda kike. Kedai naki kawai yin zubi akan lokaci._💃💃 https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Ahalin Abdul-rasheed sun cika alƙawari, dan kuwa a karo na farko suka iso garin Kano biyu ga sabon wata kamar yanda suka faɗa. Abdul-rasheed da kansa yaje tasha ya taho dasu. Ya fara kaisu makarantar su sannan suka nufo Ƙofar mata anguwar su Nasiru. A gidan su Nasirun suka fara yada zango. Bayan anyi gaisuwa da godiya bisa ga ɗawainiyar ahalin Nasiru. Suma sunyi godiya da hidimar da akai da Nasiru da yaje. Daga haka sukaci suka sha sannan mahaifin Nasiru ya shiga cikinsu aka wuce gidan kawun A'isha. Acan akai komai cike da mutunta juna da karamci. Abinka da mutanen da, ba alfahari babu fariyya babu ƙyale-ƙyale mara amfani, an bada kuɗin da hatsi har buhu uku na nagani ina so dana gaisuwar iyaye, a take akai baiko. Da za'a rabu an rabu cike da dattako da godiya ma juna. Nasiru da Abdul-rasheed suka rakasu tasha suka wuce. Dan sunce bazasu kwana a Kano ba. Abinka kuma da duniya na kwance ba'a tsoron komai..       Akwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI. Karatun Abdul-rasheed nata miƙawa, an kuma sake kawo kuɗi na biyu gidan su A'isha, tare da kayan sa rana. Huhun goro, farar alewa, sai cakuleti, sai cingam bazuka, sai alewa daima. Sai kuma tabarma karauni guda biyar, sai katifa da botikin ƙarfe da butar ƙarfe, sai zanin gado da barguna guda huɗu rigis abinsu. Kayan sarana dai sambarka dan duk wanda ya gani yasan dangin Abdul-rasheed sunyi ƙoƙari. Dan haka aka saka ranar aure watanni huɗu.           ____________        Bayan wucewar baƙi dangin Abdul-rasheed iyayen A'isha ɓangaren dangin uwa dana uba suka baje kayan sa rana aka raba. Aka bama Inna nata da danginta, dangin mahaifinta suka ɗauki nasu. Sosai A'isha take a cikin farin ciki, sai dai wani ɓangare kuma jikinta duk yayi sanyi. Ko lokacin da ƙanwar Inna da suke kira Inna Haule tai kiranta akan ta faɗi suwa zata zaɓa matsayin ƙawaye da baranya akai musu kayan saka ranar kasa magana tayi, daga ƙarshe akace taje abinta ta sanar ma da Bashir ko Tasi'u su suzo su faɗa. Haka kuwa akayi, ta gayama Tasi'u ƙawayenta biyu da take son ɗauka matsayin babbar ƙawa Lantana da Jummai, sai baranya kuma, dan haka aka ƙulla kayan sa rana aka kai gidajen iyayensu kamar yanda ake ta rabo gidan sauran dangi da abokai da makwafta.        A kwana a tashi ba wuya wajen UBANGIJI, kwanakin aurensa da A'isha nata gabatowa. Domin kuwa sai anyi bikinsu da watanni bakwai ma zai kammala karatunsa. Gabatowar abubuwa dole ya shirya yaje gida Bauchi. Dan ya samu saƙon wasiƙa daga drivern da ake yo masa aiken kayan abinci. Baba ne kuma ya rubuto ta da Ajami.         ٱلسَّلَامُ عَلَيْكُمْ إِنَا فَاتَن كَانَا فِي قُشِي لَافِيَّا عَبْدُ الرَّشِيدْ. يَا كَرَاتُنْكُو يَا جَمَاعَار دَا كَكَيْ تَرَّة سُو. تَوْ دَنْ ٱللَّهْ دُكْ أَغَايْدَا مِنْ دَا كُوَا. إِنْ بَا زَنْ تَابَا مَاكَا كَرَاتُو بَا كَيْي قُوكَارِي أَ سَاتِينْ سَمَا كَازُو غِيدَا كُونَا كْوَنَا بِي يَنْ سَا كَا كُوْمَا. دَنْ إِنَا سُون مُي يِ مَاجَنْغَا، كَاغَا كُوْمَا نِي بَا إِي يَا زُو كَانُونْ نَنْ تَاكُو زَنْ بَا إِنَا فَمَا دَا شِكَرُونَا. نَا بَرْكَا لَافِيَّا. دَاغَا مَهَافِفِنْكُو. شَيْخُ إِيسَا كُوبِي بَوَتْشِي.      Assalamu alaikum. Ina fatan kana cikin ƙoshin lafiya Abdul-rasheed. Ya karatunka ya jama'ar da kake tare da su. To dan ALLAH duk a gaida min da kowa.        Idan ba zan taɓa maka karatu ba kayi ƙoƙari a satin sama kazo gida kona kwana biyu ne sai ka koma. Dan ina son muyi magana, kaga kuma ni ba iya zuwa Kanon nan taku zan ba ina fama da shekaruna.        Na barka lafiya. Daga Mahaifinka. Shehu Isa Kobi Bauchi. Abdul-rasheed na gama karanta wannan wasiƙa baiyi ƙasa a gwiwa ba sati na zagayowa yayima garinsa na Baushi tsinke tare da asusunsa daya jima yana tarin kuɗin ɗinki a ciki. Sosai kuwa Baba ya nuna jin daɗinsa da zuwan nan. Dan a matse yake da son ganinsa. Bayan ya huta sun taɓa hira da Inna da ƙannensa ya fita gidajen yayunsa duk suka gaisa da matansu da su suma. Daga nan ya leƙa abokansa, sai bayan sallar isha'i ya dawo kasancewar yasan zuwa lokacin Baba ya shigo gida cin abinci. Hakan kuwa akayi, ya sameshi zaune a ƙofar ɗakinsa kan tabarmar karauni yana cin abincinsa a akushinsa. Sannu yay masa ya nema waje ya zauna, bai ƙara magana ba har sai da Baba ya kammala ya fuskanceshi dan kansa. Sun tattauna sosai akan batun bikinsa dake tunkarowa nan da wata ɗaya, sai batun gida da aka gina masa kamar sauran ƴan uwansa anan jikin gidansu, gini ne dai irin na wannan zamanin, wato ginin laka (ƙasa) kamar yanda aka sani ga talaka, an shafeshi da farar ƙasa ƴar aliya daga cikin ɗakunan, a waje an yarfa abin gwanin ƙyau. Abdul-rasheed yayi godiya sosai ga mahaifinsa harda hawaye, yay masa addu'ar tsahon rai da lafiya mai ɗorewa. Bayan ya lafa Baba ya ɗora masa da batun kayan lefe da dangin mahaifiyarsu suka kawo daga Maiduguri. Akwatin ƙarfe ne da irin na mutan da guda ɗaya ƙaton gaske, akwai kaya a ciki wato atamfofi irin na mutanen da sai takalma da kayan shafa kamar dai yanda ake haɗa lefe a wancan zamani. Baba ya sake da nuna masa kwalla guda biyu daga wajensa shima kuma kayan lefen ne dai a ciki, kamar yanda yayma sauran ƴan uwansa shima yayi masa tunda na dangin mahaifiyarsa daban nashi daban matsayin uba. Rasama tacewa Abdul-rasheed yayi sai hawaye kawai yake sharewa da godiya. Daga ƙarshe ya ɗakko asusun nan gaba ɗaya ya dire a gaban Baba.        Baba ya ɗan zubama asusu ido sannan ya kalli Abdul-rasheed a nutse. “Wannan asusun fa Abdul-rasheed?”.      “Baba kuɗaɗen da nake tarawa ne na ɗinki a ciki daman”.     “Masha ALLAH, ALLAH yayi maka albarka, amma ai naka ne, miyyasa zaka kawo min nan?”.             “Baba naka ne, kai amfani da shi domin rage nauyin abubuwa sun maka yawa. Nasan dai bazasuyi maka komai ba, amma dai za'a rage wani abu”.     Murmushi Baba yayi a karo na farko, ya sake saka masa albarka sannan ya ɗauki asusun ya miƙa mishi. “Abdul-rasheed bazanƙi amsar ƙyauta daga hannunku ba. Domin hakan ba nufin jinƙai da neman albarka. Kuma hakan da kai min ya sakani jin daɗi ƙwarai da gaske. ALLAH yayi maka albarka da sauran ƴan uwanka duka. Amma kaje da asusun nan ka cigaba da tara abinda kake samu, bayan ka kammala karatunka ka dawo gida akwai abinda zamuyi da kuɗin ni da kai. Dan haka ka cigaba da ajiye min su a hannunka kaji”.         Batare da Abdul-rasheed yay tunanin komai ba ya ce, “To Baba. In sha ALLAHU yanda kace haka za'ayi”. Daga haka suka cigaba da hira har lokacin barci.. >>>>>>>•<<<<<<<            Kwanakin Abdul-rasheed biyu ya dawo Kano makaranta, bai shiga anguwar su A'isha ba sai da sati ya zagayo kamar yanda ya saba. Sai dai suna tare da Nasiru a makaranta kullum. Shi ya bama tsaraba ma da ƙanwarsa ta bada a kawoma A'isha ya kai mata shi kuma sai ƙarshen sati ya shiga suka gaisa..          Rayuwa ta cigaba da tafiya bikin Abdul-rasheed da A'isha nata ƙara matsowa, ana shirye-shirye shi kuma hankalinsa nakan jarabawar da suka fara, wadda bai kammalata ba kuwa sai ana saura kwana huɗu ɗaurin aure. Zuwa lokacin gidan su A'isha ya gama cika da danginsu na nesa, har ma am sakata a lalle a safiyar yau ko muce da hantsi, wato an saka mata turare irin na al'ada matsayin kamu. Wannan yasa shima Abdul-rasheed bai ganta ba, dan a wannan zamani idan aka saka amarya a lalle keda ango kuma sai a ɗakin aurenku. Sam Abdul-rasheed bai so haka ba, dan tunda ya fara jarabawar nan basa wani samun zama da A'isha, zai iya cewa rabonsa da ita ma tun mako uku da suka wuce randa sukai hira harda Nasiru suka bata kuɗin ƙarshen zance da ake bama budurwa sule na gugar sule har sule biyar cif. To gashi kuma yau da yake son ganinta bamai yiwuwa bane, dole ya haƙura ya kama hanyar Bauchi tare da Nasiru ɗan amanarsa. Sai ana gobe ɗaurin aure zasu dawo Kano su sake komawa tare da amarya.          Koda su Abdul-rasheed suka isa Bauchi a can ma sai ya tadda gidansu taf da dangin mahaifiyarsa dana Baba, kai har ma da dangin Inna duk da ta kasance kishiyar uwa. Tuni an baje buhu-buhu na masara dana gero anata faman daka domin samar da garin tuwo harma dana MASA ƳAR BAUCHI, sai fura dama sauran nau'in abinci irin na wannan ƙarni da su shinkafa. Sun sami tarba ta farin ciki, inda abokan wasa dake dakon isowar ango dama suka lulluɓeshi aka fara zazzage masa kwalaben turare masu ƙamshi irin su ɗan duwala ana guɗa, hakan kuwa na nufin shima an saka shi a lalle kamar amarya. *_KANO_*     A nan Kano ma dai ɓangaren amarya bari muɗan dawo baya kaɗan miji a yanda aka sakata a lalle da yanda suke shagalinsu da ƙawayenta. Zamuce amarya da ƙawayenta sun fara shagali tun a ranar data kasance saura kwanaki bakwai ɗaurin aure. Amma an sakata a lalle ana saura kwana uku. Ranar litinin Inna Zainabu ta bata umarnin tsefe kanta kamar yanda yake a al'ada, da taimakon ƙawarta Jummala ta samu ta tsefe shi. Daga haka suka cigaba da sabgarsu. Washe garin ranar laraba da mutanen Bauchi suka iso da lefen A'ishatu a washe garin randa su Abdul-rasheed suka tafi kenan, akwatin ƙarfe da kwalla biyu sai tabarmi karauni guda huɗu. Gidan ya cika sosai da maƙwafta, bayan an cika baƙi da shatara ta arziƙi na abinci, anyi gaisuwa irin ta mutunta juna, dama gidan su Nasiru suka sauka, dan haka suna kammala bada lefe suka koma can abinsu, kasancewar nisa dama su huɗu ne kawai suka kawo kayan, zasu zauna kuma har a ɗaura aure sannan. Masha ALLAHU kaya sai sambarka. Dan kuwa dai amarya tayi goshi. Atamfofi ne nagartattu irinsu mai tabarma, mai barewa, akwai oni-ƴasu, sai joji da ƴalle gwaggwaro, sai t-shirt masu ƙyau, sai sufa gwaldin, sufa shadda, akori-kura, kai kaya dai sai sambarka. Kayan kwalliya da sabulai suma dai tsaf, sai turaren alwalar uwar ɗiya ƙatuwar kwalba sosai, sai ƴarduwala, miski da sauran irin yan feshi. Sai kuma gyale da su takalma kaya dai rigijib-jib komai ka taɓa akwai irin na wannan zamanin..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 10_ __________________ *_NACE ina kuke ne?!!. Al'ummar Gombawa nake magana 💃 fulanin asali ke nan 😘._* *Shin kuna da labarin cewa kuma nesa ta matso kusa gare ku?* _Maza kuzo ku sha labari da ɗumi-ɗuminsa, domin kuma fa NAKUN ya buɗe muku gidan gyara da ƙalƙale jikin mata ƴan kwalisa a kusa da ku gabb._ *_Idan kunji ana kiran maida tsohuwa yarinya to wannan katafaren shagon ne na👇_* *ALIYU HAIDAR COSMETICS PLAZA* _ADDRESS SHOP D80 WOMAN LINE GOMBE MAIN MARKET_ *_Zaku same mu a wannan numbers ɗin kamar haka👇_* *07068210505* *09133081313* _DEALER IN all kind of skin care products such as:_ moisturizer Sun screen Face Toner Eye cream Face serum Face wash Face scrub Face cream Face marsk Body lotion Body cream Shower gel Body scrub Tube Body oil Body spray Perfume Hair crm Hair spray and many more *_Harma da abinda bamu lissafo ba anan. Ku dai kawai karku bari a yi babu ku. Domin kayanmu garanti ne kuma dahir ne 💃_* Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/HCLn6awOrmP5WJmO9jPrgK?mode=ems_wa_t __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Bayan ƴan ganin lefe sun kammala kowa ya wuce an adana kaya ma sannan A'isha ta dawo daga maɓoyarta. Ganin yanda aka ɓata gidan ta ɗauka tsintsiya ta hau shara kamar yanda ta saba, tana tsaka da sharar tsakar gida duk da baƙi sun fara cika gidan nasu ƴan biki matar yayansu ɗan ƙanin babansu ta shigo gidan. Cike da shammata ta shiga zazzage mata turare a jiki tana guɗa.       Wani irin sakin tsitsiyar A'isha tayi a ƙasa, sai kuma ta fashe da kuka tana mai durƙaushewa a wajen. Kuka take sosai mai ban tausayi, har sai da akazo aka ɗagata a wajen. Abokan wasa kuwa sun samu nayi, sai binta suke da guɗa. An cire mata ƴan kunnenta da tsakiyarta ta wuya (Abin wuya, kamar sarƙa dai a yanzu). Hakama kayan jikinta ta cire an kawo mata tsohon zani da riga ta saka. Wannan alama itace amarya ta shiga lalle kenan, dan kuwa zuwa bayan sallar magriba wadda take matsayin Alwanka ɗinta tazo gidan, ƙawayenta dama tunda akai kamun sun cika gida abinsu domin zaman lalle ya fara kenan. Bayan gaishe-gaishe aka ɗakko ma alwanka tabarmin tirgeza guda uku ta kwashi amarya da ƙawayenta suka tafi gidanta. Da yake itama anan anguwar take da ƙafa suka taka abinsu. An zauna an ɗan taɓa hira kowa ya nema makwancinsa, makwancin kuwa wannan tabarmi ne da alwanka ta amso na turgeza (😂mutane na miye Turgeza? A amsa a comment akwai ƙyauta🤣, sannan miye Alwanka ma? Tambaya biyu kenan😂🙏). Biyu ƙawayenta suka kwanta, ɗaya aka bata ita kaɗai. Washe gari da safe aka dama musu koko aka sayo ƙosai aka basu sukai kari da shi. Daga haka suka koma ƙarƙashin bishiyar ceɗiya dake gidan suka zauna suna hirarsu, sai dai amarya daka ganta duk tayi sukuku, lokaci-lokaci ma takan share hawaye abinta.      A ɓangaren Alwanka kuwa ta tanadi lallenta na ƙunshi har kwano ɗaya da rabi ta kwaɓa tunda safe na TURGEZA kenan, zuwa goma ta bama ƙawayen amarya lalle da zunguru sai ledoji su ƙunsa mata. Tsaf ƙawayen amarya suka ƙunsheta kuwa da ƙunshi na tsohuwa ta faɗa kwata (🤣ina fatan kun san ƙunshin dai?), hakama a hannunta sannan aka saka mata zunguru a ciki (Miye zunguru?😂 Wanda ya faɗa akwai ƙyauta shima🤣🙏).     Bayan an gama sakama amarya lalle ƙawayen amarya suka fice zuwa gidan su Nasiru, dan kuwa ance duk abinda ake badawa na gidan anguna suje can su amsa. Bayan gaida Innar su Nasiru da baƙin Bauchi da suka samu a gidan aka danƙa musu shinkafa da manyan zakaru har huɗu, sai kayan miya da kayan magi da iccen girki da man gyaɗa, sai kuɗi wannan sune kayan kamu. Koda suka dawo gidan alwanka ɗanta Ibro ne ya yanka musu kajin, su kuma suka shiga hidimar girki amma dai Alwanka na duba musu da nuna musu yanda duk ya dace ace sunyi. Amarya kuwa na zaune da ƙunshinta har lokacin abinta. Zuwa azahar aka kammala abinci, shinkafa da miya da naman kaji zuɗu-zuɗu, mai kuwa. A ƙyallan har kana iya ganin fuskarka a ciki fes. Umarnin cire ƙunshi Alwanka ta bama amarya, dan haka ƙawayenta suka fara taimaka mata tai zaman cirewa kamar abin arziƙi, gefe kuwa manyan ƙawayen amarya sun shimfiɗa tabarma a tsakar gida, wanda suka taimaka mata ta cire ƙunshi suna gamawa ta miƙe da nufin barin wajen kawai taji an rufu a kanta, cak suka ɗagata sai kan tabarmar nan da aka shimfiɗa. A take ta birkice musu ta shiga bibbigesu da son ƙwace kanta, amma ina sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi, tuni suka danneta a wajen, dama gashi daga ita sai zani ɗaurin ƙirji, dan sanda za'a saka ƙunshi sakata akai ta cire rigar. Tsaf ƙawayen amarya suka cire zanin nan kuwa daga jikinta aka barta zir sai ɗan kamfai (😂wato mutanen da anyi shagali da ɗanyen aiki gaskiya🤣). Sauran lallan da aka saka mata ya rage da wanda aka cire matan Alwanka ta kawo musu, nan fa ƙawayen amarya suka shiga ɗiba suna saka mata a jiki ana murjeta da shi. Itako tana kai musu duka da harbinsu ƙafa da hannu tana kuka. Har cikin gashin kanta ana raira waƙa, bari na ɗan raira muku💃🤣.     Ayye yara iye TURGEZA. Ga Turgeza yazo, Turgeza. A wanketa da sauri, turgeza. Lallen iya ƙamshi, turgeza. Ayye yara amarya turgeza. Sai da ni bilyn ku😂 (magana ta gaskiya ni na ƙirƙiro muku waƙar, amma ta gaskiyar ba haka take ba, baitin farko ne kawai na gaskiya kada kakanin mu suce na musu sharri😂🤣🤣).        Sosai amarya ta dirzu da lalle. Masha ALLAH kuma sai tayi ƙyau abinta, sai dai fa kowa ya daku gwargwadon iko cikin ƙawayenta. Itama kanta ta jigata da kuka da harbe-harben data sha. Ana sakinta taja zaninta ta ɗaura, data rarumi icce tai kan ƙawayen nan nata sai gudu Malam. Tuni fa kowa yay waje, masu neman wajen ɓuya suka nema, masu haura katanga nayi masu yin hanyar zaure nayi. Da ƙyar Alwanka ta kamata ta riƙe, sai da duk suka baje sannan ta saketa, babu batun wanka, wannan lalle na jikinta haka kuma zai cigaba da zama a jikin nata har sai gobe, gefe ta koma ta dasa sabon kuka. Babu wanda ya hanata har tayi mai isarta ta gaji dan kanta ta haƙura. Bayan komai ya lafa ƙawayen amarya suka daddawo sai kuma aka ɗakko abinci da miya aka baje kuma a tsakar gida da turirrika na rabo. Haka aka raba abincin ƙunshi da nama kowa ya samu har maƙwafta, aka baje kuma aka fara ci ana hira da wasa da dariya. Bayan sun kammala aka aiko baranya ɗakko igiyar shillo, babu jimawa ta dawo, amarya ta tashi ta saka rigarta da kallabi suka kwashi igiyar nan suka fice bayan gidan wajen wata bishiyar ɓaure ƙatuwar gaske. Anan aka ɗaura wannan igiya ta ɗauru kam sannan aka fara shillo, idan wannan ya sauka wannan ya hau, har yamma suna a wajen suna waƙe-waƙensu na ƴanmata cike da nishaɗi. Sai gab da magriba suka dawo gidan Alwanka.         Washe gari alhamis ma haka suka sha shagalinsu aka ƙara yima amarya wankan lalle kamar jiya, dan kuwa yau ma zir akai mata sai ɗan kamfai aka shafeta da lalle har cikin kanta, tasha kukanta kamar jiya har yamma. Zuwa dare bayan sallar isha'i Alwanka ta tattarasu tai musu rakkiya aka maidasu gidan su A'isha. Gida kam ya gama cika da dangi tako ina. Bayan gaisuwa Alwanka tace “Ga aro na maido, ALLAH ya sanya alkairi ya fiddamu kunyar gobe. ALLAH Kuma yasa takai mutuncinta ɗakinta. Nagode, Nagode ALLAH yabar zuminci”.       Atare aka amsa mata da amin. Dangi sukai godiya suma sosai ta wuce. A ranar anan gidan su A'isha suka kwana, dan kuwa ɗaki guda aka ware musu ita da ƙawayenta. Washe gari juma'a ɗaurin aure, ta ko ina dangi maza sunata isowa, hakama tawagar ango da danginsa daga Bauchi, da abokansa na Bauchi dana Kano duk sun iso, zuwa ƙarfe sha ɗaya aka ɗaura auren A'isha da Abdul-rasheed akan kuɗi sule na gugar sule har sule goma cas. Lallai wannan yawan sadaki ya girgiza mutane, dan kuwa sule goma ba kuɗin wasan yaro bane a lokacin. Abinci kala-kala tako ina ƙamshin ke tashi na miyar taushe ga nama kamar a banza. Dangi kowa ka gani bakinsa a washe anatama juna sambarka, balle kuma ace Inna ai ba'a magana, tayi shar da ita cikin sabon ɗinki.       Amarya kuwa na can tare da ƙawayenta a ɗaki, sai dai a miƙa musu abinci. Ƙawaye sunyi wanka da kwalliya, amarya kam dai tana nan ba wanka har yanzu dai tsoffin kayanta ne a jikinta na zaman lalle, sai bayan sallar azhar kuma aka shirya yima amarya wanka dan za'a shiryata domin tafiya Bauchi. An shirya ruwan wankan amarya a cikin ƙaton masaki da yasha addu'oi daga tsoffi, aka zuba lalle sai kuma ruwan turare kala uku masu ƙamshi sosai, sai sabulu shima mai shegen ƙamshin tsiya. Bayi aka kaishi sannan aka kira alwanka da zatai mata wanka. Aifa nan abokan wasa suka miƙe domin rakkiyar amarya bayi, tana kuka aka dannata ciki bayin, dama Alwanka an kiranta. Waƙa abokan wasan nan nata suka fara rairawa suna tafi yara na tayasu....         Tsohuwa iki wanke, kin saki Kwankwaso yeee a ƙofar soro💃.... (😂Ehem-ehem lamarin fa ba'a cewa komai, amma wannan waƙar ta gaskiya ce walle bani na ƙirƙira ba😎😂).       Kuka sosai itako amarya keyi, Alwanka kuwa na wanketa lungu da saƙo har gashinta dake danƙare da lalle. Duk wannan dattin ya fita da suke kira (Saiɓi), sai ga amarya na sheƙi da ƙyalli da ƙamshi kamar ka lasheta. Zani aka bata ta ɗauro aka rufeta da wani aka fito da ita sai ɗakin Inna. Acan aka shafa mata mai mai ƙamshin tsiya mai gurguwa, aka shafe ta da turarruka kala-kala Sannan aka bata sabon zani da riga na atamfar.... Ta saka daga cikin lefe yake, sai ɗan kwali disko da wani fallen zanin na lulluɓi. Aka shafa mata hoda aka saka mata jan baki amarya ta fito tsaf da ita masha ALLAH.       To daga nan fa iyaye suka zagayeta aka shiga faɗa da nasiha, itako tana ƙunshe a zanin nan da take lulluɓe tana kuka sosai. Bayan sun gama akasa Inna tai mata addu'a tana kuka sosai, dan yau ne karo na farko da zatai nesa da ƴarta. Bayan ta kammala aka kamata aka fito da ita soro inda iyaye maza suke suma suna jira. Nan ma sabon faɗa da nasiha aka buɗe, gargaɗi dai kam amarya ta shashi gwargwadon iko kafin a kamata zuwa ƙofa gida inda motor da za'a ɗauki amarya take. Kanta ce guda biyu, sai ƙarama ɗaya da za'a saka amarya. Tuni masu zuwa sun cika kantar kuwa harda ƙawayen amarya, dan haka aka sakata cikin ƙaramar Innarta da Gwaggon na ɓangaren uwa da uba suka shiga kusa da ita, sai a gaba direba da Nasiru ne, ango da sauran abokai kuwa tuni sun ɗauki hanyar Bauchi su dama da iyaye ƴan ɗaurin aure.         Motoci na ɗagawa ƴammatan amarya suka fara raira waƙa da yara....      Ayye yaraye dide, ayye yaraye naye, ayye yara iye naye yaraye!!. Ƴammata kuzo roni, mi zamuyo roni? Aiko zaman lallen A'isha lale laya!. Ke kikace kinayi da shi, shi yakace yanayi dake, har magana takai ga manya kibar mana koke-koken tsiya. Babu mararraba ba rabawa, iccen wurma yasha harara, yasha rarraɓar masu ƴaƴa, tunda ya kada goɗiya. Iye yaraye, ke kikace kinayi da shi, shi yakace yanayi dake!. 💃🏼💃🏼😂😂Iya nan za'a tsaya, (😎kuma itama ta gaskiya ce ehe😂).         Su suna raira waƙa amarya na kuka mai ban tausayi. Haka motoci suka wuce jama'ar anguwa na binta da addu'ar fatan zama lafiya na har abada. Ahaka aka ɗauki hanyar Bauchi. Tun masu waƙa nayi har suka gaji wasu ma suka fara barci, cikin amincin ALLAH bayan magariba suka iso Bauchi. Kai tsaye kuma gidan iyayen Abdul-rasheed aka wuce da amarya, inda suka samu tarba ta mutuntawa da girmamawa. Tarba dai kam dangin Abdul-rasheed sun yima amarya ta gata ita da danginta, yayinda take ƙunshe cikin gyauton zanin da aka lulluɓa mata na atamfarta mai barewa datai mata ƙyau. An kawo musu abincin maraba kala-kala sukaci suka ƙoshi, daga haka suka baje barci dan kowa ya gaji matuƙa, ita kanta amarya tuni ta ɓingire da ƙyar ma aka samu taci abincin.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 11_ __________________ *_NACE ina kuke ne?!!. Al'ummar Gombawa nake magana 💃 fulanin asali ke nan 😘._* *Shin kuna da labarin cewa kuma nesa ta matso kusa gare ku?* _Maza kuzo ku sha labari da ɗumi-ɗuminsa, domin kuma fa NAKUN ya buɗe muku gidan gyara da ƙalƙale jikin mata ƴan kwalisa a kusa da ku gabb._ *_Idan kunji ana kiran maida tsohuwa yarinya to wannan katafaren shagon ne na👇_* *ALIYU HAIDAR COSMETICS PLAZA* _ADDRESS SHOP D80 WOMAN LINE GOMBE MAIN MARKET_ *_Zaku same mu a wannan numbers ɗin kamar haka👇_* *07068210505* *09133081313* _DEALER IN all kind of skin care products such as:_ moisturizer Sun screen Face Toner Eye cream Face serum Face wash Face scrub Face cream Face marsk Body lotion Body cream Shower gel Body scrub Tube Body oil Body spray Perfume Hair crm Hair spray and many more *_Harma da abinda bamu lissafo ba anan. Ku dai kawai karku bari a yi babu ku. Domin kayanmu garanti ne kuma dahir ne 💃_* Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/HCLn6awOrmP5WJmO9jPrgK?mode=ems_wa_t __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Washe gari an cigaba da shan biki a Bauchi, dan anyi wankan ango da ajo ɗinsa. Amarya kuwa babu wanda zai ce yaga fuskarta sam dan ko wajen wankan ango da ajo bata leƙo ba tana ɗaki ƙunshe. Hakan kuwa shine dai-dai kuma shine ɗa'a. A ranar kayan amarya suka iso dan su sai washe gari aka taho dasu. Gidanta dake nan jikin gidan sirukanta da sauran ƴan uwansa aka sauke, sauran kayan gara kuwa gidan su abdul-rasheed.        A take danginta suka koma can aka hau jere, aka barta da ƙawayenta ita kuma anan gidan. Ɗakin amarya yayi ƙyau. Iyayenta sunyi ƙoƙari sosai. Gado ne guda biyu, babba mai rumfa na miji, sai ƙarami nata. Mai rumfa yasha ƙatuwar katifa da zanin gado harda rumfarsa ta sama da filo har goma sha biyu ciff, aka saka masa labule da ake kira (Zarge shige🤣). Dan haka gadon yay ɗas kamar ka zauna kaita kallo. Itama dai natan an saka katifa da zanin gado mai ƙyau, sai kabot da ya sha jeren fantekoki a sama da kwalloli, sai kanta a cike da tasoshi ƴar girke dake ta ƙyalli da ɗaukar ido na ƴar gata, sai tangarare suma na ƴar gata. Ga languna tuwo da miya kala-kala da kwanon sha. Sai kumbo manya anyi nasu dankin uwa ta raɓe suma a gefe masha ALLAH, ga uwa ta raɓe ta fantekoki masu murtala. Kowace kusurwa an buga darduma masu ƙyau, sai labule. Sai gansarwa na garar kaka da ƙoran fulani da suka sha tarde da ludaye a cikin an sakasu a ragaya aka rataye, ledar ƙasa ma an baza masha ALLAH. Kai abunfa ba'a magana, dan ɗakin amarya sai sambarka komai yaji, kaida ka gani kaga ɗakin ƴar gata. Abin dai masha ALLAH sai wanda ya gani. Dan duk hassadarka kai kana ganin wannan ɗaki kasan an zubama Ai'shatu kayan ƴar gata.         Suna kammalawa zuwa dare aka dawo da amarya nan, suma dangin nata nan duk suka dawo aka cigaba da shagalin biki bayan an dire musu raguna manya guda biyu na jere. Washe gari buɗar kai, ranar kuma biki zai tashi, baƙi duk zasu wuce musamman ma ƴan kano. An dafa farar shinkafa, sannan amarya tayi wanka yau, dan tunda aka kawota ko kaya bata canja ba, batayi wanka ba kuma, idan kaga ruwa ya taɓa jikinta sai na alwala. Har yanzu bata saka Abdul-rasheed a idon taba shima haka bai ganta ba. Tunda safe aka fara mata kitso ƙana-ƙana masu ƙyau, sun jima sunayi dan har zuwa azhar sannan suka kammala aka haɗa mata ruwa da yaji turarruka da addu'oi ta shiga wanka da kanta. Bayan wani lokaci ta fito, an bata kaya ta canja, atamfa mai tabarma da akaima ɗinki mai ƙyau irin na wannan zamanin, yau dai gyale aka bata ta yafa ba zani ba, sabon takalmi sai tsakiyar wuya mai ƙyau tanata sheƙi. Sosai hankalinta a tashe yake, dan yan uwanta duk sun kammala shirin su, ana gama buɗar kai zasu wuce. Gida ya cika taf, dangin ango duk sun dawo nan suma. An fara yin rabo irin na al'ada ga dangin miji, bayan kammalawa ne aka fito da amarya dake lulluɓe cikin gyalenta, har yanzu dangin miji dama ƴan gari babu mai cewa ga kamaninta. Sabuwar tabarma aka shimfiɗa aka ɗora sabuwar kujerarta ƴar tsugunno a kai, ta zauna. Shinkafar nan da aka dafa fara sai gishiri kawai a cikinta, amma fa tasha mangaɗa ƙyallan aka juyo a ƙaton bangaji aka ajiye gabanta. Tana lulluɓen aka kamo hannunta biyu aka fito da su, ta haɗesu waje guda kamar mai addu'a aka cika mata shi da shinkafar nan taf. A baki ta saka, sai dai babu batun taunawa ta furzar a gefenta na dama, ta ƙara cika baki ta furzar a gefenta na haggu, ta karshe ta furza a gaba, sauran ta watsata baya. Daga nan ne fa aka shiga rangaɗa guɗa, masu kiɗan ƙwarya suka fara. Bayan an gama cashewa da kiɗan ƙwarya koma muce ana cikin cashewar iyaye a cikin dangin ango suka kwashi kayan da aka basu na baye suka koma gida, aka sake shirya amarya itama aka bisu da ita can hannunta riƙe da ƙwarya mai ƙyau. An fara kaita ɗakin Inna dake matsayin uwar mijinta a yanzu. Inna tayi addu'ar zaman lafiya, ta kawo kuɗi jaka biyu ta saka mata a ƙwaryar, danginta sukai godiya aka fito, daga nan sai ɗakin marigayiya mahaifiyar Abdul-rasheed, inda danginta suka fanshi nata, ba'a nan aka tsaya ba, sai da akabi iyaye kaf, dangin uban miji dana uwa. Kafin kace mi sai ga kuɗi shimili amarya ta tara a wannan ƙwarya, dan har makwaftansu da ake zumunci irin na mutuntawar mutanen da, makwata iyaye ne ba abokan gaba ba, nan ma sai da aka kai amarya, daga nan ne aka sake baidata gidanta inda yara da ƴammata ke cigaba da cashewa da kiɗan ƙwarya. An maidata ɗakinta, aka saka wasu cikin ƙannen ango suka zauna da ita, suko ƴan kano cikin hikima suka zare jikinsu duk suka gudu batare da amarya daketa kukanta ta farga ba. Balle kuma masu kiɗan ƙwarya na wasansu har magriba. Sai bayan sun tashi ne gida ya fara komawa tsit A'isha ta fahimci da kaf yan uwanta babu. Sosai ta ƙara ƙarfin kukanta, ƙannen ango dake tare da ita har lokacin na lallashinta.        Zuwa bayan sallar isha'i an tafi an bar amarya ita kaɗai a ɗakinta tanata kuka, sai daga baya aka turo mata wasu ƴammata huɗu su zauna da ita saboda zuwan anguna. Babu jimawa kuwa ango da abokansa suka yo masa rakkiya cikin girma. Ƙawayen nan sune suka amsa, dan amarya na can ƙarshen bango ta rakuɓe ƙudundune cikin gyale. Anyi gaisuwa tsakanin ƙawayen amarya da abokan ango, ƙawayen amarya suka gabatar musu da abinci. Kwanika ne guda biyu dake a saman tire ɗin kwano da kwanon sha dake cike da ruwa an rufesu da tuma ƙasa (😂Azo gaya min minene tuma ƙasa akwai kyauta). Gefe suka koma su kuma abokan ango suka naɗe hannayen riga suka fara ɗibar girki, gefe kuma suna hira da ƙawayen amarya. Bayan sun kammala akai sayen baki, anyi ƴar jayayya akan kuɗi, daga ƙarshe dai suka ajiye musu jaka huɗu. Ita dai amarya na nan a gefe kamar ma bata san bikin da ake ba a ɗakin, kukanta take dai kawai.      Abokan ango sunyi nasiharsu ga amarya da ango, tare da addu'a. Daga haka suka miƙe tare da ƙawayen amarya sukai musu sallama suka wuce. Abdul-rasheed ya miƙe dan rakasu Nasiru ya maida shi ya zaunar yana faɗin, “In dai mune mun huttasheka, zauna ka lallashi min ƙanwa sai munzo maka tausa”. Daga haka suka fice suna dariyar kalmar shaƙiyancin Nasiru. Abdul-rasheed ya bisu da kallo kawai yana murmushi. Bayan fitar tasu ɗakin ya kasance shiru na fin mintuna uku, dan haka kawai shima Abdul-rasheed ɗin sai yake jin kansa wani iri tamkar ba shi ɗin ba. Yau ALLAH ya cika masa burinsa ga shi ga masoyiyarsa dai a tare da shi. Itako har yanzu kukanta take mai fita da sauti kaɗan da shashsheka. A hankali ya miƙe yana mai tattare babbar rigar jikinsa ya cire gaba ɗaya, saman gadon mai rumfa ya ɗaga labulensa ya ajiyeta sannan ya taka zuwa inda take zaune a maƙure tsakanin gado da bango. A nan ma ɗan tsayawa yay kanta yana kallo na sakkanni, kafin ya kai tsugunne gabanta ya ɗaura hannunsa kan nata dake riƙe da gyalen da take lulluɓe a ciki. Ɗan zabura tai na tsorata, dan haka ya saki hannun nata, sai kuma cike da tausasawa ya furta, “Ha Giwar mata, kukan ya isa haka mana. Yau fa rana ce irin ta farin ciki gaki ga Abdul-rasheed ɗinki, kwana da kwanaki an hana min ganinki kewa na neman kaini ƙasa. Bana son kukan nan yana ɗaga min hankali da sukar zuciyata, kiyi haƙuri ki daina yinsa. Ina sha ALLAHU na miki alƙawarin zan kwatanta daga ƙoƙari irin na Inna a gareke, bazan barki kiyi doguwar kewa ba ko yin kukan rashinta a kusa dake. Zan yi ƙoƙarin maye miki gurbin su Bashir, haka kuma zan maye miki gurbi na ƙawayenki. Zan zama adali mai ƙoƙarin sauke nauyin da ALLAH ya ɗora masa na maye gurbin damuwarki da farin ciki, kukan ki da dariya. Kin san ina sonki matuƙa A'ishatu, ba kuma zan daina ba har na koma ga UBANGIJI na in sha ALLAHU”.       Sosai kalamansa ke tasirantuwa a zuciya da gangar jikin ta, dan haka a hankali ya fara sassauta kukan nata. Da wannan damar yay amfani wajen bata umarnin miƙewa. Babu musu ta miƙe ɗin, dan a nasihar da tasha an tabbatar mata biyayya ga miji shine nasararta kuma wajib ne in har ba akan saɓon ALLAH ba. Sai dai fuskata na rufe a gyalen baya gani komai na jikinta sai hannu da ƙafafu ta ƙasa.           “Je kiyi alwala muyi sallar godiya ga UBANGIJI”.    Nan ma bata musa ba akan umarninsa. Haka ta nufi hanyar fita waje ta ɗauki buta a ƙofar ɗaki, tsaidata yayi tare da takowa ya miƙa mata Torchlight ta ƙarfe da ake ma zubin batira. Ganin ba ganinsa take ba ya kamo hannunta ya saka mata a ciki, kamawar data sakata ƴar zabura kamar ɗazun. Har ma abin ya saka Abdul-rasheed sakin murmushi. Sai kuma cike da zolaya ya matsa jikinta sosai, cikin raɗa a saitin kunenta ya raɗa mata, “Ayi haƙuri a buɗe fuskar kar amarya ta ɓige da faɗuwa ko bige goshi a bango”.        Murmushi ta saki a karo na farko, sai dai bai gani ba dan ba ganin fuskata yake ba. Amma yanda ta juya da sassarfa yaji a ransa ta murmursa ɗin. Shima sai yay murmushin sosai yana binta da kallo. Kafin ya koma cikin ɗakin yana bin jeren da aka tsantsara musu da kallo daki-daki. Komai ya masa ƙyau, ya kuma ƙayatar da shi. Yana nan a haka harta dawo, baiyi magana ba ya amsa fitilar shima ya ɗauka butar ƙarfe ya fita domin yo alwalar..........✍🏼 *_Ayi haƙuri da jina shiru kwana biyu, an yi mana haihuwa ne bana samun zama shiyyasa. Naga kuma zan raba hankalina biyu sai kawai nace bara dai ayi suna sai mu dawo gaba ɗaya.😀🙏_* _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 12_ __________________ https://chat.whatsapp.com/Kf6jd57OsXHCG7cODNAje6 *_Kowace mace na matuƙar son taga ta gyara kitchen ɗinta kodan ta kalla itama taji daɗi 💃_* *_Dunƙule kuɗin ki saya ne ke miki wahala hajiyata?_* *_Ko tarasu a hannunki ke baki wahala saboda kokin fara sai ki kasa ki kashe?_* *_To kwantar min da hankalinka ƙawata, IMZEED VENTURE ta gama shirya miki komai ta yanda kema zaki mallaki naki cikin sauƙi da rahusa._* _Ta buɗe adashin gata wanda yafi bashi kwanciyar hankali da daɗi, akan farashi mai sauƙi, kaya ƴan zamani, gasu ingattatu. Za'a kai miki a duk inda kike. Kedai naki kawai yin zubi akan lokaci._💃💃 *_Za'a fara zubi 25th October in sha ALLAH 💃_* 20k monthly kayan 100k 10k monthly kayan 50k *_Arha tafi bashi, hakama adashe yafi bashi. 💃 Ga sauƙi abaka tamkar ƙyauta 💃💃😀_* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ......Alhamdullah sunyi sallah, Abdul-rasheed kuma ya musu addu'oi sosai, sannan ya ɗora da tambayoyi ga A'isha da baya haufi a kanta. Ta kuwa amsa masa dalla-dalla cike da ƙwazo. Daga haka ya ajiye musu kaza irin ta al'ada, miƙewa tai itama ta ɗakko wani ɗan ƙyaƙyawan kwanon tangaran dake a rufe ta ajiye a gabansa.        “Mina samu Matar Abdul-rasheed?”.    Ya faɗa cike da zolaya yana murmushi. Kanta a ƙasa muryarta dake a dishe na fita can ƙasa ta amsa masa.       “Abinci ne akace na baka idan kazo”.        Kansa ya jinjina yana buɗe kwanon tangaran ɗin. Gasassun ƴan shila ne har guda huɗu, sai uban ƙamshi suke na kayan yaji. Yay murmushi yana sauke ajiyar zuciya. Yunƙurawa tayi zata miƙe, ya ko riƙe hannunta yana faɗin, “Koma ki zauna”.     Zaman tayi da sauri kodan ya sake mata hannunta. Shima ganin yanda take yi ɗin sai ya saki hannun kawai yana gyara zamansa. Idonsa a kanta ya ce, “A'isha bazaki cire gyalen nan hakanan ba, ko baƙya jin zafi ne?. Ina son ki saki jiki dani dan ALLAH. Ni ba abin tsoronki bane, abokin rayuwarki ne kuma abokin farin cikin ki kinji”.     Kanta ta jinjina masa cike da girmamawa, sai kuma cikin murya dake fita can ƙasa ta ce, “Babu zafi fa, kuma ina jin kunya”.      Murmushi yayi mai matuƙar faɗi da yalwa. Sai kuma ya kai hannu ya riƙo hannunta a cikin nashi, ɗan matse jikinta tayi kanta a ƙasa, ya sake girgiza kai murmushinsa na sake faɗaɗa, muryarsa na ƙara tausasa ya ce, “Ai'shatul-humairah, yanzu ni da ke ai kunya ta ƙare ko? Kefa matar Abdul-rasheed ce yau kwana ɗai-ɗai har uku kokin manta?”.      Kanta ta girgiza alamar a'a. Ya ce, “Yauwa matar kwarai. Maza matso to muci naman kada ya huce, sai kije ki kwanta ki huta abinki nasan akwai gajiyar biki”.       Nan ma kai ta jinjina masa kawai, ta kuma ƙi yarda su haɗa ido sam da shi. Ajiye kazar yay ya saka musu kwanon ƴan shilar nan a tsakiyarsu. Laumar farko daya cira ya kai bakinta, amma sai ta duƙe da sauri tare da ɓoyewa cikin gyalen, yanzu kam siririyar dariya yayi, dan kunyar tata tsumashi take. Rarrashin duniya da dabara taƙi cin naman nan, haka ya haƙura yaci iya nashi sai ya miƙe cike da dabara yana faɗin, “Shike nan ni bari na fita, nasan idan bana nan ai zaki ci ko?”.        Kai ta jinjina alamar eh.    “Oh ni Abdul-rasheed, yau dai Shatu na ta zama kurmar ƙarfi da yaji, nazata yau idan muka haɗu har sai na gaji da surutunki, karki manta kusan mako huɗu kenan fa bamu ga juna ba, kewarki duk ta hanani sukuni ashe ke ba hakan bane”.        Cike da yarinya ta ce, “Nima haka, kawai ina jin kunyarka ne”.      “Shike nan na yarda hajiyar kunya, ni bara naje muyi sallama da baba sai na dawo. Amma fa kici naman nan, dan in na dawo naga baki cinyeshi duka ba zan miki ɗura ne. Idan kin kammala kiyi kwanciyarki kiyi barci kinji”. Bai jira amsarta ba ya fice. Tana jin takunsa yay nesa da ɗakin ta saki wata nannauyar ajiyar zuciya, sai kuma a hankali ta ɗago ta leƙo fuskarta tana kallon hanya. Shiru alamar babu shi a kusa, ko da gaske ya fitan. Wata ajiyar zuciyar ta sake saukewa sannan ta gyara zama ta fara cin naman. Wani daɗi yay mata na musamman, aiko ta shiga lumshe idanu ranta fes. Babu wata fargaba irin ta amare na yanzu, dan su lokacinsu idonsu bai buɗewar sanin mima ake a gidan auren ba balle har ya zame musu fargaba. Tana gama cin naman ta kwashe kwanikan ta maida gefe. Buta ta ɗauka ta fita tsakar gida ta wanke hannunta, sai kuma ta ɗanji tsoro. Da gudu ta koma cikin ɗakin, tana ajiye butar bata dire ko ina ba sai a saman ƙaramin gado, dan su Gwaggonta sun gaya mata shine nata, babban gado mai rumfa kuwa na miji ne.       Kamar jira barcin keyi ta kwanta kuwa ya saceta, hankali kwance ta ɓararraje taji sabuwar katifar Rimi ta shiga jan numfashi. Duk abinda take Abdul-rasheed na gidan babu inda yaje, dan da farko ma laɓe yake yana kallonta ta window, sai da zata fito wanke hannu yay saurin komawa bayan ɗakin dan karta ganshi. Sai da ta shige ya koma jikin window ɗin, yanda ta daka tsalle ta faɗa a gadon ya sashi sakin murmushi da girgiza kai. Haka ya cigaba da tsaiwa a wajen har sai da ya tabbatar tayi barcin sannan ya koma ciki.        Kwanciya ya gyara mata a hankali dan karta farka, yay mata addu'ar barci. Itama fitilar ƙwan ɗakin ya kasheta, shima ya cire rigarsa kawai ya bar wandon dogo da singlet ya haye babban gadon nan mai rumfa ya kwanta, sai dai ya zuge labulen duka ta yanda zai dinga ganin kowane motsinta ga kuma garin da zafi. Addu'a yay abinsa, ya zuba mata ido daga inda yake kwance zuciyarsa na ƙara shiga a farin ciki da alfaharin jin yau gashi ga A'isha suna barci a ɗaki ɗaya matsayin ma'aurata, ko haka aka tsaya shi kam yaci ribar zuwa kano karatu ai, sai dai a tayashi da sambarka. A haka shima yana tunane-tunanensa barci yay awon gaba da shi.             Washe gari shine ya fara farkawa da asuba, a mamakinsa sai yaga itama ta miƙe cikin lalube tana faɗin, “Inna ki kunna fitilar duhu yayi yawa. Ina son naga hanya naje na tada su Bashir suje massalaci”.       Ɓoyayyen murmushi ya saki, kafin ya kama ya saukko a gadon gaba ɗaya hannunsa riƙe da Torchlight sai dai bai kunnata ba. Jikin gadon nata yaje ya tsaya, kafin ya kunna fitilar yana haska kansa kaɗan da faɗin, “Yau ba Inna zaki gani ba a wannan ni'imtacciyar asubahin Humairah. Mijinki ne, rabin tsokar jikinki Abdul-rasheed”.         Tunda ya haska kansa A'isha ta daburce, dan cikin kici-kici ta shiga gyara zaninta da tuni ya warware daga jikinta yayi nashi waje, sai dai jikinta akwai ɗan tofi. Ganin yanda ta rikice tama kasa kamo zanin yanda ya dace ya sashi duƙowa yana dafa gadon ya kama mata zanin ya rufa mata, ajiyar zuciya ta saki tana ɗan juya fuskarta ga bango. Sai kuma kamar zatai kuka ta furta, “Na manta ne”.          Cikin kwaikwayon ƙaramar muryarta da son tsokanarta ya bata amsa da, “Na sani Ayeshat”.     Hannu tasa ta rufe fuskarta gaba ɗaya tana murmushi. Shima dai murmushin yake yana kallonta. Kafin ya bata umarnin sauka a gadon domin fita yin alwala. Ta ɗauki butar roba dake matsayin tata, shi kuma ya ɗauki ta ƙarfe. Yana gaba da fitila tana biye da shi. Fitilar ya bata yace ta fara shiga bayin, shi kuma ya tsaya jiranta a waje. Koda ta fito bai amshi fitilarba ya barta da ita shi ya shiga bayin a haka. Sanda ya fito ta kammala tata alwalar, tsayawa tai ta jirashi yayi, sannan suka koma ɗakin a tare. Ashana ya ɗauka ya kunna mata fitilar kwai, ya ɗauki Torchlight ɗin ya wuce massalaci.         Bayan ta idar da sallar asuba bata jira komai ba ta sake hayewa gadon tai kwanciyarta, dan barcin kwana biyun nan dake cin idonta ne ke damunta. Amma ita bata san wani barcin safe ba dan bata yi, a gida ma suna idar da sallar asuba ita da Inna su Tasi'u suka dawo massalaci makarantar allo suke tafiya, sai takwas hantsi ya haska suke dawowa. Suyi kari su sake tafiya wata makarantar sai kuma ƙarfe sha biyu. Daga nan sai ta yamma kuma. Amma yau sai ga Hajiya Indo ƴan gidan miji daɗi ana shan barcin safe cike da freedom. Shiko Abdul-rasheed ma bai dawo gidan ba koda aka idar da sallar, dan suna tare da Baba, bayan sun bar massalacin Baba ya tarkatasu da sauran yayunsa suka tafi gaishe da wani makwafcinsu da jiya yaji ciwo a ƙafa. Daga can kuma suka wuce gidansu....       Wajen ƙarfe takwas hantsi ya ɗaga. Rana ta leƙo mai ɗumi da hasken safiya ta ratsa cikin ɗakin da ke da ɗan sauran ƙanshin turaren wutar jiya da aka kunna mata da dare. Fitilar ƙwan harta gaji ta mutu alamar kalanzir ya ƙare a cikinta. Dai-dai nan amarya A'isha ta tashi saboda ɗumin hasken rana dake taɓa mata fuska, zaune ta tashi tana miƙa da kiran sunan ALLAH. Ɗakin ta fara bi da kallo daga inda take zaune a bakin gadon, sai kuma tai murmushi tana raya (Yanzu fa komai ba ɗakin nan nawa ne kona fasa Inna bazata min gaɗa ba) kawai sai abin ya bata dariya, ta tashi ta buga tsallen farin ciki, kafin ta sake hayewa gadon tana juyi. Sai da tayi mai isarta sannan ta sake tashi zaune, tunanin gidane kuma yazo mata, zuciyarta na sake ayyana mata yanzu fa su Inna sunyi nesa da ita da su Bashir, shike nan bata da kowa anan kusa. Shar hawaye suka fara rige-rigen sauka a fuskarta, a haka ta fara kici-kicin gyaran gadon, tana yi tana share su da sharɓar majina harta kammala.      Inna ta gaya mata tana tashi a barci ta dinga fara gyara ɗakinta kafin komai, karta sake tabar gadajenta ba'a gyare ba har wani ya gani koda Abdul-rasheed ne. Gadon nasa ta kalla, ba wani yayi barkatai bane, amma duk wanda ya kalla yasan an kwanta a kansa, gashi ya zuge labulen ana ganin kan gadon, kuma ina tace babu ƙyau wani ya gammaka sirrin gadon mijinka, rage darajar miji ne. Maza-maza ta ajiye batun kuka a gefe ta ɗakko kujera ƴar tsugunno ta ajiye a gabansa ta taka ta hau, sai kuma tai tsaye shiru cikin ɓata fuska, a fili ta furta, “To yanzu a yaya zan gyara masa, gaskiya ina jin kunyar hawa masa gado, karma yaga kamar na rainashi, kuma za'a iya rubuta min zunubi”.        Dariya sosai kalamanta suka saka Abdul-rasheed dake tsaye a bakin ƙofa batare data sani ba, dan tun sanda ta ja kujera ya iso wajen. Da ƙyar ya iya danne dariyar yana cigaba da kallonta, sai kuma ya koma kallon ɗakin ya murmusa kaɗan, komai tsaftatacce yake, kamar yadda aka bar shi a jiya, idan ka cire gadajen da suka kwanta kawai. Sai kazar al’adar ta jiya tana gefe tare da kwanikan abincin da suka ci.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 13_ __________________ https://chat.whatsapp.com/Kf6jd57OsXHCG7cODNAje6 *_Kowace mace na matuƙar son taga ta gyara kitchen ɗinta kodan ta kalla itama taji daɗi 💃_* *_Dunƙule kuɗin ki saya ne ke miki wahala hajiyata?_* *_Ko tarasu a hannunki ke baki wahala saboda kokin fara sai ki kasa ki kashe?_* *_To kwantar min da hankalinka ƙawata, IMZEED VENTURE ta gama shirya miki komai ta yanda kema zaki mallaki naki cikin sauƙi da rahusa._* _Ta buɗe adashin gata wanda yafi bashi kwanciyar hankali da daɗi, akan farashi mai sauƙi, kaya ƴan zamani, gasu ingattatu. Za'a kai miki a duk inda kike. Kedai naki kawai yin zubi akan lokaci._💃💃 *_Za'a fara zubi 25th October in sha ALLAH 💃_* 20k monthly kayan 100k 10k monthly kayan 50k *_Arha tafi bashi, hakama adashe yafi bashi. 💃 Ga sauƙi abaka tamkar ƙyauta 💃💃😀_* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Ganin ta fara kici-kicin gyara gadon batare data hau ba sai nishi take alamar wahala ya sashi ƙarasa shigowa cikin ɗakin, yay sallama a hankali yanda bazataji ba, tare da ajiye kofin hannunsa na ƙarfe mai murfi da leda baƙa. Inda take ya ƙarasa, ya tsaya daf da ita sannan ya furta, “Kin tashi lafiya?”.         Kamar wadda ta tsorata ta juyo firgigit har tana neman gocewa daga kujerar, duk da kuwa muryar sa ta fita cike da taushi ne, amma ita tajita a bazata kuma gab da ita. Da sauri yasa hannu ya tareta, hakan yasa ta faɗa masa a jiki gaba ɗaya, ya naɗe hannayensa kuwa duka a bayanta ta koma rungume a jikin nasa sosai. Sake rikicewa tai, ta shiga ƙoƙarin fita a jikinsa tana bashi haƙuri.         “Shiiii ya isa, ni baki min laifin komai ba”.     Ya faɗa cike da raɗa yana bin fuskarta da kallo, a yanda yay magana yasata nutsuwa, sai dai jikinta rawa yake na rashin sabo, zuciyarta na ɗan bugawa ƙasa-ƙasa. Idanunta dake cika da ƙwalla ta ɗago kaɗan da mamakinsa, dan ita dai tasan idan namiji ya taɓa mace iskanci ne da rashin tarbiyya kai tsaye, kuma ita ta shaida Abdul-rasheed ɗinta mai nutsuwa da tarbiyya ne, dan bai taɓa kwatanta taɓa mata ko hannu ba sanda suke Kano. Nasihar Gwaggo Laraba ce ta faɗo mata, inda take gaya mata halak ne mijinta ya taɓata yanzu, dan an ɗaura musu aure. Ajiyar zuciya ta sauke a karo na farko, dai-dai hankalinta ya dawo jikinta, ido suka haɗa da shi, ganin kallon da yake mata kamar ya samu hoto sai kunya ta mamaye ta mai tsanani. Ta sunkuyar da kai, muryarta tana rawa kamar mai shirin kuka ta ce, “Sannu da dawowa”.         “Kema sannu da gida”.      Ya faɗa da sanyi irin na wanda ya shiga yanayi. Sai kuma ya raba jikin nasu tare da ɗagata cak ya direta ƙasa akan ƙafafunta. Baya ta matsa da sauri, kanta dai na ƙasa sai faman cuɗa yatsunta take a cikin na juna. Murmushi yayi idonsa akan yatsun nata, sai kuma ya janye ya maida ga gadon yana faɗin, “Bari na tayaki gyara gadon ko. Kuma ni daga yau na yarje miki ki dinga hawa babu wani zunubi da zaki samu. Nima ai zaki dinga ara min naki ina hawa ko?”. Yay maganar ƙarshe da juyowa yana kallonta. Murmushi tayi da saka hannayenta duk biyu ta rufe fuska, sai kuma ta jinjina masa kanta alamar eh.        Ya ce, “A'a ban yarda ba magana zakiyi da baki. Dan dole ki koya surutu yanzu babu maganar shiru-shiru sai na maidaki akku”.       Dariya sosai ta sanya, tare da janye hannun ta ce, “Akku fa?”.       “Eh mana, ai kin san shine sarkin subaɗi. Ni kuma irinsa ne bana gajiya da zance amma idan ina tare da Gimbiya A'isha”.      Sosai sunan ya sata nishaɗi, dan haka cike da ƙuruciya ta ce, “Kai kuma Sarki”.       “Shike nan kuwa, ga Sarki ga Gimbiyarsa”. Ya bata amsa yana murmurshi da ƙarasa gyara gadon. Ganin zai bar wajen batare daya zuge labulen ba ta ce, “Inna tace haramun ne barin gadon miji a buɗe kowa ya gani, tace kullum na zuge labulen nan, kozan wanke in yayi datti ina cirewa na canja da wani kafin su bushe”.        Shi kam dai wannan batu na bashi dariya, amma sai ya biye mata ya ce, “To Amin afuwa, bara na zuge”. Ya juya ya mata yanda take so, gado ya koma ruff abinsa. Daga nan ya ce, “Jeki wanke ido na kawo miki wannan. Shayi ne, da ɗan madara. Ki sha kafin ki ci wani abu ko”     Kai ta jinjina masa cike da ladabi da sanyin murya ta ce, “Na gode.”         Murmushi ya mata, ita kuma ta ɗauka buta ta fice da ƴar battar garin gawayi da aka niƙa da gishiri a waje guda, sai asuwaki a cikin leda ta ɗauki ɗaya. Ta ɗan jima kafin ta koma ɗakin, yana zaune a tabarma daya shimfiɗa. A gabansa kofin shayin ne ya ɗakko ƙarami yana haɗa madara ta gwangwani da sauran kayan haɗin. Ta koma can ƙarshen bango zata zauna ya ce ta dawo kan tabarmar. Haka ta zo ta zauna a ɗarare dan biyayya amma daka gani kasan a takure take bata saba zama da namiji a irin yanayin ba, gashi su biyu a ɗaki kawai tun jiya.      Shiru ya kasance a tsakaninsu na wasu mintuna harya kammala, ya miƙa mata kofin shayin da farantin ƙosai daya juye daga leda, sai biredi guɗa ɗaya da kazar jiya da basuci ba. Shima nashi daya haɗa ya ɗauka yana kallon ta. “Ɗauka kisha mana”.      Kanta ta girgiza masa alamar a'a tana wasa da gefen zanenta”.     Shima sai ya ajiye nashi yana faɗin, “Saboda mi?”.         “Ina jin kunya”.     “Aisha kunyar nan dole a ajiye batunta. Abdul-rasheed ɗinki ne fa ba wani daban ba. Yi haƙuri muci tare mu sami ladan juna. Ko kina son mutane su fara shigowa su sameni a gidan bayan ya kamata ace nayi na fita na basu waje”.       Kanta ta girgiza. Ya ce, “Yauwa to maza muci kinji ƴar albarkata. Ai yanzu mu komai mukayi a tare lada za'a saka mana a samu a aljanna kuma.      Sai ta ɗago kai, ta amsa da murmushi kaɗan. Wannan karon, idanuwanta sun ɗan shige cikin nasa. Kallon su ya haɗu, har ta kai kowa ya kasa fara janye wa, nutsuwa ce mai girma da daraja ke ratsasu a tare, zukatamsu na ƙara jin fahimtar wata sabuwar hanya ta rayuwa da suka shiga, rayuwa irin ta soyayya mai ladabi da ƙarfi da haske fiye data da, rayuwa wadda take farawa da kunya, sannan ta cigaba da aminci da yarda.        Yatsa Abdul-rasheed ya kai kamar zai tsone mata idon, dan haka tasa hannu da sauri ta kare. Sai ya saki dariya, itama murmushi tayi mai cike da kunya. Zuciyarta na faɗa mata abin da bakinta bai iya faɗa, cewa sabuwar rayuwa ta fara a garesu kamar yanda Inna ta faɗa mata, kuma shi mutum ne da nutsuwarsa ke girmama kwarjininsa a idanun kowa a bayyane.         “Kin tafi tunanin miye kuma Matar Abdul-rasheed?”.     Kai tsaye ta ce, “Tunanin ka”. “Masha ALLAH akan mi?”. Babu kwalo-kwalo ta zayyane masa kalaman Innar tata. Ya ɗan tsaya kawai yana kallonta da murmushi. Kafin ya cigaba da cin abincinsa yana jin girma da kimar Inna na ƙaruwa a ransa. Haka dai suka karya, ya taimaka mata suka gyara wajen, ta kwashi kwanikan zuwa waje danta wanke a gaban rijiya. Shi kuma sai ya ɗauki botikin ƙarfe ya fara jawo mata ruwan wanke-wanken, sannan ya fara ɗiba a botikin yana kaiwa randunan ruwansu ɗaya bayan ɗaya. A haka suka kammala aikin yace zai yi wanka. Ita da kanta ta ɗauki ruwan takai masa bayi tare da kwandon soson wanka. Ta dawo ɗakin ta saka turaren wuta ta share. A lokacin ne kuma yaro yay sallama cikin gidan ɗauke da kwanika akan ture. Bata yayi tare da mata bayanin cewa Inna ce tace ya kawo. Bata san wacece Innar ba, amma taji a ranta daga gidan su Abdul-rasheed ɗin ne. Godiya tayi da sannu, dan haka yaron bai zauna ba ya juya ya koma. Fitarsa babu jimawa Abdul-rasheed ya shigo. Ya ce, “Sallamar wa nake ji ne kamar Amadu?”.        “Wani yaro ne dai, ban sani ba ko sunansa kenan, abinci ne ya kawo yace inji Inna”.      “Oh daga gidanmu ne. To ki zauna sai ki karya”.     Idannunta a ɗan ware ta ce, “Ba yanzu muka gama karyawa ba? Naƙoshi ALLAH”.      “To Alhamdullahi, ki ajiye sai zuwa anjima. Amma kije kema kiyi wanka kada mutane su fara shigowa suna ganinki da kaya tun na jiya”.      Babu ko musu, sai ma amsa masa da tai cike da ladabi, daga haka ta ɗiba ruwan itama ta wuce bayi. Lokacin data fito harya shirya, dan haka bai zauna ba yay mata sallama ya fice dan har yara sun fara shigowa gidan. Aiko itama A'isha a gurguje ta kammala saka kaya, ta zauna tai kwalliya gwargwadon iyakarta kuma dai-dai da lokacinsa. Daga nan ta fiddo ma yaran da suka fara taruwa a gidan tabarmin karauni, sai kuma ta kwaso shantu duk ta zube dan harda ƴammata. Ai daga nan suka kafa shiriritar kiɗan shantu da ƴammata sa'anninta a tsakar gidan nan suna raira waƙoƙin gaɗa. Kafin kace mi gidan ya cika da yara. Manya dake shigowa ganin ɗakin amarya kota kansu basa bi ma, sai dai su shiga su gano su saka albarka su fice abinsu batare da sun damu ba, dan wannan ba komai bane daga amaren wannan zamanin nasu saboda ƙuruciya da ƙarancin shekaru.. Amarya A'isha bata sake tunawa da batun Abdul-rasheed ba har yamma ta samu abokan shargalle, abincin rana da aka sake kawowa ma daga gidansu, dana safen duk sun cinye ita da ƙawayen nata. Sai gab da magriba an kawo mata tuwon dare mai kawowar data kasance ƙanwar Abdul-rasheed ce Khadijah da bata koma Maiduguri ba ta kora yaran duka, sannan ta saka A'isha yin wankan dole ita kuma ta rufo gidan ta hau gyara tsakar gidan da sukama kaca-kaca. Ɗakin dai da yake ba zama sukai ba a ciki da haskensa, sai ƴan ganin ɗaki da ke shiga. Amma duk da haka shima sai da Khadijah ta sake sharo mata shi ta kunna turaren wuta, zata kunna fitila taga babu kalanzir. Dole ta ɗauki kalbar da aka aje dan sayen kalanzir ɗin ta fita samun yaro ya bada a suyo sukaci karo da Abdul-rasheed ya dawo. Koda ya tambayeta ina zata haka ta sanar masa sai shi ya amshi kwalbar yace ta koma shi bari ya sayo. Haka kuwa akayi, dan haka a gurguje Khadijah ta taya A'isha shiryawa. Sai gata ta fito tsaff kamar ba itace tai buɗu-buɗu ba. Ta bajeta da turare. Sai ga ango ya dawo. A tare suka masa sannu suka gaisheshi, Khadijah ta amshi kalanzir ɗin tana zubawa a fitila shiko yana satar kallon A'isha datai masa ƙyau a cikin jojin da Khadijah ta sakata sakawa. Yasan wannan kwalliya haka sai da taimakon Khadijan, dan ta fita wayo kuma ta girmeta. Khadijah na gama kunna musu fitilar tai musu sallama zata wuce. Amma ya tsaidata kan ta zauna har ya dawo massalaci dan kar A'isha taji tsoro. Haka dole ta zauna sukai salla tare, shi ko yay alwala da ruwan da A'ishan ta kawo masa a butar karfe ya fice massalacin...........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 14_ __________________ https://chat.whatsapp.com/Kf6jd57OsXHCG7cODNAje6 *_Kowace mace na matuƙar son taga ta gyara kitchen ɗinta kodan ta kalla itama taji daɗi 💃_* *_Dunƙule kuɗin ki saya ne ke miki wahala hajiyata?_* *_Ko tarasu a hannunki ke baki wahala saboda kokin fara sai ki kasa ki kashe?_* *_To kwantar min da hankalinka ƙawata, IMZEED VENTURE ta gama shirya miki komai ta yanda kema zaki mallaki naki cikin sauƙi da rahusa._* _Ta buɗe adashin gata wanda yafi bashi kwanciyar hankali da daɗi, akan farashi mai sauƙi, kaya ƴan zamani, gasu ingattatu. Za'a kai miki a duk inda kike. Kedai naki kawai yin zubi akan lokaci._💃💃 *_Za'a fara zubi 25th October in sha ALLAH 💃_* 20k monthly kayan 100k 10k monthly kayan 50k *_Arha tafi bashi, hakama adashe yafi bashi. 💃 Ga sauƙi abaka tamkar ƙyauta 💃💃😀_* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Abdul-rasheed bai dawo ba sai bayan sallar isha'i. Yana shigowa Khadijah tai musu sallama ta wuce. Shi kuma ya zauna yana zolayar A'isha akan yau dami-dami tayi da baya nan?. Sai da ta ajiye masa abincin da aka kawo daga gidansu gabanshi sannan ta zauna tana bashi labari cike da farin cikin tabbacin yau ɗin ya mata daɗi. Shima sai yaji nashi farin cikin ya sake girma, da jin damuwar yanda zai tafi ya barta nan da kwanaki kaɗan dan zai koma Kano makaranta. Dole dai ya ture tunanin a ƙarshe ya lallaɓata sukaci abincin tare, daga nan suna hira yaga ta fara hamma yace taje ta kwanta. Shi kuma ya ɗakko kayan karatunsa ya fara nazari. Daga baya shima ya kwanta a nashi gado batare da yau ma yama A'isha komai ba.      Kwanakin da suka biyo baya sun cigaba da gudana ne cike da shaƙuwa a tsakanin Abdul-rasheed da A'isha. Domin kuwa cikin hikima irin ta masu ilimi yanata jan ra'ayinta da janta a jiki kamar aboki tana sake sakin jiki da shi. Gayyar yaranta kuwa na anguwa kullum tare da su take yini, a haka suka cika kwanaki goma Abdul-rasheed ya shirya komawa Kano dan kwanakin hutunsa sun ƙare. Gashi yana ƙarshen zango baya buƙatar wasa da karatunsa. A'isha taci kuka sosai har ya dinga jin kamar shima ya tayata, daga ƙarshe dai da ƙyar ya lallasheta ya tafi ya barta zukatansu cike da ɗaci.       A'isha ta koma sukuku da ita, kuma yanzu tana yini ne kawai a gidanta, amma da daddare can gidan su Abdul-rasheed take zuwa ta kwana. Da safe sai ta dawo gidanta sai kuma dare taje can. Tun tana tsangwamar kanta harta saki jiki saboda ƙannensa biyu da suke kusan sa'anni ƴammata. Ga Inna ba ruwanta, faɗanta kawai dai idan anyi ba daidai ba. Sosai A'isha take saka hannu suyi aikin gida tare da su Alawiyya, idan zasu fita ne dai Inna ke hanata binsu, ko in zasu tafi makarantar allo. Tun abin na sakata kuka harta fahimci hakan fa shine ƙa'ida da doka, tunda sauran matan yayunsa bataga suna fita ko'ina ba sai da dalili, dan haka sai ta saki jiki.       Tun A'isha na ƙirga kwanakin tafiyar Abdul-rasheed harta bari, kwanci tashi sai gashi da watanni har huɗu. A lokacin ne Baba ya aika masa wasiƙar tunatarwar yazo gida ko kwana biyu yayi, koya manta yana da iyali ne yanzu. Ya kamata ya dinga sara yana duban bakin gatari. Wasiƙa ta isa ga Abdul-rasheed. Kuma ya gamsu da tunatarwar Baba, sai dai baya son zuwa gida ne saboda kaucewa abinda zuciyarsa da gangar jikinsa ke raya masa akan A'isha. Yana son ya bata damar ƙara fahimtar kanta har gaɓar kammala karatunsa daya rage watanni biyu rak. Dan haka ya maida saƙon wasiƙar baba da amsar ban haƙuri data neman uzirin bashi damar kaiwa zuwa watannin da suka rage masa. Acewarsa karatunsu ya ɗauki zafi a yanzu kuma suna gab da fara jarabawa. Bayan an kawo wa baba amsar Abdul-rasheed dole ya haƙura ya bishi da addu'a, dan ya fahimci manufarshi kai tsaye. Haka kuwa aka ci gaba da rarrafawa har watanni biyun Abdul-rasheed na karatu suka cika. A lokacin ya shirya baro Kanon dabo zuwa Bauchin Yakubu gida. Sun sha kuka sun sha ruɗani shi da amini kuma ɗan uwa Nasiru da ogansa Yaya Zubairu. Daga ƙarshe dai dole suka sallamawa tunda mai rabawa ta raba, sai dai ance sabo turken wawa ne, a wannan gaɓar wannan turke ne kafe da zukatan su Abdul-rasheed. Yaje yayma Innar A'isha sallama, dan dama yana zuwa duk kwanakin mako da yake yi a anguwar kullum safiya gaisheta, hakan yasa abincinsa daga gidansu A'isha kullum kwano ukun nan babu fashi a kwanakin ƙarshen makon. Shiko baya gajiya da godiya da yin kuma cefane ya kai ma Inna. Ya kuma yi ƙoƙari ya lallaɓata ta yarda ya saka Bashir da Tasi'u a makarantar primary da ƴaƴan gidan su Nasiru ne kawai ke zuwa a layin. Inna ta haɗa tsaraba mai yawa sai ƴar sana'ar da amarya kanyi irinta ƙulle-ƙullen kayan lwaɗayi. Haka Nasiru yay masa rakkiya har tasha tare da su Bashir, basu dawo gida ba sai da motar su Abdul-rasheed ɗin ta ɗaga zuwa Bauchi....     _________________      BAUCHI A bisa al'adar wannan zamanin zaman mace babu ƙunshi a ƙafa da hannu kamar wani zunubi ne. Kahama kitso ƙa'idane wani na tsufa kina sake wani akai-akai. Wannan wajibi ne ga mace mai aure a kowane yare na arewacin ƙasar. Dan haka koda Abdul-rasheed baya nan a duk sanda ya dace A'isha tayi ƙunshi da kitso Inna na sakata tsefe kai cikin matan yayun Abdul-rasheed wata tai mata kitso. Hakama tana yin ƙunshi tare da su dan sukan shirya yinsa ne a tare. Dan haka da wahala ka samu A'isha babu irin wannan tsaftar. Kamar dai yau a jiya Inna ta sakata yin sabon kitso, inda Magajiya ta zuba mata ƙanana masu ƙyau harda na gaba sak dai irin na barebari. Yau kuma suka shirya yin lalle a ƙafafunsu tun safe. Haka kuwa suka sakashi har yamma yana jikinsu. Sai la'asar suka kunce, A'isha batai niyyar zuwa gidanta ba yau sam dan haka ta ɓararraje suna hira da sauran facalolinta dan a gidan ɗaya daga cikinsu akai ƙunshin. A dai-dai kuma wannan lokaci Abdul-rasheed ya iso. A gidansu ya sauka kamar yanda ya saba, dan haka Inna ta tareshi tarba mai girma. Cike da hikima irin ta manya yana zaman gaisawa da Baba ta aika akai mata kiran babbar surukarta, a soro suka tsaya, bayan ta gaisheta ta shaida mata Abdul-rasheed ne ya dawo, maza su saka A'isha ta koma gida ta gyara jikinta. Sannan su taimaka mata sauri-sauri su tayata gyara gidan shima kafin ya iso. Ta amsa da ladabi ta fice. Tana zuwa ta gwargwaɗama sauran ƴan uwanta dan haka suka tasa A'isha a gaba. Tana son jin ba'asi babu wanda ya bayyana mata, sai dai sunce umarnin Inna ne hakan. Girman suruka koda matsayin kishiyar uwar miji take girma gareshi a wannan lokacin, dan haka A'isha bata sake tari ba ta bisu, dan yanda Innarta zatai mata magana ko bata umarni ta bi haka Inna itama zatayi tabi dole dan matsayin uwar miji take a garesu.       Dan danan suka taimaka mata da dukkan abinda ya dace, ruwan wankanta kanshi yasha turare kala-kala a cikinsa. Hakama ɗakin suna kammala gyara mata suka baɗesa da turaren wuta. Basu taɓa mata gadon miji ba suka barta ta gyara da kanta suka fice zuwa nasu gidajen lokacin anata kiraye-kirayen sallar magriba. Hakan yasa cike da mamaki A'isha ta fara kici-kicin gyaran baban gado dake matsayin na mijinta Abdul-rasheed, zuciyarta kuwa cike da wasi-wasi akan mike faruwa ne wai? Gashi kafin su tafi sai da sukai mata kashedi akan ta zauna a gida karta ce zata biyosu ta jira. Bata fahimci mi suke nufi ba sai da Abdul-rasheed yay sallama yara biye da shi da kaya niƙi-niƙi. Ita jitai ma kamar ta firgita, dan haka ta fito wuff da fitilar ƙwai a hannu domin haskawa, hakan ya bama Abdul-rasheed damar ganinta fes a cikin sirritaccen hasken mai cike da ƙayatar da mai kallo. Tayi ƙyau cikin atamfa mai tabarma sabon ɗinki ne daga cikin kayan lefenta da sai yau ta saka. Turus ta tsaya tana kallonsa itama kamar yanda yake kallonta, sai dai shi nashi kallon na shauƙi ne da kewa matsananciya. Itako na mamaki ne da ruɗanin bazatar tasa. Sun zubama juna ido harna fin minti ɗaya har yaran nan suka ajiye kayan suka fice abinsu suka barsu dan saurin komawa suci tsarabar daya bayar a basu a can wajen Inna. Sai da aka kabbara salla ne hankalin Abdul-rasheed ya dawo jikinsa. Numfashi ya furzar a hankali yana janye idanunsa daga cikin na A'isha da suka tara ƙwalla, cike da sanyin murya ya furta, “Bani buta kada na rasa salla gaba ɗaya”.       Sukuku ta koma ciki kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki ta ɗakko masa butarsa ta ƙarfe, tazo gabansa ta durƙusa ta miƙa masa. Amsa yay yana kallonta shi dai, dan harga ALLAH sai ya ga ta ƙara masa cika a ido da girma, shi yana can tunaninta na hanashi sukuni da isasshen barci, itako da alama ko'a jikinta daɗinta take ci, ƙaramin murmushi yayi kawai, kafin ya maida hankali yayi alwalar ya fice gudu-gudu sauri-sauri dan har anyi raka'ar farko ma. Sauƙin ma massalacin kusa ne da su gab. Koda aka idar da magriba bai dawo ba, A'isha ma data idar da tata sallar tana zaune shiru, tama rasa miya kamata tayi ita kam, a haka yaro yayi sallama, ta amsa tana miƙewa hannunta riƙe da fitila. Tire ne da kwanika akan yaron, dan haka ta ajiye fitilar tana faɗin, “A'a Salihu kayan nan basu maka nauyi ba?”.         “A'a basuyi ba. Inna ce tace na kawo miki. Tace tana gaisheki sai da safe”.        “To na gode Salihu, amma kace mata ai yanzu ma zan taho gidan nima”.     Shi dai Salihu ya amsa da to ya fice abinsa. Itama dai ta ɗauki turen ta shige da shi ciki. Tuwo ne da miya sai fura damammiya a kwanon sha, ta tabbatar furan Baba ne aka ɗibo, dan Abdul-rasheed akwai son fura kamar Baban. Baki ta kuskure tai sallar isha'i dan an fara. Bayan ta idar ta miƙe, tabarma dake matsayin ta miji dake can saman babban gadon a maƙale ta taka ƙaramin gado zata zaro. Sai dai hannunta yaƙi ya kai, dan dole sai ta hau gadon zaifi mata daɗi amma bata son hawa ta saɓa a ganinta laifi ne. A yanda take ta amsa masa sallamar da yayi, ta cigaba da ɗiɗɗishenta na son ɗakko tabarmar. Inda take ya ƙaraso, ya tsaya a bayanta gab sosai, cike da kulawa da tausasawa ya ce, “Mizaki ɗauka haka Matar Abdul-rasheed?”.         Da yanayin shagwaɓa na wahalar da take sha ta ce, “Tabarman can mana, amma kamar ance ta gudu min na kasa na jawo”.         Hannayensa ya harɗe a ƙirji yana kallonta, ya ce, “To banda abin A'ishatu ai ta miki nisa ne, ga hanya mai sauƙi ki taka gado ki hau ki ɗakko kawai, tanan inda kike baƙya tsoron ma ki faɗo”.           “A'a zan iya a haka, kuma fa na faɗa maka tun ranar hawan gadon nan babu ƙyau”.       “Okay na manta haka ne fa, amma ai nima nace ki hau na yafe miki tun a waccan ranar ko. Kinga nidai sakko na tayaki ni”. Yay maganar yana kamata cak ya sauke ƙasa. Kafin ta ankara ya sakata a jikinsa ya rungume...........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 15_ __________________ _A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._ _me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._ INSTAGRAM 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr CALL/WHATSAPP 👇🏻👇🏻 wa.me/2349030398006 TIKTOK 👇🏻 https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1 Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Zata fara mutsu-mutsu ya ce, “No Matar Abdul-rasheed relax mana, haka matan ƙwarai suke tarbar miji idan ya dawo daga tafiya. Shin bakiyi kewata bane? Wata shida ba kwana shida ba A'ishatul-humairah. I miss you fiye da yanda kike zato”.        “Shi miye A mis ɗin?”.    Ta faɗa cike da jin kunyar yanda ya dabaibaiyeta, gashi yaƙi bata damar fita a jikin nasa yanda take fata. Siririyar dariya yayi yana ɗago fuskarta ya lakace mata hanci. Sai kuma cikin raɗa ya furta, “Nayi kewarki buhu-buhu”.         Itama murmushin tayi kanta a ƙasa. Sai kuma tace, “To wane yare ne kayi?”.        “Turanci”.    Ya bata amsa muryarsa na ƙara shigewa cikin maƙoshi, dan zuwa yanzu ta nutsu ta daina masa mutsu-mutsun son ƙwacewar. Zata ƙara magana ya ce, “Adana tambayoyi nan duk zan amsa ma Matar Abdul-rasheed anjima. Yanzu dai banu ruwa da abinci yunwa nake ji”.      Zabura ta ɗanyi alamar tunawa, sai kuma ta janye jikinta a nashi ta durƙusa har ƙasa ta ce, “Kayi haƙuri ina yini, ka dawo lafiya ya hanya? Ya ka baro mutanen Kano?”.         Idanunsa a kanta yay murmushi, sai kuma ya duƙa batare da ya amsa ba ya kamo kafaɗunta duka da hannu biyu ya miƙar da ita. Sake rungumeta yayi sannan ya amsa mata gaisuwa. Kafin ya rufe da faɗin, “Mutanen Kano duk na gaisheki harda gidaje da motoci. Gaisuwar Inna da tasu Tasi'u kuwa tafi rabin buhu”.              Cike da farin ciki ta ce, “Na gode! Amma miyasa Inna bata biyoka ba dasu Tasi'u. ALLAH kullum sai nayi kuka idan na tuna su”.      “In sha ALLAHU daga yau bazan sake bari hawayen kewar su Inna su zuba ba, zan dinga share su da murmurshi da farin ciki. Su Tasi'u kuwa karki damu zasu zo, Nasiru yace zai kawo miki su. Inna ce dai ba lallai anan kusa ba, ƙila sai kin haihu”.            Ba ƙaramin kunya kalmar sai ta haihun nan ta sakata ba. Dan haka bakinta ya mutu bata sake magana ba daga nan tama zame jikinta daga nashi dake mata daɗi kanta a ƙasa. Tabarmar daya ɗakko mata ta amsa ta shimfiɗa masa, shiko yana faman binta da murmurshi ganin yanda take ta faman sinne fuska dan yace zata haihu. Tsaff ta shirya masa abincin a tabarmar, shima sai ya zauna yaci dan yunwa yake ji sosai.       Yaci ya ƙoshi yasha fura. Itako daya mata tayi tace ta ƙoshi bai takurata ba. Yana kammalawa ta kauda kwanikan, shi kuma ya hau zame kaya yana faɗin, “Saura wanka. Bari nai amfani da ruwan drum ɗin can ƙila yafi ɗumi, tunda naga da alama amarya bata fara girki ba a gidan nan har yanzu”.          “Inna tace ba yanzu ba”.      Ta bashi amsa kanta tsaye. Ƴar dariya yayi da faɗin, “Ƴar gatan Inna kenan, wato ba yanzu ba”.      “Eh mana, sai na ƙara girma tace”. “To Inna ta shirya kayan girki kam dan yau zaki girma”.           Sam A'isha bata wani gane mi yake nufi ba. Shima kuma bai ƙara cewa komai ba ya fita. Koda tace bari tazo ta kai ruwan sai yace ya hutar da ita ta zauna ta jira shi...          Koda Abdul-rasheed ya fito wanka samun A'isha yayi ta ɓingire barci, bai tadata ba ya saka babbar riga a jikinsa ya fita a gidan, bai wani jima ba ya dawo da ledar nama tsire sai ƙamshi yake. Tadata yayi cike da lallaɓawa, zata fara masa shagwaɓar ya barta ita barci take ji ya dai lallasheta taje ta wanko fuska. Naman ya bata yace taci. Da farko kunya ta hanata ci saboda shi. Ganin haka yasa shi fita ya bar mata ɗakin, sai ta samu taci kuwa sosai, ta ɗauki sauran ta ajiye gefe. Ta fito danta kuskure baki ta ganshi zaune a waje, miƙewa yay yana tambayarta mi take so? Tace zata wanke baki ne.        Bakinta ta wanke da gawayi da gishiri kamar yanda Inna ta koya mata tun a gida safe da dare idan za'a kwanta. Shima sai ya amsa yayi duk da yana da brush shi kam, itama kuma ya sayo mata. Suna komawa ɗaki A'isha ta kama gadonta zata haye. Riƙo hannunta yayi, dan haka ta juyo, suna haɗa ido tai maza ta duƙar da kanta ƙasa. “Barci kike ji?”. Ya tambaya cike da kulawa. Kanta a ƙasa ta jinjina masa. Ya ce, “Na baki gado na ki ɗana yau?”.         “A'a ga nawa nima zan kwanta anan, kaima sai ka kwanta a naka”.      “Miyasa baƙya so?”.   “Saboda kowa yana da nashi”. “Toni nazo na ɗana naki?”. “Ai bazai ishemu ba”. “To shike nan ki hau nawa sai ki bani naki”. Bai jira tayi magana ba ya ɗauketa camak ya dire a saman gadonsa bayan ya ɗago labulen. Wani daɗi ya ratsa A'isha, a ranta tace (Ashe gadon daɗi ne da shi haka, kai miyasa ban taɓa ɗanawa da baya nan ba) shi dai dake kallonta bai san abinda take ayyanawa ba ya ce, “To kwanta sai da safe”. Ya zuge mata labulen mai suna zuge shige. Aiko tana ganin ya rufeta ruf ta wani baje a gadon tana murmushi, ALLAH a kwai daɗi, ga taushin katifa gana zanin gado. Ga filo sun zagaye gadon reras har sha biyu gwannin sha'awa, ai saiga hajjaju matar Abdul-rasheed cikin ƴan mintina barci yayi awon gaba da ita. Duk abinda take Abdul-rasheed na kallonta ta tsakanin labulen yana danne dariya. Sai da ya bari barcin ya mata ƙarfi yaje ya rufe gida ya dawo. Duk abinda ya dace tayi matsayin matar gida sai shine yayi. Ya kashe fitilar ƙwan su gaba ɗaya dan baya son kwanciya da haske shi kam sam, sai dai akwai Torchlight a kusa da shi koda yaushe. Labulen ya ɗaga kaɗan ya leƙasata, ganin yanda ta ɓararraje dole ya dara kaɗan yanzun kam. Dan da alama dai gadon nan ya lula da matar Abdul-rasheed ba ƙarya. A haka ya samu ya hau shima ya gyara mata kwanciya, sannan ya zuge labulen suka koma ruff. Haskata ya ɗanyi da fitila, da gaske barcinta take hankali kwance alamar bata da wata matsala, wato babu abinda yakai ƙuruciya daɗi, ita yanzu bata san mi yake ji ba, shiko tsahon watanni yana azabtuwa a kanta. Hora kan nasa kuwa ya zame masa alkairi, dan tabbas da ya taɓata kafin tafiyarsa da bazai iya sati biyu a Kano baizo Bauchi ba. Amma gashi Alhamdullah har ya cika watanni shida ciff ya dawo garinsa na haihuwa dawowa ta har abada, inma da abinda zai sake biyo baya da zai sa ya fita bazai kai kamar wanda yayi a baya ba, duk da yana da burin sake zurfafa iliminsa again. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, tare da kashe fitilar ya ajiyeta gefe ya gyara filo da ƙyau shima ya kai kwance..        Cikin barci A'isha ta fara jin saɓanin abinda bata taɓa ji ba tsayin rayuwarta. Wato hannun mutum a jikinta a firgice ta farka tare da zabura ta ƙwalla masa ƙara. Ƙarar data sashi saurin ɗora hannunsa a saman bakinta ya rufe shi ruff, tare da kamota ya riƙeta a jikinsa da ƙyar tana fisgewa. Babu shakka da ace akwai wani a gidan sai ya jita, ALLAH ya soshi su biyu ne. Da ƙyar ya tausata ta nutsu, bayan ya maimaita mata kalmar shine da Abdul-rasheed yafi sau goma kafin ta fahimta. A hakan ma bata nutsu ba ta saka masa kukan ita ta haƙura zata koma gadonta ta kwanta. Lallashinta yake da iya iyawa da kwantar da kai amma taƙi fahimta. Shi ko yana cikin wani hali, dan haka ya fara mata nasiha da son fahimtar da ita da yaren da zata gane. Ina hajjaju bata gane ɗin ba, daga ƙarshe dai dole ya barta ta sakko a wannan gado kuwa, dan neman shiɗe masa take alamar dai ta riga ta tsorata da shi.     A gurguje Please 🏃🏼‍♀️ >>>>>•<<<<< Wasa fa farin girki tsakanin Abdul-rasheed da A'isha, dan tun yana ɗaukar al'amarin mai sauƙi harya fahimci baya samuwa cikin sauƙi. A washe gari wasan ɓuya ta sanya da shi. Zuwa wani daren yana fita sallar magriba ta sulale itama tabar masa gidan. Koda aka idar da salla bai dawo ba sai da akai isha'i. Nan ɗin ma Baba yabi gida duk dan ya bata dama ta yi barci cikin salama, dan ya fahimci yinin yau gaba ɗaya a ɗarare take da shi ko fara'a batayi ma har yara dake shigowa. Wajen ƙarfe tara baba yace ya tashi yaje gida dare nayi. Haka yay musu sallama shi da Inna ya taho, koda yazo gida ya shiga ɗaki wayam babu A'isha, sai yay tunanin taje bayi ne. Zaman jiranta yayi, duk da yayi mamakin ganin tiren abinci da aka aiko daga gidansu a ƙofar ɗaki, sai shine ma ya shigo da shi ciki. Shiru-shiru babu motsin Indo, dole fa ya miƙe ya fito tsakar gidan da Torchlight a hannu, ya gama haske-haskensa babu alamarta, ƙarshe dai har bayin ma ya leƙa nan ma babu ita. Hankalinsa ne ya tashi, babu shiri ya fito ya nufi gidansu, abinka da ba wani nisa ba, dan can hankalinsa kawai ya bashi zata iya zuwa. Inna da Baba na haramar shigewa suma su kwanta ya shigo, da mamaki suke tambayarsa lafiya?. A ruɗe yace, “A'isha. Naje gida ban sameta ba, na zata tana bayi ne sai dana ga daɗewan yayi yawa na leƙa babu alamarta, ashe ma ban lura bane buta na nan a ɗaki. Sosai hankalin Baba ya tashi shima, sai dai ita Inna abinka da mace sai ta tafi tunani. Ganin suna sallallami tace, “Ku dakata, nasan babu inda zataje tunda ba wani waje ta sani ba daga nan dai sai gidajen ƴan uwanka, kuma dai duk gamu a kusa. Bari mu fara duba nan gidan kota shigo”. Inna ta amshi Torchlight ɗin baba ta fara leƙa ɗakuna tana haskawa. Ilai kuwa sai ga A'isha a cikin yara su Alawiyya ƙannensa da yaran maƙotansu da suke zuwa kwana gidan tana shaƙar barcinta hankalinta kwance. Inna ta ce, “Yau ga ja'ira, ai gata nan tsakkiyar su Nana kuwa tana barci. Bara na tasota”.             Lokaci ɗaya shima Baba tunaninsa ya harba, dan haka yace, “Kinga barta kada ki tasheta Karimatu.”       “A'a ya zakace kada a tasheta Malam. Miye amfanin kwanciyar anan?”.           “Barta ke dai, kai jeka sai da safe”.      Duk da ba haka Abdul-rasheed yaso ba bazai iya musawa ba, cike da ladabi yay godiya ya tafi ransa fal mamakin A'isha. Ya fahimci yarinyar nan so take ta ƙwaɓa masa aiki dai kawai. Ashe labarin da abokinsu ya basu akan tashi matar data dinga komawa gida ma ita ana maidota kasancewar garinsu ɗaya suna masa dariya ashe shima tashi Shatun jiransa take. Tirƙashi akwai aiki kenan dai...........✍🏼 🤣🤣🤣Babban yaƙi kam😂.             _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 16_ __________________ https://chat.whatsapp.com/Kf6jd57OsXHCG7cODNAje6 *_Kowace mace na matuƙar son taga ta gyara kitchen ɗinta kodan ta kalla itama taji daɗi 💃_* *_Dunƙule kuɗin ki saya ne ke miki wahala hajiyata?_* *_Ko tarasu a hannunki ke baki wahala saboda kokin fara sai ki kasa ki kashe?_* *_To kwantar min da hankalinka ƙawata, IMZEED VENTURE ta gama shirya miki komai ta yanda kema zaki mallaki naki cikin sauƙi da rahusa._* _Ta buɗe adashin gata wanda yafi bashi kwanciyar hankali da daɗi, akan farashi mai sauƙi, kaya ƴan zamani, gasu ingattatu. Za'a kai miki a duk inda kike. Kedai naki kawai yin zubi akan lokaci._💃💃 *_Za'a fara zubi 25th October in sha ALLAH 💃_* 20k monthly kayan 100k 10k monthly kayan 50k *_Arha tafi bashi, hakama adashe yafi bashi. 💃 Ga sauƙi abaka tamkar ƙyauta 💃💃😀_* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ......Aiko dai akwai aikin babba ma kuwa. Dan kuwa da asuba dai koda Inna tasa su Alawiyya su rakota gida suna juyawa suka fita tai alwala sai ta shige ɗakin girkinsu dake a tsakar gidan, da yake ba girkin ta taɓa yi ba babu komai a ciki sai icce da aka tara da kayan ruwa da abubuwa da take kaiwa ciki ta aje, anan tayi sallar sai da gari ya waye sannan yaji motsinta zata fara shara. Fitowa yay daga ɗakinsu yana kallonta. Dan massalaci ma kasa zuwa yayi saboda ciwon daya kwana da shi na ciki. Tana ganinsa ta ajiye tsintsiyar zata gudu ya ce, “Kinga yi haƙiri tsaya. Cigaba da shararki in dai nine ma na koma”. Ya koma cikin ɗakin ya ƙyaleta. Baki ta tura itama, ta ɗauki tsintsiyar ta cigaba da sharar.          Haka yau ma sukai wannan yini tana masa wasan ɓuya. Da yaga ta takura a gidan sai ya lallaɓa ya fita ya koma tsohon ɗakinsu dake soron gidansu ya kwanta a can. Abinci ma aikowa yayi aka amsa aka kai masa can duk da kuwa daga gidansu aka aiko. Hajjaju amarya Indo ba jiya taji daɗin gudu ba, yau ma ana yin sallar magriba ganin ya shigo yace zaiyi wanka a lokacin dan bai samu yayi da rana ba, yasan kuma bazai iya barci ba in baiyi ba. A ɗarare takai masa ruwan bayi, yana shiga ta sulale zata gudu, sai dai ta samu ƙofa a rufe ta gidan. Kamar zatai kuka ta juyo ta dawo. Amma mi sai dabarar shigewa ƙasan gado tazo mata. Dan haka sauri-sauri ta shimfiɗa tabarma ta kawo wasu ƙorai da babu komai tasa a gaba-gaba ta yanda bazaka kawo da mutum a ƙarƙashin gadon ba ta shige abinta ta kwanta ko tsoro ma bata ji.       ALLAH sarki bawan ALLAH Abdul-rasheed, hankalinsa kwance ya fito yasan dai bazata iya buɗe gidan ba, koda ya shigo ɗakin bai ganta ba yayi tunanin tana inda ta maƙale ɗazun da asuba. Sai ya ajiye kayan wankan yaje ya lallasota ta dawo, amma mi babu ko alamarta, da sauri ya nufi soro kofa a rufe yanda ya bari, ya sake dawowa ciki neman duniya ba A'isha. Mamaki da tsoro suka kama shi, to ta ina tabi ta fita? (Katanga), zuciyarsa ta ayyana masa. Zama yay yana dafe kansa kawai, dan wlhy kunya yake ji bazai iya zuwa gidansu ba yau kuma. Idan jiya basu gano shi ba ai yau sai su gane. Haka ya haƙura ya miƙe ya tafi massalaci sallar isha'i. Duk abinda yake tana jinsa, daya fita kuma bata kawo a ranta ya fito ba ta fice gidan ta cigaba da kwanciya a ƙarƙashin gadon har barci yay awon gaba da ita anan.      Bayan sallar Isha'i Abdul-rasheed ya dawo, haka ya zauna shiru zuciyarsa na masa saƙe-saƙe, gefe yana ƙalubalantar kansa da rashin haƙurinsa, dan ƙila da bai mata abinda yay matan ba da hakan bata faru ba. Ga tsaraba ma ta kasa zama ta duba sam. In sha ALLAHU zai daure ya riƙe kansa ya bita a hankali. Da wannan tunanin ya ɓingire. Da asuba fitsari ya kama A'isha har yana neman zubowa, dan haka ta fito cike da sukur-sukur ɗin daya tada Abdul-rasheed, dan haka ya haska fitila da tunanin ko ɓera ne ya shigo musu. Amma yana kunnawa ya haske A'isha na fitowa a ƙasan gado. Mamakin duniya ya ishe sa, ya zuba mata ido kawai. Itako tayi tsuru-tsuru kanta a ƙasa tana matse ƙafafu dan fitsarin neman kufce mata yake. Fahimtar hakan da yayi ya saka shi sakin murmurshi, muryarsa a sauƙaƙe yace, “Amshi fitila kije kiyi”.      Da sauri ta amsa kuwa ta fice. Shima ya miƙe ya sauka a gadon yana sauke ajiyar zuciya. Amma lallai yarinyar nan ta cishi wasa jiya. Yanzu nan tana ƙasan gado dama duk bulayin daya dinga yi. Wato ita dai mace duk ƙanƙantarta akwai wayo da dabara. Da wannan tunanin ya fito da buta a hannu, baice mata komai ba ya ɗauki fitila data ajiye zata fara alwala ya wuce bayi, sanda ya fito ta gama zata wuce. Dan haka cike da lallashi ya ce, “Dan ALLAH ki zauna a gida to kada kije ko ina na dawo na baki tsarabarki da saƙon Inna, kada yazam akwai abin lalacewa a ciki kinga zai lalace”.      Kanta dake ƙasa ta jinjina masa. Sannan sum-sum ta shige ciki. Shima yay alwala ya fita. Koda ya dawo da wannan buɗe tsaraba yaja ra'ayinta, har hantsi ya fito ya fita ya sayo mata shayi, sai kuma ga kayan kari Inna ta aiko. Da lallaɓa, da lallashi da kwantar da kai ya samu wannan yini dai aka yi shi lafiya. Da dare kuma ya kafa ya tsare ya nuna mata shi tayi duk yanda take so. Ganin yaƙi kulata da abinda take gudun a yinin ma ko kusa da ita bai zauna ba balle ya taɓa mata hannu sai ta haƙura ta kwanta a gadonta, amma acewarta da ido ɗaya zatai wannan barci. Da yake shi barcin ya fita wayon bata ma san ya kwasheta ba har wanda take tsoron ya zauna a bakin gadon kusa da ita yay mata addu'ar barci sannan ya koma nashi gadon. Wannan sabon yin biris daya ɗauka ya kawo masalaha a tsakaninsu, itama ta sake jiki suka koma kamar da. Sai dai kwana kusan shida kuma yaji fa yana neman halaka, a daren ya kasa haƙuri ya sake maimaita na wancan daren, koma muce abinda yafi na wancan daren dan ya sameta fiye da waccan ranar, sai dai kuma ta fitgice masa dole ya barta batare da cimma buri ba. Daga nan ne fa ta sake birkice masa. A daren washe gari kuwa bata kwana a gidan ba, ta sake gudawa gidansu cikin su Nana ta kwana. Ita kanta Innar da su Nanar basu farga da ita ba sai da asuba da Inna ta tashesu suyi salla. Rasama abin faɗa tayi, yau ma sai tace su Alawiyya su rakata gida kawai.       Kwanakin da suka biyo baya har huɗu A'isha bata daina yo tsere ba. Abdul-rasheed kuma ya zuba mata ido, hasalima ya koma maida hankalinsa batun buɗe wajen ɗinkinsa ya ƙyaleta. Hakama Baba yana sane A'isha a gidan take kwana, amma bai ce komai ba sai dai yayi murmushi kawai. Koda Inna tai masa magana a cikon kwana na huɗun sai cewa yay, “To mizance, tunda shi bashi da haƙuri da kawaicin barin yarinya ta sarara kaɗan ma kenan. Ke kuwa naga kema haka kika dinga yi min Karima, ƙarshe sai da Baba ya rakoki da tsumagiya gidan nan saboda can kike zuwa.”           “Ai kai ka jika Malam, ana maganar arziƙi saika dinga sakko wadda ba'a tambayeka ba. Amma ka bani dabara nima da tsumagiyar zan korata yau. Ina laifin yaron nan ai yayi kawaici ma. Aure wata shida haba ai a yaba masa. Abdul-rasheed da haƙuri da zurfin ciki. Su sauran ƴan uwansa wa yayi wannan haƙurin. Tijjani ma da yafi kowa rashin ta idonsa ko tsallake rana yayi”.  Haka ta fita tana sababi. Baba kuwa sai murmushi yake abinsa kawai...        Washe gari kuwa Inna ta shiryama A'isha tsaff, dan yanzu dai sune iyayen tunda babu wani nata a kusa. Kuma a wannan zamanin nasu na adalci ɗa na kowa ne. Babu wani surukutar mugunta ga matar ɗa da uwar miji, yanda suke ma ƴaƴansu haka suke ma matan ƴaƴansu saboda adalci da ƙyaƙyƙyawar zuciya, haka suma surukan suna ɗaukar iyayen miji iyayensu ba irin na yanzu ba da suke ganinsu kamar koshiyoyi. Kamar ko yanda ta saba ana cikin sallar isha'i sai gata ta shigo soron gidan da sanɗarta. Caraf Inna dake a soron ta dalleta da Torchlight, A'isha tai tsaye cak tsuru-tsuru da idanu, sai kuma ta duƙa tana gaida Inna dake tsaye kawai tana kallonta. Batare da Inna ta amsa mata ba ta ce, “Juya muje”.       Kallonta A'isha tayi kamar zata fasa kuka, Inna ta haɗe fuska kuwa ciɗin-ciɗin. Sum-sum ta nufi ƙofa dan tasan dai yau ruwa ya ƙarema ɗan kada kam. Haka Inna ta sata a gaba har gida da ƴar tsumagiyarta a hannu, badan ta daketa ba sai dan ta tsoratata. Karo na farko da Inna tazo gidan kenan, suna isa ƙofar ɗaki taci karo da buta, ɗauketa tai ta maida gefe suka shiga ɗakin. A mamakinta sai suka samu Abdul-rasheed a ciki kwance a tsakar ɗaki kan tabarma. Ashe ma yana gidan ta fita, baida lafiya, amma saboda wauta saita wayance da ɗaukar buta kamar zata fitsari daga nan ne ta sulale, butar ce Inna taci karo da ita yanzu da suna shigowa. Ganin Abdul-rasheed ɗin a ɗakin kuma yasata fahimtar ma'anar zaman butar a waje. Tashi yay da ƙyar cikin dauriya yana ma Inna sannu da zuwa. Inna dake binsa da kallo ta ce, “Lafiya kuwa ana salla kana gida Abdul-rasheed?”.        “Ba komai Inna kawai banjin daɗi ne, shiyyasa ma ban shigo gidan ba ɗazun da yamma”.      “Subahanallahi, amma shine ja'irar nan ta sulalo ta taho can. Nikam ya zanyi da A'isha jama'a. Mijinki na kwance a gida babu lafiya amma kina guduwa wani waje. A'isha wane haline wannan? Idan baki taimaki mijinki ba wa zaki taimaka. Kina son ki mutu a saki wuta ne? Ko kuwa na shirya naje Kano na gayawa Innarki halin nan da kike yi?”.          Cikin sauri A'isha dake kuka ta shiga girgiza kai. “Dan ALLAH Inna kiyi haƙuri bazan ƙara ba wlhy na tuba”.        “A'a nasan zaki ƙara A'isha. Wata nawa ana abu guda. Ai gara dai na tafi Kanon nan tunda mu baki ɗaukemu iyaye ba. Shima Abdul-rasheed ɗin ne ya ƙyaleki, sai kace wadda tafi ƙarfinka. Kafi son kaita fama da ciwo sai ka halaka kanka ne......”     Inna dai nata sababi ta inda take shiga bata nan take fita ba. Taima A'isha dake durƙushe tana kuka, taima Abdul-rasheed dake zaune kansa a ƙasa kunya da ciwo duk sun dabaibayesa. Sai da tai musu tas sannan ta wuce tana sake jaddama Ai'sha idan ta sake ganin ƙafarta a waje koda da rana ne ma zuwa can gidan saita zane ta, kuma sai ta tafi Kano ta sanarma Innarta. A'isha tasan aka sanarma Inna ai taga boni, dan haka ta sake rikicewa, dan Innarsu akwai zafi sosai tana da faɗa, duk da tana jansu a jikinta idan sukai ba daidaiba bata raga musu, balle ma ita ɗin nan da take kamar ƴar fari. Dan kafin ita Inna ta haifi yara kusan biyar suna rasuwa ne itace ta fara zama, a tsakanin ta da Bashir ma wani ya rasu shiyyasa ta bashi kusan shekara biyar........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 17_ __________________ _A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._ _me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._ INSTAGRAM 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr CALL/WHATSAPP 👇🏻👇🏻 wa.me/2349030398006 TIKTOK 👇🏻 https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1 Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Bayan ficewar Inna ɗakin yay shiru, sai shashshekar kukan A'isha daya cikashi, shi dai Abdul-rasheed yana zaune har yanzu kansa a ƙasa yana saurarenta. Sai da yaga ba dainawa zatai ba sannan ya ɗago cike da ƙarfin hali dan da gaske baida lafiya ya zuba mata idanunsa dake jajur irin na mai ciwo. Muryarsa da sanyi sosai ya ce, “Kibar kukan nan ya isa haka, ko kina son kanki yay ciwo ne?”.     Kanta ta girgiza masa alamar A'a. Ya ce, “To share hawayen ya isa. Kin daiji abinda Inna tace. Ke ko tsoro ma baƙyaji kiyita kai kawo a tsakanin dare. A'isha auren soyayya mukayi bana ƙiyayya ba. Mu da kanmu muka zaɓi juna muka kuma so mu zama ma'aurata ba haɗamu akai ba balle muce an mana auren dole ne. Kina da muhimmancin da bazan iya bari wani ya cutar dake ba balle ma ni kaina. Abinda kike gani yana faruwa tsakanina dake shi ne aure. Ina ga dole zamu fara karatu daga gobe, ba karatun Alkur'ani kawai kike buƙata ba a rayuwa da ibada, duk da Alkur'ani yazo mana da komai, amma dole sai mun haɗa da hadisi sannan zamu san su wanene mu da abinda ya kamata muyi. In sha ALLAHU hakan zai sa ki fahimci minene auren ma kansa”.        Kanta ta jinjina masa, sai kuma cikin rawar murya ta ce, “Kayi haƙuri bazan sake ba. Kuma dan ALLAH ka bama Inna haƙuri, sannan kace dan girman ALLAH kada taje Kano ta faɗama Innata, ALLAH idan ta gaya mata zata iya zane ni, kuma tayi fushi da ni”.       Ƙaramin murmushi yayi, a ransa yana ayyana ga tsoro ga rashin ji. A fili kam sai yace, “Shike nan zan bata haƙuri. Nikam baki min laifin komai ba. Tashi ma kije ki wanke idonki. Kinyi sallar isha'i kuwa?”.         “A'a”.     “To maza yo alwala kizo kiyi. Sai ki matsa min lemon tsamin can a ruwan zafi ai da saura a cikin flaks ɗin ko?”.     “Eh, tun wanda kasha shayi ɗazun ba'a ƙara ɗiba ba ai”.     Yauwa to yi sallar sai ki haɗa min wani shayin nasha kinji. ALLAH yay miki albarka ya shirya min ke ki daina haura katanga, dan nasan yanzu dai Shatuna ta girma, ta girmi haura katanga ta barma ƴan baya ko?”.      Kanta ta jinjina masa, sai kuma ta ce, “Nifa bana haura katanga ALLAH. Kullum ta ƙofa nake fita”.       Dariya yayi yanzu kam. Ya ce, “Oh oh matar Abdul-rasheed tafi Abdul-rasheed wayo”.      Dariya tayi itama tana rufe fuska da tafukan hannunta. A haka ta fita a ɗakin, shiko yana binta da kallo da murmushi...      Bayan A'isha tayi salla ta haɗa masa shayin lemon tsami ya sha. Ita kuma ta haɗa mai madara dan tace bazataci tuwo ba. Shi kuma bazai iya fita sayo mata nama ko kifin daya saba kullum ba. Dan bayi ma da ƙyar ya iya fita yaje. Hira ya dinga janta da shi yanda suka saba. A hankali ta saki jiki tanata masa dariya, dan labarin ƙannenta su Bashir yake ta bata da yaran gidan su Nasiru. Sai da yaga ta fara hamma sannan yace taje ta kwanta.       Maimakon ita shi zaman lalubo litattafan da zai fara mata amfani da su ya shiga yi. Dan dama yana da burin hakan a kanta tuni. Sai da ya ajiye komai sannan yay tashi kwanciyar a ƙasa ma yau, dan bai hau gadon ba. Washe gari kamar yanda yay alƙawari hakan akai. Da hantsi bayan ta kammala aikin gida ya fita ya dawo sukai zaman karatu. A ɓangaren Alkur'ani kam A'isha Alhamdullah, sai gyara na abinda baza'a rasa ba dai. Dan haka ya fara mata da sauran littatafai. Abin nasu kamar wasa sai ya fahimci tana ɗokin karatun, cikin kwanaki kaɗan kuma ta maida hankali. Har takai yanzu karatun ma yafi cinye lokacinta fiye da biyema yara masu shigo mata da rana. Sun ja kwanaki suna karatun yana buɗe mata komai yanda zata fahimta da ƙyau, abinda yake na kunya taita sinne kai sai yayi kamar bai ganta ba ma, a dalilin wannan karatun ya fahimci A'isha ko jini bata fara ba ashe. Eh lallai aiki babba a gabansa, dole kam ta dinga masa gudun fanfalaƙe ashe. Ganin tana fahimta ya haɗa mata da karatun boko, sosai al'amarin ya fara bashi mamaki, dan gaskiya Alhamdullah tana da brain na fahimtar abu da wuri, gata kuma da nacin son karatun.       Satin su uku da fara wannan karatu al'amarin UBANGIJI A'isha ta samu baƙuncin prioud ɗinta a bazata, babu ciwon mara babu komai. Da yake ya karantar da ita hakan sai bata ruɗe ba, sai ma matsananciyar kunya data sata ɓoye masa, ta shiga kici-kicin gyara kanta ita kaɗai. Sai dai ba'ai nisa ba tun a yinin ya ganota. Haka ya zaunar da ita ya sake mata dalla-dalla akan abinda ya shafi jinin haila, ya kuma sake koya mata yanda zata dinga tsaftace kanta da ƙyau. Wato ilimin addini duniya ne, dan kuwa babu mace ƴar gata kuma sarauniya irin mai ilimin addini, mata mu farka dan ALLAH musan kammu, ba'ace karki boko ba, amma ki tuna shifa bokon nan amfaninsa nada iyaka, shiko wannan da muke ɗauka ƙauyanci da shine za'a mori rayuwa mafi tsada dake can gaba garemu. Ba zaki gane wannan zancen ba sai randa mala'ikan mutuwa ya ƙwanƙwasa miki ƙofar amsa kiran ALLAH wlhy😭.          Kwanaki uku A'ishatul-humairah tayi, a kwana na huɗu tai wanka abinta ta koma salla, sai da ta koma sallar ne ma Abdul-rasheed ya fahimci baƙo dai ya tafi, ya zaunar da ita ya mata tambayoyi akan yanda ta tsaftace kanta. Tana ɓoye-ɓoyen fuska ta sanar masa da komai. Shi dai nashi dariya ne. Fara ɗinkinsa da samuwar aikin koyarwa ta rage masa zaman gida, sai dai kuma a ɗan tsakanin ya gama shiryama tsuntsuwarsa. Dan kuwa a wani dare na juma'a ya maida Shatunsa cikakkiyar mace. Ya dai sha rigima mai saka ciwon kai da rakinta. Haka yayta lallashi da riritawa, dan sai da ya koma komai shike mata a wannan yinin. Ya kuma sanarma Inna cewar A'isha ta kawo mutuncinta, bawai da baki ko gatsal ba, a'a ya sayi abubuwa ne ya kai ma Innar, kansa a ƙasa ya furta, “Saƙo ne da za'a kai can gidansu A'isha, ai musu godiya da karamci”.        Wannan batu nashi kai tsaye ya fahimtar da Inna ina ya dosa, dan wannan al'adace mai girma da a wannan lokacin baka da dalilin ɓoyewa kodan mutunta matarka da kimanta iyayenta a idon naka iyayen.      Sosai Inna ta nuna farin ciki tare da sanyawa A'isha albarka matuƙa itama. Shi dai Abdul-rasheed kansa a ƙasa yana amsawa a laɓɓa. Ƙanwar mahaifinsu da suke kira Gwaggo Gaji aka aika aka kira, itace taje can wajen A'isha domin bata kulawa. Anan kuma Inna ta shiga haɗa garar arziƙi itama bayan ta sanar da Baba wannan daddaɗan labari. Ba A'isha kawai aka shiryama garar arziƙi ba, harda mutanen Kanon dabo. Dan abubuwa sosai aka haɗa aka tada ɗan aike tun daga Bauchi har Kano gidansu A'isha shaidar ta kawo mutuncinta gidan aurenta, hakan kuma shine zai ƙarama iyayenta nutsuwa da farin ciki. Dan kuwa abin zai baka mamaki, sanda ɗan saƙo yaje da wannan albishir guɗe-guɗe aka dinga yi a gidan Inna. Daga ƙarshe aka raba kayan arziƙin da aka aiko aka dinga kaisu gidajen maƙwafta da abokan arziƙi. Suko sai gasu suna shigowa taya Inna murna da barka da arziƙi. Dan kuwa ashe anata ƴan ƙananun magana tun bayan auren A'isha cewar ba'aji komai daga dangin miji A'isha takai budurci ba, ashe-ashe angon mai kunya ne da kamun kai. Sai ko aka shiga yabonsa dan ya nuna dattako mai girma. Ita kanta Inna ranta fes, dan harda hawayenta tayi sosai a wannan gaɓar. A'isha ta gama biyanta, ita kaɗai ƙwalli ɗaya mace dama gareta.               ________★            Anan Bauchi ma dai A'isha taga gata tako ina daga gidan su Abdul-rasheed dama dangin mahaifiyarsa. Dan labari har Maiduguri, haka suma kuwa suka haɗo garar arziƙi aka kawo mata har Bauchi. Bawai ana zancen bane haya-haya, a'a cikin hikima ne irin ta manya kawai. Kamar dai yanda Abdul-rasheed ya nuna alama ga Inna ta hanyar sayen abubuwa masu daraja yakai yace a aika su Kano gidan su Ai'sha ai musu godiya irin ta mutuntawa. Bayan ƴan kwanaki ta miƙe, sai dai ƴar kunya tsakaninta da Abdul-rasheed, shi dai nashi lallashi da lallaɓa. Gashi yanzu an bata girki, zata fara girki da kanta a gidanta an daina kawo mata daga gidan surukanta kuma.         Wannan shine tushe kuma mafari, na fara gina sabuwar ƙyaƙyƙyawar rayuwa tsakanin A'isha da Abdul-rasheed data ninka ta farkon aure matuƙa. Kuɗi suka fara shigo masa ta ɓangaren albashinsa na aiki da harkar ɗinkinsa. Lokacin da suke cika shekara ɗaya da rabi da aure ya gyara gidan Baba sannan ya ƙara gyara nashi, ba wani gini ne sabo kona zamani ba, a'a buhunan siminti ya saya aka shafe ko'ina ginin laka ya ɓoye. Bai tsaya anan ba suma ƴan uwansa ya fara bin nasu gidajen yana gyarawa. Ya kuma dinga ƙara musu jari a harkar sana'o'in su. Bai tsaya anan ba ta kai har haihuwa idan anyi musu shine mai ɗawainiyar komai, yaransu kuwa ya ɗiba yakai makaranta. Baba kuwa ya hanashi yin komai hatta zuwa gidan Sarki yin hidima. A haka rayuwa ta shura suka cika shekara biyu cif da aure, sai kuma lokacin ne ALLAH ya bama A'isha ciki. Abdul-rasheed yayi farin ciki ƙwarai da gaske da wannan ciki, hakama A'isha da sauran dangi, sai dai kunya tanasa su ɓoye a gaban kowa sai sun keɓance.          A shekarar 1972 data kasance shekarar cikar samun ƴancin ƙasa goma cif, auren A'isha da Abdul-rasheed cikin na uku cikin jikin A'isha ya fara haramar fitowa duniya, domin kuwa ya tsufa sosai, dan ma abinka da cikin fari ga ƙuruciya harkokinta take kai tsaye kamar bata jin nauyinsa, sai dai Abdul-rasheed shi yayta tausayinta da hanata wasu abubuwan musamman idan yana gidan, dan wani lokacin koya hana daya fita take tashi tayi, idan ya dawo yana faɗan ba yace ta bari ba, sai ta marairaice tace ba ita tayi ba su Alawiyya ne, dole zai haƙura yay shiru..........✍🏼         _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 18_ __________________ LADY'S BEAUTY PALACE SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai?ko kina neman inda za,a gyara maki Kai ne wato saloon To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS BEAUTY PALACE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S BEAUTY PALACE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Lace Hijabs Supplements Kayan yara Saloon Kunshi na salatap Dana zane Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko Sari Zamuyi promo din kayan mu na hijabs da Kuma zuma Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 Whatsapp or call 08169307477 Tiktok Hajara Rabiu (lady's beauty palace) Instagram Hajara Rabiu __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........Ranar 10 ga Oktoba, shekara ta 1972, garin Kobi na cikin Bauchi ya tashi da sanyi mai ɗauke da ƙamshin ƙasa na ruwan da aka sha da asubahi. Saukar ruwan data kasance kusan dai-dai da farkawar A'isha dake gidan su Abdul-rasheed ɗakin Inna tashi a gigice da ciwon mara. Inna ma dai dama ta farka, dan haka tai kanta tana salati, tunfa lokacin aka fara gumirzun naƙuda, makwafciyarsu Inna Salame dake unguwar zoma tuni ta shigo suna kanta ita da Innar, baba nata addu'a a cikin ruwa Inna na amsowa ana bata da sauran saƙe-saƙin ruwan magani da Inna Salame tazo da su. Dama kuma tunda cikin ya shiga watanni bakwai take shansu kala-kala, duk da Abdul-rasheed baya so dole ya haƙura, amma yana ɗaukarta a ɓoye ya kaita asibiti gudun kar su Inna suyi faɗa dan basa so. Shi kuma yana son lafiyar matarsa da kulawa mai tsafta.              Har gari ya waye tangaran, matan yayun Abdul-rasheed ma da maƙwafta suka shigo A'isha bata haihu ba, sai zuwa can hanci ya ɗaga kaɗan, rana ta leƙo kaɗan da yanayin ɗuminta mai daɗi da armashi dake ma mutane daɗi. A cikin ɗakin Inna kukan jariri baƙon duniya ya ratsa kunnen duk wanda ke cikin gidan Baba a wannan hantsi. A take farin ciki ya mamaye fuskokin kowa, dan kuwa dai A'isha ta sauka kenan, UBANGIJI ya kawo iyaka.       “Alhamdulillah!” in ji tsohuwa Inna Salame mai karɓar haihuwa, ta share gumi tana murmushi bayan kammala yanke cibiya. Cikin ɗan hasken ranar daya hudo tagar ɗakin ta Inna ta ɗagashi da ƙyau tana faɗin, “Barka-Barka yar nan kinji, yaro ne, kuma lafiyyayen gaske masha ALLAHU.”      A'isha, sabuwar uwa, ta saki hawayen farin ciki tana kallon yaron ta gefen ido daketa motsi a cikin hannun Inna Salame tana gogeshi zata naɗeshi a farin mayafi na auduga na ɗaukar jariri da Inna ta kawo. Addu'a ta shiga jera masa a zuciyarta, kamar yanda take yi masa tun tana a gaɓar ɗanɗana zafin naƙuda, hakan a gareta koyarwar Abdul-rasheed ce, dan tunda ta samu cikin nan ya ƙara ƙaimi wajen koya mata rainon ciki da fara masa tarbiyya irin ta musulinci tun a ciki, addu'oi yanayi itama tanayi. Inna Salame ce ta shiga gyarata bayan ta mikama Inna baƙon duniya daketa callara kukansa tamkar yana shelantawa ƴan Kobi da garin Bauchi baki ɗaya zuwansa duniya. Sosai wannan haihuwa ta saka mutane da yawa a farin ciki, yaro yasha addu'a kala-kala ga iyaye da kakanni. Yayinda bakin Abdul-rasheed ya kasa rufuwa dan ana haihuwa yara suka je suka sanar masa a ƙofar gida shi da su baba. Dan bayan idar da sallar asuba ya rako Baba gida kamar yanda ya saba, ga ɗan yaf-yaf na ruwa da ake yi har lokacin, shine sukaci karo da Inna a ruɗe zata fita kiran Inna Salame take sanar musu A'isha ce ke naƙuda, tun daga lokacin bai iya barin gidan ba yana nan tare da Baba yana mata addu'a a zuciya.          Bayan ɗan lafawar hayaniyar gidan da saukar garwar ruwan wankan maijego aka kwashe mata zuwa bayi, aka ɗiba na jariri shi kuma zuwa ɗakin Inna. Saura kuma nata ƙoƙarin ɗaura kunu da za'a dama na jego a wuta. Gefe ga kawunan akuyoyi masu ƙyau da Abdul-rasheed ya shigo da su yanzun nan babu jimawa. Ransa fal yake da son ganin A'isha, amma ya daure bai takura ba kada ace ya cika rashin ta ido. Sai ma wajen Baba dake ɗaki daya shiga kamar yanda Inna ta bashi umarni dan a kawo masa abinci ya karya. A lokacin ne aka kawo baƙon duniya daya sha wankan ruwan zafi yay luff a cikin showal yana barcin huce gajiya. Baba ya amsheshi fuska da murmurshi yana faɗin, “Baƙon hantsi ne zance kona asubahi”.       Cikin dariya Inna tace, “Mai tada mutane da asuba dai baƙon hantsi”.     Dariya Baba yayi kaɗan da faɗin, Kinga yaci suna biyu kenan, KIƊA A RUWA MAI TADA HANKALIN DODO”. Abdul-rasheed dake saurarensu ma na ɗan murmushi da cin abincinsa sai dai yana satar kallon ƙyautar da ALLAH ya bashi ta gefen ido. Baba ya furta, “Masha ALLAH, wannan dai gida ka ɗakko abinka baka tafi kalar dangi Kano ba. Gashi nan kamar ranar aka haifi ubansa kwabo-da-kwabo sai hasken fata na ɗaukar magana na kanawa”.       Inna ta ce, “A gida kam ya ɗakko, ni kaina tun kan ma a gogeshi nace wannan Abdul-rasheed sak. ALLAH yasa yayo halinsa shima ɗan albarka”.         “Amin ya rabbi”.    Baba ya amsa mata yana masa addu'a. Sai da ya kammala ya miƙama Abdul-rasheed shi. Kasa amsarshi yayi saboda kunya. Sai da Baba ya ce, “Ka jimin ja'irin kaya, amsheshi mana ka masa addu'a ka sanya masa albarka. Ga dabino ka tauna ka bashi”.       Hannu biyu Abdul-rasheed ya saka ya amshi gudan jinin nashi, kuma tsokar jikinsa daya fito daga masoyiyarsa A'ishatul-humairah. Ƙasa-ƙasa ya saki ajiyar zuciya yana kallonsa. Lallai kamaninsa da yaron a bayyane take, Banbanci kawai shi jinkiri ne ɗan a wanni a duniya kuma mai hasken fata irin ta A'isha, shi kuma uba daya fara nisa a gwagwarmayar rayuwa zuwa yanzun. A cikin zuciyarsa yake faɗin (Zakina kazo duniya a ranar da ƙasarsa ke murnar cika shekaru goma da kwana goma da samun ƴanci, jarumin da aka haifa cikin sabuwar ƙasa mai sabuwar fata. A zahiri ƙasa bata san tana buƙatarka ba, amma ina sha ALLAHU sai ka zama wani ginshiƙin riƙeta a yayin girma da ƙarfin ikon ALLAH. ALLAH yay maka albarka, yasa ka zama mahaddacin Alkur'ani da sauran ilimomin littatafan addini, ka zama mai aiki da su bamai karatu kawai da shagala ba. UBANGIJI ya wadata zuciyarka da soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W) UBANGIJI ya soka damu gaba ɗaya ya yarda da mu. ALLAH yasa ka zama mai jin ƙan iyaye da al'umma, ALLAH ya ɗora nasarar ka akan ta maƙiyanka, ALLAH ya rayaka rayuwa mai tsaho da nagarta, ya shimfiɗa tausayin al'umma a zuciyarka, ya baka zuciyar nema daga halak ya saka maka ƙyamar haramun).        Yana kammala wannan addu'a a zuciyarsa ya tauna dabino kamar yanda Baba ya bashi umarni ya sakamasa a baki. Da farko fuska ya yamutse, sai kuma ya fara motsa ɗan bakin nashi a hankali. Inna dake kallonsu cike da tsokana tace, “Anya wannan mai gidan bazai fini kwaɗayi ba”. Dariya Baba da Abdul-rasheed suka sanya suma. Inna ta sake faɗin, “To jifa yanda ya lamushe abinsa tsaf.”          Nan ma dariyar dai sukayi, kafin baba ya saka Abdul-rasheed yayma yaron huɗuba da sunan da yake da ra'ayin saka masa. Nan ma yayi sannan Inna ta amsheshi ta koma da shi. Abdul-rasheed ya sanarma Baba sunan da yay masa huɗubar da shi, Baba ya sanya albarka tare da tambayar ma'anar sunan. Daganan suka cigaba da hirarsu. Duk yanda Abdul-rasheed yaso ganin maijego a yinin ranar bai yiwu masa ba, sai dare bayan sallar isha'i Inna tana ɗakin Baba kai masa abinci ya samu wuff ya shige, dan kuwa zuwa yanzu babu kowa duk matan yayunsa sun koma gidanjesu da maƙwafta sai kuma gobe idan ALLAH ya kaimu. Sai ƙannensa biyu ƴammata Nana da Alawiyya. Yana shiga ɗakin ya aike su dan kawai ya musu wayo, a bazata A'isha taji ya rungumeta. Kunya ya sakata fara mutsu-mutsun janyewa.       Cikin raɗa ya ce, “Haba Shatuna matar Abdul-rasheed ki barni naji ɗuminki, na samu tubarrakin jego mana. Na rage kewarki ta kwana da kwanaki. Sannu-sannu kinji baiwar ALLAH, ALLAH yay miki albarka, lallai yau UBANGIJI ya azurtani da babbar ƙyauta ta hanyarki, ke mace ce mai daraja da kimar da bata da misali a wajena. Ina fatan kina lafiya babu inda ke miki ciwo ko?”.        Kanta ta jinjina masa alamar eh. Ya ce, “Alhamdullahi, zuwa safe zan roƙi baba ya bari na kaiku asibiti a ƙara dubaku kinji. Goben kuma in sha ALLAHU saƙo zai isa gasu Inna suma na samun jika mai kama da Babansa, yanzu kin yarda na fiki ƙarfin jini ba”.         “Ni ban yarda ba, kawai dan ya ɗanyi kama da kai kaɗan kake cika baki”.       Abdul-rasheed ya yi dariya, yana kallon jaririn da idonsa cike da jin daɗi. “Indo kiji tsoron ALLAH, wato kamar ma kaɗan yayi dani ashe, wannan dai kishi ne kawai kike dani. Amma kowa yaga Zakina yasan photo copy ɗinane ai. Za mu sa masa suna *Haysam*.”       Karon farko ta ɗan kallesa, “Wannan wane irin suna ne? Karfa ace ka sama ɗanka sunan aljanu”.       Murmushi yayi da ja mata hanci kaɗan, “Sunane kamar kowane suna, kuma yana da nashi tarihi shima. Fassararsa na nufin (Zaki). Ina fatan nawa Zakin ya tashi da ƙarfin zuciya da jarumta irin ta baradan Zakuna. Yayi nagarta irin ta mutane masu dattako da tsaftataciyar zuciya, mai jinƙai gana ƙasa da shi, mai ƙyautatawa da girmamawa gana sama da shi. Mai kishin ƙasa da son cigabanta, da haka ina fatan ki bani gudunmawa wajen gina tarbiyyarsa da waɗan nan jimlolin, amma ginshiƙinsu ya zama ilimin addini dana zamani ne”.       Cikin sauke ajiyar zuciya ta ce, “In sha ALLAHU zaka sameni mai biyayya a gareka. ALLAH ya bamu tsahon rayuwa mu da shi mai albarka”.      “Amin ya rabbi Matar Abdul-rasheed, sannan Maman *_Haysam Abdul-rasheed Shehu Kobi_*”.         “Niba mamarsa bace, ga iyayensa nan cike da gida”. Ta faɗa tana kauda kai irin na kunya. Dariya yayi shima da sake rungumeta, kafin sallamar su Nana ta sakashi mata sallama ya fito kamar ba shi ba..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 19_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Washe gari bisa roƙon da yay ma Baba ya amince ya kai A'isha asibiti, an dubata ita da jaririnta aka basu magunguna tare da rubuta masa takardar haihuwa kamar yanda Abdul-rasheed ya buƙata. Daga haka suka dawo gidan. Kwankin zaman bakwai sun cigaba da gudana cikin farin ciki da daɗin rai ga maijego. Tana shan ruwan zafi a hannun Inna Salame anguwar zoma. Sannan tana cin abinci mai inganci daga hatsi da kunu, ga mijinta ya tsaya mata da nama da abubuwa masu inganci da maijego take buƙata bayan namu na gida. Ƴan Maiduguri sun iso kwana biyu da haihuwa. Hakama ƴan Kano mutane uku sun iso saura sai ana gobe suna. Abubuwa fa nata ƙara armashi Alhamdullah, ana gobe suna gida ya gama cika taf da dangi tako ina, tako wane ɓangare kayan arziƙi ne ke shigowa daga ƴan uwa da abokan arziƙi, haihuwa tayi albarka kenan. An raɗama yaro suna da safe tare da yanka ƙatoton rago daga Baba. Sunan daya bama mutane mamaki da tunanin ina Abdul-rasheed ya samo wannan suna, dan kuwa suna ne da ba'a saba jiba a ƙasar hausa. Amma dai kowa yayi addu'a ga jinjiri Haysam, daga haka aka cigaba da shagalin suna. Taro yayi armashi, ya kumayi daɗi yanda ya kamata, anci ansha anyi asuwaki da naman kaji dana sa guda da aka yanka bayan ragon suna. Ita dai A'isha nata ido, dan kuwa ƴar gata take komai sai dai taga anayi, idan ka cire kewar mijinta da ganinsa ke mata wuya yanzu babu abinda ke damunta. Balle ga ƴan uwanta zagaye da ita.      Washe garin suna bisa al'ada dangin A'isha suka wuce da ita Kanon dabo wankan jego, ta samu rakkiya daga wasu a dangin Abdul-rasheed, yayinda shi kuma sai daga baya zai je ganinsu Kanon, dan a yanzu baida damar binsu. Nasiru ma da yazo suna yana nan sai bayan sati zai koma Kano, baiyi aure ba har yanzu, amma na saka ranar auren nasa shida wata ƴar ƙanwar mahaifiyarsu da suke zaune a Kaduna. Tana makaranta ne shiyyasa ake jira ta ƙarasa, kuma yanzu saura kaɗan ɗin ta kammala asha biki in sha ALLAHU...         <<<<<•>>>>>      A yau Inna ta samu baƙuncin sabon jikanta Haysam Abdul-rasheed Shehu da ƴarta mai jego A'ishatu. Ranta fes da farin ciki, hakama su Bashir da suka ƙara girma suna cike da farin ciki. A'isha kam farin cikin ta baya misaltawa, tunda tai aure sai yau ne take zuwa Kano shekara uku ciff. Aiko dole tai kuka, tayi kewar Inna matuƙa mara misali, har tana jin kamar an rabata da itane gaba ɗaya. Dan tasha zama tayi kukan kewar Inna da su Tasi'u. Garama su sunje mata har sau kusan uku hutu. Amma Inna bata taɓa zuwa mata ba. Tun randa aka lulluɓa mata zanin aure sai yau ne suke ganin juna.      Ƴan uwa da abokan arziƙi da maƙwafta da basu sami damar zuwa Bauchi suna ba sunata shigowa ganin jariri ɗan mutanen Bauchi. Yana shan addu'a kuwa daga bakuna masu albarka. Lallai dawowar A'isha Kano ta sake tabbatar da ita ƴar gata ce, dan kuwa jego take irin na ƴan gata masu capacity. Ba aikin fari babu na baƙi sai dai taci abinda take so ta ƙoshi tasha barcinta ta more. Idan kaga Haysam a hannunta abincinsa zata bashi. Amma koyaushe yana bayan Inna. A mata abinci mai rai da lafiya taci tayi nak abinta. Ai kafin kace mi ta ƙara wani uban ƙyau ta murje ta sake haske da cikar jiki. A kuma yanzu ne kayan arziƙi suka ƙara bayyana kansu. Maƙerin budurcin na gaskiya ya bayyana gareta, dan kuwa tana cika shekaru sha takwas ne a duniya. Satinsu uku Abdul-rasheed ya iso Kano da shatara ta arziƙi. Shi kansa yanda A'isha ta koma sai da ya ƙara bashi mamaki, kamar jira take tazo Kanon ta sake canjawa da buɗewa ne. Ga yaronsa Masha ALLAH, shima yayi ɓul-ɓul alamar yana samun kulawa mai daraja a wajen Inna kakar ƙwarai. Sai yaji ƙaunar tsohuwa Inna ta ƙara girma a zuciyarsa da daraja irin ta uwa mahaifiya bawai suruka uwar mata kawai ba. Satinsa ɗaya ya koma Bauchi. Daga nan sai yazamto duk bayan sati Uku yake zuwa ganinsu. A haka sukai arba'in uku ciff, arba'in uku kuwa kwana 120 kenan, watanni huɗu har Haysam ya fara ɗan wayo na jarirai. Daga nan aka fara shiryama A'isha komawa, bayan ta zagaya dangin uwa dana uba, sai dai ta jinkirta har akai bikin Nasiru da matarsa kuma ƴar uwarsa. Ƴan Bauchi sunyi kara sosai dan sunzo, a lokacin ne kuma yan Bauchin suka koma da ita, amma tare da rakkiyar danginta itama.        Bayan A'isha ta dawo gidan aurenta sun sake gina sabuwar rayuwa da mijinta Abdul-rasheed da ɗansu. Ya ɗauketa zuwa Maiduguri dangin mahaifiyarsa a karo na farko, sun yo musu sati har biyu. A kuma wannan zuwa ne shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakanin A'isha da Yakura, idan bamu manta ba Yakura dai itace akama Abdul-rasheed tayin aurenta a lokacin bikin ƙanwarsa Khadijah. Yarinya ce mai natsuwa da hankali, ga haƙuri da ilimin addini, ga ƙalubalen rayuwa da take fuskanta hannun mijin mamanta saboda marainiya ce babanta ya rasu. A wannan zuwa ma su Baba Kalla sun sake kwaɗaitama Abdul-rasheed auren Yakura, halin daya sake ganinta a ciki kuma yasa ya amsa babu wani jayayya, koda ya tunkari A'isha da maganar tun a can sai yaga tanata farin ciki. Hakan ne ya saka masa nutsuwa yana dawowa ya sanar ma Baba. Baba yayi murna sosai kuwa shima, ya kuma saka masa albarka. Daga haka aka shiga kai-kawon maganar aure. Mata nada ba kishi ne basu da shi ba, zata iya yiwuwa ma sunfi matan yanzu kishi sosai. Sai dai akwai dattaku da kamun kai da sauƙaƙawa zuciya damuwa dama ɗaukar rayuwar aba komai ba. Dan haka A'isha koda ta nuna murnarta a fili a ɓoye tasha kuka, dan kuwa tana son mijinta sosai, amma son da take masa bazai saka ta tauyesa akan ƙarin aurensa ko bijire masa ba, ita dai aljannarta take nema da burin samu a wajen UBANGIJIN da yace ai aure kuma ayi biyayya ga maza, suma kuma su sauke haƙƙokinmu, wanda bai sauke ba kuma zaiga sakamakonsa. Iya ƙoƙari mijinta nayi akan ƙyautata mata da sauƙe hakkokinta dake kansa, ya ɗauki ɗawainiyar Innarta da karatun ƙannenta su Bashir, ga kulawar da Haysam ke samu ta musamman irin ta ɗan gatan ɗa, to mi zaisa kuma ta butulcema ALLAH. Yayta aurensa zata bishi da addu'a da kuma fatan zaman lafiya ita da amaryar. Dan a wajenta Yakura abar a tausayama ce ga duk mai imani. Gefe ɗaya kuma har cikin ranta son Yakura take ji, dan haka kawai ALLAH ya haɗa jininsu....        Haysam nada shekara ɗaya da wata ɗaya akasha bikin Abdul-rasheed da amarya Yakura, itama dai an kawota nan gidan kusa da A'isha, Alhmdllh kuma A'isha tasha yabo ga dangin mahaifin Abdul-rasheed dama na mahaifiyarsa saboda dattakon data nuna ƙwarai da gaske akan auren nan kamar ba ƙaramar yarinya ba. Babu wanda zai ce yaga fushinta ko ɓacin ranta koda a fuska ne, balle wata magana mara daɗi, hatta shi kansa ango Abdul-rasheed ma da take kwana take tashi da shi zakuma ayi kishin a kansa babu wani abun ALLAH wadai da zai ce ya gani daga A'isha, hasalima wani abun ita take dagewa akan ayi. Haka dai akai biki aka tashi lafiya kowa na san barka da sanya alkairi da addu'ar zaman lafiya na har abada.       Tsabar kunyar A'isha da nauyinta da Abdul-rasheed keji bai bar aboki ko ɗaya ya masa rakkiya gidan da nufin sayen bakin amarya ba, hatta kuwa da Nasiru. Haka ya shigo shi kaɗai. Kai tsaye kuma ɗakin A'isha ya nufa, abin mamaki sai ya samu ita harma tayi barcinta, Haysam na jikinta shima yana nashi. Ya jima a kanta tsaye yana kallonta da mamaki, har zuciyarsa na masa tambayar wai kuwa anya A'isha na sonsa? To dole yace hakan, yasha jin tarihin matan abokansa idan zasu ƙara aure akan kishi, amma ita ko da wasa babu abinda ta nuna masa mara daɗi, kuma dai ance kishi nan na mata shike nuna tsantsar soyayyarsu gareka. Haka dai yayta saƙawa da kwancewarsa, daga ƙarshe yay musu addu'a ita da Haysam ɗin ya kashe mata fitila ya fito tare da karo ɗakin ya nufi ɗakin amarya.          Washe gari ma Abdul-rasheed yata zuba ido yaga canji ga A'isha ko'a fuska amma shiru, sai ma wani annuri data tashi da shi da farin ciki. Wanda ya sashi kasa gane daga ina ta samosa. (Bai san daga sallar dare bane. Dan cikin dare ta farka tai alwalarta a cikin ɗaki a botiki, ta shiga kaima UBANGIJI buƙatunta da addu'ar zaman lafiya da kwanciyar hankali ita da amarya da shi, Alhamdullahi kuma ta tashi ranta fes babu wani damuwa balle nauyin zuciya da take fama da shi a kwana biyun nan). Haka yay ta binta da kallo, musamman da zasuyi kari yaga ita da Yakura nata shan hirarsu hankali kwance kamar ma wasu ƙawaye. Kai daga ƙarshe ma sai bar musu gidan yayi, koda ya dawo samunsu yay suna aiki a tsakar gida suna hirarsu cike da nishaɗi da dariya. Ga Haysam a bayan Yakura a goye tana ƙulla aya da gyaɗar saidawa da A'isha keyi. Ita kuma tana girki. Harga ALLAH sai ya sake jin nutsuwar zuciya da kwanciyar hankali, harma da son A'isha yana sake nunkuwa a ransa. Dan haka da daddare ya sake haɗasu yay musu nasiha da roƙon su ɗore a yanda suka fara, su toshe kunnensu daga munafukai, su kauda idonsu daga azzalumai masu haddasa fitina a bayan fage. Sun tabbatar masa zai samesu fiye da yanda yake fata, suma kuma sun roƙeshi ya kasance adali a tsakaninsu mai tsayar da gaskiya. Shima ya amsa da tabbatarwa...        Tabbas Alhamdullah, babu abinda Abdul-rasheed da Ai'sha da Yakura zasu ce a wannan gaɓar sai tarin godiyar ALLAH. Dan kuwa gidan aurensu ya zama gidan farin ciki da ni'imarsu da kwanciyar hankali. Bawai basa kishin bane, sunayi, sai dai kowacce tana yin kishi mai amfani wajen ganin ta ƙyautata ma mijinta a ɓoye batare data sosa zuciyar ƴar uwarta ba. Haka shima mijin na ƙoƙarin yin adalci, wadda yafi so kuwa ya barma ransa ne.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 20_ __________________ _A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._ _me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._ INSTAGRAM 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr CALL/WHATSAPP 👇🏻👇🏻 wa.me/2349030398006 TIKTOK 👇🏻 https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1 Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Sakanni sun zama mintuna, mintuna sun koma awoyi, awoyi sun rikiɗe zuwa kwanaki, kwanaki sun haɗu sun zama sati, satittika sun dunƙule zuwa wata, wattani suka haɗa shekara. Shekaru sun cigaba da shuɗawa. Har amarya Yakura ta cika shekara uku a gidan Abdul-rasheed. Bata samu ciki ba har yanzu, hakama A'isha tunda ta yaye Haysam shekara biyu kenan bata samu wani cikin ba. Abdul-rasheed kuwa nata sake samun ɗaukaka a wajen aiki da kasuwancinsa na ɗinki, dan zuwa yanzu ya koyar da yara da yawa aikin tela, kuma Alhamdullah suma suna cin gashin kansu, ga shagon saida kayan ɗinki ya buɗe duk sati Nasiru na aiko masa da kaya daga kano. Wani lokacin kuma yaje da kansa yayo daga nan yayo zumunci ya siyama Inna kayan abinci ya dawo. Zuwa yanzu kusan duk ɗawainiyar zuri'arsa ta dawo kansa ne. Yayima su Baba yayima yayunsa da ƙannensa, yayi ma dangin mahaifiyarsa, yayima dangin matansa. Sannan ya sauke hakkin gidansa. Haysam yaro ɗan shekaru huɗu a duniya, ya tasa abinsa masha ALLAH, kyakkyawa mai lafiyar jiki ga gatan iyaye dana kakanni, ya tashi yaro mai shiru, mai son karatu da tambaya. Wayonsa ya girmi shekarunsa, damma baida surutu ne. Yana da shekara biyar a duniya kwatsam a ɗan tsakanin sai ga A'isha da ciki, ya salam zo kaga murna wajen Abdul-rasheed da Yakura dama su Baba, cikin A'isha nada wata biyu itama Yakura ta fara nata laulayin, ya rabbi, rasa ina Abdul-rasheed zai saka kansa yayi dan farin ciki, dan harga ALLAH yana matuƙar son yara. Kamar yanda A'isha ta fara samun ciki itace ta fara haihuwa, santalelen yaro namiji a wannan karon ma, mai kammani da Abdul-rasheed shima. Ansha shagali yaro yaci suna Ja'afar. Ja'afar nada wata biyu da kwanaki itama Yakura ta sauka, itama dai ta santalo nata namijin mai kama da Abdul-rasheed, shima dai yaci suna Ma'aruff. Haysam cike yake da farin cikin samun ƙanne da suka tashi tamkar tagwaye, dan kuwa ma tagwayen ake kiransu. Su Ja'afar nada shekara ɗaɗɗaya aka saka Haysam makaranta, dan kuwa ya cika shekaru shida a duniya cif.       Duk da kuwa kafin ma sakashi makarantar tuni ya fara ɗaukar karatu a wajen mahaifinsa da ma A'isha da Yakura. Dan Abdul-rasheed tsaye yake akan tarbiyyar Haysam, sannan akwai shaƙuwa a tsakaninsu mai girman gaske. Akoda yaushe zaka sameshi  zaune a gefen mahaifinsa yana sauraron karatun Alƙur’ani ko labaran tarihi na Annabawa da jarumai. Hakama sauran litattafai dai-dai fahimtar yaro mai irin shekarunsa. Duk lokacin da mahaifinsa ya karanta masa tarihin jarumtar Annabawa data sahabban MANZON ALLAH (S.A.W) irinsu Abubakar As-Siddiq (RA). Abokin ANNABI mafi kusa kuma khalifa na farko, mai haƙuri da sanyin hali Umar Ibn Khattab (RA). Khalifa na biyu, adalin shugaba jarumi kaifi ɗaya. Usman ibn Affan (RA). Khalifa na uku, ya tattara Al-Qur’ani cikin littafi, mai yawan ƙyauta kuma mai sadaukarwa ga bayin ALLAH mabuƙata. Aliyu ibn Abi Talib (RA). Khalifa na huɗu, kuma ɗan’uwan ANNABI, jarumi da baya tsoro sai dai kafirai suji tsoronsa, dan ya basu wuta iya wuta a filin daga, Mijin Nana Fateema ƴar MANZON ALLAH (S.A.W). Ga su Abdulr-rahaman ibn Awf (RA). Irinsu Sa'ad ibn Abi Waqqas (RA). Talha ibn Ubaidullah (RA). Zubair ibn Al-Awwam (RA) ɗan uwan Ummul Muminin Khadija. Bilal ibn Rabah (RA), mai kiran salla na farko jarumi na gaske. Salmanul-farisi (RA) da ire-iren su da yawa da in lissafosu zamuyi da irin rawar da suka taka a musulunci da tsayawa kusa da MANZON ALLAH mu kammu mun san jarumai ne abin koyi da ba Haysam kawai ba ƴaƴanmu ma ya kamata ace muna basu tarihinsu domin su tashi da burin koyi da su ba zindiƙan wannan zamanin ba da yaranmu ke koyi da su koyi mara amfani da amfanarwa. A ɓangaren hikayoyi yana bashi irin nasu Iliya ɗan Mai Ƙarfi, Jatau Ɗan Mariya, Sarkin Zamani, da makamantansu. Dan a wancan lokacin, ana yaɗasu a gidajen  rediyo kamar su rediyo Nigeria da jaridu irinsu Gaskiya tafi Kwabo da sauransu.       Irin waɗan nan tarihi da hikayoyi sunyi tasiri matuƙa a zuciyar Haysam, dan har yana ji a ransa yana son yayi koyi da su wajen hidimtawa addini. Sai dai abinda ke saka lissafinsa ruɗewa shine zamanin da yake saɓanin nasu ne, tunda shi bai zo zamanin yaƙe-yaƙe ba. Dan haka sai yayta jerama Babansa tambaya. Abdul-rasheed kuwa baya gajiya da bashi amsa, tare da kawo masa misalai akan idan su anyi yaƙe-yaƙe a zamaninsu shi kuma zai iya zama Ɗan sanda, ko SOJA ko wani dai aikin kaki domin bama ƙasarsa gudummawa. Ba wani fahimta Haysam yake da ƙyau ba, amma hakan na sashi jin eh lallai zai iya hakan. A haka ya fara makaranta sai abubuwansa suka sake faɗaɗa. Bayan yaye ƙannensa Ja'afar da Ma'aruff iyayensa sun sake samun ciki kusan a tare, amma Yakura ma ta riga A'isha a wannan karon, dan haka ta rigata haihuwar ɗa namiji mai kama da ƴan uwansa. Shima dai yaci suna Bilal, bayan wata uku da kwanaki itama A'isha ta haihu mace. A karo na farko Abdul-rasheed ya samu mace, dan haka taci suna Halimatu mahaifiyarsa Iya kenan suna mata alkunya da (Ummie). Itama dai akasha shagalin sunanta. A wannan lokacin ma Yakura ta sa sake yin gwanne kuma, dan Bilal nada shekara ɗaya ta sake samun ciki, dole A'isha ta cigaba da shayar da Bilal da Ummie a tare, aka bar Yakura da laulayin sabon cikinta har ALLAH ya kaishi haihuwa ta haifi mace itama da taci sunan Inna wato Karimatu suna mata alkunya da (Mommy).           Bayan haihuwar Mommy babu jimawa UBANGIJI ya amshi ran Baba, jiyyar kwanaki biyu rak. Wannan rasuwa ta girgiza wannan zuri'a, barema Inna data koma kamar ta ruɗe. Haka dai akasha kuka da kai-kawo kowa ya haƙura a ƙarshe. Ashe wata na tafe, dan Inna na cikin takaba itama dai ciwo yay mata tsanani, ta matuƙar sakama kanta damuwar rashin baba, ashe itama ciwo ne na tafiya, itama dai a cikar wata na shida da rasa baba tabi bayansa. Su Abdul-rasheed suka sake gigicewa da ƴaƴanta. Nan ma akasha kuka kowa kuma ya haƙura, shike nan gida ya faɗi, an bar su Abdul-rasheed daga su sai dangi. A lokacin Haysam nada shekara goma sha ɗaya a duniya. Yana primary 5, yana shirin gamawa kenan ma, tunda aji 5 ce a lokacin 1983. An gama kukan rasuwar su Baba da Inna babu jimawa itama mahaifiyar Yakura ta rasu, haka suka kwasa sai Maiduguri. Satinsu guda suka dawo ko muce A'isha da Abdul-rasheed suka dawo tare da yara. Yakura sai data ƙara kusan sati biyu ma sannan ya dawo. A lokacin A'isha ta sake samun ciki, cikin daya dinga bata matuƙar wahala, daga ƙarshe ma ta haifeshi a bakwaini, har sai da aka sakashi cikin kwalba na wasu watanni, ita kuma tasha jiyya tamkar bazata rayu ba, mafi yawan mutane idan suka je dubata gani suke kafin su ƙaraso gida za'ace A'isha ta rasu. Abin birgewa kuma Yakura ke jiyyarta kai bakace kishi bace ba sam. Haka dai tasha fama tsahon watanni kafin ALLAH ya bata lafiya ta miƙe tamkar ba'ayi ba, dan kafin cikar wata biyu jikinta ya murje sarai harta fara dawo da ƙibarta. Kamar jira sai ita kuma Yakura ta shiga nata sabon laulayin cikin.          A yanzu dai Abdul-rasheed nada ƴaƴa bakwai a duniya. Haysam, Ja'afar, Ma'aruff, Bilal, Ummie, Mommy, sai autan A'isha Ammar. Family ya haɗu sai dai Alhamdullah. Ga kuɗaɗe Abdul-rasheed na samu na ban mamaki, sai dai baya tarawa kullum cikin hidimar ƴan uwa yake da ƴaƴansu, kai hatta maƙwafta da abokai cin arziƙinsa suke yi, dan mutum ne mai ƙyauta da hidima. Ga dai kuɗi ana wasa da su, amma idan ka cire gidan da yake rayuwa bai ajiye kaddarar komai ba. Hakan kuma bai taɓa damunsa ba bai taɓa kuma damun matansa ba. Ba shi kawai ba su kansu sun koya daga alkairinsa, ko baya kusa sukan yi a madadinsa da ɗan abinda yake basu da sana'o'in su duk da kuwa ƙananu ne. Abdul-rasheed bai taɓa sayen kaddara koda ta fili ya ajiye ba balle gona idan ka cire ta mahaifinsu da yake nomawa, bayan rasuwarsa kuma aka raba musu gado, daya tashi sai ya barma ƙannensa da suke ɗaki ɗaya ma kason sa. Dan a lokacin ne autan ɗakinsu ke shirin yin aure, shima dai ya gado Abdul-rasheed duk tsawon lokacin nan yana yawon karatu ne, daga ƙarshe dai zaiyi aure a yanzu cikin wannan satin. Auren daya taka rawar gani mai ban tsoro da razanin zuciya a zukatan zuri'ar Abdul-rasheed Shehu Isa Kobi dama al'ummar anguwa, kai harma duk wanda yasan wannan sunan wannan aure ya kawo masa tarihin da bazai manta da shi ba.........✍🏼        Shin miya faru ne a wannan aure daya zame ma wannan zuri'a tambari da bazasu manta ba? Wane ajiyayyen tarihi wannan aure zai bari haka?🥲. Kudai kumuje zuwa dan har yanzu a shinfiɗa muke. Cakwakiyar da shagulgula na gaba🏃🏼‍♀️. _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 21_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .......Tabbas an ɗauro auren Umaru lafiya a garin Barno, dan kuwa shi a can ya ɗakko tashi matar da suka haɗu a wajen karatu a Zaria. Su Abdul-rasheed sunyi gangami sun halarci wannan aure a sabbin motocin daya saya musu shi da yayunsa biyu, akan suma sauran zuwa ƙarshen shekara in sha ALLAHU zai saya musu nasu, sannan ya biya hajji zasuje shi da Babban yayansu. Amma rayuwa bata da tabbas, a yayin dawowarsu Bauchi motar Abdul-rasheed tayi haɗari, a ciki kuma shine da yayansa na uku a ciki, sai abokansa biyu da Haysam. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, haɗari ne mai gigitarwa da tada hankalin wanda ya gani, dan kuwa babbar mota ce ta hayesu tsaf. A take ɗaya a abokan Abdul-rasheed da Yayansa suka rasu, dan kuwa sune a gaban motar, abokinsa driver, yayansa a gefensa. Sai Abdul-rasheed da ɗayan abokin da Haysam dake tsakkiyarsu a baya. Wani hikima ta UBANGIJI sai akai kamar anyi wurgi da Haysam ta tagar motar, dan can waje gefe aka tsuntoshi babu rai, yayinda nan su Abdul-rasheed mota ya danne su, shi rabin jikinsa a waje ƙafafunsa zuwa ƙugu na ciki ƙarfen mota ya rabasu kaɗan ya rage ƙugunsa ya rabu da gangar jikin. Yana kuka da kiran sunan ALLAH yana kuma ambatar sunan Haysam da roƙon mutane su taimkesa su duba masa yaronsa karya mutu. (ALLAH sarki ɗa da mahaifi kenan😭, yana cikin azabtuwa amma bata kansa yake ba. Ya ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭 🙏🏼, ka yafe musu laifukansu ya rabbi😭😭).          Da ƙyar aka iya zaro su Abdul-rasheed a wannan mota, akai asibiti da su. Kafin ma a isa ɗayan abokinsa shima ya cika. Shi ko sai da yay kusan awa guda ma likitoci nata kai-kawo a kansa kafin ALLAH ya amshi abinsa. Wannan rana dole ya zama ranar ruɗani da ahalin Abdul-rasheed bazasu manta da ita ba a rayuwarsu. Ranar da ta raba su Haysam da mahaifinsu, ta zo cikin rashin shiri. (Wato mutuwa! Mutuwa! Mutuwa nada tashin hankali ƴan uwana, mutuwa nada gigita ƙwarai da gaske, wlhy bazamu gane wacece mutuwa ba sai randa tazo kammu. Wane shiri kai mata, wane shiri kake mata? Ka kammala baka kammala ba ko bakama fara ba wlhy sai tazo, zuwan da babu ɗaga ƙafa balle jiranka koda na sakan ɗaya danka kammala abinda ka fara😭😭).                  Mata ƴan biki nata kai-kawo anan Bauchi, sai dai jikin A'isha dana Yakura duk a sanyaye kamar marasa lafiya. Ga yawan faɗuwar gaba da suke samu da nauyin zuciya. Ita Yakura sai kowa ke ɗauka ciki ne. Itako A'isha ganin tasha jiyya bata ko jima da miƙewa ba sai kowa ke mata uzirin da sauran nauyin jiki. Sai dai ba haka bane ba, mutane kuma basu gane ba haka bane sai lokacin da labari ya iso cikin Bauchi, tun anayi ƙasa-ƙasa kada su A'isha su fahimta lokacin ma da ran Abdul-rasheed har dai ta fasu bayan rasuwarsa. Dan dole aka kwaso gawarwakinsu huɗu reras idan ka cire Haysam ɗan shekara goma sha ɗaya dake gadon asibiti likitoci na ƙoƙarin ganin sun ceto tashi rayuwar. Hakama matar Ayuba Yayan Abdul-rasheed dake fama da tsohon ciki duk tayi sukuku.          A lokacin da aka shigo da gawar Abdul-rasheed data Ayuba rawa jikin A'isha da ƙus-ƙus ɗin mutane ya fara shiga kunnenta ya fara. Cikin ɗimuwa ta fito daga ɗakinta batare data fahimci inama take ajiye ƙafa da ɗaukewa ba ta durƙushe a gaban gawar mijinta da aka shimfiɗar a ƙofar ɗakin nata, hawaye na zuba kamar ruwan sama da ba ya ƙarewa. Hannunta na karkarwa ta kaishi kan babbar rigarsa da aka rufa masa dake jiƙe da jini ta yaye a hankali, fuskarsa dake da ƴan ƙananun raunuka ce ta bayyana, sai kawai ta tafi luuuu ta kife akan fuskar tashi ta sume musu. Dai-dai faɗuwar Yakura itama data fito daga ɗakinta a guje, ita kam jini ne ya ɓalle mata abinka da mai ciki. Ga matar Ayuba can ma ƙudar dole ta sameta. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, ya rabbi ya rabbi mun tuba, mun tuba ya ALLAH 😭😭.            Gida ya ɗauki koke-koke da ƙyar ake tsawatama mutane. Yayinda aka zubama A'isha ruwa a jiki ta farfaɗo, Yakura kam dole Inna Salame ce a kanta ana ƙoƙarin tsaida jinin daya ɓalle mata. Haka aka shigar da Abdul-rasheed ɗakin A'isha da Ayuba cikin jini babban Yayansu da mai bi masa sukai musu wanka aka shiryasu a tufafinsu na gaskiya. Tufafin da kai da ni suke jiran mu ma. Duk yawan kaya masu tsadar man da kika tara bango guda na drawer da wanda ka tara duk nan za'a barsu dama anan muka samesu. A naɗemu a wannan yankin farin ƙyalle tal kamar yanda a yau akama Abdul-rasheed da Ayuba. Haka ma sauran abokansa biyu an kaisu nasu gidajen ana musu nasu shirin suma...             ALLAH sarki rayuwa kenan, taron biki ya koma taron makoki, da ƙyar aka samu A'isha ta iya sallama da gawar Abdul-rasheed. Yakura kam ma anata ƙoƙarin ceto rayuwar ta ne da abinda ke cikinta. Hakama matar Ayuba. Sauran ƴan uwansu makusanta sunyi sallama da gawar Ayuba da Abdul-rasheed kafin a fita da su ƙofar gida inda aka haɗe da sauran abokansa akai musu salla, sannan aka wuce da su makwancinsu na gaskiya. Makwancin da yake jiranmu ni dake, yanzu ko anjima ko gobe, koma yaushe ne dai sai tazo😭.         Babu wanda hankalinsa ya koma kan batun Haysam sai washe gari. A'isha ta ɗan dawo hankalinta duk da a jiyan ma ba wani kukan shirme take ba. Yaran suna zagaye da su ita da Yakura da aka samu nasarar tsaida jinin daya ɓalle mata tun a jiya da dare. Sai Yakura ta ce, “Yaya ni naga kowa amma banga ɗan albarka na ba tunda gari ya waye”.     A karo na farko A'isha tabi yaran da kallo itama. Su duka biyar suna nan, wanda take goye yana bayan Alawiyya. Cikin girgiza kai ta ce, Mama (dan haka take kiranta kamar yanda yaran ke faɗi) bana jin tun jiya ma ni naga ɗan nan naki ai”.         A ɗan rikice Yakura ta tashi a zaune jikinta na rawa, idonta cike da hawaye ta ce, “Yaya tun jiya fa? Mun shiga uku ni Yakura, dan ALLAH ku nemo min cikin kawun nan ku, Haysam fa tare suke da Babansu Yaya. Kai Ma'aruff tashi maza kira min Kawu Nuhu”.         Ba Yakura dake magana jikinta na rawa ba, itama A'isha rawar jikinta keyi, sai dai kamar wadda aka dokema ƙafafu ta gagara koda tashi balle cewa komai daga inda take. Har ita Yakuran ma tai ƙoƙarin daddafawa ta sauka a gadon tasa Ummi ta taimaka mata. Dai-dai nan Khadijah ta shigo, itama ido luhu-luhu alamar ansha kukan rasa ƴan uwa. Ganin halin da Yakura take ya sata saurin ajiye kwanon fura dake hannunta, dan ganin A'isha bataci komai ba tun jiya gashi yanzu har an kusa sallar azhar shine ta nema fura ta damo ta kawo mata nan ɗakin Yakura da taga ta shigo tare da yara duba ta.          “Yi a hankali Maman Haysam (da yake haka suke ma Yakura alkunya, ita kuma A'isha suce Maman Ma'aruff) kin san da halin da kike ciki, inama zaki ke da akace ba'a son kina dogon motsi”.      Muryar Fauziyya na rawa tace, “Yaya Khadijah Haysam, kin san fa tare suka tafi da Babansu, amma babu wanda yay batunsa tun jiya”.        Sosai gaban Khadijah ya faɗi itama, dai-dai nan Ma'aruff ya shigo tare da kawunsu Nuhu, shima yana jin batun da suke tattaunawar hankalinsa ya tashi, sai lokacin ya tuna cewa lallai tare da Haysam aka wuce da Babansa asibiti, duk da shima babu wani alamu daya nuna yana a raye, amma yaji sanda ake sakashi a ambulance likitan na faɗin zuciyarsa na harbawa kaɗan-kaɗan, shiyasa ma ba'a sakashi cikin gawar su Ayuba ba. Ai babu zama ya fita da gaggawa, kai tsaye asibiti suka wuce shi da su Nasiru. Cikin amincin ALLAH suka samu Haysam ya farfaɗo tun da safe, likitoci nata cigiyar ƴan uwansa an duba kaf sun wuce tun juya kasancewar a rikice kowa yake. Tunda suka shiga ɗakin da Haysam yake kalma ta farko daya fara jeho musu shine “Kawu ina Babana?”.       Babu wanda a cikinsu gabansa bai faɗi ba, amma suka dake cike da mazantaka suka zagaye shi suna lallashi da tambayar jikinsa. Shi ko yaro ne mai wayo, duk da shekarun nashi duka 11 ne a duniya ALLAH ya bashi basira sosai, sai ya ƙi amsa musu ya zuba musu ido kawai. Tausayinsa mai tsanani ya kama Nasiru, dama ga alhinin rasa aboki, kuma amini zagaye da ruhinsa. Sai hawaye sharr suka shiga rige-rigen zubo masa. Kafin ya kauda fuska Haysam ya ganshi.       Kawai sai ji sukai ya ce, “Baban Kano kuka kake yi?”.       Da sauri Nasiru ya shiga girgiza masa kai yana share hawaye. Amma sai Haysam ɗin ya ƙara faɗin, “Babanmu ya rasu ko? Irin rasuwar Baba da Inna da Gwaggon Maiduguri. Dama ranar nayi mafarki ai, dana gaya masa yace nai shiru kada na gayawa kowa mafarki ba gaskiya bane, gashi kuma ya zama gask....”      Ya kasa ƙarasawa sai haɗiyar zuciya. Sai suka ga ya rufe idanunsa kawai. Gaba ɗayansu hawaye suke sosai, amma abin mamaki Haysam ko ɗigon hawaye babu a idanunsa, tunda ya rufe idanun nan shike nan, bai kuma sake magana ba har suka baro asibitin. Koda suka dawo gida mutane nata hamdala da ganin Haysam ɗin yana lafiya sai ƙananun raunuka. Kowa kuma na ƙara jinjina hukuncin UBANGIJI, dan duk wanda ya kalla motar su Abdul-rasheed da yanda su suka kasance, dan su dukansu likafaninsu sharkaf da jini aka bizne su a kabari amma ga Haysam ko babban ciwo babu a jikinsa. Babu wanda zai tunanin za'a samu wani mai sauran rai a motar nan.          Rungume Haysam Yakura tayi tana kuka, amma A'isha ido kawai ta zuba musu. Koda Haysam ɗin yazo gabanta ya zauna bata iya ce masa komai ba, shima kuma bai iya yama kowa magana ba har lokacin. Duk wanda yace kuma yaga kukan Haysam a zahiri game da wannan rashi yayi ƙarya. Sai da dare A'isha ta kama shi a wani ɗan lungu cikin ɗakin Abdul-rasheed yana kuka shi kaɗai a cikin duhu. Hakan na nufin yazo ya ɓuya ne anan baya son kowa yaga yana kuka. A karo na farko taje kusa da shi ta zauna, tare da kamoshi jikinta ta kwantar da kansa a saman kafaɗarta, sai ya sake fashewa da kuka shima ya rungumeta. Itama kukan take yi sosai.        Ranar a ɗakin nan suka kwana ita da shi, tana zaune dangan-gan, shi kuma tun yana a kafaɗarta har tai masa dabara ya zame ya kwanta kansa a cinyarta, a haka gabannin asuba barci ya sacesu su duka. Sai kiran salla ne ya farkar da su........✍🏼 Matan da suka rasa mazajensu ALLAH ya gafarta musu, ALLAH ya baku haƙuri bayin ALLAH, ALLAH ya raya muku zuri'arku ya albarkacesu, yasa su zama masu jinƙai a gareku😭😭🙏🏼. _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 22_ __________________ _A KANO KI KE…? Kina neman inda zaki siyi abinci mai daɗi? Kina ƙiyar yin girki gashi zaki yi baƙi?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daɗi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daɗi akwai a lallaɓa. Kina son ki siyi abincin da zaki ɗauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daɗi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan ɓangare, tazo muku da nau’in abinci kala-kala na gargajiya da na ƙasar waje. Tana siyar da MANDI RICE, GRILL CHICKEN, CHICKEN BIRYANI, FUNKASO, ALELEN GWANGWANI, BREAD POCKET da sauran su. Fannin abin sha akwai natural ZOƁO mai zaƙi, wanda aka yi shi da ingantattun kayan marmari masu ƙara lafiya, akwai wanda bashi da zaƙi domin masu ciwon sugar da masu gudun ƙiba._ _me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram ko TikTok domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ƙasan rubutun nan._ INSTAGRAM 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr CALL/WHATSAPP 👇🏻👇🏻 wa.me/2349030398006 TIKTOK 👇🏻 https://www.tiktok.com/@leemars_delicious?_t=ZS-90ZQJ2mNJKc&_r=1 Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuɗi gida.❤️❤️🫶🏻 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Anyi addu'ar uku, ranar addu'a mutane sun cika fal harma da wanda ba'a sani ba abokan aiki dana kasuwanci na Abdul-rasheed daga gari-gari. A washe garin cikon kwana na huɗu mutane suka fara raguwa. Sai ƴan uwa na jiki kawai da danginsu na Maiduguri sai su Innar A'isha ƴan kano. Bayan addu'ar bakwai ma kowa ya wuce sai su A'isha kawai da Innarta da zata zauna da su. Sai wata ana kiranta Gwaggo Laraba ƴar Maiduguri dake matsayin kamar kaka a wajen su Abdul-rasheed ɗin. Zasu zauna da su har su kammala takaba, koda yake A'isha ce mai gama takaban a kusa. Yakura kam sai in ALLAH ya sauketa lafiya kuma. Gashi cikin ƙarami ne zubar jinin da tayi kuma zai iya sakawa ma ya koma baya.        A yanzu kam Alhamdullah, basu da matsalar abinci da abubuwan buƙatu na rayuwa, dan suna samun ɗauki daga ƴan uwa da abokan arziƙi, musamman ma Nasiru dake yin iya bakin ƙoƙarinsa. Bai gajiya da yawo tsakanin Kano da Bauchi. A haka A'isha ta kammala takaba, sai Yakura dake jan ciki, tana kuma samun kulawa sosai daga Inna da Gwaggo Laraba har ma da A'isha kanta. A tsakanin Haysam ya kammala primary ɗinsa, sai su Ma'aruff kuma daya kamata ace anyi haramar sakasu, amma a ƴan uwan na Abdul-rasheed babu wanda yayi magana. Sai da Nasiru yazo yaga shirun yayi yawa shi ya ɗaukesu ya sakasu, ya kuma ce saura a jira takardar Haysam ta fito shima ya wuce Secondary, ƙananun kuwa Ummi, Mommy, Bilal. Aka sakasu ta allo kamar yanda Haysam ke zuwa. Daga haka ya juya ya koma Kano.       Watan Abdul-rasheed bakwai a cikin ƙasa ALLAH ya sauki Yakura lafiya. Sai dai kuma haihuwa tazo da tangarɗa da tashin hankali, dan tunda dama cikin ya tsufa gata nan ne dai babu isashiyar lafiya. Yau kuma data haihu sai jini ya ɓalle mata. Abu kamar wasa Inna Salame anguwar zoma zata iya tsaida shi, ga su Innar A'isha da Gwaggo Laraba na taimaka mata har abu yaci ƙarfi akace a wuce asibiti. Amma mi babu isasshen kuɗin zuwa asibitin, A'isha ta fita hankali a tashe zuwa gidan babban Yayan su Abdul-rasheed sanar masa, amma sai ya nuna shi wlhy baida kuɗi, hasalima yau haka ya tashi baida ko sisi, sai dai taje wajen ƙaninsa mai bi masa. Shima koda ta shiga ma sai matarsa tace baya nan. Hankalinta ya tashi ta dawo gida, bama ta iya sanar ma su Inna yanda akai ba ta sake fitowa, abinka da babu waya balle ta kira Nasiru dake tsaye akan al'amarin su. Wajen makwafcinsu dake saida dabbobi ta nufa, tace ya taimaketa ya bata kuɗi zasu kai Yakura asibiti idan sun dawo yazo ya kama akuyarta da take kiyo. Bai musa ba ya bata kuɗin, cikin farin ciki ta juya zuwa gida, tana isa aka ɗauki Yakura aka nufi asibiti. Likitoci sunyi faɗa sosai, daga ƙarshe dai suka amsheta.      To ashe wasa farin girki, dan kuwa dai Yakura jiyya ce mai girma a tare da ita. Dan abu tun ana ɗaukarsa na marmari har ya wuce gaban kwatance. Tun ƴan uwa na zarya da bada ɗan taimako har kowa ya naɗe hannunsa ya bar A'isha da Nasiru kawai da Innar A'isha akan al'amarin Yakura. Sai Khadijah da autan su Abdul-rasheed angon da sukai haɗari ran aurensa da suma suke nasu ƙoƙarin duk da ba masu ƙarfi bane, dama dai ƴaƴansu Abdul-rasheed ɗin ne taƙamarsu, yanzu kuma ya tafi abubuwa duk sun tsaya musu. Shima Nasiru ƙarfin hali ne kawai ba wani ƙarfi ne da shi ba, gashi yana shirin tafiya ƙara karatu daya samu scholarship a ƙasar waje. Ana cikin wannan kai-kawo maganar tafiyar tashi kuma ta tashi, da farko yace ya haƙura A'isha taita roƙonsa akan yaje dan ALLAH kada ya fasa. Nan dai su Inna ma suka saka baki haka ya tafi bayan ya ajiye musu ɗan abinda zai iya na iya ƙarfinsa, bayan tafiyarsa matarsa da ƴarsa ɗaya Raihana da bata wuce shekara biyu ba sukabi bayansa.      Tun ana zaman asibiti da Yakura har rashin kuɗi yasa suka tattaro suka dawo da ita gida, Gwaggo Laraba ma ta sulale ta tafi abinta, sai A'isha kawai da Innarta, ga yara har takwas dan yarinyar da Fauziyya ta haifa ma sai A'isha ke shayar da ita. A wannan halin A'isha ta ƙuƙuta ta saka Abdul-rasheed a Secondary school, ta fara sana'ar masa da safe. Sai kuma ƙananun tsogumin ya fara tashi akan zaman Inna, wai ya kamata ya tattara ta koma Kano, rasuwa shekara ɗaya da rabi amma ta tare a gidan ƴarta. ALLAH sarki Inna uwa mai dattaku, haka ta tattara ta wuce A'isha na kuka Yakura dake kwance komai sai an mata da yara nayi ta wuce. Tafiyar Inna baifi da wata guda ba Babban yayan su Abdul-rasheed ya lallaɓo yazo wa A'isha da batun wai yana son ya aureta, dan su haɗu su riƙe ziri'ar Abdul-rasheed. Takaici ya saka A'isha rufe ido tai masa tass, wannan abu da tayi kuma babu bincike mutane da dangin Abdul-rasheed suka sakata gaba saboda shi ya juya maganar a baibai. Haka aka dinga zuwa har gida ana cin mutuncin A'isha, sai dai su haɗe kai da Yakura da bata ɓoye ma komai ba suyita kuka. Ana tsaka da wannan rikicin jikin Yakuran ya rikice matuƙa, A'isha ta dinga bin dangi tana neman taimakonsu amma kowa ya nuna bazai iya ba bai da shi. Sai kawai ta yanke shawarar saida gidan da suke domin takai Yakura asibiti. Abinda ya bata mamaki sai ga ƴan uwan Abdul-rasheed sunyi uwa sunyi maɗaukiya, ƙarshe ma Yayan nan nashi da suke kira da Yayan gandu daya ce yana son aurenta ne ya sai gidan. Haka ta share bata nuna ta damu ba takai Yakura asibiti, ta biya kuɗi za'a mata aiki da tun farko likitoci suka faɗa rashin kuɗi ya hana. Sai dai UBANGIJI mai hikima bayan yin aikin da kwana biyu ALLAH ya ɗauki ran Yakura😭.        Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, wato gigita da magagin tashin hankalin da A'isha ta shiga da Haysam mai ɗan wayo a cikin ƴaƴan ɓata lokaci ne ma wajen zana shi. Dan Yakura haihuwar Haysam ne kawai batai ba. Amma komai da uwa take ma ɗa ta masa. Haka tsakanin Yakura da A'isha zamane na amana da ba'a batun wani kishi. A ranar da Yakura zata koma ga ALLAH ta kama hannun A'isha dana Haysam ta jaddada musu ta bar musu amanar ƴaƴanta. Bata yarda A'isha ta bama wani su Ma'aruff ba a duniya koda ƴan uwanta ne da suke uwa ɗaya. Tace ta baiwa A'isha har abada, ta kuma bama Haysam dake matsayin Babban yaya ya koma Uba a yanzu. A haka ALLAH ya ɗauki rayuwarta hannayensu riƙe a hannunta.        A wannan rasuwa A'isha ta sake tabbatar da lallai suna cikin halin shiga uku ita da waɗan nan yara har takwas, dan kuwa Yakura batai wata biyu da rasuwa ba Yayan gandu ya sake zuwama A'isha da batun auren da yay mata a wancan karon, da tace bata yarda ba yace to ta tattara yara ta bar masa gidansa, ya bata sati ɗaya kacal. Hankalinta ya tashi, ta kira Jamilu autan su Abdul-rasheed ta sanar masa komai dake faruwa, harna sharrin farko da Yayan gandu yay mata, shima hankalinsa ya tashi, dan basu taɓa sanin gaskiyar zancen ba sai yanzu, amma sai yace su koma gidansa dan babu yanda zai yi tunda yayansa ne. Dan haka suka shiga tattare kayansu, abinda zai zama kaya A'isha ta saida shi, sai kayan sakawarsu da abubuwa masu muhimmanci kawai suka koma gidan Jamilu da zama. Sai dai ko wata basu cikaba sabon kalubale ya ɓullo daga matar Jamilu, dan ƙiri-ƙiri ta nuna ita bata yarda da wannan zama ba. Taya tana amaryarya haihuwa ɗaya (dan zuwa yanzu itama ta haihu) ace azo a cika mata gida da ƴaƴa. Rikici ita da mijinta A'isha taga aurensu na neman mutuwa ta shiga tsakani da roƙon Jamilu ya barta ta wuce Kano. Zai tada hankalinsa ta lallaɓasa da nuna masa muhimmancin yin hakan. Badan yaso ba haka A'isha ta hau shiri, da taimakonsa da rakiyarsa A'isha da ƴaƴanta takwas tai bankwana da garin Bauchi ta koma garinta na haihuwa Kanon dabo....         Babu zato babu tsammani Inna ta wayi gari da baƙin Bauchi. Al'amarin ya girgiza mata zuciya, duk da kuwa kullum dama addu'arta ALLAH ya kawo ma A'isha mafita, dan tunda taje rasuwar Yakura ta sake tabbatar da Bauchi bazata zaunu ga ƴar tata ba. ALLAH sarki rayuwa, bayan shekaru goma sha shida A'isha ta dawo gidansu babu Abdul-rasheed a duniya. Tayi aure tana da shekara sha huɗu. Shekararsu goma sha huɗu da Abdul-rasheed, yanzu yana shekara biyu da wasu wattani da rasuwa. Haysam nada shekara goma sha uku da wasu watanni a duniya. Ja'afar da Ma'aruff nada shekara takwas, Bilal nada shida, Ummi nada biyar. Mommy nada huɗu da wata takwas, Ammar nada uku da wata huɗu, sai ƴar da Yakura ta haifa a ƙarshe da taci sunan A'isha suna kiranta MiMi nada ɗaya da rabi. A yanzu A'isha nada shekara talatin da ɗaya ne cif a duniya.       Inna ma ba mai ƙarfi bace, dama Abdul-rasheed ne ke mata komai a yanzu, hatta da karatun su Bashir, dan tunda ya rasu suma su Bashir ɗin karatun ma ya nema taɓarɓarewa sai da Nasiru ya shiga ya fita ya samar musu wani taimako sannan. Ƴar sana'ar koko Inna keyi da safe yanzu, sai daddawa, da itace take ruƙe su ita da su Tasi'u da yake ba zama suke ba a gida koyaushe suna ma makaranta ne a Zaria, yanzu ga A'isha da iyalanta sun ƙaru. Lissafin ya canja ƙwarai da gaske. Ita kanta A'isha tunda ta shigo gidan take tattauna abubuwa a zuciyarta, da yanda rayuwa zata sake kasancewa. Amma dai tasan zama bashi yiyuwa, babban tashin hankalinta karatun yaran, duk rintsi bata fatan karatun yaran ya tsaya musamman Haysam dake jss 2 zai tafi jss 3 ne nan da ƴan watanni. Haka taita lissafi tun a daren da suka iso Kano ko rintsawa batayi ba. Washe gari karatun ya fara mata maimaicin kansa a cikin ƙwaƙwalwa. Ga Haysam tunda suka zo ya tsangwami kansa sai dai ka gansa zaune gefe shiru. Koda yake tunda Yakura ta rasu rashin maganarsa ta sake girmama fiye da bayan rasa mahaifinsu. Ya sake zama mara fara'a da yawan walwala.........✍🏼 _Rayuwa kenan, akowane motsi bawa baya rabo da jarabawa da sabbin ƙaddariri, ALLAH ya baki wuyan ɗauka A'isha🥲._ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 23_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .......Zak-Shadow da su Mammah sun wuce Kano, zasuyi hutu na makwanni har shida. Ashe walima Mammah ta shirya masa. Dan haka suka iske gida cike da danginta anata girki. Ƴan Bauchi dai iya kawunsa ne kawai sai Khadijah da Alawiyya suka zo. Bai damu ba, wanda ya gani ɗin ma sun wadatar. Anci ansha an masa addu'oi kala-kala harda mutanen anguwa.      Bayan kwanaki biyu gida ya koma sai su kaɗai, Zak-Shadow ya sake fahimtar rayuwa ta canja ga mahaifiyarsa, ta tabbata dai bata tare da sabon mijinta. Sai dai yanzun ma bai tambaya ba saboda girmamawa har sai da Mammah ta sanar masa komai a wannan karon da bakinta. Tabbas zuciyarsa ta hasala matuƙa, amma bai ce komai ba dai a zahiri. Itama Mammah data fahimci yanayin nasa sai tai masa nasiha da gargaɗinsa akan kar taji wani abu daga garesa. An riga anyi ya wuce sai a tari gaba. Badan yaso ba yay shiru kamar yanda ta gargaɗe san.       A cikin wannan hutu ya samu damar bibiyar karatun ƙanensa, har zuciyarsa kuwa ya gamsu da yanda komai ke tafiya Alhamdullah. Musamman ma su Ja'afar ƴan Secondary. Ya ji daɗin kuma ganin yanda kasuwar Mammah tai tasiri a gida. Ya ziyarci Malam Zayyanu da abokinsa Malam Datti. Sun masa addu'a sosai da nuna jin daɗin nasarar da ya samu a NDA.      Duk da yana cikin hutu bai daina yin motsa jiki da safe da yamma ba, kamar yadda suke yi a NDA. Wani lokacin idan yana fama Mammah har faɗa take masa ya huta. Yakan yi murmurshi ne kawai ya ce, “Mammah idan banyi ba jikina zai yi ciwo ne”.     Haka dole ta ƙyaleshi har hutunsu ya ƙare, kamar kuma yanda yay alƙawari yaje Bauchi tare da su Ma'aruff cikin weekend. Sun ziyarci kabarin mahaifinsu da Umma har ma da kakaninsu su Malam. Babu wanda yasan yaje a ƴan uwan mahaifinsu sai kawunsu Jamilu kawai, dan basu kwana ba a ranar suka juyo Kano.        A watan Agusta ya koma Jaji, domin yin Young Officers Course, inda ya sake haɗewa da Imran, a wannan karon ma a ɗaki ɗaya suka zauna, dan sai da sukai duk yanda zasuyi aka haɗasu cikin amincewar UBANGIJI. Alhamdullahi sun kamalla course ɗin su a farkon shekarar 1999, daga nan kowa aka turashi inda zai fara aiki. sai dai an samu matsala dan anyi posting ɗinsu waje daban-daban shi da Imran, amma da yake suna da oganni tuni suka nema oga Adetunji suka sanar masa damuwarsu. Shine yay ta kai kawo har aka haɗasu waje ɗaya yanda suke fata, antura su aiki zuwa 82 Division Enugu, inda suka fara rayuwar soja ta zahiri. A can suka gane cewa aikin soja ba na jarumtaka kaɗai ba ne, aikin zuciya da sadaukarwa ne. ★Su Zak-Shadow na Enugu cikin sabuwar rayuwar aikin soja, anan rayuwar Mammah da marayun ƴaƴanta na neman canja salo da fuskantar sabuwar jarabawar rayuwa. Domin kuwa Zak-Shadow bai wuce watanni uku a Enugu ba Tasi'u ƙanin Mammah ya zo kwatsam. Zuwan daya saka Mammah a farin ciki dan tayi tsammanin har abada ta rasa dukkan ƴan uwa a duniya.        Da farko dai kamar abin arziƙi tsakaninta da Tasi'u, dan harda zama ya bata labarin rayuwar da yake ciki ta tashin hankali. Yarinyar daya aura basu ko ƙulla shekara ɗaya ba a rayuwar aure suka rabu, ya shiga halin rayuwa mai tsanani a sabuwar ƙasar da bai san kowa ba, haka ya jure saboda karatun da yake yi. To zuwa yanzu ya kammala, acewarsa har ya samu aiki, yanzu ma yazo gida ne domin wani aiki da zai yi na wata uku ya koma. Mammah ta jajanta masa ta kuma tayashi farin ciki.       Sunyi sati kamar uku a wannan farin cikin kwatsam rana tsaka sai ga Tasi'u da lauyoyi har biyu da wasu mutane, wai yana son a raba gida a bashi nashi kaso. Mamaki ya kama Mammah, ta kalla gida ta sake kallo, tabbas gidansu babba ne, gashi a bakin titi, kusan a yanzu ma gidan yafi duk wani gida na layin ƙyau saboda gyaran da Alhaji Nura yay masa lokacin daya aureta. Da farko ta ɗan so tirzawa tai masa faɗa, ya nuna mata shifa ba yaro bane, sannan gidan nan dai yana da hakki ai kuma dolene a bashi nashi hakki. Ganin yana son su zubar da mutunci a anguwa tace ba damuwa yayi duk yanda yaso, ko ɗaki ɗaya ta samu ALLAH ya amfana zata zauna da yaranta. Haka kuwa akai yayta shiga da fita batare daya bari tasan yaya komai yake tafiya ba. Kwatsam a cikin wata na biyu da zuwansa ta nemeshi ta rasa. Duk inda ya kamata ta bincika kuma tayi amma babu shi. Hankalinta yaso tashi kawunsu yace karta damu kanta, ta barshi duk ma inda yaje zai dawo tunda ba yaro bane. Haka dole ta haƙura ta share. Abin mamaki cikar wata ɗaya saiga wasu mutane wai sunzo gidan nan da take ciki nasu ne an sayar musu, suka nuna mata takardu harma da shaidun gani da ido da akai ciniki da su. Hankalin Mammah ya tashi kwarai da gaske, sai ta rasa inama zata saka kanta dan tashin hankali, kawai ta yanke jiki ta faɗi sai da aka kaita asibiti. Kwananta biyu aka sallamota, abu dai kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba Tasi'u ya saida gida ya gudu. Masu gida kuwa sun bata wata ɗaya kacal suna buƙatar gidan akwai abinda zasuyi da shi.      Wannan tashin hankali ya saka Ma'aruff da Ja'afar sulalewa suka tafi Enugu suka sanar ma Zak-Shadow. Kwatsam babu zato ya gansu, mamaki ya kama shi ya balbalesu da faɗa domin a ganinsa ai kasada ce zasu kamo hanya batare da sanin gari ba su taho. Su dai haƙuri suke ta bashi, Imran dai ya kwacesu da ƙar, shine ya basu abinci sukaci ya basu wajen kwanciya. Zak-Shadow bai saurarensu ba sai dare, anan ne suka sanar masa abinda ke faruwa da halin da Mammah ke ciki, suka tabbatar masa a yanzu ma sunzo ne bada saninta ba, dan sun tabbatar tana can tana nemansu ƙilama hankali a tashe..          Jin wannan zance ya sake ɗaga hankalin Zak-Shadow, haka ya samu da ƙyar da kamun ƙafa aka bashi damar zuwa gida kwana uku kawai. Ya taso ƙanensa gaba suka nufi Kano. Aiko hasashen su ya tabbata, dan sun sami Mammah cikin tashin hankalin rashin sanin ina su Ja'afar ɗin suke, sai kuma gashi ta gansu harda uban gayya Haysam. Kukan dake danƙare da ƙirjinta sai a lokacin ne ta samu ta yi shi. Wannan al'amari ya sosa zuciyar Zak-Shadow matuƙa. Wanda ma bai san fushinsa ba a wannan karon ya gani kwarai da gaske.      Ɗan kuɗin albashinsa da yake faman ajiyar taro da kwabo a account ya kwashe domin sayen fili, sai dai a karo na farko Kano ta fita masa a rai gaba ɗaya, yana son yin nesa da ita nisa mai yawa ko mahaifiyarsa zata samu salama tamkar yanda ta baro Bauchi, amma kuma bai san ina zai maidasu ba, dan haka ya nema shawarar Imran ta hanyar kiranshi a wayar landline. Babu wani ja'in-ja Imran ya bashi shawarar zuwa Abuja kawai, ya kuma haɗashi da yayansa.     A ranar Haysam ya bar Kano zuwa Abuja. Inda da taimakon yayan Imran suka samu fili suka saya. Sauran kuɗin daya rage ya sayi siminti da bulo aka fara ginin ɗakuna ƙwara biyu kacal. Kwana uku aka bashi kawai a wajen aiki, dan haka dole ya koma Kano yabar sauran aikin wajen yayan Imran. Yana zuwa Kano ya sanar ma Mammah komai, mamaki ya kamata sai kuma ta shiga yi masa faɗa akan dammi zai yi hakan. Shi dai kansa a ƙasa kawai yana bata haƙuri ne. Sai da ta kammala yace su fara shiri kawai, nan da kwanaki kamar goma zasu koma can shi kuma ya shirya ya koma Enugu.       Haka kuwa akayi, kwanaki goma bayan komawar Zak-Shadow yayan Imran yazo har Kano da mota ya kwashi su Mammah da yaranta. Tafiyar data sakata kuka sosai, jikin ƴan uwanta yay sanyi da rashin taimakonta da basuyi yunƙurin yi ba har Haysam ɗin ya yanke hukunci. Dan sun so hanata da nuna mata zasu ɗauki mataki tace ba komai zata koma Abujan kawai dan itama bata son zaman Kanon a yanzu.     Wannan shine sanadi kuma mafarin barin Kano dasu Mammah sukai suka dawo Abuja. Ɗaki ne guda biyu kawai, sai aka zagaye gidan da kwanon langa-langa. Dan Zak-Shadow ya nuna baya son taimakon komai daga wani saboda Yayan Imran yaso yin hakan. Shima kuma Imran ɗin yaso yin hakan amma ya haƙura dan yasan wanene Zak-Shadow, idan yace baya son abu to kawai baya so ɗin da gaske.      Yana sake ɗaukar albashin watan ya nufo Abuja, kuɗin yay amfani da su wajen maida ƙannensa duk makaranta, su Ammar ma da ba'a saka ba ya sanya su. Dama Mammah tunda suka dawo bata zauna ba, haka ta dinga shiga tana fita wajen nunama mutane kayan sana'arta ta koli. Sannu a hankali aka fara ganewa, kasancewar sabuwar anguwa ce kafin mutum yaje kasuwa sai yafi ganewa zuwa wajenta sayen abu a sauƙaƙe. Ganin haka ta fara haɗawa da kayan miya, da wannan sana'ar da albashin Zak-Shadow suka cigaba da rike rayuwarsu, idan an samu ɗan rarar kuɗi a sai siminti a ɗan ɗora gini. Kwatsam sai kuma ga wata ƙaddarar ta sake afkawa Zak-Shadow lokacin da yake shekara biyu da fara aikinsu, wai ya buɗe wata gaskiya wani ogansu yayi kutun-kutun an saka shi a prison. ALLAH sarki rayuwa, a wannan gaɓar ALLAH dai ya ƙaddara Mammah kam bazata rasa ranta ba. Dan bama ita kawai ba hatta su Ma'aruff sun shiga wata irin gigitar rayuwa.     Haka Mammah ta dinga bin duk wanda ta sani cikin roƙo da magiya don ganin Haysam ya kuɓuta. Amma ina, Imran ma iya bakin ƙoƙarinsa yake amma al'amarin kamar da wani babban shiri a cikinsa. Hatta su Adetunji sunyi iya yinsu Zak-Shadow bai fito ba. Ga baƙar wahala suna bashi ta tashin hankali kamar sun sami criminal, duk mai hankali yaga wannan al'amari yasan akwai lauje cikin naɗi a ciki, sai dai kai tsaye basu san wa zasu fuskanta suce yayi ɗin ba..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 24_ __________________ LADY'S BEAUTY PALACE SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai?ko kina neman inda za,a gyara maki Kai ne wato saloon To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS BEAUTY PALACE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S BEAUTY PALACE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Lace Hijabs Supplements Kayan yara Saloon Kunshi na salatap Dana zane Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko Sari Zamuyi promo din kayan mu na hijabs da Kuma zuma Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 Whatsapp or call 08169307477 Tiktok Hajara Rabiu (lady's beauty palace) Instagram Hajara Rabiu __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Haysam na samun damar cigaba da zuwa makaranta a rana ta farko bayan an tashesu maimakon gida bakin kasuwa ya nufa, inda ya jima yana zuwa zagaye batare da sanin kowa ba, kai tsaye rumfar wani dattijo da ake kira Malam Zakiyyu ya nufa, malam Zakiyyu kuwa ya kwana biyu yana ganin Haysam, dan in zai wuce yakan gaisheshi, wani lokacin kuma yakan gansa tsaye can nesa yana kallonsa, a farko ma ya dinga tsarguwa ko aiko yaron ake ya cutar da shi, sai daga baya ya fahimci sam ba haka bane, hasalima ba rumfarsa Haysam kaɗai ke laɓewa yana kallon abubuwa ba harda wasu rumfunan na abokan kasuwanci. Yau koda Haysam yazo ya gaida shi sai ya dubesa da murmushi. “A'a ɗan baba dama kai ɗan makaranta ne amma kullum kake zuwa kaita yawo a kasuwa?”.      Haysam baida yawan magana, amma akwai ladabi da girmama manya, gashi yaro akwai na tsuwa. Cike da ladabi ya ce, “Baba yau ne na cigaba da zuwa makarantar dai, da ba'a nan nakeyi ba”.         Malam Zakiyyu ya ce, “Oho to ALLAH ya bada sa'a, sai a dage da karatu kaji, ALLAH yayi maka albarka. Kaga ga wannan maza kaje gida kar Innarka ta nemeka ko”.         Kallon kuɗin Haysam yayi, maimakon ya amsa duk da yasan suna da buƙatarsu, amma sai ya girgiza kansa da faɗin, “A'a baba na gode ba kuɗi nake so ba, da dai zaka min wani taimako”.       Cikin mamaki Malam Zakiyyu ke kallonsa, amma sai ya danne ya ce, “Wane irin taimako ɗan Baba?”.         Kai tsaye Haysam ya ce, “Idan na dawo makaranta ka dinga kasa min kayan nan ina talla cikin kasuwa, idan na sayar na kawo maka kuɗin sai ka bani hakkina”.       Ba Malam Zakiyyu ba hatta maƙwafcinsa Malam Datti sai da ya tsaya yana kallon Haysam, gashi yaro ƙarami da bai wuce shekara sha huɗu ba amma a nutse yake, ga magana kuma irin ta masu dattako a tare da shi. Malam Zakiyyu yayi murmushi, tare da shafa kan Haysam ya ce, “ALLAH yay maka albarka, amma yaro ina iyayen ka? Sannan miya baka sha'awa da yin hakan? Bayan kai ɗan boko ne?”.        Shiru kamar Haysam bazai ce komai ba, da alama baya son faɗar abinda ke zuciyarsa, amma kuma baya son yima Malam Zakiyyu ƙarya, bayan ya jinjina abinda zai faɗar a zuciyarsa ya ɗago ya kalla Malam Zakiyyu. “Baba ni mai neman ilimi ne,  iyayena kuma Mammah ta ce kawai, Babanmu ya rasu. Ina son nayi wannan sana'ar dan na taimaki Mammah ne da ƙannena suma su dinga zuwa makaranta kamar yanda nake zuwa”.      Sosai Malam Zakiyyu ke kallonsa, idanunsa kuwa na cika da ƙwallar tausayi, sai kuma ƙaunar yaron ta kamashi. “ALLAH yay maka albarka yaro ya sunanka?”.        “Haysam! Mammah na kirana Muhammad, Babana yace dani Zakinsa”.     “Tabbas gaskiya mahaifinka ya faɗa kai zaki ne Muhammad Haysam. A ina gidan naku yake?”. “Anan bakin kasuwa ne baya kaɗan, gidan kakarmu ne Inna mai Koko”.       Malam Zayyanu daya ɗan shiga nazari ya ce, “Ko gidan su Bashir? Dan ana kiran mahaifiyarsu da Inna mai-koko”.        “Eh nan, kawuna ne”.     “ALLAH yay maka albarka Haysam, kaje gida yanzu, gobe idan ALLAH ya kaimu kazo zan fara kasa maka kaya”.       Wannan kalma taima Haysam daɗi, dan kuwa a karo na farko su Malam Zayyanu suka ga murmushin sa, cike da farin ciki ya nufi gida, ya iske Mammah ta kammala wanki tana saurin shirin tafiya gidan aiki dan ta isa da wuri saboda a ƙafa take zuwa sai ta dawo a abin hawa, wata rana ma idan babu kuɗin a ƙasan take zuwa ta dawo a ƙasa, ƙafafunta duk sunyi fashewar faso, haka hannunta duk yaja ruwa saboda azabar wanki, amma bata damuba, yaranta dai suyi farin ciki shine matsalarta.. Kayan makaranta kawai Haysam ya cire yayi wanka ya zauna cin abinci batare daya gayama kowa ba, Inna na masa hira shi dai nashi saurare, idan kuma yaso ya bata amsa, amma amsar tafi yawa a uhhmm ko eh ko a'a.            Kwatsam bayan sallar magriba saiga mahaifin su Nasiru ya shigo gidan yake sanar da Inna cewar wani baƙone keson yin magana da su iya da A'isha. Abin bai ba Inna mamaki ba, dan kwana biyun nan mutane keta aikowa akan suna son A'isha da aure amma tace ita ba aure ne a gabanta ba yanzu yaranta ne. Itama Inna kuma batace mata komai ba dan tasan gaskiya ta faɗa, ina zata tabar waɗan nan ƴaƴa har takwas duk ƙananu?, waye kuma zai yarda taje masa da su gidansa?. Har A'isha taso ƙin zuwa dan tasan irin masu zuwa neman auren nata ne Inna dai ta matsa mata suka fito soron. Sai dai kuma bayan sun gaisa da baƙo daya kira kansa Malam Zayyanu ya buƙaci a kira Haysam. A'isha da kanta ta leƙa ta kirashi yana tsakar gida yana sakama su Ummi da yayma wanka da kansa kaya. Koda ya fito yaga malam Zayyanu sai tsoro ya bayyana a fuskarsa, ya saci kallon A'isha ya saci kallon malam Zayyanu. Malam Zayyanu na lure da shi, sai yaron ya bashi tausayi ya kuma sake birgesa dan ya fahimci yana tsoron ɓacin ran mahaifiyarsa. Cikin hikima ta manya sai bai fito fili ya sanar dasu yanda sukai da Haysam ba, ya nuna musu hankalinsa da nutsuwarsa ne yasa shi da kansa yake son Haysam ya dinga zuwa yana koya masa sana'ar da yake ta kayan koli da gyaran agogo.        Haysam ya sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya, yana tsammanin Mammah zatai farin ciki sai yaji tace a'a sun gode sosai, amma Haysam karatu yake yi kuma tana son ya nutsu a karatun kawai. A firgice Haysam ya kalleta, sai kawai suka ga yazo gabanta ya durƙusa yana roƙon ta barshi shi dai yana so. Koda ta masa tsawa bai fasa roƙon nata ba, amma A'isha taƙi. Daga ƙarshe zata tashi tabar soron ma Baban su Nasiru ya dakatar da ita. Shine yay mata nasiha da nuna mata illar abinda take son yi, ya kuma tabbatar mata yasan Malam Zayyanu shekaru da yawa, sai a lokacin Inna itama tasa baki, da ƙyar sukaci kan A'isha ta amince. Sai dai Haysam yasha harara dan ta fahimci koma minene da saninsa. Aiko bayan wucewar Malam Zayyanu ta tirke Haysam a ɗaki, bai iya ƙarya ba, dan haka ya sanar da ita komai. Sai kawai ta kamashi ta rungume tana hawaye.           Wannan shine mafarin fara gwagwarmayar rayuwa ga Haysam Abdul-rasheed Shehu, ko da yake ƙarami ne, ya ɗauki nauyi fiye da shekarunsa. Yakan tashi da asuba ya ɗebo ruwa ya cika ko'ina da ruwan saboda yasan Mammah zata nema na wanki, sannan yay shiri ya tafi makaranta. Dama da kayansa na gida a jaka, da'an taso daga can zai wuce kasuwa wajen Malam Zayyanu, ya canja kayansa ya ɗauki tallar ƴan kunne na mata da ɗan kayan koli irin su jambaki, masilla, allura, ƴan kunne, hoda, kwalli, madubi da sauransu. Tausayinsa kesa Malam Zayyanu saya masa fura ko abinci, amma sai yaƙi ci sai ya matsa masa zai tsakuri kaɗan ya tashi ya wuce tallarsa. Haysam da ƙoƙari, cikin ikon ALLAH kafin la'asar sai dai ya dawo da tiren, ko da kaya kaɗan, ayi lissafi a bashi haƙƙinsa ya ɗauki jakarsa da kuɗin sai gida. Idan ya tarar da Mammah ya bata, idan ta tafi wajen aiki ya bama Inna yayi shirin tafiya makarantar allo shida ƙannensa. Ba'a nan Haysam ya tsaya ba, wani lokacin sai dare yayi su Inna sun kwanta da wuri musamman A'isha da ba doguwar hira take ba saboda wahalar kai-kawo sai ya kwaso wankin da ake kawo mata wankau ya hau yi, sai dai kawai su tashi da safe suga kaya fululu a shanye a igiya abin mamaki. Ranar farko da A'isha tai masa faɗa sai Inna ta kwaɓeta, dole tai shiru, Ganin haka sai ya cigaba, sai dai idan Mammah ta ɓoye kayan ne babu yanda zai yi dole ya haƙura, ita kuma tana masa haka ne saboda tasan aikin yafi ƙarfinsa balle ma wanki, dan ma yaro ne mai juriya da ƙoƙari. Ganin ga yanda ALLAH ya saka albarka a tallar tasa sai ya fara ɗan asusu, a cikin sallamar da Malam Zayyanu ke bashi ya dinga ajiye wani abu, da suka ɗan taru ya sai Rula, fensil, biro da ire-iren su kayan karatu ya zuba a jakar makaranta, idan yaje sai ga dinga yima yara talla a ɓoye yace musu yana sayarwa, tun ba'a gane shi ba har aka gane yaran suna saye. Wani mugun malamin su yayi ƙoƙarin hanashi amma headmaster yace a barshi hakan abu ne mai ƙyau, balle kowa yasan Haysam da ƙwazo baya wasa da karatu. Ga ƙoƙarin zuwa makaranta akan lokaci, da wahala ka kamashi da latti ko wani laifin faɗa da wani. In dai kaga yana faɗa an ƙureshi ne gaskiya.        A duk lokacin da Aisha ta kalle shi, sai ta tuna da mijinta. Tana ganin ƙarfinsa, nutsuwarsa, da hakurinsa a cikin ɗanta. A lokacin da wasu yara ke wasa da keke ko tsere, shi kuma yana zaune a ƙarƙashin bishiya yana karatu cikin shiru ko kasuwa cikin zafin rana ko ruwan sama ko sanyi yana yawon talla, a makaranta ma bai huta ba, yazo gida kuma ya tadda hidima, dare lokacin barci amma shi ƙoƙarin rage mata wahalhalu yake dan ita ta huta. Sai dai babu abinda zatace da UBANGIJI sai godiya, domin kuwa da wannan neman na Haysam take hidimar karatunsa data ƴan uwansa, na aikinta da wankau kuwa suci abinci. Ana haka su Bashir suka kammala karatunsu suma suka dawo gida, tana murna mataimaka sun ƙaru sai labarin ya canja, dan kuwa kai tsaye Bashir yace shi aikin soja yake so, shi ko Tasi'u da batun auren wata yarinya da sukai karatu tare yazo musu. Hankalin Inna ya tashi matuƙa da wannan batu nasu, suka dinga lallashin su ita da A'isha amma babu wanda ya saurare su. Burin Bashir bai damesu ba, dan kuwa aikin soja ta daɗe tana jin labarinsa a bakin Abdul-rasheed da yanda yake burin shima Haysam ya zama soja, dan yaso ma daga primary military school kawai Haysam zai yi Secondary ɗinsa, amma burinsa bai cika ba, amma ya barshi gine a zuciyar ɗansa dan har yanzu babu abinda Haysam keso kamar aikin soja, na Tasi'u mai aure yafi ɗaga hankalinsu, dan kuwa wadda yake so ɗin ƴar masu kuɗi ce, suko ina suka ga kuɗin auro masa yar talaka ma balle ta masu kuɗi. Amma sun kaɗa dambu taliya yaƙi fahimta.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 25_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .......A haka Bashir ya nema shiga soja, shiko Tasi'u ya fara shirye-shiryen aure dan gidansu yarinyar sunce zasu masa komai. Hakan kuwa akayi, sun masa komai sun aura masa ƴarsu sun kuma biya musu kuɗin karatu zuwa ƙasar waje, sai dai abin takaici da tausayi ko saka su A'isha a hidimar bikin baiyi ba wai suna masa baƙin ciki ita da Inna, haka akai shagali daga shi sai abokansa sai dangin matar ya tare, bayan sati ɗaya yazo yay musu sallama shi ya wuce ƙasar waje karatu da amaryarsa. A'isha da Inna suka masa addu'a kawai ya buga ƙeyarsa yay gaba abinsa.       Bayan tafiyar Tasi'u shima Bashir ya samu aikin soja, dan haka ya wuce ya barsu, sai dai shi da sanya albarkar Inna da ƴar uwarsa A'isha.... <<•>><<•>><<•>> Lokaci ya ja, shekaru sun matsa Haysam ya kammala js3 ɗinsa ya shiga ss1, a ranar su ta farko a aji wani al'amari ya faru tsakanin malaminsu dasu su Haysam ɗalibai. Suna zaune cikin natsuwa, kowanne da littafinsa a gaban tebur. Malam Sulaiman, wanda ake kira da Mallam Su a kamarantar ya shigo da murmushi yana ɗauke da takarda da kwalkwalinsa kan nan sai ƙyalli yake, bayan ya gama ƙare musu kallo ya basu izinin zama daga gaisuwar da sukai masa ya ce, “Kafin na fara darasi ina da tambaya mai sauƙi ga ɗalibai na sabbi fil a sabon ajin fara girma wato ss”, ya ƙare maganar yana kallon ɗaliban ajin ɗaya bayan ɗaya.        Cike da girmamawa suka amsa da, “Okay Sir!!”.       “Ku gaya min, idan kun girma me kuke son zama?”.      Yara suka fara ɗaya bayan ɗaya. “Ni likita!” “Ni injiniya!” “Ni matuƙin jirgi!”        Wasu ko sun kasa faɗa dan basu san mi zasuce ba. Sai idon malam ya sauka kan Haysam dake zaune a tsakiyar kujerar farko yay shiru idonsa akan bangon littafin Iliya ɗan Mai ƙarfi dake gabansa.        “Haysam ibn Abdul-rasheed Shehu!”. Ya kira sunansa cike da tsokana dan shi mutum ne mai barkwanci. ya cigaba da faɗin, “kai fa? Me kake so ka zama idan ka girma?”       Haysam ya ɗago kai a hankali. Idonsa ya ɗan bushe kamar wanda ke da tunani mai nauyi. Ya ɗan ja numfashi kafin ya ce cikin nutsuwa: “Ni… so nake in zama SOJA Mallam.”          Aji ya ɗan yi shiru na ƴan daƙiƙu, sai wasu yara suka yi ƙaramar dariya, amma Mallam Su ya ɗaga hannu yana nuna musu su yi shiru. Ya ce, “Soja fa? Haysam! Mi yasa soja?” ya maimaita cikin mamaki matuƙa dan a lokacin ba kowa ke son soja ba.       Haysam ya maida idonsa ƙasa kamar bazai ce komai ba, sai kuma a hankali muryarsa na canjawa da alamar rauni ya ce, “Abiy na ne... mahaifina. Yana so in zama soja kafin ya rasu shiyasa ma yake kirana da ZAKINSA, nima kuma tunda ya fara bani labarin su waye soja naji ina so, ina son na zama jarumi, kozan iya kwatantawa daga jarumtar magabatan da suka shuɗe a zamanin MANZON ALLAH da wanda suka biyo baya irin su Iliya ɗan mai ƙarfi”. Ya ɗan yi shiru kaɗan, yana wasa da yatsun sa. “Ban san ko zan iya ba, amma kullum ina jin kamar idan nayi hakan Abiy zai yi alfahari idan na cika burin nan nasa, dan shi yaso zama soja amma gida baza'a barshi ba, shiyasa yay fatan ni na zama na cika masa burinsa.”        Malam Su ya ɗan ɗaga kai yana kallonsa da murmushi mai cike da birgewa, dan harga ALLAH yaron ya ƙara ƙayatar da shi.  Cike da son ƙarfafawa ya ce, “Zaka iya Zaki mazan fama, in sha ALLAHU sai ka iya, sai ka zama abin alfahari ga babanka damu al'ummar ƙasa. Na maka alƙawarin zan taimaka maka in ALLAH Ya yarda.”        Abinda ya bama kowa mamaki sai akaga Haysam yayi murumushi, abinda kuma bai cika yi ba, cike da farin ciki ya ce, “Malam kayi alƙawari?”.        “In sha ALLAHU Zakin babansa in dai ina rayuwa nayi alƙawari. Dan ina da ɗan uwa soja daga yau ɗin nan ma zan bashi labarinka”.       A wannan lokacin babu wanda ya sake dariya. Kowa ya kalli Haysam da wani sabon kallo na girmamawa da tausayi. Shiko ya koma gida da farin ciki ya sanarma Mammah da Inna. A kuma dalilin wannan alƙawari shaƙuwa ta shiga tsakanin Malam Sulaiman da Haysam, har ofishinsa yake zuwa suyita hira da labarin aikin soja. A haka rayuwa ta shuɗa yau da gobe kayan ALLAH. Ranar da Haysam ya kammala Secondary School, Aisha ta kasa boye hawayenta na farin ciki da na tsoron duk a lokaci ɗaya. Domin tana ganin ɗanta zai tashi neman hanyar rayuwa ta girma da gwagwarmayar da tafi ta shekarun ƙuruciyarsa girma da haɗari. Domin zuwa yanzu Haysam ya gama yanke shawarar shiga aikin soja kamar yanda yasha faɗa mata tun bayan alƙawarin da malaminsu yay masa. A duk lokacin da ya faɗa mata haka, sai ta yi shiru na dogon lokaci kafin ta ce: “Ka tafi idan hakan ne ka ga daidai, amma ka tuna da addu’a. Rayuwar soja ba wasa bace Muhammad, sai dai bazan hana ka ba, ba kuma zan tunɓuke maka burin mahaifinka a zuciyarka ba saboda ina jin tsoro, zan cigaba da maka addu'a da karfafawata ALLAH ya fimu sanin abinda ke ɓoye ai, sannan kowane bawa yana rayuwa ne da ƙaddararsa, kwazonsa a cin jarabawarsa ne ke bashi makoma bisa ga rahamar mahaliccinmu.”        To a yau ma aka kammala bikin gama Secondary ɗinsu daya tuna mata cewar lokacin zama soja yayi amsar data bashi kenan. Sai kawai ya durƙusa ya rungumeta tare da faɗin, “Mammah na gode da ƙarfafawarki a gareni a koda yaushe, amma ki sani ni bana zuwa neman suna, amma zanje neman ƙarfi da adalci. Na ga yadda rashin adalci ke cinye mutane, zan so in tashi da takobin gaskiya, ko da zai zama ƙarshena, daga karshen dai na cika burin Abiy na kuma cika nawa burin, na kuma maida sunanki UWAR GWANI ko UWAR MAYAƘI.”        Murmushi Aisha tayi da share hawaye, ta ɗagosa daga jikinta tana mai ɗan dungure masa kai. Murmushi yayi yana mai risinar da idanunsa ƙasa, dama idan kaga sakewa ta musamman ga Haysam to yana a gaban Mammah ne. A'isha dake hawaye itama ta kamo hannayensa cikin nata ta runtse tana addu’a kamar haka, “ALLAH ya taimake ka Muhammad. Ka zama zaki mai adalci kamar yanda mahaifinku ke fata ba wanda ke cin mutane ba. Ka zama ZAKI mai amsa sunan SARKI a rundunar adalci ba Sarkin dabbobi mai mulkinsu ta ƙarfi yana halakasu matsayin abincinsa ba. Ka zama ZAKI mai kassara maƙiya da karya mugayen burunsu da manufofin su. ina fatan wannan  jarumin na Abiy da Umman-Haysam (Yakura) ya zama Zaki wanda rayuwarsa ta samo asali daga haske da nagarta, daga hawaye da fata, daga ƙaunar iyaye da ƴan uwa da nauyin al’umma. Kaje soja da fatana da addu'ata Muhammad, kaje soja da amincewata da farin cikina Muhammad Haysam. Amma ina mai gargaɗinka da shaye-shaye, bana so! Bana so! Bana so Muhammad. Ka kiyaye Zina, tana ruguza bawa da zuri'arsa, bana so! Bana so! Bana so Haysam. Ka yaɗa ilimi ka cigaba da neman ilimi musamman na bautama UBANGIJI, kaga dai zuwa yanzu kayi saukar Alkur'ani, ka samu ilimin hadisi mai yawan gaske, ka haddace litattafai da yawa na addini da koni mahaifiyarku kana koyar dani a yanzu. Ka tuna yan uwanka suna kiranka da suna (DADA) a yanzu saboda kai suke gani madadin mahaifinsu, idan ka ɓata ɗan wani kaima za'aci nasarar ɓata maka su Haysam. Yau babu Innata a duniya shekararta ɗaya kenan da rasuwa, tunda Tasi'u yabar ƙasar nan bamu sake jin labarinsa ba shekara huɗu kenan, an kashe mana Bashir a aikin soja, wanda labarin rasuwarsa yasa Inna yanke jiki ta faɗi bata sake lafiya ba sai da ta koma ga UBANGIJI. Haysam banda kowa sai ALLAH NA, sai ku ƴaƴana guda takwas, kune uwata kune ubana, kune dangina. Babu kalar zagin da bana sha saboda naƙi yin aure, ni kuma bana son nayi aure ne wani yazo ya ƙuntata min rayuwarku koda da harara. A kowace rayuwa zaka tsinta kanka ka tuna kai wanene dan ALLAH Haysam ka tuna”.     Kuka ya sarƙeta, shima sai ya kwantar da kansa a cinyarta yana hawaye. Sun jima a haka kafin ta koma lallashinsu, sai kuma ta koma bashi labarai masu daɗi na rayuwarta da mahaifinsu Abdul-rasheed. A haka su Ma'aruff da a yanzu suma suke js 1 Secondary suka shigo, ba jimawa Ummi da Bilal da Momy suma suka dawo. Ammar da Mimi kuwa ba'a sakasu a makaranta ba har yanzu dai. Aiko zama sukai suka zagaye Haysam da a yanzu suka maida sunansa Dada suna taya shi murnar gama Secondary. Idan ka gansu dole su burgeka su kuma baka tausayi.      Akwai zuminci mai ƙarfi a tsakaninsu, akwai ginanniyar soyayyar juna mai tsafta a zukatansu, akwai shaƙuwa mai rahama a tsakaninsu, akwai tausayi mai yalwa a tsakaninsu. Su ba masu arziƙi bane, amma ALLAH ya basu arziƙin farin ciki da so da ƙaunar junansu, ALLAH ya basu arziƙin JARUMAR UWA mai sadaukar da farin cikinta domin gina nasu. Sun rasa uba amma suna kallon babban yayansu madadin uba a wannan lokacin. Dan kuwa shine ke musu ɗawainiya irin ta uba. A dalilin gwagwarmayar talla daya sha ta kayan koli da kayan karatu dama wasu wahalhalu, da aikatau na mahaifiya da wankau, dama wasu abubuwa da tayi bayan nan, dan akwai gaɓar da aka koreta a aikatau ɗin ma, wankin ya daina yiwuwa saboda ciwo daya kwantar da ita, ɗan abinda suka samu ta koma yin abincin sayarwa safe da rana wani lokacin har tuwo da dare ta fita da shi bakin kasuwa. Kai har dakau A'isha tayi domin iyalanta, haka zatayi surfe ta maida dakan gari hannunta na baroro da fashewa amma bazata kula ba, aikin gona tasha yi ta tasa yaranta gaba suyi a biyasu, sussukar hatsi na gona ta ɗure a buhu a biyata. Ga jiyyar Innarta da ciwo ya kayar, da al'amarin ya ƙwaɓe har itace A'isha tayo a daji ta sayar dan samun abinci da kuɗin maganin Inna dan abinda Haysam ke samowa a kasuwa bawai zai wadacesu bane duka amma yana rage musu sosai dan dashi ake biyan komai na karatunsa dana ƙannensa. Da kuma ALLAH ya sakama abin albarka har ya kafa jarin kansa sai yazama har anan gida ana zuwa nema a saya kayan kolin, daga haka ya barma Mammahnsa wannan sanar kolin har ma da kayan karatu na yara ya maida hankali a zana jarabawar ƙarshe da sukayi yau suka kammala. Sai kuma Alhmdllh yaga a gida ma kamar ALLAH yafi sanyama sanar kayan kolin ma albarka, wannan ƙwarin gwiwa ne ya ƙarfafashi a yau ya sake tabbatar ma Mammah zai je aikin sojan da yake ji da kamar zai fasa saboda kar ya barta da nauyi, amma yanzu yana fata wannan sanar tasa data dawo gida zata taimaka musu sosai.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 26_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Addu'ar mahaifiya ba wasa ba, dan kuwa dai Haysam ya tsallaka ajin jarabawa ko muce ƙaddararsa ta uku bayan rayuwar jin daɗi da iyaye, data maraici da uwa ɗaya tilo, zuwa soja a yanzu, sojan ƙasa mai girma irin ƙasarsa. Matakin ƙaddarar soja dake tafiya da fara shekarun hankali da mallakar kai da kai matsayin cikakken mutum, dan kuwa ya ɗauki hanyar tsallake shekaru ashirin ɗin farko zuwa matakin rayuwa ta biyu a masomin cikar hankali da fara sanin ainahin micece ma duniyar, dan a wancan matakin an san duniyar ne a gaɓar banbance iya abinda ƙwaƙwalwa da zuciya kawai ke iya fuskanta da karamin nisan tunani da hange.      Matakin farko na samun gurbi a NDA (Nigerian Defence Academy), Haysam Abdul-rasheed Shehu ya samu wannan gurbin Karatu da taimakon Malamin nan nasu da yay alƙawari tun shekaru uku da suka shuɗe wato Malam Su. Bayan Haysam ya gama Secondary School da ƙwazo da halin kirki ya samu result ɗinsa na SSCE yayi ƙyau sosai. Cike da zumuɗi ya nufi ofishin Malam Su ya kai masa, ai ko ya tayashi murna ya kuma ce yaje ya shirya a gobe zasuje Kaduna wajen ƙaninsa wanda yake Major a Nigerian Army, wanda kuma yake da alaƙa da masu duba takardun shiga NDA (Nigerian Defence Academy).        Haka kuwa akayi, Mammah tai ɗan cuku-cukunta ta samawa Haysam kuɗin mota da ɗan na guzirin cin abinci, washe gari suka ɗauki hanyar Kaduna. Sun samu tarba ta muntatawa kuwa, bayan sunci sun sha Malam Sulaiman ya gana da ƙaninsa. Bayan ya ƙara tisa masa wanene Haysam, da kwazon yaron da halin manya ya ce,        “Wannan yaron bai da uba kamar yanda na gaya maka tun shekarun baya, amma yana da hali irin wanda ya fi zinariya daraja. Ka taimaka a duba takardunsa ba don alfarma ba, sai don cancanta da tabbatarwa irinsu ƙasarmu ke buƙata, dan an gina wannan burin a zuciyarsa tun kwakwalwar sa na jinjira ita da zuciyarsa. Kai da kanka zaka tabbatar da hakan kuma kayi alfahari da gina rayuwar wannan yaron akan wannan aikin watarana in sha ALLAHU”.         Cikin jinjina kai Major Abdullahi ya ce, “In sha ALLAHU Yaya, nama alƙawarin baza'a samu kowace irin matsala ba. Dan a takardun yaron kawai na tabbatar shi ɗin mai ƙwazo ne. Sannan a wannan zaman awannin da nayi da shi na fahimci abubuwa da yawa atare da shi masu girma da daraja. Kaje in ALLAH ya yarda zakaji labari mai daɗi”.         “Alhamdullahi Na gode Abdullahi, idan kaimin hakan bazan gushe ba ina mai maka addu'a, domin kuwa ka taimakeni wajen cika alƙawarin dana ɗaukama marayan ALLAH.”       Aranar suka koma kano akan za'a neme su... ><><><><><       Bayan bincike da gwaji, an sake kiran Haysam zuwa interview a Kaduna, inda ya nuna basira, nutsuwa, da ilimi mai zurfi har ma jami’an da sukai interviewn ya basu mamaki suka kuma yabama kwazonsa kwarai da gaske. Kamar wasa, sai sakamakon shigar NDA ya fito, sunan Haysam Abdul-rasheed Shehu ya fito cikin jerin waɗanda aka ɗauka. Kwatanta muku irin farin cikin da A'isha da Haysam da ƴan uwansa harma da Malam Sulaiman sukayi ɓata lokaci ne a wannan gaɓar, amma dan musamu mu wuce kowa ya ƙiyarsa a tashi zuciyar kawai.. ^^^^^^^^^^^^^    3/12/1992 shirin tafiyar Haysam ya kammala zuwa NDA, inda A'isha tai ƙoƙari matuƙa ta haɗa masa dukkan abinda aka buƙata daga iyaye. Ta ƙara tisa masa nasihar da a kullum bata gajiya dayi masa shi da ƴan uwansa. Ranar farin ciki ga Haysam ga ahalinsa, ranar kuma kuka da alfahari.       Haysam ya shirya cikin shigar kamala, ya goya jakarsa a baya. Cikin nutsuwarsa yazo gaban Mammah ya durƙusa, gefe A'isha ta kauda kanta kaɗan tana ƙoƙarin maida ƙwallar da suka cika mata idanu, kafin ta dawo da fuskarta garesa tana kallonsa zuciyarta cike da ƙauna da fargabar rabuwa da shi, tunda ta haifesa bai taɓa yin nesa da ita na abinda ya wuce sati biyu ba. Dama dai Mama Yakura ce kan ɗaukeshi suje Maiduguri suyi kwanaki sannan tana raye. Tunda kuma mutuwa ta ɗauke mata ita ta ɗauke mata mahaifinsu kuma bata taɓa nesa da su ba, shine abokinta a yanzu, shene babban ɗa, shine ƙani, shine yaya, shine uba ga ƙannensa, shine ƙawa, dole taji raɗaɗin nesantarsu da zai yi, sai dai bazata iya daƙile hakan ba dan tana matuƙar son shima ya samu cikar burinsa ya kuma cika burin mahaifinsu. Addu'a ta sake masa mai ratsa zuciya cikin danne kuka. “ALLAH ya sa wannan tafiya ta zama alheri a garemu baki ɗaya. Ka tuna da addu’a, ka tuna da asalinka. Idan ka zama soja, ka zama soja mai gaskiya.”       Karo na farko Haysam ya kalleta da idanunsa da sukai jaa, murmushi yay mata irin na kwantar da hankali da ƙarfafawa. “Mammah in sha ALLAHU zan yi kamar yadda kike so koma fiye da hakan. Zan zama soja don na kare ƙasata da al'ummar kamar yanda kika zame mana garkuwa bayan rasa iyaye guda biyu, zanyi haƙuri koda banci ba domin wasu suci, zan sadaukar da farin ciki na dan wasu suyi, zanyi komai da ƙarfin zuciya da ƙarfin addu'arki. Zan kiyaye dokin UBANGIJI da biyayya ga umarnin MANZONSA.”        “ALLAH yay maka albarka”. Ta faɗa kuka na ƙwace mata. Shima idanunsa sun sake yin jazur sai dai babu hawayen. Ƙannensa ma duk sun masa addu'a. Cikin share hawaye Bilal ya ce Dada kada ka daɗe fa... ka dawo da wuri!”          “In sha ALLAHU Bilalu na zan dawo da wuri, kai dai kaimin addu'a”. Yay maganar cike da kulawa yana rungume yaron. Suma sauran duk sai suka matso suka rungume juna, “Ku kula da Mammah, kada ku barta tayi tunani ko damuwa. Kada ku sakata yawan magana ko ɓacin rai. Duk wanda ya dinga mata laifin da zai ɓata ranta babu ruwana da shi kona dawo, sannan bazan masa tsarabar komai ba”.       Kawuna suka shiga ɗaga masa. Ya ɗan jajja musu hanci cikin so da jin kewarsu. Sai suka shiga yin dariya ga hawaye. Shima murmushi yay musu mai sanyi, kafin ya miƙe, kallo ɗaya yay Mammah yaga yanda ta duƙar da kai yasan kuka take, sai ya fice da sauri shima nashi idon na tara hawaye... >>>>>>•<<<<<<<       *_NIGERIAN DEFENCE ACADEMY, KADUNA_*    Haysam ya fito daga motar da jakarsa a kafaɗa, jakar da Mammah ta zuba masa kayan da duk ta tanadar masa, bakinsa da addu'a ya shiga bin tarin sabin ɗaliban dake cike tam da ƙofar gate ɗin tamkar ba safiya ba da kallo. Yaron da aka saba gani cikin damuwar maraici da wahalhalun rayuwa da yawan shiru, yau zuciyarsa cike take da jin daɗin samun cikar buri, da alfahari. Jinsa yake a yau tamkar ya fara wata sabuwar rayuwa, inama Abiy na raye ya gansa a wannan mataki, inama idan ya ɗaga kai ya faɗa domin shi ace kunnensa zasu iya jinsa...       A bakin ƙofar gate ɗin akwai jami’an soja dake tsaye. Kowanne sabon ɗalibi sai an bincika jakarsa, an duba sunansa a cikin jerin waɗanda suka samu shiga. Haysam kuwa na cikin ƴan farko-farko da aka fara kira. Dan dai-dai yana tunaninsa akan Abiy aka ambaci cikakken sunan nasa Haysam Abdul-rasheed Shehu. A karo na farko sai zuciyarsa ta buga da ƙarfi, goshinsa ya ɗan tara zufa, amma cikin dakewarsa ya ɗaga kai da girmamawa ya amsa da nufar inda ake buƙatar ganinsa yana ɗaukar matakin soja na farko a rayuwarsa, shekarar farkon balaga dan yanzu yana da 17years a duniya da wasu watanni. A dai-dai nan kuma yay sallama da Malam Sulaiman da yay masa rakkiya. Hannunsa Malam Su ya riƙe cike da so da ƙauna da jin alfaharin cika masa alƙawari, fuskarsa da murmurshi ya furta, “ALLAH ya tsare ka ɗana, banda wasa, banda biyema abokan banza, ka zama jarumin da ƙasa zatai alfahari da kai ba kuka ba”.        Kan Haysam a ƙasa cike da girmamawa ya ce, “In sha ALLAHU Malam zakayi alfahari dani kai da su Mammah..”        “ALLAH ya tabbatar da hakan Haysam”. Malam Sulaiman ya faɗa yana sakar masa hannu da shafa kansa.....     Haysam na shiga ciki sai duniya ta canza. Cikin nutsuwarsa ya shiga layin ƴan uwansa da wasu sojoji suketa duba su, suna karɓar takardu, suna aika su wurin medical check-up. Ana duba nauyinsu, tsayinsu, tare da basu lambar cadet. Sannan suka bi jerin sabon layin da ake rabawa sababbin ɗalibai uniform da kayan horo. Sai amsar uniform ɗin suke kuwa cike da farin ciki da zumuɗi, sai manyan takalma da sauran abubuwan buƙata na kwanakin farko.       Sai da aka kammala musu komai daya dace a wannan lokacin Sannan aka tafi mataki na gaba. Bayan karɓar kaya, an kai su wani babban hall mai ɗauke da gadaje da yawa da zasu iya kai 200 ma. Kowane gado akwai katifa sabuwa fil. Nanfa bakunan wasunsu suka shiga washewar farin ciki. Wasu suna dariya, wasu suna kallon juna da murmushi. Shaƙiyan ciki masu rawar kai suka fara rawa suna ɗaga hannuwa cikin nishaɗi, yayinda wasu suka fara kiɗa da ƙarfen gado wasu cokula da plate da aka raba musu.        Dariya suka bama Sojojin da ke kula da su, dan haka suka tsaya suna kallon suna murmushi kawai. Dan basu da zaɓin daya wuce su bar su suyi farin cikin farko kafin a fara horo na gaskiya, a wannan gaɓar idan ma ance suyi wannan nanayen bazasu yin ba. Duk wannan abin da ake Haysam na zaune ne kawai a gefe bakin wani gado yana kallonsu, bai yi waka ba balle rawa, amma murmushin da ke gefen fuskarsa ya tabbatar da shima yana jin irin farin cikin da suke ji. Kai da ka kalla idanunsa kasan akwai tsananin buri amma a zuciyarsa akwai tambayoyi da yawa. Sai faman ayyanawa yake a zuciyarsa (Zan iya jure wannan sabuwar rayuwar kuwa? Yanzu ko mi Mammah take yi da su Ja'afar. Ƙilama Ammar da Mimi sunyi kukan rashin ganin yau bani zan kaisu makarantar allo ba, bani zan musu wankan dare ba, bazamu ci abinci tare ba. Ƙilama suna can sunama Mammah rigimar kuka). Haka dai ya zurfafa a tunani shaƙiyancin ƴan uwansa ɗalibai na yin nesa da kunensa.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 27_ __________________ LADY'S BEAUTY PALACE SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai?ko kina neman inda za,a gyara maki Kai ne wato saloon To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS BEAUTY PALACE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S BEAUTY PALACE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Lace Hijabs Supplements Kayan yara Saloon Kunshi na salatap Dana zane Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko Sari Zamuyi promo din kayan mu na hijabs da Kuma zuma Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 Whatsapp or call 08169307477 Tiktok Hajara Rabiu (lady's beauty palace) Instagram Hajara Rabiu __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........A wannan dare na farko Haysam bai iya bacci ba saboda tunanin gida. Ga hayaniyar sabbin abokai, ko gajiya basayi sukam duk sun cika hall ɗin da ɗumi, kaida ka gansu kasan ƙuruciya da farin cikin samun cikar buri ya baibaiye rayuwarsu gaba ɗaya. A hankali Haysam dake kallonsu kawai ya lumshe idanunsa, zuciyarsa na ayyana masa, “Rayuwa ta ta fara daga yau. Farin ciki a Bauchi tare da Abiy, Umma da Mammah, rayuwar ƙunci da kukan rasa Abiy da Umma. Fuskantar ainahin rayuwa da fara gwagwarmaya a Kano tare da Mammah da Inna, kukan rasa Inna, samun cikar burin ɗakko hanyar zama soja a yau. Ko mi gobe zata zo da shi idan da rayuwa? Wane sakamako zamu kalla a jibinmu ta duniya da lahira. Ya ALLAH kasa inyi nasara, nasara mai albarka ta duniya da lahira”.       Ganin dai barci yaƙi zuwa masa sai kawai ya tashi ya fita tare da ɗaukar sallaya a cikin jakarsa. Alwala yayo ya dawo barandar hall ɗin ya shimfiɗa abin sallar ya kabbara salla. Wannan horo ne da Abiy yay masa tun bai kai haka ba, bayan rasuwarsa kuma Mammah ta ɗora daga inda ya tsaya, shiyyasa sallar dare ta zamar masa jiki sosai, idan ma baiyi ba har jinsa yake kamar mara lafiya. Sai gab da asuba yaji barci na ɗibarsa, sannan ya tattara ya koma ciki, zuwa yanzu hall ɗin ya koma shiru, duk sunyi barci, sai tashin minshari kawai kake ji. A gadon da ya ajiye jakarsa yaje ya kwanta, baima kammala addu'a ba barci yay awon gaba da shi.... _________★        Asubar fari wani ƙarar whistle mai kaifi ya karaɗe kunnuwansu. A firgice suka shiga tashi, kafin su gama nutsuwa aka shiga faɗin, “Get up! Move it, move it, move it!”      A hankali Haysam ya shiga buɗe idanunsa ba kamar yanda sauran ke kwaramniyar tashi ba, a nutsensa ya tashi zaune yana mai karanta addu'ar tashi a barci. Wannan safiya ce ta farko bayan shigar su NDA, daga kuma yanzu sun sake tabbatar da kowane motsin rayuwarsu zai koma ne akan tsari.        Sauran ƴan uwansa ya fara bi da kallo, yanda wasu ke tashi da sauri, wasu suna neman takalminsu, wasu kuma suna a yanayin na tsoro sai abin ya bashi dariya, murmushi ya ɗanyi yana kauda kansa, dai-dai nan yaji muryar na kusa da gadonsa yana faɗin, “Dan ALLAH ko kaga takalmi na?”.       Karon farko ya kalli gefen damar tasa inda yaron yake, ba shi da girman jiki sosai, dan a cikar jiki da tsayi ya fishi, yana neman takalmin ne da hawaye cike da idonsa. Hakan ya bayyana rauninsa sosai. Tausayi ya bama Haysam, dan sai yaga kamar Ma'aruff ko Ja'afar ne a gabansa, duƙawa yay yana ƙoƙarin tayashi nema, sai ko gashi ya ɗauko masa takalmin a ƙarƙashin bunk ɗinsa daya shige, miƙa masa yayi.        “Ka kwantar da hankalinka gashi nan, saka muje kafin su dawo su same mu anan kaga kowa yana ƙoƙarin fita”      Karɓa yaron yayi yana murmurshi, sai kuma cikin ƴar rawar muryar tsoratar da har yay bata barshi ba ya ce, “Na gode ɗan uwa, sunana Imran... Imran Abbas, kai fa miye sunanka?”.         Haysam dake miƙewa ya ɗan murmusa cikin kasaita, yana miƙa masa hannu dan ya taimaka masa ya tashi. Fahimtar hakan yasa Imran miƙa masa nashi hannun shima ya miƙe. Sai da suka je kusa da hanyar fita a hall ɗin gaba ɗaya sannan ya bashi amsa da, “Haysam Abdul-rasheed Shehu”.      Imran ya kalle shi fuska cike da murmushi ya ce, “Woow sunanka mai daɗi”.         “Kaima naka yana da daɗi ai”.    Cewar Haysam yana masa ƙaramin murmushi, dan haka kawai yaji son Imran ɗin ya shige masa rai.     Imran ya ce, “Naka yafi nawa daɗi, dan kamar sunan larabawa”.      Kafin Haysam ya ce komai ƙarar whistle ta sake cika kunnuwansu da karfi.        “OUTSIDE NOW! FORM UP!”.     Aka faɗa cikin bada umarni ga na ciki da suka rage. Ai da gudu suka shiga rige-rigen fita, gadajen su na girgiza, ƙasan hall ɗin na ƙarar takalman boots ɗin ƙafafunsu. Koda Haysam ya duba gefensa tuni Imran yabi ayarin masu fita da gudu, sai ya girgiza kansa kawai shima ya fice. A ransa kuwa yana raya, “Yanzu wannan matsoracin a haka zai zama sojan?”. Bashi da mai bashi amsa, dan haka ya shiga cikin sauran ƴan uwansa.       Fili ne fetal, ga ɗan karan sanyin asuba dake ratsasu na cikin watan sha biyu, sai da sojojin dake zagaye da su suka gama ƙare musu kallo sannan aka bada umarni ga masu yin salla suje suyi. Dama abinda ke tsunkulin zuciyar Haysam kenan. Ai shine gaba-gaba a masu barin wajen, suna idar da sallar asuba cikin jam'i aka sake kaɗosu cikin sauran ƴan uwansu. Babu wani ɓata lokaci aka shiga koyar da su discipline, bin layi cikin tsari, da bin umarni. Suna tsaye a wannan fili har rana ta fara haskakawa, iska mai sanyi ta safiya na cigaba da busa su tako ina, masu rawar sanyi tun sunayi har sun dake. Wani instructor ya ɗauki megaphone ya fara magana cikin rashin wasa.        “This is NDA, not your father’s house! You eat when I say you eat! You sleep when I say you sleep!”     Da yawansu hanjin cikinsu sai kaɗawa suke, sai ƙalilan masu taurin zuciya irinsu Haysam. Imran kuwa yana gefensa yana ƙoƙarin tsayawa dai-dai amma jikinsa yana karkarwa. Haysam ya kalle shi ta gefen ido kaɗan, sai yaji tausayinsa ya kama shi, dan haka ya matsa kusa da shi a hankali, kafadarsa ya ɗan taɓa da tashi kafaɗar dan ya samu daidaiton tsayawa a layi kamar kowa. Kallonsa Imran ɗin yayi shima, dan baisan ma shine a kusa da shi ba. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, tare da yimasa kallon godiya cikin yanayin lumshe ido. Sai kuma ya shiga haɗiye hawayen da suka cika masa idon.       Murmushi kaɗan Haysam yay masa ya ɗauke kansa ya maida ga mai musu jawabi, sai dai a zuciyarsa yana ayyana “Tabbas na yarda da maganar Abiy dake cewa (Ba kowa ne ake haifa da ƙarfi ba… amma akwai wasu da zuciyarsu ta fi ƙarfinsu. Karaya ba ita ce rashin jarumta ba, amma tana bayyana rauni ga namiji. A komai ka tsaida zuciyarka, ka yarda UBANGIJI shike sarrafa al'amura sai ka samu jarumta irin ta MAZAJEN FAMA da suka gabata). Ɓoyayyar ajiyar zuciya yayi yana mai jinjina kai da ayyana “Hakane Abiy, maganarka nakan gaskiya. Dan haka daga yau na ɗauki alkawari zan kula da Imran har sai wannan runduna ta san cewa ƙarfi ba daga tsokar jiki kawai yake ba, ƙarfi na asali da gaskiya daga zuciya yake.”         Tsawar da aka sake daka musu ta dawo da Haysam a zahirinsa ya saki batun tunani ya sake nutsuwa kamar saura yana sauraren abinda ake faɗa kamar kowa.       “When I say go, you move! When I say stop, you freeze! You understand me?!”     “Yes, Sir!!!”. Suka amsa da ƙarfi, a tare.      “Good! Today, we start your Morning PT, that’s your first test! You will run two kilometers around this field!”     Shiru kake ji gurin ya sake nutsuwa, sai zukatansu dake bugawa da sauri-sauri a ƙirazansu.       “Go! Move it! Move it! Faster!”   A tare suka motsa kowa ya ara cikin ta kare, jikake tiff!! Tiff! Tifff!! ƙafafunsu suna ta dukan ƙasa, ƙarar takalma na bada sauti kamar saukar ruwan sama. Imran yana gefen Haysam, yana ƙoƙarin yin sauri kamar kowa amma numfashinsa yana sarkewa. Kamar mai shirin faɗuwa, sai faman danne ƙirjinsa yake, yana shakar iska da ƙyar.        “Haysam ba zan iya ba...”    Ya faɗa cikin shashsheka “Imran! Kada ka tsaya, ka karfafa kanka, Abiy na yana cemin (Namiji baya zama rago garkuwa ne), dan haka kada ka tsaya kaji!” Haysam ya faɗa yana riƙe masa hannu. Sai ko Instructor ɗaya ya hango su daga nesa, cikin ihu da tsawa ya ce, “Keep moving, you two! No one stops! You stop, you fail!”.      Sakin hannun Imran Haysam yayi ya matsa yana ɗan tura shi gaba, cikin son kwantar masa da hankali ya ce, “Ka tsaya ta gabana. Idan ka faɗi, nima zan tsaya. Amma ba za mu faɗi ba in sha ALLAHU”.       Idon Imran cike da hawaye, cikin son ƙarfafa kansa kamar yanda Haysam ya faɗa ya jinjina masa kai. A haka suka ci gaba da gudu, duk da cewa jikinsu ya fara gajiya, zufa kam ta jiƙe goshinsu dama illahirin jikinsu tamkar ba safiya ba. Lokacin da suka iso ƙarshen filin, sauran ɗalibai suna ta rige-rigen samun abin dafawa, wasu suna tsaya suna tari, wasu suna hawaye. Haysam ya riƙe hannun Imran har suka ketare layin ƙarshen gudun sannan ya jinginashi da jikinsa suna sauke numfashi a tare.       Instructor ɗin da yake biye da su ya tsaya yana kallonsu ɗaya bayan ɗaya ba tare da yayi magana ba, sai kawai ya murmusa yana mai girgiza kansa.       “Discipline. Determination. Teamwork.”      Ya furta kalmomin cikin karsashi kamar yana jin daɗin yanayin daya gansun.     Zubewa Imran yay ƙasa yana shakar iska da ƙarfi, jikinsa na dan rawa ga zufa tai masa sharaf. Durƙusawa Haysam yay kusa da shi shima, yana share masa gumi da hula. “Na faɗa maka, idan ka tsaya, nima zan tsaya. Kuma ba zan bari ka faɗi ba, kada ka sare Imran, domin ba'a fara komai ba, dan yanda Abiy na ya gaya min wanene soja a labari wannan matsayin sharar fage muka fara”       Imran ya ɗaga ido cikin hawaye, amma wannan karon hawaye ne na tsoro, da rauni mai tafiya da godiya da jin ƙarfin gwiwa daga sabon aboki a sabuwar duniya. “Na gode Haysam, kai ne jarumi na farko da ya tsaya saboda ni, tabbas kai ZAKI na ne, kuma inuwa ta ne. My Zak-Shadow”.      Kai Haysam ya girgiza ya ɗan yi murmushi mai sanyi, yana duban rana wacce ke fara fito da haske ɗumi. Sai kuma ya kalla Imran ɗin daya miƙe tsaye akan ƙafafunsa, shima miƙewar yay yana kallonsa. “Imran kaima Zaki ne ai, domin anan babu wanda yake shi kaɗai. Saboda Soja ba ya tafiya shi ɗaya sai da runduna.”        “Ni ai kaine tawa rundunar kuma inuwa ta Zak-Shadow”.      Kai kawai Haysam ya sake girgizawa, hakan yayi dai dai da busawar iska mai daɗi dake tafe da ƙarar murya daga nesa, “Fall in! Line up, cadets! Next exercise, push up!”      Imran ya kalli Haysam cikin murmushi, shima Haysam ya murmusa, zuciyarsa na ayyana masa abu ɗaya cike da tabbaci. Rayuwarsa ta soji ta fara a yau, amma abota ta gaskiya ta riga ta samun tushe da mafari a zukata guda biyu.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 28_ __________________ LADY'S BEAUTY PALACE SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai?ko kina neman inda za,a gyara maki Kai ne wato saloon To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS BEAUTY PALACE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S BEAUTY PALACE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Lace Hijabs Supplements Kayan yara Saloon Kunshi na salatap Dana zane Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko Sari Zamuyi promo din kayan mu na hijabs da Kuma zuma Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 Whatsapp or call 08169307477 Tiktok Hajara Rabiu (lady's beauty palace) Instagram Hajara Rabiu __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Rana ta biyu ta kasance da sabon sauyi ga su Haysam duk da dai zamu kira sauyin bamai yawa da tsanani ba ne. Domin kuwa daga gudu, sai tsalle-tsalle, da kiran Yes, Sir! da karfin murya, kowanne cadet ya fara jin cewa jikinsa na canzawa, kamar yanda rayuwa take canjawa daga barin ƙuruciya zuwa sabon ƙalubale mai banbanta kai da sauran jama'ar gari. Ba su da lokacin tunani na zahiri, amma kowannensu ya fara fahimtar cewa a cikin NDA duk suna amsa sunan masu daraja ɗaya ne da fuskantar ƙalulabe ɗaya a ƙarƙashin ɗoki, zumuɗi da burin zama soja... >>>>>>>>•<<<<<<<<          Yau kwanakin mako cif da shigowar su Haysam NDA, a satin gaba ɗaya rayuwa mai sauƙi ce da cigaba da morar ƙuruciya da ƙarasa zazzage sauran wautar data rage a gaɓɓan jiki irin ta masu shekarunsu. Domin kuwa satin gaba ɗaya babu wani abin kuzo mu gani dake nuna musu ma an fara wasan, shiyasa wasu a cikinsu suka fara shagala da maida hankali a nishaɗi da ƙulla abota kawai a tsakani.      Saɓanin Haysam yaro mara kwaramniya da yawan magana. Ba ruwansa da kowa sai Imran, komai nasa a nutse, akoda yaushe yana gefe nesa da hayaniya da nishaɗin sauran. Sai dai a duk inda yake Imran sabon aboki sabon ɗan uwa na manne da shi. Da yake shima Imran ɗin baida hayaniya sosai sai abotar tasu tai dai-dai. Sai dai shi yanada surutu, dan a kwanakin kaf har ya kammala bama Haysam labarin ƴan gidansu A to Z. Yayin da shi kuma Haysam bai iya gaya masa komai ba bayan sunansa da garinsu Bauchi da Kano da suke a yanzun.         Kamar yanzu ma suna can daga bayan hall ɗin kwanan nasu ne suna hira ko nace Imran na zuba masa surutu kiran da akema su sabbin ɗalibai ya riskesu. A tare suka miƙe suka zagayo ta gaba, batare da neman ba'asi ba suka bi ayarin saura dake tafiya amsa kiran suma a babban filin taro. Bayan sun gama hallara kaf kowa yana daga tsaye a nutse babban Officer ya tsaya a gaban su da takarda mai ɗauke da jerin sunaye ya fara jawabi kamar haka..        “Today, you will be assigned to your permanent Companies. Once your name is called, move to your Company’s block. That will be your new home.”       A tare suka amsa da kalmar, “Yes Sir!”.       An fara kiran sunaye ɗakunan da sunayen wanda zasu kasance a cikinsu ɗaya bayan ɗaya. Duk wanda aka kira zai amsa ya nufi inda aka nuna masa. Kowane ɗaki da iya adadin mutanen da ake buƙata. Kasancewar ana binsu a jere ne a kiran sunayen har aka zo kan H, Haysam na cikin H ɗin ƙarshe, cikin sa'a kuma Imran na cikin I ɗin farko. Kamar yanda ake kiran kowa aka kira sunan, Haysam Abdul-rasheed Shehu.”      Cike da nutsuwarsa ya amsa yana mai miƙewa tsaye, “Yes, Sir!”, ya faɗa yana nufar inda aka nuna masa an rubuta Alpha room. Kamar abin almara sai ya sake jin an furta, “Imran Abbas.”       Haysam ya juyo cikin mamaki, Imran ma yana kallonsa cike da farin ciki har murmushi na ƙoƙarin bayyana kansa akan fuskarsa. Shi kansa Haysam sai da ƙaramin murmushi ya bayyana kaɗan a saman tashi fuskar. Dan bayan ƙanensa Imran shine na biyu daya ji yana so tamkar jininsa. Gashi dai suna matsayin sa'anni ne a shekaru, amma raunin Imran dake a bayyane yasa yana jinsa kamar ƙaninsa daya kamata ya bama garkuwa. Badan Imran ya bashi labarin shine yake son aikin soja da kansa ba da ya ce an tilasta masa ne da tsiya saboda yanda yake a raunane. An ƙaro mutum biyu cikinsu, dan kowanne ɗaki na ɗaukar mutane huɗu ne. Gado biyu ne sama da ƙasa. Biyu a sama biyu a ƙasa. Sai  lockers da sauran abin amfani kowa da nashi da ma sunansa a jiki.      Kowane group an haɗa su da Officer ɗin da zai kula da su. Bayan sun shigo nasu ɗakin wanda ya jagorancesu ya nuna musu ɗakin da faɗin, “Each room, four cadets! You are brothers now. You eat together, you fight together, you win together.”       “Yes Sir”.   Sunan Haysam ya fara kira yana nuna masa nashi gadon. “Haysam Abdul-rasheed Shehu bunk na ƙasa, Imran Abbas kuma gadon saman Haysam. Da wani irin farin ciki Haysam da Imran suka kalli juna suna murmushi kamar ɗazun, wannan lokacin ya tabbatar musu cewa rayuwarsu zata ci gaba da tafiya a tare kenan, abotar da aka ƙulla batare da tabbacin rayuwar waje ɗaya ba bisa rahamar UBANGIJI da dubin zuciya ta tabbata..      Suma sauran kowa an bashi nashi. Basu zauna ba suka fara shirya abubuwansu a inda ya dace da yanda suke buƙata. Musamman ma abokai biyu da farin cikinsu ya kasa ɓoyuwa.        ★Da daddare bayan kowa ya kwanta, sai Imran ya ɗan leƙo daga sama, yana magana a hankali da kallon fuskar Haysam da yay kwanciyar rigingine a gadonsa yay filo da hannayensa duk biyu.        “Zak... kana jin kamar rayuwa ta canza ko?”    Buɗe idanun Haysam yayi a hankali ya sauke su kan fuskar Imran daya leƙo ta sama. Wani ɗan guntun murmushi yay masa. Kamar bazai ce komai ba sai kuma a ciki ya furta, “Imran!. Tabbas rayuwa ta canza, canjawar data nisanta mu da ahalinmu da su kaɗai muka sani a rayuwar jiyanmu. Amma da kai tare a nan sai ta zama mai ɗebe kewa da koyar da sabon darasi”       Ƴar dariya Imran ya yi cike da jin daɗin kalaman sabon abokinsa Haysam. Hankali kwance kuma kai tsaye cikin son fidda abinda ke zuciya ya ce, “Ni ma haka nake ji My Zak-Shadow, kamar kai ne garkuwata, ɗan uwana jinin jikina da ya ɓuya sai yanzu ne ya bayyana min kansa”.      Hannu Haysam ya miƙa masa, shima Imran ya miƙo nashi suka riƙe juna. Cike da tabbatarwa ya ce, “Ni kuma ba zan bar ka ka faɗi ba in sha ALLAHU Imran. Ba'a nan kawai ba, a ko inama. Ka sani kana cikin lagona da in har aka hareni ta hanyarka tabbas zan faɗi, faɗuwa irin ta kwanciyar da babu juyi a ciki. Ka riƙe alƙawari, ka riƙe amana, ka tuna wannan koda anan gaba”.        A hankali hawayen da suka cika idon Imran suka gangaro suna ɗiga a fuskar Haysam. Bai share ba, bai sakar masa hannu ba kuma har wani lokaci. A wannan daren kafin su rufe idonsu, sautin bugun tambarin alƙawarin riƙe amanar juna ya gama zagaye zuciyoyinsu. Rayuwar soja ta gaske ta fara a cikin ƙwaƙwalensu, sun yarda su biyu sun riga sun zama abokai, aminai, kuma ƴan uwan juna a cikin ɗakin Alpha dake wannan makaranta ta NDA.       Ƙarfe 4:30 na asuba aka busa ƙararrawa mai ƙarfi. Duk da har yanzu duhu ne muryar ɗaya daga cikin senior cadets ta farkar da su Haysam kamar sauran ƴan uwansu sabbin ɗalibai.      “Wake up, gentlemen! You’ve got 5 minutes!”     Imran sarkin tsoro kuwa ya zabura yana neman faɗowa a gadon, jikinsa sai rawa yake saboda tsoro. Haysam kuwa ya tashi da natsuwa kamar yanda ya saba a gida idan Mammah ta tashe sa. Gadon ya dafa cikin sanyi da muryar wanda ya tashi a barci ya furta, “Ka nutsu Imran, ka sauka a hankali. Ka tsaya a gefe na, ka koyi komai a hankali da nutsuwa, gaggawa taɗiye mutum take daga cimma burin nasara, haka Abiy na ke gaya min sanda ina yaro”. Ya ƙare maganar yana kama hannun Imran ya taimaka masa ya sauko a hankali.       Suna fita daga ɗakin iska mai sanyi ta bugi fuskokinsu, sai ƙarar ƙafafun ɗalibai kake ji a kan ƙasa. Wani senior mai ƙarfin jiki ya tsaya a gaban su da fitilar hannu yana ta faman haskesu cikin ido da faɗin, “Down for push-ups! Let me see soldiers, not boys!”      Gudu suka fara iya ƙarfi kamar yanda aka basu umarni. Tun ba'ai rabin filin ba wasu suka fara kukan gajiya. Imran kam da ba ƙarfin zuciya yana neman kaiwa ƙasa ne ma, amma Haysam ya matsa kusa da shi, yana faɗin, “Ka cigaba, kada ka tsaya Imran. Ka kalle ni kaji. Idan ka faɗi ka sani nima zan faɗi”.      Wannan magana ta ƙarfafa shi sosai har ya yi mamakin kansa, ɗan daga nan yaji kawai ya ƙara ƙaimi har suna tafiya a jere da Haysam, Alhamdullah cikin nasara suka kammala round ɗin farko. Koda aka ɗan huta aka koma kuma nan ma bai sare ba sam. Dama shi oga kwata-kwata ko'a jikinsa. Komai Haysam na yinsa ne da ƙarfin jiki da zafin nama kasancewar zuwa yanzu ya saba da wahalar rayuwa, to tallar da yake yi ɗin nan zagaye kasuwa ai ba wasa ba. Wankau ɗin Mammah, ɗibar ruwa. Hatta daka idan ta amsa tare sukeyi in dai yana gida. Wannan wahalhalu sun taka rawar gani a rayuwarsa ƙwarai da gaske har yake jin wannan ƙwarin gwiwar a yanzu da son ƙarfafa irin su Imran masu rauni da gata yasa basu saba da wahala ba. Bayan an gama sunyi sallar asuba, suka dawo wajen rarraba breakfast packs. Imran yana jin kamar ƙafarsa bata motsi da ƙyau, sai Haysam ya karɓi nasa kwanon ya riƙe masa zuwa wajen zama. Sannan ya taimaka masa ya zauna yana jera masa sannu. A gefe ɗaya, wasu senior cadets suna kallon Haysam cikin mamaki, sauran ƴan uwansa duk a galabaice, amma shi a tsayensa yake kamar ma baiyi komai ba yana a nutsuwarsa da karfin hali, ga kuma yana da tausayi fiye da kowane sabo a cikin su. Wani daga cikinsu ya ce, “Wato wannan yaron akwai wani abu daban a idanunsa, ku kula sam bashi da tsoro ko fargaba balle jin karaya kamar yanda sauran suka nuna”.        Wanda ke kusa da shi ya ce, “Ƙaryar banza, yo mi aka fara da mazan. Yau kawai kake masa wannan yabon. Ka bari suci watan farko dan Babansa wlhy sai ya rusuna wannan zafin kan nasa yabi iska”.      Dariya suka sanya suna mai tafawa cike da shaƙiyanci. Duk abinda suke faɗa kuwa a kunnen Haysam, amma ya basar kamar ba jinsu yake ba yana maida hankalinsa ga Imran dake shan ruwan zafi a wahale. Koda Imran ya kallesa sai ya sakar masa murmurshi, baki Imran ya ɗan tura tare da faɗin, “Ka bar yi min wannan murmushin naka mai kama dana ƙeta. Wlhy da kai ne kawai nake jin karfin hali a nan, amma ji nake kamar na fasa na gudu gida”.       Haysam ya sake murmusawa yana daidaita beret ɗinsa a saman kai. “ Haba mazan fama wane gudu kuma ana zaune ƙalau, ai in ka ganka a waje hutu zamu, in sha ALLAHU kuma mu dawo da ƙafafunmu a ɗora daga inda aka tsaya. Daga yau ka ɗauka mu biyu ne a tare, wani bazai bar wani a baya in sha ALLAHU. Ba zan a taɓa barin wani ya cutar da kai ba. Kaima bazaka taɓa barin wani ya cuta min ba”.        “Yes Sir! Ina sha ALLAHU”. Imran ya faɗa yana salute ɗinsa. Dariya Haysam yayi yana kai masa naushi. Da sauri ya kauce shima yana dariya. Idan ka gansu dole su birgeka, dan a kallo ɗaya zaka tabbatar da aminci mai tsafta ya shiga zukatan waɗan nan matasan zakunan guda biyu. Kuma ina sha ALLAHU zasu kafa tarihi mai ban mamaki da taɓa zuciyar duk wanda zai bibiyi labarinsu.........✍🏼 __________ TALLAH Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JuUwr2QU7XMEYXZ7L7 Mmn surayya me kayan kamshi Ina amaran da uwayan gidan tou kumatso kusa Mmn surayya ta gwangwaje ku da kayan kamshi munada Turaran wuta na danal banat Kajiji Turaran kaya watau abbasiyya Kabbasa spray Humra Kwallacca Uwa uba Ina kuyarda yadda xaki hadasu Zaku iya samuna ta wannan number wayar kamar haka👇 08103143517 Ina katsina Ina aika kaya ko ina _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 29_ __________________ https://wa.me/+23408067422528 Kina son rage kiba ba tare da kin daina cin abunda kike so sannan ba tare da kinyi gudawa ba? To kimin magana domin samun hanyoyi da zaki rage kiba ba tare da kinsa wahala ba. Ko kuma matsalar gashi ce ke damunki, ko rashin tsahon gashi ne, shima muna da solution dinsa. Ko kuma fatar ki tana lalacewa ne a sanyin? Muna da ingantaccen man da zai gyara miki kafafunki ko kuma kamar ta jarirai. Ko kuma kafarki ce take kaushi a sanyin nan muna da ingantaccen mayuka Ko kuma man gyaran fata kike so da zai gyara miki jikinki a sanyin Nan ?duk muna dasu ba tare da kinsa wahala ba sannan 100% natural ne. Yar uwa idan ma bangaren samun kudi shima kike nema shima duk zamu koya miki. Kedai kawai ki mana magana domin karin bayani. https://wa.me/+23408067422528 “Shin Ke uwa ce, kina son samun kuɗi ba tare da kin fita kin bar ’ya’yanki a gida ba?” ko kuwa ke student ce kina son samun karin kudin shiga ko kuma ma dai kawai kison karin side hustle ne Tare da Oriflame, za ki iya yin kasuwanci daga wayarki a gida. Ba tare da kin fita ba. Mata da yawa sun riga sun farga da wannan Kasuwanci kuma suna moriya dashi sosai, suna making kudi daga gida, kuma ke ma za ki iya sannan bayan ribar ki zaa biyaki salary a karshen wata. ko kuma kina son yin siyayya for personal use ne ba tare da anci riba dake ba ga link nan a kasa zaki iya register da kanki it's free👇 https://shop.oriflame.com/NG-salmaibrahimismail/3M3HmQWe __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........WASHE GARI su Haysam suna tsaye a layi, jiki a sharɓe da zufa, wasu har suna rawar tsoro saboda an ce yau ce the real beginning. Major Adetunji, babban jami’in horo, ya tsaya a gaban su da ƙarfi, yana ta kallonsu ɗaya bayan ɗaya kamar mai tantance fuskokinsu. Kafin cikin buɗaɗɗiyar muryarsa mai kaɗa hanjin marasa ji ya shiga faɗin, “Welcome to the Nigerian Defence Academy. From today, you are no longer civilians! You are cadets, and you will either become men here or quit!”. Sai kuma ya ƙara ƙarfin muryarsa cikin sabon ihu ya sake faɗin, “Drop down! Ten push-ups… No, make it twenty!!”.         Cike da zafin kai irin na farkon balaga da jin kansu su maza ne wasu a cikinsu suka fara gunaguni ƙasa-ƙasa. Sai dai babu damar cewa baza'ayi ba. Dan haka suka fara kamar yanda aka umarcesu a tare kuma. Ai ba'a wuce 7-8 ba wasu suka fara zubewa ƙasa saboda gajiya. Sai ƙalilan a cikinsu irin su Haysam masu taurin zuciya da sabon wahala ne suka cigaba da yi har ƙarshe. Haysam da  idanunsa ke a rufe yana kammala nashi push-ups ya miƙe tsaye a kan ƙafafunsa daram, kamar wanda yake numfashi ne kawai, ba wahala yayi ba.      Cike da mamaki Senior cadet ɗaya ya zo da fuskar tsoro, yana ƙoƙarin tsoratar da shi, “You think you’re tough, new boy?!!”.       Haysam dai bai ce komai ba. Yana tsaye kuma akan ƙafafunsa yana kallon sa kai tsaye idanu ƙyam babu alamar jin shakka. Kawai sai Senior ɗin ya ɗan tsaya yana kallonsa shima cikin ido, ganin fa Haysam bazai janye nashi ba sai shi ya janye nasan yayi murmushi mai cike da ma'anoni yana girgiza kai da faɗin, “Hmm… we’ll see how long you last”.       Nan ɗin ma ko gezau Haysam baiyi ba. Imran kuwa yana gefensa yana rawar jiki, a ransa yana mamaki taurin kan Haysam. Bashi akema tsawar ba amma ji yake ƴan cikinsa na motsi wlhy. Amma kalla shi wanda akemawa ɗin ko a slippers ɗinsa ma. Ba Imran kawai ba, sauran mate ɗin nasa ma da Seniors ɗin hankalinsu ya koma kan Haysam ɗin, sai dai babu wanda ya sake cewa komai aka cigaba da basu horo.       Bayan horo na farko, aka shiga weapon drill. Ana koya musu riƙe bindiga da tsaye kamar sojoji na gaske. Wasu sai mutsu-mutsu suke sun kasa daidaita hannayensu, amma Haysam yana gefe yana riƙe da bindigarsa tamkar wanda ya shekara yana yi. Tsayawa Captain Adetunji wanda yake lura da su yay a kusa da shi.         “You! what’s your name, cadet?”. “Cadet Haysam Abdul-rasheed Shehu, sir!”       “Good stance. Good grip. You’ve done this before?”      “No, sir. But I learn fast.”    Captain ya ɗanyi shiru yana masa kallon mamaki, sai kuma ya ɗan murmusa da ba kasafai yake yin haka ba dan irin mutanen nan ne da sam basa fara'a basa wasa.       “Keep that spirit. Nigeria needs men like you”. Ya sake faɗa yana ɗan bubbuga kafaɗar Haysam ɗin. Kai Haysam ya jinjina masa cike da girmamawa.      Bayan an kammala an sallamesu suna shiga hostel, Imran ya jingina da gado yana magana cike da raɗa idonsa akan Haysam.       “Kai Haysam kana bani tsoro wlhy, ni kam ban taɓa ganin wanda yake da karfin zuciya da rashin tsoro irin naka ba.”      Ɗan harararsa Haysam ya yi da murmushi mai sanyi kawai yana girgiza kai. Sai da ya kai zaune a bakin gadon su yana cire takalmin ƙafarsa sannan ya bashi amsa da, “Ba ƙarfin zuciya bane ko rashin tsoro Imran. Imani ne da abin da nake so in zama, tare da son cika burin Abiy na”.       Zama shima Imran yayi yana sauke ajiyar zuciya. Ya ce, “Gaskiyar ka kuma Zaki na. Nima in sha ALLAHU zan dinga jin ƙarfi da ƙarfin son cikar burina kamar kai. Da yardar ALLAH wataran sai mun tuna hakan munyi dariya tare munyi kuka tare”.         “ALLAH ya tabbatar”.    Cewar Haysam yana kaiwa kwance a gadon.     __________★         Da daddare gari ya yi sanyi sosai a NDA. Ko ina ya cika da shiru sai ƙarar iska dake kaɗawa da motsin fallen langa-langar rufin ɗakunansu. An kashe fitilun waje, sai hasken ƙaramin bulb da yake haskaka ɗaki na 17 Alpha room da sautin minsharin room mate ɗinsu biyu masu saurin barci.  Haysam yana kwance kan gadonsa, jikinsa har yanzu na ciwo amma zuciyarsa cike da natsuwa. Imran kuwa yana daga sama shima ya kasa barci sai faman juyi yake a gadon, yana gumi alamar wanda ke mafarki mai nauyi.       Can kuwa sai ga muryarsa na fita kamar cikin kakari irin na wanda yasha shaƙa a hannun wani. “Ka barni… don ALLAH kar ka sake min haka… Mama… Mamaaa!”.      Da sauri Haysam ya tashi, ya sauka daga gadonsa cikin sassarfa. Tsaye ya miƙe tare da kai hannu kan Imran ya shiga jijjiga kafaɗarsa, “Imran… hey, wake up. Lafiya kuwa? Kaga tashi…”       A firgice Imran ya buɗe ido da sauri, sai kuma ya zabura zaune jikinsa na rawa. Idonsa cike da hawaye, numfashinsa na fita da sauri kamar wanda aka fito da shi daga ruwa. Hannun Haysam ya damƙe tare da matsowa sosai kusa da shi cikin muryar kuka ya ce, “Na… na sake ganin su.. sun sake kamani Haysam”.       Kallonsa Haysam yake cikin tausayi, sai kuma ya ɗan dafa kansa kamar mai dafa kan Bilal.      “Shhhh… ka yi shiru. Mafarki ne. Ba kowa a nan. kai da ni ne kawai da su Peke. Kayi addu'a ka canja kwanciyarka ta wannan ɓarin”.       Sai kuma ya juya ya ɗakko ruwa ya miƙa masa. “Ka sha ruwa, ka huta. Kada ka bari mafarki ya firgita ka. Ka dinga ƙarfafa kanka Imran, kaifa soja ne da wasu ke jira ka basu garkuwa anan gaba”.      Imran ya kalle shi da hawaye, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya yana faɗin cikin rawar murya, “Haysam mutanen nan bazasu barni ba, duk da iyayena sunyi nasarar fiddani a ƙungiyarsu tare da baro yankinsu gaba ɗaya lokaci-lokaci suna cigaba da bibiyata a mafarki. Wlhy gaba ɗaya a tsirace nake. Kai dai kamar komai ba ya tsoratar da kai.”       Shiru Haysam ya yi na ɗan lokaci, yana kallon tagar da iska ke busowa, sai kuma ya dawo da dubansa kan Imran ɗin, “Kowa yana da tsoro Imran. Amma na koyi ɓoye nawa, dan idan na bari duniya ta gan shi, zata yi amfani da shi wajen zubar da ni, lalatattun mutane masu ƙazamar zuciya subi takai na su taka tamkar yanda suke taka ƙasa. Ni mutum ne kamar kowa. Amma Abiy ya sanar min sai na zama jarumi a zuciya sannan jarumtar jiki ke tabbata har wasu su kalleni wataran suce wannan shine wane. Kasa a ranka babu abinda mutanen nan suka isa suyi maka kamar yanda basuyi maka a baya ba. Idan suna taƙama da tsafi kai ka tuna ALLAH kake da shi”. A hankali ya saki murmushi mai ciwo yana ƙoƙarin danne damuwarsa, “Imran! Idan har Mammah dake mace mai amsa sunan UWA zata ɓoye dan mu rayu cikin salama da nagarta bayan ta rasa daga kowane garkuwarta ni data haifa na zame mata farkon nauyi kuma ƙalubale a yau mizai hana bazan jure ba kodan na maida murtani daga ahalin da suka nuna mata amfaninta ya ƙare garesu saboda mai musu amfani ya gusa daga jikinta a yanzu. Zan cigaba da ɓoyewa domin na zama abinda nake fata iyayena ma suke fata. Amma kai kada ka koyi ɓoyewa. Tsoron ka… shi ne dalilin da yasa kake da rai da jinƙai Imran.”      Lumshe idanu Imran yayi yana jin kalman Haysam masu fita da harshen damo da saƙo na musamman suna ratsa shi kamar magani. Koda ya motsa lips dan yin magana sai Haysam ya girgiza masa kai, tare da masa nunin ya kwanta kawai. Bai musa ba a hankali ya kwanta, shiko kuma ya cigaba da tsaiwa a jikin gadon yana tofa masa addu'ai har sai barci ya kwashe shi. Kwanaki sun cigaba da shurawa, sannu-sannu su Haysam sun zama ƴan gida a NDA. Dan kuwa zuwa yanzu watanni na biyar suke ƙoƙarin cikawa. Jiki da zuciya sun saba da sabon waje sun kuma karɓi sauyin horo da suke fuskanta. Hakama ƙwaƙwalwa tana ɗauka daga koyarwa da dabarun rayuwa irin ta mazan fama.       Ranar yau asabar ta zo da rana mai tsananin zafi. An fito dasu Haysam duka don wani obstacle training na tsalle, gudu, juyawa cikin laka, da rarrafe ƙarƙashin waya. Duk wanda ya yi wasa ko nauyin jiki kuwa  yaji a jikinsa ne a hannun Seniors. Kamar ko yaushe Haysam yana cikin ƴan gaba-gaba yana yin komai da cikakken natsuwa kamar wanda ba ya jin ciwon gaɓɓansa. Yayin da wasu ke gunaguni, shi kuwa ko numfashi bai tsananta ba. Wannan yasa wasu senior cadets da suka fara saka masa tsama suka fara saka masa ido sosai. Bayan horon rana, lokacin da su Haysam suka koma sashen su, Senior Cadet Garba ya kalli abokansa yana murmushi mai ɓoye makirci, “Na fahimci fa yaron nan mai kama da haihuwar sahara ya fara kama da jarumi yana son fara yima mutane ɗagawa da girman kai, ya kamata mu gwada wane irin ƙarfe ne da shi.”       Dariya John ya sanya da faɗin, “Wato Garba kaifa mugun icce ne. Na kula ka saka idonka akan yaron nan kamar yana barci a kanka cikin NDA ɗin nan”.       Hararsa Garba yayi, cikin ƙyaɓe baki ya ce, “Shi ɗin banza da zai yi barci a kaina. Kawai na tsane shi ne, wlhy tun randa yay mana rashin kunyar nan nake ji kamar na kashe banza dan na tsane shi har cikin raina”.      “Ba kai kaɗai ba fa, ALLAH nima bana son shi sam a raina. Gashi naga ya fara kama zuciyar basawan gidan nan”.        “Mtsowww! Zai ci uwarsa ne. Mune maganinsa ai”.      Dariya suka sanya suna tafawa su da sauran abokansu da basuce komai ba.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 30_ __________________ https://chat.whatsapp.com/L3BXH7JYlBRHIkFRiOjeW3?mode=ems_copy_t UMMU KHALIFA COLLECTION Ina Mata Yan kwalisa ina mata masu san kayan ado kamar Egyptian abaya sleeping drees kids were shos bags musk dahara original. To kukanku yazo karshe domin ummu khalifa sun zo muku da duk wadannnan kayan dierct suke order dinsu daga Egypt zuwa gida Nigeria kaidai kawai kashiga link dinsu domin gani ya kori jiii.. Ba nan ummuh khalifa suka tsaya ba suna nemawq mutane visa masu shaawar shugowa kasar ta Egypt karatu ko yawon bude ido ko kasuwanci ku tuntubeta a number dinta +201017018846/07048811474/ KO kuma shafinta na tiktok https://vt.tiktok.com/ZSU1FEkjc/ __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Da daddare kuwa lokacin da aka gama evening parade, suka umarci Haysam ya tsaya a gefe. “Cadet Abdul-rasheed! Step forward!”      Babu wani ɗar Haysam ya matso, idonsa a ƙasa, jikinsa a nutse cikin tsarin jarumin matashin soja.        Garba ya kalle shi fuskar cike da izza da wulaƙanci,  “Na lura kana ɗaukan kanka wani shege can kamar fa ko. Kana so mu girmama ka ko kallonka wani ƙuru ko jarumi halan?”.      Karo na farko Haysam ya kallesa cikin ido. Kamar zai yaɓa masa baƙa sai kuma ya dake da ƙyar ga haɗiye ya furta, “Ba haka bane senior. Ina yin abin da aka koya mana ne kawai, shi jarumi kuwa ba duniya yake gayama shi jarumi bane. Ita duniyar da kanta take gaya masa shi ɗin jarumi ne koda hassada tana ƙoƙarin danne bakinta da yashin ƙasa. Mizai sa naso ku girmamani bayan UBANGIJI NA shike bada girma ga wanda ya so. Ai ni tun a gidanmu mai girma ne, domin kuwa ƙanne bakwai na baro dake min kallon uba ba yaya kawai ba, saboda tsabar girmamawa ma Dada suke kirana. Kaga kuwa duk wani girma bayan wannan ai lissafi ne na yaro ɓata hankalin dare kayi suna. Ni kuma bana ɓata hankalin dare don yin suna, KIƊA A RUWA nake MAI TADA HANKALIN DODONNI”.      Cikin matsananciyar fusata Senior Garba ya nuna Haysam da ɗan yarda tamkar zai tsokale masa ido. Shi ko gogan yana tsaye ƙyam a binsa idanun akan Garban ko ƙyaftasu bayayi balle nuna alamar tsoron kar'a tsokale masa su. “Oh da gaske kai kana jin kanka wani shege ne dai kenan? Shi kenan to ka tabbatar yau da gaske ka iya juriyar da kake faɗa, sauran kalamanka kuwa jikinka ne zai baka amsarsu ɗaya bayan ɗaya”.      Uffan Haysam bai sake cewa ba, yama ɗauke kansa tamkar bada shi akeyi ba. Tsabar mugunta tashin farko suka ɗaura masa kaya masu nauyi da suka tabbatar sunfi ƙarfin sa, jakar dutse amma ya dake saboda taurin kai, cikin daka tsawa sukace ya zagaya filin horo sau uku a cikin duhun daren nan. Wasu daga cikin mate ɗinsa suka tsaya suna kallo cikin tsoro. Imran kam hawaye yake yi cike da tashin hankalin muguntar da akema ɗan uwansa.        Shi ko gogan naku Haysam ko nuna gajiya ma yaƙi yayi. Tafiya yake akan ƙafafunsa cike da jarumta zuciya a tsaye ƙyam, ga iska tana busawa, amma shi zuface ke kwarara masa a jiki. Haka yayi sau ukun da sukace, tun a zagayen farko suke tunanin zai sare amma sai da ya ukun nan cif  kusan awa ɗaya, babu wani alamar rauni na zahiri atare da shi, duk da a jikinsa da zuciyarsa ya gajin amma ya shanye ya zo ya tsaya a gabansu cikin nutsuwarsa. A dake ya ce, “I’m done, senior.”     Wani daga cikinsu mai suna Badaru yay dariyar mugunta da ɗan ɗaga kai yana masa kallo wulaƙanci. “Hmmm… zaka iya kam. Amma mu kuma ba za mu huta ba har sai mun ga inda iyakarka ta tsaya tunda kace kai Iliya ɗan mai ƙarfi ne”.       Haysam bai tanka masa ba. Hakan ya ƙara ƙular da su Senior Garba. Sai dai babu wanda ya sake cewa komai a cikinsu suka bar wajen. Da sauri Imran ya ƙaraso ya kama jakar duwatsun. Ɗan murmushi Haysam yay masa da faɗin, “Barshi kawai zan iya”.       Kamar Imran zai yi kuka ya ce, “Haysam mi yasa ka biye musu? Waɗan nan fa daga gani basu da imani, kazo muje mukai report ɗinsu dan sun wuce gona da iri”.       Haysam ya kalle shi cikin murmushi, “My Imran sarkin tsoro, kada komai ya dameka babu wani report da zamu kai. Muguntar tasu kuwa mu irinta muke nema ai. Abin da suke kira karya lago a gare ni. Ni gina sabuwar rayuwace a gareni. Ka gane sai da irin waɗan nan ake nasara a rayuwa”.        “Ka cika taurin kai wace nasara kuma da wannan azabar dan ALLAH. So kake sai sun illata maka lafiya sun karya ma ƙashi”.      “Imran kenan. Ba zan bari su karya min ƙasusuwa ba, saboda ƙasusuwa na ne ginina, ba shaidar girman kai da suke kallona da shi ba”.       Sai Imran ya tsaya yana kallonsa da mamaki kawai. A wannan dare, ya fahimci cewa Haysam ba soja bane kawai, mutum ne da aka raini zuciyarsa da jarumta da juriya tun daga ƙuruciya. Aka kuma gina burin zamansa soja a ƙwaƙwalwarsa tamkar yanda abinci ke gina tsokar jiki.... >>>>>>>•<<<<<<<< KANO          Yayinda Haysam ke can NDA na gwagwarmaya anan Kano Mammah ma ta cigaba da tata gwagwarmayar ne. Dan kuwa tamkar jira dangin mahaifinta keyi Haysam ɗin ya wuce makaranta suka sakata gaba akan batun yin aure. Da farko ta nuna musu ita fa sam bazata ƙara aure ba a rayuwarta. Amma suka nuna sam bazasu amince da hakan ba, da ƙuruciyarta bazata ce bazatai aure ba. Tace musu idan tayi aure wazai riƙe mata yaranta ne? Ba dai kowane namiji ne zai riƙe yara har takwas daba nashi ba, ya basu ci ya basu sha ya biya kuɗin makaranta abune mai wahala ai. Sai suka nuna mata basai tai zamanta a gidan ba kawai shi mijin ya dinga zuwa. Saboda su barta sai ta ce musu ta amince da hakan, dan tasan dai ba duk namiji ne zai yarda da hakan ba ai. Da wannan damar ta samu suka sama mata lafiyar kuwa.         Ta cigaba da rainon yaranta tare da bin Haysam dake nesa da ita da addu'a. A mutanen Bauchi dai babu mai zuwa sai Jamilu sai ko Khadijah da Alawiyya, dukansu kuwa ƙannen Abdul-rasheed ne uwa ɗaya uba ɗaya. Sukam suna iya bakin ƙoƙarin su akan ziyartarta ita da yara da kawo mata ɗan abinda ya samu. Sai ko mutanen Maiduguri da wasu basu manta alkairin Abdul-rasheed ɗin a garesu ba sukan kwatanta suma gwargwado musamman idan su Khadijah zasu zo dubasu.      A yanzu Alhamdullah sanar da Haysam ya kafa ya bari itace ke riƙe da mafi yawan buƙatunsu. Dan Mammah ta rage yawan aikin wahala kasancewar sana'ar na tasiri ana zuwa har gida a saya. Idan suka ƙare ta shiga kasuwa ta saro komai. Zuwa yanzu harda su robobi turamen zani da ƴan kayan yara. Kayan koli dai na sanar cikin gida na mata komai Alhamdullah.        Watannin su Haysam takwas suka samu hutu. Hutun da yay matuƙar saka Mammah da ƴan uwansa a farin ciki mai yawa da girman gaske. Nanfa aka shiga hidima da shi, dan abinci na musamman Mammah tai masa. Murmushi da hawaye sun kasa barin fuskarta. Mamaki take sosai na ganin yanda Haysam ya ƙara girma, yaron da ta tura makaranta cikin talauci da wahala, yanzu ya koma soja mai kwarjini. Gaba ɗaya ya juye kamanin mahaifinsa, farar fatarta kawai za'a ce ya ɗebo. Ya zama wani ingarman namiji a tsaye kamar ba ɗan shekara sha takwas ba..       Shima Haysam zuciyarsa cike take da farin cikin ganin Mammah ta samu nutsuwa ta rage yawan wahalhalun da take, sana'ar daya gina ta kafu kowane motsi cikin sallamar sayen abubuwa ake. Sai yaji kwanciyar hankali na ratsashi da nutsuwar zuciya.      “Muhammad Haysam” ta faɗa cikin raunin murya duk da ba kasafai take kiran sunansa ba, kafin ya samu amsawa ta cigaba da faɗin, “Na daɗe ina addu’ar ALLAH ya cika maka burinka. Yanzu kam ka zama abin alfaharin Mahaifinku”.      Matsawa yay gabanta sosai tare da kama hannunta ya runtse a cikin nashi, cikin taushin murya da tsantsar ƙaunar da yakema mahaifiyarsa ya ɗora kansa a ƙafafunta. “Mammah. ba ni da abin da zan biyaki da shi sai godiya da tarin addu'a a wannan duniyar. Addu’ar ki ce ta zama garkuwata, tarbiyarki ta zama jagorana, burin Abiy ya zama ƙarfina, Jajircewar Umma ta zama nagartata ta. ALLAH ya ƙara miki lafiya da tsawon rayuwa, ya gafartama Umma da Abiy yasa mu da su duk mu shiga aljanna”.         “Amin ya rabbi Haysam”. Mammah ta faɗa yana share hawayen da suke sakko mata. Ɗagowa yay yakai hannu yana share mata hawayen da murmushin ƙarfafawa a gareta kan fuskarsa, duk da kuwa shima tashi zuciyar a raunane take, sai dai mazan maza ne na gaske masu iya jurewa da danne kowane irin ɗaci.        Bayan ya gama share mata hawayen ta kalle shi da damuwa, “Ka kula da kanka Haysam. A koda yaushe wannan yawan shirun naka na sani a damuwa da tunanin ko kana farin ciki. Idonka yana ɓoye abubuwa da yawa, kar ka bari zuciyarka ta sha wahala fiye da jikinka kaji Zakin Abiy”. Ta ƙare maganar da ɗan jan hancinsa tana murmushi.       A karo na farko shima yayi murmushi mai ɗaci, sai ya sake kwantar da kansa a kan ƙafafun nata, “Mammah zuciyata tuni ta saba da komai a yanda yake. Kisa a ranki ɗan Umma da Abiy a koda yaushe yana cikin farin ciki gwargwadon rahamar UBANGIJI. Ba kowane shiru bane na damuwa, ba kowane shiru bane kuma mara alkairi. Wani shirun shine amsa ga rayuwar kowa da mai shirun kansa”.         Mammah tai murmushi tana shafa kansa. A koda yaushe ɗabi'u da kalaman Haysam na juye mata tamkar Abdul-rasheed a gabanta bai ɓuya cikin ƙasa ba. Ta kowane ɓangare shi photo copy ɗin mahaifinsa ne. Tana fatan ALLAH ya bashi tsahon rayuwa mai albarka ya ida cika buruka na Abdul-rasheed ɗinta masoyi na gaskiya........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 31_ __________________ 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH?mode=ems_copy_t *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF 'YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Kwanansa biyu ya huta Mammah ta zaunar da shi tai masa bayani akan matsin lambar kawunanta game da aure. Abin mamaki sai taga Haysam yay kicin-kicin da fuska har idanunsa sun kaɗe. Cikin son kwantar masa da hankali dan ta fahimci kishin mahaifinsu yake ta ce, “Nima ba auren nan nake so ba, dan da ina da damar dazan bijire musu tabbas da nayi hakan. Bani da wani buri sai na ganin na tsaya a kan tarbiyyar ku, rayuwarku ta inganta kuma. Amma na rasa ta inda zan zamewa al'amarin su. Yanzu haka jiya-jiya Kawu Rayyanu ya kawo min wani mutumi wai makwafcinsu ne, yanata damunsu a kaina, shi da gaske yake ba wasa yazo da shi ba. Ban ɓoye masa akan ku ba yace yaji ya gani ya kuma yarda nai zamana anan shi zai dinga zuwa.”          Karo na farko Haysam ya ɗago yana kallonta, idanun nan sun kaɗe jazur. Cikin ɗacin murya ya ce, “Kuma kin yarda Mammah?”.      Rasama mi zatace masa tayi, dan gaba ɗaya ya juye mata tamkar Abdul-rasheed a gabanta. Sai kawai ta girgiza masa kai. “A'a ban amince ba”.      Ajiyar zuciya Haysam ya saki tare da furzar da huci, harma abin yaso mata dariya amma ta gimtse. Daga ranar bata yarda ta sake masa batun auren nan ba, har hutunsa ya ƙare ya shirya ya koma ya sake barinsu da kewa. Ya wuce da sati biyu aka ɗaura mata aure da Alhaji Nura. Harga ALLAH ba son auren nan A'isha take ba, amma haka ta daure ganin Alhaji Nura mutumin kirki ne, baida damuwa bai da hayaniya kuma. Kamar yanda yay alƙawari kuma ya riƙe mata marayu kamar ƴaƴansa. Bai rabata da sana'arta ba ya kuma shiga gyara mata gida. Matsalar abinci babu ita, haka ma ya shirya Malam Sulaiman ya rakashi har Kaduna ya duba Haysam. Shi Haysam bai fahimci komai ba, a tunaninsa abokin Malam Sulaiman ne kawai. Dan haka ya gaishesa da girmamawa tare da sakin jiki yana amsa masa tambayoyin daya dinga masa.      Rayuwa ta cigaba da shuɗawa Mammah ta sake samun kwanciyar hankali da mijinta. Tayi ƙyau yaranta sunyi ƙyau suma sunata karatunsu. Duk da dai su Ja'afar da farko basu saki jiki da Alhaji Nura ba suma sai da Mammah ta dinga musu faɗa da nasiha. A haka Haysam ya sake zuwa hutu ya tarar da abinda bai masa ba. Amma da yake ya kwankwaɗi tarbiyya ya ƙoshi haka ya danne a ransa bai ko nunama Mammah ba har hutunsa ya ƙare ya koma. Tafiyarsa babu jimawa ciki ya bayyana a jikinta. Sosai Alhaji Nura ya nuna farin ciki mai tsanani da wannan ciki, dan matansa biyu babu wadda ta taɓa ko ɓatan wata shekaru fin goma-goma yana tare da su kuma sai Mammah a yanzu. Aifa kafin kace mi zance ya zagaye ko'ina, Mammah na samun gata iya gata a wajen mijinta kamar zai lasheta da wannan ciki, in dai kaga bata samu abu ba sai dai in batace tana so ba. Haka aka cigaba da rainon wannan ciki.       Cikin Mammah nada wata bakwai abubuwa suka fara canjawa a yanda suke. Hidimar Alhaji Nura ta fara raguwa, hakama ɗokin wannan ciki, kai takai yanzu sai yay sati bai leƙo gidanta ba. Tun mutane basa fahimta har aka fara fahimta, wasu suka fara faɗin bai san haihuwa ne ai dama, wasu suce matansa ne sukai masa asiri, dan yaje ya tare a gidansu sai hidima yake musu. Al'amarin kamar wasa ƙaramar magana ta fara zama babba, takai Mammah tayi wata guda bata saka Alhaji Nura a idonta ba. Su Ammar da suka buɗi ido da shi suna kallonsa matsayin mahaifi sunci kukan har sun gaji sun haƙura. Inda ta godema ALLAH yanzu sana'arta ta zauna da ƙafafunta, dan tunda ta samu ya ƙara mata jari ta sake miƙewa da ƙafafunta. Ganin haihuwa ta kusa zuwa mata ta samu kawunta da batun abinda ke faruwa duk da tasan ya sani.       Haƙuri ya bata da mata nasiha, ya tabbatar mata subi komai a hankali Alhaji Nura baya cikin hayyacinsa ne, dan al'amarin nasa akwai ƙamshin gaskiya game da asirin da ake faɗa matansa sun masa. Amma dai zai sameshi yaji mike faruwa. Jiki a sanyaye tace to ta koma gida.            ________★   Kamar yanda Kawu ya faɗa zai samu Alhaji Nura ya same shin, amma mi abin mamaki sai Alhaji Nura ya murje ido ya fara tujara ma Kawu, daga ƙarshe ma yace shi ba cikin shi bane ba, A'isha taje ta nema wanda yay mata ciki. Idan kuma aka matsa zai kai kotu. Kai shi yama saki Mammah taje can ta nema uban cikinta. Wannan magana ta girgiza kawu matuƙa. Ya ce, “Haka kace?”.       “Eh haka nace, ku kaini duk inda zaku kaini, ina kan gaskiya ta ciki ba nawa bane ba. Kuma na saketa saki uku”.            “Babu inda zamu kaika, amma zamu zauna tare da waliyanka ka maimaita dukkan abinda ka faɗa kodan watarana kar kace sharri akai maka”.     Daga haka Kawu ya miƙe yayi gaba abinsa. Kamar yanda ya faɗa haka yaje ya samu waliyyin Alhaji Nura daya kasance mahaifinsa ya sanar masa. Shima kansa ya girgiza da wannan magana, babu ɓata lokaci ya nemo ɗan nashi akan batun, abinda kuma ya gayama Kawu shi ya maimaita ma mahaifinsa da waliyyan Mammah babu tsoro babu shakka. Sai kuma zancen yaso zama hayaniya a tsakani, dan kuwa ya sheganta cikin da cewar ba nashi ba, kamar wasa sai da aka dangana da mai-anguwa akai zama tsakanin Mammah da Alhaji Nura, anan ɗin ma bai canja ba daga batunsa na ciki ba nashi bane. Mammah taci kuka matuƙa da yin nadamar aurensa, daga ƙarshe akace sai a bari saita haihu aga mi zata haifa, idan gwaji ya kama sai aje ayi. Da wannan batu aka kashe magana, Mammah taje ta cigaba da rainon wannan ciki cikin matsanancin yanayi da ƙuncin zuciya da kewar Abdul-rasheed, har ALLAH ya kaita ga haihuwa aka samu mace. Abin mamaki yarinya kamar Alhaji Nura yayi kaki ya ajiye saboda kamanni, dan tun tana jinjirarta kamanin a bayyane suke. Mammah ta gode ma ALLAH mutane kuma sun tayata murna. Ita kuma daga nan ta hau kan nata dokin zuciyar, ta tabbatar ma Alhaji Nura bata buƙatar komai daga gareshi game da rainon ƴarta, kuma ko anan gaba kada yace yana da wata alaƙa da yarinyar. Babu ko musu yace ya amince tabbacin yana cikin mayen asiri har lokacin. ALLAH sarki sai mahaifinsa ne yay komai na sunan yarinya aka saka mata suna Habibah. Suna kiranta Biebah. Haysam yazo hutu lokacin yana shekara ta biyu a NDA ya tadda Biebah, yanda yake son sauran ƴan uwansa haka yake jin ƙaunar ta. Mammah bata gaya masa komai daya faru ba shi ma kuma bai tambaya ba duk da yaga Alhaji Nura baya zuwa gidan, a haka ya kammala hutunsa ya koma.... >>>>>>•<<<<<<<               Shekaru Sun shuɗa, Sabbin Jarumai Sun girma. Lokaci ya tafi kamar iska mai kaɗawa a zamanin rani da damuna. Shekaru uku sun shuɗe cikin gumi, jini, da hawaye ga matasan soji. A yau Haysam Abdul-rasheed Shehu, wanda aka fi sani da Zak-Shadow ya zama ɗaya daga cikin fitattun senior cadets na NDA. Yanzu idan ya wuce, sabbin cadets suna tashi tsaye domin girmamawa a garesa.        A gefe kuwa Imran Abbas wanda a da yaro ne mai rauni ya zama ɗaya daga cikin masu kwarewa a sashen signals and intelligence unit. Ba wanda ya taɓa zato cewa shi ne sarkin kukan nan da ya shiga makaranta a shekarun uku da suka shuɗe. Duk inda suka shiga ana kiran jaruman biyu da suna (The two Shadows). Domin kuwa suna aiki tare tamkar gangar jiki ɗaya da zuciya biyu. Sunan Zak-Shadow da Imran ya sanya ma Haysam ya bishi, har takai Zak-Shadow ɗin yayi gaba fiye da sunansa na yanka.        A yau suna aji ɗaukar darasi da Major Adetunji ke ɗaukarsu, wanda ya horar da su tun farkon shigowarsu NDA. Bayan ya kammala ya sallamesu su Zak-Shadow suka iso gaban allo ɗaukar masa kayansa domin yi masa rakkiya kamar yanda suka saba. Kallonsu ya tsaya yanayi cikin murmushi, “Haysam Abdul-rasheed Shehu, Imran Abbas the two Shadows”.       Murmushi sukayi a tare, duk da kuwa idan yana jin nishaɗi yakan kirasu da sunan ne daman. Batare daya jira amsawar su ba ya cigaba da faɗin, “Kuna cikin waɗanda suka fi nuna mana menene juriyar soja a wannan mate ɗin naku. Shiyasa kuke na daban a zuciyata yaran albarka, ina son a shekarar ƙarshen nan ku ƙara ƙwazo da jarumta fiye da shekaru uku da suka shuɗe, dan ina son ku zama misali ga duniya idan kuka fita ba cikin makarantar NDA kawai ba”.        Ƙaramin murmushi Haysam ya yi tare da salute ɗinsa, hakama Imran, a tare suka amsa da murya mai zurfi,  “Yes, sir.”       Major Adetunji yay murmushi shima, dan har cikin zuciyarsa yake jin ƙaunar Haysam da Imran. Yaran akwai tarbiyya da nutsuwa. Babu wanda zai ce yau ga wani laifinsu ko wani ya kawo ƙararsu ana faɗa dasu a cikin ɗalibai. Gasu da maida hankali akan komai. Duk wahalar da Haysam yaci a hannun Seniors bai taɓa kai ƙarar kowa ba, sai idan su sun gani su hukunta Seniors ɗin musamman idan muguntar tayi yawa. Sai gashi a yanzu komai yana neman zama tarihi, dan watanni kaɗan ta rage su shiga shekarar ƙarshe a NDA ɗin........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 32_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Komai ya cigaba da canzawa a kowane sakan zuwa minti da awoyi tamkar yanda kwanaki suka shuɗa zuwa watannin suka bada shekara uku data shuɗe. Su Senior Garba dake shekarar ƙarshe suna nan akan bigiren iska mai wahalar da kayan kara, domin kuwa har zuwa yanzu suna jin haushin yadda Haysam ya zama abin koyi, har officers ke yaba masa a bainar jama’a da yi musu misali da shi matsayin abin koyi. Sai dai kasancewar Haysam da kowa ke kira Zak-Shadow a yanzu ya zama jan wuya yasa su kansu shakkarsa suke basa iya yimasa abu kai tsaye kamar yanda sukeyi a shekarun baya na farkon shigowa.        A yau ma ya fito massalaci da yay zaman yin azkar ɗin yamma bayan sallar la'asar Senior Garba ya kira shi gaban sabbin cadets da yake jagoranta. Harga ALLAH shi Zak-Shadow baiga ma Senior Garba ba, saboda hankalinsa yayi kan tunanin ina Imran ya shiga ne dan batare sukai sallar la'asar ba. Bayan an idar shi kuma ya zauna ɗaukar karatu kamar yanda ya saba a wajen malaminsu, daga nan yay azkar shine yake fitowa a yanzu.       Yanayin yanda akai kiran nashi ya sashi dawowa daga duniyar tunaninsa akan Imran, cike da nutsuwarsa ya juyo sai sukai ido huɗu da Senior Garba ɗin, kamar zai shareshi ya wuce dan yasan shashasha ne sai ya fasa ya nufi inda yaken. Cike da son zubarma da Haysam ɗin mutunci a gaban yara Senior Garba ya furta, “Cadet Haysam! You think being praised makes you a soldier? We made you, remember that.”       Idanu Zak-Shadow kawai ya ɗan zuba masa kamar bazai tanka shi ba, hannuwansa a cikin aljihun wandonsa, har yay niyyar yaɓa masa baƙar magana dan ya iyata kwali-kwali, bashi da yawan magana, amma idan ya yaɓa maka baƙa ɗaya sai ka kwana ka yini tana cizon zuciyarka, amma miya tuna sai ya fasa, a taƙaice ya ce, “With all due respect, senior, the Academy made us all.”      Garba ya yi murmushi mai cike da baƙin ciki da tsana wanda ke ɓoye fushi, shifa duk sanda yaga yaron nan ji yake kamar ya shaƙeshi ya mutu ya huta ALLAH. Cikin kallon idon Haysam ɗin da shima ke kallonsa ƙyam ya ce, “Hmm.. perfect cadet. Zamu ga yadda zaka fuskanci Special Night Drill”.        Kai kawai Zak-Shadow ya girgiza yana barin wajen, dan lokuta da dama ɗaukar al'amarin Garba yake matsayin soki burutsu da motsuwar kai. Yasan night drill ba abune mai sauƙi garesu ba cadets, ana amfani da shi ne wajen gajiyar da mutum ta jiki da ta zuciya matuƙa, gudu cikin duhu, rarrafe cikin laka, da ɗaukar kaya masu nauyi har zuwa safe. Wasu ma daga cikin cadets suna jin tsoro idan aka ce “special night drill”, amma shi bai taɓa ɗaukar hakan matsayin wani abun tsoro ko tashin hankali ba balle ya nuna damuwa. Ɗaki ya koma abinsa inda ya samu Imran ya dawo yana jiransa.        ★ Da daddare kamar yanda Senior Garba ya faɗa ɗazun da yamma su Zak-Shadow suka fita Special night drill. Kasancewar akwai abinda Garban da abokansa suka shiryama Zak-Shadow yana gefe yana kallonsa cikin murmushin mugunta.        John da shima ke kallon Zak-Shadow cikin taɓe baki da ƙwafa ya ce, “Wai shi yana jin kansa wani shege ko, zamu bashi banbancin kare da uban gida a yau, wannan karon sai mun karya shi”.       Ƙwafa kawai sauran sukai batare da sun tanka ba. Shima Zak-Shadow da bai san sunayi ba ma ya cigaba da motsawa cike da karsashi da ƙarfin jiki mai tafiya dana zuciya. Sam babu gajiyawa a tare da shi, sai ma taimakawa waɗanda suka faɗi a hanya yake yi. Sun dawo a zagaye na biyu wasu sun fadi ƙasa, wasu suna shashshekar wahala harda masu share hawaye, amma shi yana tsaye, yana kallon Garba kai tsaye cikin shirun daya saba kowa kuma ya sanshi da shi. Shiru ne mai zurfi dake ƙona zuciyar maƙiyansa. A zuciyarsa kuwa ayyanawa yake.        (Yau zan nuna maka Ba ruwan jarumta da wanda ya fara zuwa duniya ko ajin karatun duniya Garba. Ba zan rushe ba, in sha ALLAHU har abada bazan faɗi a ƙasanka ba sai dai kabar NDA da takaici na a zuciyarka kuwa. In yaso ka ajiye aikin soja ka koma rawar ƙoroso).        Yanda Zak-Shadow ke kallon Garba sai ya ɗan ji tsarguwa a zuciyarsa ga shakka da kwarjininsa na cizonsa a rai, amma sai ya dake saboda izza, shawarar da zuciyarsa dake gargaɗinsa yabi cike da gadara ya ce, “Dismissed!”.       Ba abinda Zak-Shadow da abokan Garba sukai tunanin ji zai fito a bakin Garba ɗin ba kenan. Dan haka ya bama abokansa haushi. Zak-Shadow kam ya wani bisu da kallo cikin ƙyaɓe baki ya bar wajen. Yana fara tafiya Imran ya ƙaraso suka jera yana goge laka daga fuskarsa.       “Wallahi ba soja bane kai Zak… kai dutse ne. ALLAH tsoro ka bama Garba fa amma wata maganar banza yaso gaya maka da farko kamar yanda ya saba”.       Zak-Shadow ya murmusa cikin nutsuwa da kallon Imran ya ce, “Kaji tsoron rabbi Imran. Ai dama dutse baya jin zafi, ni kuwa mutum ne ina ji, kawai ban bari su gane ne dan har abada bazasu ga Haysam Abdul-rasheed a ƙasan takalmansu ba in sha ALLAHU”.          “In sha ALLAHU kuwa ƴan wahala.” __________★       KOMAI NISAN JIFA....    Alƙawarin ALLAH ya cika. Shekaru sun wuce cikin wahala da zafi, ƙura da ruwan sama harma da sanyi. Haysam Abdul-rasheed Shehu da abokinsa Imran Abbas sun girma a cikin NDA kamar ƙasar da take haifar da ƙarfin hali da gwagwarmayar neman ƴanci.. Tabbas zuwa yau an manta da lokacin da ake kiransu “new boys.” Yanzu sune manya Seniors dake faɗa aji da shugabantar masu shigowa har ma da masu bi musu. Tabbas shekarar ƙarshe shekarar ƴanci amma shekara mafi tsaurin gwagwarmaya da karatu mai tabbatar da yaro soja. Haka su Zak-Shadow sukai juriya ƙwarai da gaske wajen tsallaketa tamkar yanda suka shallake na baya da suka shuɗe. Alhamdullah ga burin ƴan maza ya cika, NDA ta zama tarihi tamkar yanda primary da Secondary suka zama tarihi suma.        A daren da suka karɓi takardar kammalawa, Zak-Shadow ya tsaya yana kallon harabar NDA, zuciyarsa cike da tunani. Wajen da ya sha ruwan sama, gudu a cikin laka, da azabar push-ups har yatsunsa suka kumbura, yau shi ne wurin da zai barwa tarihin da sai dai a tuna a bama ƙanne da ƴaƴa labari watarana.       Imran ya matso kusa da shi murmushi na bayyana cikin fuskarsa mai tarin nutsuwa, “Zak-Shadow” ya kira sunansa da murya mai sanyi, bai jira amsawarsa ba ya cigaba da faɗin, “ka tuna ranar farko da muka shigo nan?”.        Juyowa yay yana kallonsa fuskarsa da murmushi mai nauyi, cikin buɗaɗɗoyar muryarsa mai fita da amon mazaje ya amsa masa da, “Idan zan mance da wannan ranar tabbas zan mance da kai My Imran. Yanzu kamar jiya ne... kai da kukan nan naka da yasa na tsaya ina kallonka tamkar Ma'aruff ko Ja'afar a gabana”.       A tare sukayi dariya, abinda Zak-Shadow bai cika son yi ba. To dama mai ganin suruntun nashi kamar hakan sai dai Imran ɗin ai.             ★Alƙawarin ALLAH ya cika, Haysam ya samu cikar burinsa daya ginu bisa burin mahaifinsa. Ya kammala NDA bayan shekaru huɗu na wahala, gwagwarmaya, juriya da jarumta. A yau suke bikin Passing Out Parade ɗin su, musalta irin farin cikin da yake aciki abu ne mai wahala. Ba shi kaɗai ba, hatta Mammah da ƴan uwansa da malam Sulaiman da kawunsa da yazo daga Bauchi, da Innarsa Khadijah da Alawiyya suna cikin farin ciki. Domin kuwa sun halarci bikin passing out ɗin nasu su duka. Yanzu Haysam ba ɗan takara ba ne, soja ne cikakke, Second Lieutenant Haysam Abdul-rasheed Shehu (Zak-Shadow).      Sun yi parade a gaban manyan jami’an soja da iyaye da ƴan uwa da abokan arziƙi. Ɗalibai da yawa da suka nuna ƙwazo a fannoni daban-daban sun samu ƙyautittuka na girmamawa, ciki kuwa harda Haysam. Lokacin da aka kira sunan Cadet Haysam Abdul-rasheed Shehu, sai dukan ɗakin ya amsa da ihun kiran sunansa daga mate ɗin nasa.       “Sarki! Sarki! Zak-Shadow! Zak-Shadow!”.      Kai kace zasu fasa hall ɗin ne har iyaye da suka halarci taron najin ƙagara da mamakin wane yarone wannan mai farin jini ga yaransu haka?, sai da aka tsawatar musu saboda ihun kiran Haysam da ya kasa miƙewa sai da Imran ya kama shi ya miƙar tsaye. Cike da nutsuwarsa ya tako ya fito inda ake buƙatar ganinsa. Ba ƙaramin ƙyau kayan sukai masa ba, sun zauna a ginannen jikinsa na asalin zakin ga ƙƴawu ga nutsuwa ga addini, dan goshinsa kawai ya isa baka shaidar shi mai ibada ne kodan damɓareren tabon sallar da yake da shi. Ba tabon salla kawai ba a yanayin nutsuwar Haysam kawai zaka tabbatar da akwai ilimin addini sosai a tare da shi.. Zak-Shadow ya amshi lambar yabo ta Discipline and Endurance. Ya kuma samu ƙyautar girmamawa ta Best in Field Tactics & Discipline, abin da ya sa Mammah da ƙannensa suka yi kukan farin ciki a wajen kallon taron da suka halarta. A tare ƙannensa suka tashi mazansu da matansu sukaje suka rungumeshi. A karo na farko idonsa ya cika da ƙyallin hawaye, wannan ba kawai nasara bace, ƙarshen tafiyar jarumta ce da cika burin Abiy da samar da farin ciki a zukatan ƴan uwansa da Mammah, inama Abiy na raye ya cimma wannan rana.. isowar Imran daya ɗan buga kafaɗarsa da dariya ya sashi haɗiye hawayen nasa. Sai kuma ya juya yana kallonsa, suma ƙanensa sakinsa sukai suka koma wajen zamansu.       Kashe masa ido ɗaya Imran yay da faɗin, “My Zak-Shadow yanzu zai koma gida a matsayin soja na gaskiya. kaga yanda Mammah take kukan murna ita da su Ma'aruff.”       Haysam ya murmusa, yana mai lumshe idanunsa ya sake buɗewa akan su Mammah sannan ya dawo da su kan Imran.          “Tabbas Mammah tana kuka ne irin na farin ciki da cikar burin mijinta Imran, ba kukanta ita kaɗai take ba harda kukan Abiy da Umma duk a tare. Amma nima ba zan taɓa manta nan ba Imran. Wannan wuri ya juya ni daga maraya marar gata, zuwa mutum mai ƙarfi da damammaki da samun cikar burin mahaifi. Imran in sha ALLAHU sai na kaima Abiy wannan albishir har Bauchi a gobe-goben nan in dai ina da rayuwa”.          “ALLAH ya cika maka burinka, kuma ba kai kaɗai zaka Bauchi ba harda Imran Abbas ɗan Abiy da bai sani ba”.        Wani ɗan dukan basawa Zak-Shadow ya bama Imran a kafaɗa, sai kuma ya rungume shi hawayen da yake ta shanyewa suka samu damar ɗigowa. Shima Imran hawayen ne ke zubo masa. Yana ƙaunar Haysam, yana tausayinsa ƙwarai da gaske. Dan shi har yanzu bai san maraici ba, uwa da uba duk suna raye, kai shi tunda yasan kansa ba'a taɓa mutuwa a gidansu ba ma gaskiya. Sai dai a dangi haka sai kakarsu da ta rasu yana yaro sosai. Sannan gidansu su suna da kuɗi.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 33_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .......Zak-Shadow da su Mammah sun wuce Kano, zasuyi hutu na makwanni har shida. Ashe walima Mammah ta shirya masa. Dan haka suka iske gida cike da danginta anata girki. Ƴan Bauchi dai iya kawunsa ne kawai sai Khadijah da Alawiyya suka zo. Bai damu ba, wanda ya gani ɗin ma sun wadatar. Anci ansha an masa addu'oi kala-kala harda mutanen anguwa.      Bayan kwanaki biyu gida ya koma sai su kaɗai, Zak-Shadow ya sake fahimtar rayuwa ta canja ga mahaifiyarsa, ta tabbata dai bata tare da sabon mijinta. Sai dai yanzun ma bai tambaya ba saboda girmamawa har sai da Mammah ta sanar masa komai a wannan karon da bakinta. Tabbas zuciyarsa ta hasala matuƙa, amma bai ce komai ba dai a zahiri. Itama Mammah data fahimci yanayin nasa sai tai masa nasiha da gargaɗinsa akan kar taji wani abu daga garesa. An riga anyi ya wuce sai a tari gaba. Badan yaso ba yay shiru kamar yanda ta gargaɗe san.       A cikin wannan hutu ya samu damar bibiyar karatun ƙanensa, har zuciyarsa kuwa ya gamsu da yanda komai ke tafiya Alhamdullah. Musamman ma su Ja'afar ƴan Secondary. Ya ji daɗin kuma ganin yanda kasuwar Mammah tai tasiri a gida. Ya ziyarci Malam Zayyanu da abokinsa Malam Datti. Sun masa addu'a sosai da nuna jin daɗin nasarar da ya samu a NDA.      Duk da yana cikin hutu bai daina yin motsa jiki da safe da yamma ba, kamar yadda suke yi a NDA. Wani lokacin idan yana fama Mammah har faɗa take masa ya huta. Yakan yi murmurshi ne kawai ya ce, “Mammah idan banyi ba jikina zai yi ciwo ne”.     Haka dole ta ƙyaleshi har hutunsu ya ƙare, kamar kuma yanda yay alƙawari yaje Bauchi tare da su Ma'aruff cikin weekend. Sun ziyarci kabarin mahaifinsu da Umma har ma da kakaninsu su Malam. Babu wanda yasan yaje a ƴan uwan mahaifinsu sai kawunsu Jamilu kawai, dan basu kwana ba a ranar suka juyo Kano.        A watan Agusta ya koma Jaji, domin yin Young Officers Course, inda ya sake haɗewa da Imran, a wannan karon ma a ɗaki ɗaya suka zauna, dan sai da sukai duk yanda zasuyi aka haɗasu cikin amincewar UBANGIJI. Alhamdullahi sun kamalla course ɗin su a farkon shekarar 1999, daga nan kowa aka turashi inda zai fara aiki. sai dai an samu matsala dan anyi posting ɗinsu waje daban-daban shi da Imran, amma da yake suna da oganni tuni suka nema oga Adetunji suka sanar masa damuwarsu. Shine yay ta kai kawo har aka haɗasu waje ɗaya yanda suke fata, antura su aiki zuwa 82 Division Enugu, inda suka fara rayuwar soja ta zahiri. A can suka gane cewa aikin soja ba na jarumtaka kaɗai ba ne, aikin zuciya da sadaukarwa ne. ★Su Zak-Shadow na Enugu cikin sabuwar rayuwar aikin soja, anan rayuwar Mammah da marayun ƴaƴanta na neman canja salo da fuskantar sabuwar jarabawar rayuwa. Domin kuwa Zak-Shadow bai wuce watanni uku a Enugu ba Tasi'u ƙanin Mammah ya zo kwatsam. Zuwan daya saka Mammah a farin ciki dan tayi tsammanin har abada ta rasa dukkan ƴan uwa a duniya.        Da farko dai kamar abin arziƙi tsakaninta da Tasi'u, dan harda zama ya bata labarin rayuwar da yake ciki ta tashin hankali. Yarinyar daya aura basu ko ƙulla shekara ɗaya ba a rayuwar aure suka rabu, ya shiga halin rayuwa mai tsanani a sabuwar ƙasar da bai san kowa ba, haka ya jure saboda karatun da yake yi. To zuwa yanzu ya kammala, acewarsa har ya samu aiki, yanzu ma yazo gida ne domin wani aiki da zai yi na wata uku ya koma. Mammah ta jajanta masa ta kuma tayashi farin ciki.       Sunyi sati kamar uku a wannan farin cikin kwatsam rana tsaka sai ga Tasi'u da lauyoyi har biyu da wasu mutane, wai yana son a raba gida a bashi nashi kaso. Mamaki ya kama Mammah, ta kalla gida ta sake kallo, tabbas gidansu babba ne, gashi a bakin titi, kusan a yanzu ma gidan yafi duk wani gida na layin ƙyau saboda gyaran da Alhaji Nura yay masa lokacin daya aureta. Da farko ta ɗan so tirzawa tai masa faɗa, ya nuna mata shifa ba yaro bane, sannan gidan nan dai yana da hakki ai kuma dolene a bashi nashi hakki. Ganin yana son su zubar da mutunci a anguwa tace ba damuwa yayi duk yanda yaso, ko ɗaki ɗaya ta samu ALLAH ya amfana zata zauna da yaranta. Haka kuwa akai yayta shiga da fita batare daya bari tasan yaya komai yake tafiya ba. Kwatsam a cikin wata na biyu da zuwansa ta nemeshi ta rasa. Duk inda ya kamata ta bincika kuma tayi amma babu shi. Hankalinta yaso tashi kawunsu yace karta damu kanta, ta barshi duk ma inda yaje zai dawo tunda ba yaro bane. Haka dole ta haƙura ta share. Abin mamaki cikar wata ɗaya saiga wasu mutane wai sunzo gidan nan da take ciki nasu ne an sayar musu, suka nuna mata takardu harma da shaidun gani da ido da akai ciniki da su. Hankalin Mammah ya tashi kwarai da gaske, sai ta rasa inama zata saka kanta dan tashin hankali, kawai ta yanke jiki ta faɗi sai da aka kaita asibiti. Kwananta biyu aka sallamota, abu dai kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba Tasi'u ya saida gida ya gudu. Masu gida kuwa sun bata wata ɗaya kacal suna buƙatar gidan akwai abinda zasuyi da shi.      Wannan tashin hankali ya saka Ma'aruff da Ja'afar sulalewa suka tafi Enugu suka sanar ma Zak-Shadow. Kwatsam babu zato ya gansu, mamaki ya kama shi ya balbalesu da faɗa domin a ganinsa ai kasada ce zasu kamo hanya batare da sanin gari ba su taho. Su dai haƙuri suke ta bashi, Imran dai ya kwacesu da ƙar, shine ya basu abinci sukaci ya basu wajen kwanciya. Zak-Shadow bai saurarensu ba sai dare, anan ne suka sanar masa abinda ke faruwa da halin da Mammah ke ciki, suka tabbatar masa a yanzu ma sunzo ne bada saninta ba, dan sun tabbatar tana can tana nemansu ƙilama hankali a tashe..          Jin wannan zance ya sake ɗaga hankalin Zak-Shadow, haka ya samu da ƙyar da kamun ƙafa aka bashi damar zuwa gida kwana uku kawai. Ya taso ƙanensa gaba suka nufi Kano. Aiko hasashen su ya tabbata, dan sun sami Mammah cikin tashin hankalin rashin sanin ina su Ja'afar ɗin suke, sai kuma gashi ta gansu harda uban gayya Haysam. Kukan dake danƙare da ƙirjinta sai a lokacin ne ta samu ta yi shi. Wannan al'amari ya sosa zuciyar Zak-Shadow matuƙa. Wanda ma bai san fushinsa ba a wannan karon ya gani kwarai da gaske.      Ɗan kuɗin albashinsa da yake faman ajiyar taro da kwabo a account ya kwashe domin sayen fili, sai dai a karo na farko Kano ta fita masa a rai gaba ɗaya, yana son yin nesa da ita nisa mai yawa ko mahaifiyarsa zata samu salama tamkar yanda ta baro Bauchi, amma kuma bai san ina zai maidasu ba, dan haka ya nema shawarar Imran ta hanyar kiranshi a wayar landline. Babu wani ja'in-ja Imran ya bashi shawarar zuwa Abuja kawai, ya kuma haɗashi da yayansa.     A ranar Haysam ya bar Kano zuwa Abuja. Inda da taimakon yayan Imran suka samu fili suka saya. Sauran kuɗin daya rage ya sayi siminti da bulo aka fara ginin ɗakuna ƙwara biyu kacal. Kwana uku aka bashi kawai a wajen aiki, dan haka dole ya koma Kano yabar sauran aikin wajen yayan Imran. Yana zuwa Kano ya sanar ma Mammah komai, mamaki ya kamata sai kuma ta shiga yi masa faɗa akan dammi zai yi hakan. Shi dai kansa a ƙasa kawai yana bata haƙuri ne. Sai da ta kammala yace su fara shiri kawai, nan da kwanaki kamar goma zasu koma can shi kuma ya shirya ya koma Enugu.       Haka kuwa akayi, kwanaki goma bayan komawar Zak-Shadow yayan Imran yazo har Kano da mota ya kwashi su Mammah da yaranta. Tafiyar data sakata kuka sosai, jikin ƴan uwanta yay sanyi da rashin taimakonta da basuyi yunƙurin yi ba har Haysam ɗin ya yanke hukunci. Dan sun so hanata da nuna mata zasu ɗauki mataki tace ba komai zata koma Abujan kawai dan itama bata son zaman Kanon a yanzu.     Wannan shine sanadi kuma mafarin barin Kano dasu Mammah sukai suka dawo Abuja. Ɗaki ne guda biyu kawai, sai aka zagaye gidan da kwanon langa-langa. Dan Zak-Shadow ya nuna baya son taimakon komai daga wani saboda Yayan Imran yaso yin hakan. Shima kuma Imran ɗin yaso yin hakan amma ya haƙura dan yasan wanene Zak-Shadow, idan yace baya son abu to kawai baya so ɗin da gaske.      Yana sake ɗaukar albashin watan ya nufo Abuja, kuɗin yay amfani da su wajen maida ƙannensa duk makaranta, su Ammar ma da ba'a saka ba ya sanya su. Dama Mammah tunda suka dawo bata zauna ba, haka ta dinga shiga tana fita wajen nunama mutane kayan sana'arta ta koli. Sannu a hankali aka fara ganewa, kasancewar sabuwar anguwa ce kafin mutum yaje kasuwa sai yafi ganewa zuwa wajenta sayen abu a sauƙaƙe. Ganin haka ta fara haɗawa da kayan miya, da wannan sana'ar da albashin Zak-Shadow suka cigaba da rike rayuwarsu, idan an samu ɗan rarar kuɗi a sai siminti a ɗan ɗora gini. Kwatsam sai kuma ga wata ƙaddarar ta sake afkawa Zak-Shadow lokacin da yake shekara biyu da fara aikinsu, wai ya buɗe wata gaskiya wani ogansu yayi kutun-kutun an saka shi a prison. ALLAH sarki rayuwa, a wannan gaɓar ALLAH dai ya ƙaddara Mammah kam bazata rasa ranta ba. Dan bama ita kawai ba hatta su Ma'aruff sun shiga wata irin gigitar rayuwa.     Haka Mammah ta dinga bin duk wanda ta sani cikin roƙo da magiya don ganin Haysam ya kuɓuta. Amma ina, Imran ma iya bakin ƙoƙarinsa yake amma al'amarin kamar da wani babban shiri a cikinsa. Hatta su Adetunji sunyi iya yinsu Zak-Shadow bai fito ba. Ga baƙar wahala suna bashi ta tashin hankali kamar sun sami criminal, duk mai hankali yaga wannan al'amari yasan akwai lauje cikin naɗi a ciki, sai dai kai tsaye basu san wa zasu fuskanta suce yayi ɗin ba..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 34_ __________________ https://chat.whatsapp.com/L3BXH7JYlBRHIkFRiOjeW3?mode=ems_copy_t UMMU KHALIFA COLLECTION Ina Mata Yan kwalisa ina mata masu san kayan ado kamar Egyptian abaya sleeping drees kids were shos bags musk dahara original. To kukanku yazo karshe domin ummu khalifa sun zo muku da duk wadannnan kayan dierct suke order dinsu daga Egypt zuwa gida Nigeria kaidai kawai kashiga link dinsu domin gani ya kori jiii.. Ba nan ummuh khalifa suka tsaya ba suna nemawq mutane visa masu shaawar shugowa kasar ta Egypt karatu ko yawon bude ido ko kasuwanci ku tuntubeta a number dinta +201017018846/07048811474/ KO kuma shafinta na tiktok https://vt.tiktok.com/ZSU1FEkjc/ __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Lamarin kamar wasa sai da Zak-Shadow yay watanni shida sannan aka sake shi. Tsabar azabar da akai masa ana fiddoshi asibiti aka wuce da shi. Dan kai bazaka kallesa kace zai ƙara rayuwa ba a wannan duniyar ko moruwa. Da yake ita rayuwar ta UBANGIJI ce kuma sai gashi bayan jiyyar watanni kusan biyu ya miƙe. Miƙewar data sake canja Haysam Abdul-rasheed Shehu zuwa Zak-Shadow ɗin da yake a yau. Wanda baya ɗaukar raini, baya ɗaukar wasa daga kowa, koda kuwa kowan na sama da shi ne. A bisa bincike kuma aka gano Ogan nashi ne mai laifi ya kuma zaluncesa, dan haka aka ɗauki mataki a kansa aka maida Zak-Shadow bakin aiki tare da ƙarin girma. Ƙarin girman daya sashi wucewa mate ɗinsa a shiga soja su Imran.        Ya fito a prison baifi da shekaru biyu ba ya kammala ginama Mammah muhallin zamanta. Gini mai ɗakuna huɗu dai-dai ƙarfin talaka, sai sauran fili babba kuma a gidan da za'a iya gina wasu parts ɗin ma. A wannan gaɓar ne kuma kwatsam Nasiru abokin Abdul-rasheed ya dawo gida Nigeria da iyalansa. Dawowar daya fuskanci matuƙar tashin hankali saboda jin halin da zuri'ar Abdul-rasheed suka shiga bayan wucewarsa. Da kuma saƙon daya dinga aiko musu da baya zuwa hannunsu. Kwanansa ɗaya a garin kano ya shiryo yazo Abuja. Ranar yaci kuka da takaici kwarai da gaske, ya rantse ya maya akan saƙon da ya dinga aikowa garesu ta hanyar wani abokinsa, saboda tunda ya tafi hankalinsa na kansu ne. Sai gashi koda yasa aka nemo wanda yake bama saƙo ashe shi yanata hidima ne da abinda yake aikoma marayun ALLAH, takaici ya saka shi sawa a rufe shi, sai da ƙyar daban haƙuri ya bari aka sake shi. Amma duk da haka sai da Zak-Shadow yasa aka cimasa ubansa ta bayan fage dai-dai gwargwado.          Dawowar Uncle Nasiru ta sake canja rayuwar Mammah da ahalinta zuwa ni'imtacciyar rayuwa, duk da Alhamdullah dama zuwa yanzu basu tare da kowace damuwa. Dan sana'arta ma tayi girman da a yanzu har shago suke da shi a ƙofar gida da Zak-Shadow ya gyara musu. Karatun yaran kuma duk yana tafiya yanda ya kamata. A wani weekend da Zak-Shadow yazo ya samu babbar ɗiyar Uncle Nasiru a gidan tazo hutu. Yarinya ƙyaƙyƙyawa son kowa ƙin wanda bai samu ba, sunanta Nabiha, girman turai rainon biscuits da madara. Ga ilimi ga shagwaɓa ga gata. Tunda ta ƙyalla ido akan Zak-Shadow ta kafa ta tsare tace tayi mijin aure. Ko damuwa da sharetan da yake ma batayi, dan ita ba komai ma yaja hankalinta a kansa ba sai wannan jin kan nashi da tarin izza da nutsuwa. Harga ALLAH tana matuƙar son namiji maiji da kansa da kamun kai. Daɗin daɗawa ga jarumta, dan ko makaho ya shafa Zak-Shadow yasan sojan ne na gaske ba wasan yara ba. Ga ƙyawun ga gayu ga ilimin addini. Kannensa na girmamashi tamkar mahaifi a garesu. Mammah kanta na ji da shi sai dai bata nuna wa saboda kawaicin ɗan fari.      Babu wani kunya ko tsayawa jan aji tace tana so shi. Shi kuma a take yace mata no. Shi bashi ma da burin aure nan kusa. Aiko ta sanya rigima harda kai ƙararsa wajen Mammah. Mammah kuwa najin wanga batu ta hau ta zauna abinta. Dan dama kullum cikin tunanin ta yanda Haysam zai nema auren mace take yi. Dan ta kula sam hankalinsa baya akan auren, ga Imran har an kai kuɗin nashi auren shi, hakama Ummi yayan Imran ya kafa ya tsare yana sonta.       Ko tsayawa yin shawara da shi batai ba ta sanar ma Uncle Nasiru. Shima ba karamin farin ciki yayi ba da hakan, sai dai mahaifiyar yarinyar ta nuna bata so, a ganinta su Mammah talakawa ne sannan aikin soja ma kamar wani aikin wahala ne. Dama kuma a tsakanin tanata faman tafka tsiya da Uncle Nasiru ɗin akan su koma ƙasar waje ita bazata iya zaman Nigeria ba shi kuma yace ya dawo ƙasarsa kenan, sai kawai wannan batun auren Zak-Shadow da ƴarta ya ida tunzurata suka rikice har ya sake ta. Ya kuma aurama Zak-Shadow Nabeeha, dan itama dai ta bijirema uwar akan itafa babu gudu babu ja da baya. Haka takaici ya saka uwar tattarawa ta tafi ta barsu shi da ƴarsa, ta wuce da sauran ƙanen Nabeeha ɗin guda biyu. Shi ko Uncle Nasiru ya ƙara sabon aure.       Anyi bikin harda na ƙanwarsa Ummi da Secondary kawai ta kammala, aka kaita gidan su Imran itama.. Matar Zak-Shadow kuwa anan gidan Mammah aka ajiye amarya, dan gefensu kaɗan aka yanki fili shima akai masa gini. Zak-Shadow bai fahimci son Nabeeha yake ba shima sai da akai musu aure, dan cikin ƙanƙanin lokaci suka ƙulle. Wata irin soyayya suke ma juna mai tsayawa a rai da zuciya. Sai dai a zahiri baka isa kace hakan ba saboda yanda shi gogan ke kame kansa. Shima Imran anyi nashi bikin da amaryarsa. Anan kuma cikin anguwar su Zak-Shadow yay ginin gidansa mai ƙyau aka sakata.      Rayuwa ta cigaba da tafiya nasarori na cigaba da zagaye Zak-Shadow, ƙarin girma akai-akai har UBANGIJI ya ƙaddara a 2003 ya zama Captain, a Kuma lokacin wani sabon guguwar rikici ta taso a wani yankin ƙasar, an turasu matsayin nayaƙa, turawar data basu nasarori masu yawa har takai sun kada rundunar ƴan ta'addan wanwar, suka samu ƙarin girma kuwa Zak-Shadow ya zama Major. A 2006 kuma rikicin ya sake sauya salon da aka sake turasu wannan jejin dai sai dai a wani yankin ne daban, a inda suka haɗu da waɗan nan mata harda mace mai ciki da tai masa alƙawarin bama ɗanta. Ya kuma tabbatar mata zuwa ya amsa da hannunsa.      Zak-Shadow ya matuƙar taka rawar gani a wannan jeji shi da mayaƙansa, dan kuwa ya hana ƴan ta'addan kowane irin motsin kirki koda na numfashi mai ƙarfi ne. Sannan ya daƙile haƙo ma'adanan da ake a tsakanin ƙauyukan wanda kowa ya tabbatar da saboda su ne ake haddasa rikicin dan masu ɗibarsu su samu damar diba cikin salama a lokacin da su al'ummar ƙauyukan yankin keta rayuwarsu. Sai kuma wata babbar kasuwa dake ata wajen data haɗa kasuwancin wasu ƙasashe itama aka tarwatsata domin cimma wani buri da manufa. Amma zaman Zak-Shadow da yaransa komai ya canja daga yanda yake. Ya sake samun ƙarin girma zuwa Lieutenant Colonel a 2010, har kuma a yanzu 2013 yake a matsayin tare da rundunar mayaƙa a wannan jejin dai da suka samar da zaman lafiya bisa girma da ƙudirar UBANGIJI. Zuwa yanzu kuma ƙanensa mata duk sunyi aure Biebah ce kawai a gabansu. Mazan dai bayan shi babu wanda ya sake aure, kuma har yanzu matarsa bata haihu ba....     Wannan kenan. ________________★         A CIGABA DA GASHI..... 2013...☺️🏃🏼‍♀️     Sosai Zak-Shadow yasha barcinsa, dan bai farka ba sai kusan goma da rabi. Har lokacin kuma da alama babu wanda yasan yana gidan bayan ƙaninsa Bilal. Wanka yay ya kimtsa cikin shigar kamala duk da kuwa ƙananun kaya ne na shan iska a cikin gida. Hankalinsa nakan mahaifiyarsa Mammah, dan haka bai ɓata lokaci ba ya fito.       Gaba ɗaya falon ya kacame da surutu, yara ne ƴammata da zasu iya kaiwa shekaru 17-20-25. Suna akan dining table kowacce kayan barci ne a jikinta. Wata mata da ba tsohuwa ba kuma bazamuce yarinya bace tsaye a dining ɗin tana zuba musu abinci a plates ɗin gabansu. A mistake ta ɗan zubama yarinyar dake kusa da ita da zata iya kai shekaru 20 suger akan waya data ajiye saman table ɗin. Ji kake tasss saukar mari na bazata a fuskar matar, ba kowa bane kuwa da wannan aiki sai wannan yarinya. Cikin ɓacin rai da masifa ta ce,         “Amma ke wawiya ce ko? Dan jakanta a kan wayata ma zaki zuba shuger salon ya shiga min speaker ɗin waya”.       Jikin mai aikin na rawa idannunta cike da ƙwalla ta shiga girgiza kai hannunta dafe da kumatu. “Dan ALLAH Aunty Amima kiyi haƙuri, wlhy kuskure aka samu....”        “Uwar kuskure ba kuskure ba jaka kawai baƙauya. Dalla tashi min aka kona watsa miki ruwan shayin nan a wannan baƙar fuskar taki mai kama da daddawa”.      Da sauri mai-aikin da har hawaye sun fara ma gudu a fuska tai yunƙurin barin waje. Yayinda sauran ke dariyar ƙeta da izgili wai Amima ta kirata mai baƙar fuska kamar daddawa.          “Koma ki rama!!”.      Razananniyar muryarsa dake a buɗe kuma a dake irin ta jaruman maza tsayayyu ta ratsa kunnuwansu. Ta kuma saka mai aikin sake rikicewa da daburcewa amma ta tsaya cak. Haka suma yaran a mugun zabure duk suka miƙe jikinsu na mazari, sai kuma duk suka zube ƙasa duƙe suna faɗin, “Dada sannu da zuwa”.     Idan kujerun dining ɗin sun tanka ya tanka, hasalima ko kallon inda suke baiyi ba. Mai-aikin ya sake tsarewa da idanu cike da bada umarni ya sake furta, “Baki jini bane?”.        Hawayenta ta share da sauri tana jinjina kai, ta ce, “Naji Dada kayi haƙuri, amma na yafe mata”.         “Ni kuma ban yafe ba, kar kuma ki bari na sake maimaita abinda na faɗa”.      Sosai Hinde mai aiki tasan wanene ubangidan nata, dan kuwa shekaru kusan huɗe kenan take zaune a gidan tana aiki. Ai baima gama rufe baki ba ta isa gaban Amama. Ji kake ɗauuuu! Tasss-tasss! Na saukar marin data rama, har sai da Amama ta tuntsura zata faɗi.       “Ƙara mata”.   Ya sake faɗa cike da umarni. Haka Hinde ta sake saukema Amama mari na biyu daya sakata ƙwalla ƙarar azaba. Dan da alama itama dai Hinde ta daɗe tana fatan wannan ranar, shiyyasa ta buɗe kwanji ta sauke ma fuskar Amama duk wani takaicinta.        Cike da sassarfa wata mata ta fito a wata hanya tana faɗin, “Mike faruwa? Wa yake kuk......”       Cak ta tsaya batare data iya ƙarasa abinda ta faro faɗar ba sakamakon saukar idannunta akan wanda batai zaton gani ba. Shi ko tamkar ma bai san ALLAH yayi ruwanta a wajen ba yayi wani kicin-kicin da fuska yana danna waya hankali kwance. Ga Amama tasa hannu ta danne bakinta dan kar kukan da takeyi ya fito, dan inta bari hakan ta faru lallai zata gwammaci Hinde taita marinta fiye da hukuncinsa.      Jiki a saɓule matar ta ƙaraso inda yake, itama dai bazata wuce 30years ba, sai dai daga gani kasan anaji da gayu sosai. Cikin kame kai da aro nutsuwar dole ta ce, “Sannu da zuwa My D! Shigowar yaushe haka babu labari?”.     Maimakon amsa maganarta ko kallonta ma baiyi ba. Sai da yaja iska tafi ta minti ɗaya batare da ya kalletan ba ya furta, “Su tattara su wuce gida”. Daga haka ya miƙe abinsa ya fice a falon gaba ɗaya. Sororo ta bishi da kallo zuciyarta na bugawa da sauri-sauri, haka suma yaran gaba ɗaya firgici ya bayyana akan fuskar su. Balle Hinde da take jin har fitsari ya fara ɗiga mata a jiki, dan tasan uwar ɗakin nata sai ta huce a kanta, itace zata sha wahala bayan ya koma. Yana gama ficewa ta afka kitchen da tafiyar baya-baya. Su kuma ƴammatan suka zabura kan Nabiha suna hawaye.........✍🏼        _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 35_ __________________ 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH?mode=ems_copy_t *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF 'YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........ƘAUYEN BANKAURA.      BANKAURA dai wani ƙauye ne da mutanen cikinsa bazasu wuce adadin dubu uku da ɗari biyar ba. Ƙauye ne sosai domin kuwa akaf gidajen dake cikinsa babu wani gida ginin siminti duk gidajen laka ne. Mutanen wannan ƙauye duk manoma ne. Idan ka cire harkar noman nasu babu wani cigaba da suke da shi na sabuwar rayuwar wannan ƙarnin. Kai idan mutanen wannan ƙauye sukace maka basu san ma akwai gwamnati ba karka zagesu. Dan kuwa babu wani abu da gwamnati ta taɓa musu na cigaban rayuwa. Basu da makaranta koda primary ce balle ai maganar wutar lantarki ko ruwan fanfo, Kai hatta asibiti basu da shi. Amma abinda zai baka mamaki idan zaɓe yazo sai kaga an shiga har ƙauyen ana son su kaɗa ƙuri'arsu.       Wannan rashin cigaba da koma bayan cigaba da suke da shi yasa mafi yawan yaran garin kan fita neman kuɗi wasu jihohi bayan an kwashe amfanin gona, amma fa da ance ruwa ya zuba zaka gansu sunata dawowa gida. Maza na fita neman kuɗi a lokacin rani, da damina suyi noma. Mata kuwa kanyi ƙuli-ƙuli da mai da man-kaɗe da sabulun salo su kaishi manyan ƙauyukan dake kusa da bankaura domin siyarwa. Da damunar ma dai ba'a barsu a baya ba, masu himma kan yi noma suma nasu na kansu ko suyi ƙwadago a gonakin wasu. Zagaye da ƙauyen bankaura akwai wasu ƙauyukan da zasu iya kaiwa bakwai ma. Suma kuma kamar hakan ne basu da wani cigaban rayuwa da duniya ke kallo. Haka suke rayuwa tsawon shekaru, sai a shekarar 2002 wani matashi mai suna Tanimu yay sanadin wani tagomashin arziƙi ma ƙauyukan yankin ba Bankaura kawai ba, duk da kuwa shi ɗin haifaffen ɗan bankaura ɗin ne.          Tanimu irin mutanen nan ne masu wayewar kai tamkar a jinin jikinsu, dan kuwa baiyi karatun boko ba sai na allo kawai a cikin garinsu. Yana da shekara sha takwas ya shiga cikin matasa masu tafiya neman kuɗi zuwa Lagos. Tun fa a fitar farko Tanimu ya fahimci duniya tayi nisa mai yawa ta barsu, ya dinga ji a ransa basu da maraba da dabbobin dake rayuwa a jeji sai dai suci su kwanta suyi barci. A take zuciyarsa ta fara sosuwa da jin kishin yankinsa da al'ummarsa. Dan haka ya shiga bincike a iya ɗan tunaninsa da hangen nesan sa, sai ya fahimci idan fa har suna son irin cigaban da al'ummar birni ke ciki dole-dole sai sun tashi daga barci da suka jima sunayi, su cire tsoro, su cire gidadanci. Yaransu su shiga makarantar addini data boko ba noma kawai da fita neman kuɗi cikin birane ana musu kallon ƙasƙantattu ba.        Tun a Lagos ya fara latsa tunanin ƴan uwansa, ƴan garinsu dama ƴan wajen garinsu akan al'amarin. Kai tsaye wasu ke bashi goyon baya, yayinda wasu ke ɗaukarshi mahaukaci. Bai damu ba ya cigaba da son fahimtar da su har lokacin da ruwan damina ya fara sauka suka koma gida. Kowa ya duƙufa noma, shi ko ya duƙufa nazari da tuntuɓar manyan ƙauyukan musamman masu gari. Kai tsaye ba kowa ke fahimtar Tanimu ba, dan wasu ma kance yana son zuwa musu da kafirci ne kawai da lalata tarbiyyar yaransu da al'adarsu. Sai dai baya nuna jin haushi ko ƙosawa, sai ya zauna yay musu bayani na gamsuwa da nuna musu ai a yanda ɗin suke bai hana yaran nasu su lalace ba, dan akwai da yawan matasan da tunda suka fita neman kuɗi birni a ƙauyukan sunƙi su dawo gida, wasu ma sun faɗa mummunar hanya acan birnin. Kamar wasa sai al'amarin ya fara tasiri, a shekarar 2007 da akazo zaɓe sai suka haɗe kai suka nuna bazasu kaɗa ƙuri'arsu ba suma. Sai ƴan takarar dake ƙasa-ƙasa sun musu alƙawrika sannan. Shi ɗan siyasa babu abinda yafi ƙauna musamman a lokacin zaɓe sai kuri'a, idan kuma za'a haɗa ƙauyen bankaura da sauran ƙauyukan dake makwabtaka da shi dole za'a samu ƙuri'a mai yawa. Aiko sai ga ƴan takara kowanne na nashi alƙawarin musamman ƴan takarar chairman da kansiloli. Sunko cika alƙawari, dan cikin dabarun Tanimu aka samu tsara yanda za'a kaɗama kowanne ƙuri'ar, kunga duk wanda ya dace yaci bashi da bakin cewa basu zaɓesan ba.     Bayan gama zaɓe da samun sakamako chairman ɗin da yaci da kansiloli suka nema saɓa alƙawari, Tanimu bai gajiya ba ya cigaba da zungurar masu gari shima yana haɗa gangamin matasa zuwa garin da chairman ɗin yake suna masa tini. Da suka ga anƙi ɗaukar abin da muhimmanci sai suka nuna ai zaɓe zai sake zagayowa. Daga haka suka watsar da batun su suka koma kan harkokinsu.     Wannan abu da sukai ta farkar da masu wayon cikin ƴan siyasar, musamman ma kansiloli sai suka fara ƙoƙarin yin fanfon tuƙa-tuƙa a kowane ƙauye. Fara kuma wannan fanfuna ya saka ƙauyukan a farin ciki sosai, sai dai kuma masu aikin fanfuna suna fahimci kauyen bankaura da ƙauyikan gefensa akwai wasu ma'adanai dake rayuwa a wajen. Ma'adanai ne kuma masu ɗunbin daraja da zasu zama dukiya. Waɗan nan ma'aikata sune suka tsogunta batun ga wanda suka sakasu aikin fanfunan nan, suka nuna idan aka basu dama zasu dinga tonowa da wayo ana kashe muraba.      Kuɗi ƙunbar susa, dan danan kuwa suka amince musu. Aka sake zuba ayyukan fanfuna tuƙa-tuƙa tako ina. Su ƴan gari na farin cikin ana masu aiki masu aiki na farin ciki da ɗibar ganimar dukiya. A hankali-ahankali zance ya kai ga kunnen manya irinsu chairman da ɗan majalisar yankin, ai babu ɓata lokaci hankalinsu ya fara dawowa ƙauyukan. Amma sai basu nuna a fili ba aka cigaba da yaudarar su da ayyuka. Dan kuwa babu wani jimawa akai musu makarantun primary, aka kuma musu asibiti ƙarami, hanyar ma an gyara amma ba kwalta aka zuba ba. Ba'anan aikin ya tsaya ba sai ga wutar nefa an jawo musu. Bayan yin waɗan nan ayyuka ne wasu a manyan garin suka fara farga, nan fa ƙaramar rigima ta tashi har abu dai ya kai ga manya, sai ga baƙin fuska sun fara shigowa ƙauyukan harda ƴan ƙasar waje. Wannan al'amari ya fara tada hankalin mutanen wannan yanki, sai kawai suka miƙe da addu'a tamkar anyi ruwa an ɗauke masu haƙar ma'adanai dama shugabannin yankin dai suka ja baya.      A shekarar 2008 kwatsam wasu mutane daban suka shigo yankin suka cigaba da aikin haƙa, sai dai suna a ƙauye guda ne ba duka ƙauyukan ba. A ƴan ƙananun magana suka fahimci akwai bakin wasu a manyan garin, sannan masu wannan haƙa sun sha banban da na baya. Akwai kuma kasuwa babba a yankin da ake cinikin amfanin gona da dabbobi tamkar ba'a so itama al'amarinta ya fara canja salo. Wannan kasuwa dai itace taƙamar wannan yanki gaba ɗaya bama ƙauyikan ba, kai arewa ma kasuwa ce ta alfahari ga kowa. Dan haka suka shirya ɗaukar mataki dan basa son rasa kasuwarsu, batun ma'adanai ma bai canja ba, dan yaransu sun dawo sune masu haƙa ana biyansu maƙudan kuɗi, ta wani fannin kuma basu san darajar ma'adanan ba sam.     Ƙoƙarin hana taɓarɓarewar kasuwar nan da daina fitar yara neman kuɗi ne ya fara jawo rikici, rikici babba da ya kai har gwamnatin jiha ta shiga, daga ƙarshe ma aka turo sojoji domin kwantar da tarzomar su kuma tarwatsa ƴan ta'addar. Haka kuwa akayi dan wannan shine sanadin zuwan su Zak-Shadow cikin dajin yankin a karo na biyu. A lokacin yana matsayin Major Haysam Abdul-rasheed Shehu. Akwai runduna a ƙarƙashinsa, rundunar tasa kuma itace ta kawo dai-daiton cigaban kasuwar da har ya zamto an ƙaramasa muƙami na bayan abubuwa sun lafa gaba ɗaya. Sun bar jejin har na tsawon shekara ɗaya da wasu watanni da tunanin komai ya dai-daita, sai dai a shekarar 2010 wasa na biyu ya nema fin na farko, dan kuwa horarrun ƴan ta'adda da ba'asan daga ina suke ba sunzo sun ragargaza jama'ar wani ƙauye da ake kira Gunda gaba ɗaya, an kashe wasu an jikkata wasu. Wannan rikici shine yay sanadin sake dawowar sojoji a yankin, ba kowa kuma aka maido ba sai Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu Zak-Shadow ganin shine ya dai-daita rikicin farko.         Zak-Shadow ya kafa ya tsare a wannan yanki matuƙa, ta yanda ƴan ta'addan nan sun kasa ko numfashi mai ƙarfi, dan tarwatsawar da yay musu ta ƙarshe sai da ya samu nasarar kashe shaƙiƙin ƙanin shugaban ƴan ta'addar. Maganar tonon ma'adainai kuwa tuni ya dakatar da shi sai a ɓoye, a ɓoyen ma yana musu wuya sosai.        Wannan ƙauye na Bankaura shine ƙauyen su matar nan mai ciki da su Zak-Shadow suka haɗu dasu a shekarar 2006 da suke shigowa jejin. Ita da mijinta duk asalin ƴan ƙauyen ne. Mijinta Maude, shine yaya ga Tanimu da yayta gwagwarmayar jawo cigaba a wannan ƙauye. Ita ko sunanta Hafsatu, amma ana kiranta da Hassatu a gaba ɗaya ƙauyen. Shekararsu tara da aure ALLAH bai basu haihuwa ba, sai daga baya kwatsam ta samu ciki, cikin daya saka duk wani masoyansu a farin ciki da su kansu.      Kamar yanda Hassatu ta faɗa tana jin labarin aikin sojoji ne a rediyon ƙanin mijinta Tanimu idan ya kunna musu, yakan kuma bata labarai irin na birni da abubuwan cigaba da ƙoƙarin da jami'an tsaro musamman sojoji keyi a yankin nasu kan ta'addacin dake faruwa dan su ƙauyensu lafiya lau yake zaune har lokacin. A hankali zuciyarta ta dinga kwaɗaituwa da son abinda zata haifa ya zama soja, kullum wannan shine fatanta, har mutane kan mata dariya a kan hakan da ɗaukarta shashasha, burinta ya sake girma da faɗi a lokacin data haɗu da su Zak-Shadow, haka ta dawo gida cike da farin ciki a wannan ranar, ta bama mijinta Maude labarin komai daya faru. Shi mutum ne mai sanyin hali da rashin yawan magana, sai kawai yay dariya dan ya ɗauki zancen nata kawai shiririta irin ta mata ne. Ita kuwa tun daga ranar ta addabeshi da labarin sojoji da fatan haihuwar namiji ɗanta ya zama soja. Tun yana mata dariya har ya fara jin haushin hakan yana mata faɗa, da taga haka sai ta daina masa maganar kawai. Cikin aminci UBANGIJI kwanaki goma sha shida da haɗuwarsu da su Zak-Shadow a daren juma'a ta haihu, sai dai kash maimakon ɗa namiji da take fatan haihuwa dan kawai ya zama soja sai aka samu mace........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 36_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Duk da namiji Hassatu taso batai baƙin cikin samun macen ba, sai ma farin ciki mara misali ta shiga, tare da addu'ar ALLAH ya bata namijin a can gaba. Ranar suna shagali akayi sosai saboda wannan haihuwa ta farin ciki ce a garesu, hidimar da Maude yayi da danginsu har ba'a magana. Yarinya taci suna *_NAJA'ATU_* sunan mahaifiyar su Maude, dan haka sukai mata alkunya da Ummi, sai Tanimu yace tsohon yayi ne a dinga kiranta *_Nimrah_*. Tun mutane na kananun magana akan sunan aljanu Tanimu ya sakama Naja'atu ƴar Hassatu har suka haƙura, dan kuwa itama uwar ƴar Hassatu sunan ya mata daɗi.         Bayan haihuwar Nimrah burin haihuwar ɗa namiji da zai zama soja bai bar zuciyar Hassatu ba, sai dai wani ikon ALLAH har Nimrah takai shekara biyar ko ɓatan wata Hassatu bata sake yi ba. Sai dai bata fidda rai daga rahamar UBANGIJI ba ta cigaba da addu'a da fatan samu.      Nimrah yarinya ce ƙyaƙyawa. Irin black beauty ɗin nan da baka gajiya da kallo, akwai dogon hanci da manyan idanu masha ALLAH. Sai ƙaramin bakinta na surutu da tsiwa. Dan kuwa idan kaji ance shugaban rashin ji da rikici to Nimrah na layin farko ne. Ga gata kawunta na mata Tanimu, hakama iyayenta kasancewar sun jima basu haihu ba kuma ita kaɗai ce. Koda yaushe zaka sameta tsaf cikin kayan kwalliya irin na zamani, dan Tanimu baya gajiya da saya mata kaya duk da shima yana da yaran amma duk maza ne su biyu. Amma yanda yakema Nimrah gata sai ka ɗauka shine ya haifeta, dan har abun na damun matarsa shiyasa ta tsani Nimrah da iyayenta, kullum cikin son raba mijinta take da su amma shi ya tsaya tsayin daka akan bata isa ba. A kwana a tashi yau ga Nimrah na shekara ta bakwai da wasu watanni a duniya.... >>>>>>•<<<<<<          Cikin takunsa na nutsuwa da ƙarfin jiki ya shigo falon. Babba ne sosai, dan ya ninka falon sashen matarsa sau biyu girma. Amma duk da haka a gyare yake ƙal ga wani ƙamshi mai saka zuciya nutsuwa na tashi da sanyin ac. Shiru babu hayaniyar komai sai ta ƙarar ac da tv dake kunne tashar mbc 3. Duk da babu kowa sai da yay sallama sannan ya shiga, sai lokacin idanunsa suka sauka akan yaron dake zaune hankalinsa gaba ɗaya a kan tv. Yaron bazai wuce 9years ba, yana da ƙiba gashi ƙyaƙyƙyawa masha ALLAH. Tvn ya ɗan zubama ido shima, kafin ya maido su kan yaron yay ƙaramar gyaran murya.        Da sauri kuwa yaron ya juyo inda yake, suna haɗa ido ya zabura tare da dirgowa a saman kujerar yayo kanshi da gudu cike da farin ciki. A karo na farko ya saki wani ɗan murmushin gefen baki, sai kuma ya ɗan kai dirƙushe gwiwar sa ɗaya a ƙasa ɗaya a zaune ya tokare ya warema yaron hannayensa ya shige. Gaba ɗayansa ya rungumeshi, hakama yaron yay masifar ƙanƙamesa cikin matsanancin farin ciki yana faɗin, “Oyoyo Dada na”.          Murmushi ya sake yi yana rungume da shi, dai-dai ya ɗagoshi daga jikin nashi wata ƴar budurwa da bazata wuce 17years ba ta fito daga wata ƙofa hannunta ɗauke da ƙaramin bowl dake tururi alamar abinci ne a ciki. Sosai itama farin ciki ya bayyana a fuskarta, ta ƙaraso wajen da sassarfa tana faɗin, “Dada sannu da zuwa”.        Kansa kawai ya jinjina mata, sai itama tai saurin sake risinawa tana gaishe shi. Bai amsa ba sai da ya miƙe tsaye hannunsa riƙe dana yaron, sai dai idanunsa a kanta shiyasa ta sake nutsuwa sosai amma har lokacin fuskarta da murmushin farin cikin ganinsa.           “Miya hanaku zuwa makaranta?”.      Ya faɗa cikin buɗaɗɗiyar muryarsa. Da sauri ta ce, “Anyi hutu ne jiya Dada”.        Nan ma kansa ya jinjina da maida kallona kan yaron daya amshe zancen yana bashi labarin yazo na biyu a ajinsu. Hannunsa yaja suka ƙarasa cikin falon sosai, zama yay a kujera ya zaunar da yaron a kusa da shi. Itama budurwar da yaron ya kira Aunty Biebah bowl ɗin hannun nata mai ɗauke da dafaffiyar indomie ta ajiye a gaban yaron.      Ta miƙe zata bar wajen ya ce, “Ina Mammah?”.         “Tana ciki Dada, tayi sallar walha ne dama zan gaya mata kazo ne”.      “Barta, haɗa min breakfast, bana son jagwalgwalo kuma”.     “Yes Dada, yanzu fa na iya duk irin abincin da kake ci, tunda ka tafi na dage inata koya. Da Yaya Ma'aruff yaga na dage shine ya sani makarantar koyon girki ma”.         Shi dai idanu kawai ya zuba mata tana zuba surutu. Dukan ƴan uwansa yana son su ƙwarai da gaske. Amma tausayin autar tasu Biebah mai girma ne a zuciyarsa saboda ita kaɗai ce ba mahaifinsu ɗaya ba, sannan kamaninta daban da su. Mahaifinta na raye, amma bata da maraba da su da suka rasa nasu, dan har yanzu Alhaji Nura yaƙi karɓarta a matsayin ƴarsa, duk da kuwa har yanzu ba'a sake masa haihuwa ba bayan ita. Tunanin nasa ya ture gefe, sai kuma ya miƙe yana faɗin, “To akku sarkin magana jeki min abinda na saki”.      Daga haka ya nufi wata hanya, itama dake tura bakin shagwaɓa sai ta juya hanyar kitchen cike da farin cikin yau zatama Dada abinci mai daɗi. Dan a wani zuwa da yay ya taɓa sakata ta haɗa masa salad kawai tai masa shirme, tako sha faɗa, shiyasa ta dage da burin duk randa ya dawo zata faranta masa rai da abinci.               Dai-dai ƙofar farko ya tsaya, a buɗe take sai labule dake a sake, cike da nutsuwa yay sallama. Daga ciki wata dattijuwar murya ta amsa masa a tausashe. Labulen ya ɗaga ya shiga cikin ɗakin, mamallakiyar muryar na zaune akan sallaya alamar salla ta idar take addu'a ta ɗago tana kallonsa. Tabbas shekaru sunja, fata ya canja daga mai laushi da santsi zuwa mai ɗan tattarewa da hasken kwarjinin ibada, bazamuce da ita tsohuwa ba, amma zamu kirata dattijuwa dan kuwa a sittin kaɗan ne babu. Tana nan da hasken fatarta da annurin fuska. Tunda tai masa kallo ɗaya ta ɗan kauda kanta tana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya. A duk sanda yay nesa da su kewarta gareshi mai girma ce, idan ya ziyarcesu tana jin nutsuwa amma takan danne da yanayi irin na masu dattako. Gaba ɗayansa a halittar jiki Abdul-rasheed take gani, duk da kuwa ya fishi buɗewa da ginannen jiki, dan Zak-Shadow irin mutanen nan ne masu ƙirji gashi a murɗe sosai musamman daga sama, cikin nan a lafe tamkar ba'a zuba masa abinci. Sai hasken fatar ta daya ɗauka kawai, da halin rashin yawan magana irin tata data kakarsa mahaifiyar Abdul-rasheed. Dan tun yana ƙarami Baba yasha faɗin halayyar Haysam ta rashin yawan magana da murɗin hali irin na Inna ne, kawai shi dan ya haɗa biyu ne dana mahaifiyarsa shiyyasa abin yay masa yawa.....          “Barka da hantsi Mammah”.    Ya faɗa cikin tausasawar data katse mata tunaninta. Wata ajiyar zuciyar ta sake saukewa ta shafa addu'ar data kammala sannan ta fuskanceshi tana gyara zama da faɗin, “Wannan tafiyar daren dai bazaka dainata ba, ko tsoro baka ji Muhammad”.        Murmushi yayi mai ƙayatarwa yana ɗan sunkiyar da kansa. “Kiyi haƙuri Mammah, tafiyar daren ce tafi sauƙi a garemu kodan yanayin rayuwar”.        “To ALLAH ya rufa mana asiri, ya baku kariya ya tsare mana ku da tsarewarsa”.      “Amin ya rabbi Mammah ina kwana. Na sameku lafiya?”.             “Komai lafiya lau Alhamdullah. Fatan kuma kuna cikin ƙoshin lafiya?”.        “Alhamdulillahi, sai kewarku”.    “Kewa kam muma a cikin taku muke akoda yaushe. Amma ya za'ayi tunda haka UBANGIJI ya tsara”.      Murmushi yayi nan ma kawai, ita kuma ta jawo ƙaramin flaks dake gefenta da wani kyakkyawan mug, shayin dake ciki ta zuba ta miƙa masa.         “Mammah kamar kin san nayi kewar shayin nan naki kuwa”.      “Ai gashi sai kaita sha har ka koma. Jiya muke zancenka da Momy ashe kana tafe?”.       “Tafiyar tazo ne kawai nima. Bata daina yawon nata ba kenan dai”.          “A'a yanzu kam ta rage ai, tanata fama ma da laulayin ai yawo dole a barshi”.      “Mammah baki son laifinta dai kawai”.     Karo na farko Mammah tai dariya, dan kusan su duka haka suke gaya mata akan Momy idan suna faɗan yawonta tana kareta. Sun cigaba da hirarsu cikin nutsuwa, anan ma yake jin Ma'aruff da Ja'afar sun wuce Chaina. Dan su harkar kasuwanci suke yi. Tun dai kasuwar daya zama sanadin kafawa itace ALLAH ya sanya ma albarka zuwa yanzu har suna da manyan shaguna kusa shida da zamu iya cewa ma sune sanadin arziƙin da suke ciki a yanzun haka. Dan haka Ja'afar da Ma'aruff tagwayen Mammah ke kula da su, sune suke zuwa ƙasashe kawo kaya kuma da kansu.         Sunyi nisa da hira akan dai lamarin sauran ƴan uwan nasa da bikin su Ja'afar dake tunkarowa Biebah tai sallama. Amsa mata sukai da bada izin shigowa. Ta shigo ɗauke da tire yaron nan na ɗazun biye da ita. Sai da ta durƙusa a gabansa sannan ta ajiye tiren, yaron kuwa yaje kusa da shi ya zauna. Dukan abinda Zak-Shadow zai ci yanada ƙa'ida da tsarinsa, baya cin abinci sai mai amfani da gina jiki, shiyasa kayan ganye, nama, ƙwai, kifi, vegetables, fruits sunfi yawa a abincinsa. Sauran kuwa yana cin komai dai-dai misali da kuma tsari. Kwata-kwata baya shan suger, baya cin magi da yawa da gishiri. Baya cin mai da yawa koda nama mai kitse ne, hakama duk wani drinks.      Yanzun ma ƙwai ne guda huɗu da nama sai vegetables wadatacce a ciki da agada ta kawo masa. Sai fruits salad data haɗa masa kaɗan. Fuskarta washe da murmushi ta ce, “Dada idan kaci abincin nan yau nasan har ƙyauta sai kayi mini”.        “Ko kuma kisha zana ba idan babu daɗi”.      “ALLAH Dada akwai daɗi, ai Mammah ma ni nake mata girki yanzu ko?”.      Tai maganar tana juyawa ta kalla Mammah ɗin cike da shagwaɓa. Dariya Yaron nan ya sanya, dan haka ta maida dubanta kanshi tana harararsa. Dai-dai Zak-Shadow na kai naman bakinsa. Kusa da shi ta koma cike da ƙosawa tana jiran ya yaba mata, harda yin tagumi fuska a shagwaɓe. Sai da yay lauma ta biyu sannan ya ɗago kyawawan idanunsa yana kallonta, sai ta waro masa idannunta. Harararta ya ɗanyi, tai saurin risinar da su. Ya ɗan girgiza kansa da faɗin,          “Irin wannan sakani a gaba Auta, shike nan yayi daɗi, tashi ki bani waje karna ƙware”.      Ai da wani irin murna ta miƙe ta fita, yaron nan da Mammah ta kira Mu'azz ya bita yana tayata. Kansa kawai ya girgiza nan ma, Mammah kuwa tai murmushi.        “Ai daga nan kuma munga boni a gidan nan wajenta, yanzu zata fara bazama sauran ƴan uwan a waya duk da nasan tunda ta ganka ma ta kira kowansu. Amma kai miyasa ba zaka saka matarka tai maka girkin ba, nifa bana son ana tauye mutum ka sani”.           “Kiyi haƙuri Mammah nima bana tauyeta bane, idan tayi na rana ba sai naci ba, itama Autan ina son ganin farin cikinta, tana son tayi bai kamata na sare mata gwiwa ba”.       “Shike nan, a dai dinga kula”.     “In sha ALLAHU”.             Kamar yanda Mammah ta faɗa kuwa tuni Biebah ta bazama sauran ƴan uwan batun zuwan Dadan, kafin 12 har sun cika gidan. Idan ka cire Ma'aruff da Ja'afar da basa nan. Hatta Ammar dake Zaria yana makaranta yace sai yazo gida komai dare.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 37_ __________________ https://chat.whatsapp.com/L3BXH7JYlBRHIkFRiOjeW3?mode=ems_copy_t UMMU KHALIFA COLLECTION Ina Mata Yan kwalisa ina mata masu san kayan ado kamar Egyptian abaya sleeping drees kids were shos bags musk dahara original. To kukanku yazo karshe domin ummu khalifa sun zo muku da duk wadannnan kayan dierct suke order dinsu daga Egypt zuwa gida Nigeria kaidai kawai kashiga link dinsu domin gani ya kori jiii.. Ba nan ummuh khalifa suka tsaya ba suna nemawq mutane visa masu shaawar shugowa kasar ta Egypt karatu ko yawon bude ido ko kasuwanci ku tuntubeta a number dinta +201017018846/07048811474/ KO kuma shafinta na tiktok https://vt.tiktok.com/ZSU1FEkjc/ __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Taron yara ne a filin da ake kira dandali a ƙauyen. A wannan dandali duk wani abun kwalam da maƙulashe ana saidawa, da daddare kuma nan ƴammata ke taruwa yin gaɗa da hira da samari. Yanda ƙura ke tashi da ihun yaran da suka taru zai baka tabbacin faɗa akeyi. Gashi hantsi ne maza duk suna gona, kusan duk ta inda ka zagaya yaran ne sai mata masu satar fita anguwa ganin mazan basa nan.       Tafe take tana ƴan waƙe-waƙenta da ƙaramar galon fara mai cin kwalba uku ta mai an zuba man gyaɗa da zai iya kai kwalba ɗaya da rabi a ciki, sai leda baƙa a ƙulle. Yanda aka ɗaure bakin galon ɗin harda leda zaka gane anyi haka ne dan karta zubar. Harta kama hanyar da zata sadata da gidansu ta canja saboda hango ƙurar dake tashi a dandali da ihun yara irinta. Sauri-sauri gudu-gudu kuwa ta nufi can, dan a duniya babu abinda ke burge Nimrah irin damben tsiya, iyayen sunyi faɗa har sun gaji, ga kawunta Tanimu na ɗaure mata ƙugu, da anyi magana yace a barta dan ita *_Zakanya_* ce soja ma zata zama. Tsabar fitinar Nimrah idan nace kowa ya santa a ƙauyen nan banyi ƙarya ba.       Cike da rigima ta fara kutsawa ta cikin yaran dan son ganin abinda ke faruwa, ko tsoron a zumar da man gyaɗan dake hannunta batayi. Bako ta tsaya ko'ina ba sai tsakkiyar filin faɗan. Tana shiga kuwa ta ajiye galon ɗin man da ledar ta cire ɗan hijjabinta taci ɗammara ta koma tsakkiyar masu faɗan ta tsaya. Cikin tsiwa da rawar kai ta ce, “Ke Abubu matsa na sayi faɗan nan, dama haushin wannan shegiyar Ɗaharen nake ji. Babu musu Abubu ta matsa ta bama Nimrah waje, dama ba ƙarfi gareta ba tun ɗazun Ɗahare ke jibgarta, dan kuwa ta girmeta har ita Nimrah ɗin ma. Ɗahare zata kai shekara tara ma.      Ɗahare dake kallon Nimrah tana huttai ta nunata da yatsa tana faɗin, “Ke Nimrah wlhy ki fita a wannan faɗan ba ruwanki, dan sai na haɗa ke da Abubun naci uwarku a filin nan”.       “Sai dai kici uwarki”.   Cewar Nimrah cike da tsiwa tana girgije-girgijen jiki ita a dole mai ƙarfi, sai kuma ta duƙawa ta dimtsi ƙasa a hannu biyu, ta sake matsawa gaban Ɗahare sosai ta nuna mata. “Gata tsiya gata arziƙi ki zaɓa”.      Cikin takaici Ɗahare ta kaɓe ta tsiyar, ai ko sai kokawa ta kacame tsakaninta da Nimrah. Nan fa ihun yara ya ƙaru dan kamar wasa sai ga mutuniyar taku takai Ɗahare ƙasa ta dimbiji ƙasa ta cika mata baki da ita. Dambe yay dambe aka tambaɗar da man gyaɗar Nimrah, ledar ma dake ɗauke da ƙuli-ƙuli ciki tuni yara sun saka mata wawa. ALLAH ne ya kawo wata mata ta raba wannan tsiya da ƙyar bayan ta kori yaran wajen da bulala. Nimrah na huci tayi buɗu-buɗu da ƙasa har cikin gashin kanta ta fara neman galon ɗin mai da ledar ƙuli, yayinda Ɗahare ke kuka da zaginta da cewa sai ta rama. Da ƙyar matar nan ta janyeta ita kuma Nimrah ta ɗauki galon ɗin manta data kimbiɗe matar ta sakata a gaba suka wuce. Sai lokacin kuma kuka da tsoro sukazo mata. Amma taƙi bari kukan ya fito har matar ta rakata ƙofar gida tace ta shiga ita kuma ta wuce...          Hassatu da a yanzu Nimrah ke kira Umma nata aiki da kallon yanda rana ke ƙarayi zuciyarta cike da tunanin ina Nimrah ta tsaya, ta ajiye iccen data ɗebo zata ƙarama wutar dambu da take yi. Gidansu gidan yawa ne mai sassa daban-daban dan haka ta shiga ƙwala kiran sunan ɗan facalarta da take jiyo suritunsa a sashensu. Daga can ya amsa yana fitowa, yazo gabanta yana faɗin, “Umman Nimrah gani”.         “Lawwali taimakeni dan ALLAH ka bimin sawun Ninrah gidan Inna Yalwa na aiketa sayen mai da ƙulli tun gama karin kummalo ga shi har sha biyu ta wuce bata ba labarinta, maza ka duba min ita kaji”.      “To”. Ya faɗa yana nufar hanyar babbar ƙofarsu, sai ga Nimrah dake jin duk abinda ma ke faruwa rakuɓe a bango da galon a hannu.       “Ke Nimrah kizo Ummanki na kira”.     Harararsa tayi, cikin son huce haushin faɗan da tayi a kansa ta ce, “Baza'azo ba ɗin, munafuki”.         “Kece munafuka dai, minai miki zaki ce min munafiki?”.      Duka takai masa da galon ɗin man, ya koma cikin gidan da gudu.     “Lawwali ina aikar da nai maka kake shigowa da gudu?”.         Nimrah ce zata dakeni, tana zaure”.      Umma najin hakan tasan tayi tsiyar ne, in dai har ba'a zubar mata da mai ba to an zubar da kuɗin ne. Batace komai ba ta cigaba da aikinta. Sai da ta kammala ta shiga wanka ganin azhar ta gabato sannan Nimrah ta lallaɓo ta shigo cikin sanɗa ta ajiye galon ɗin. Ta juya zata koma da gudu Umma data fito a bayin ta manta sabulu ta kamata caraf. Wani ihu ta fasa mata kuwa.        “Wayyo ALLAH na shiga uku Umma dan ALLAH kada ki dakeni, Inna ku kawo ɗauki Umma zata tumurmusa ni, wlhy kunkuru na da kafaɗata ciwo suke, na mutu na lalace a taimakeni.”      Tsayawa kawai Umma tai tana kallon yanda take ihun da dire-diren iskancin. Sai ko ga kakarta da wasu a matan gidan sun shigo. Dai-dai Umman ta kai hannu zata mangareta surukar tata ta dakatar da ita.          “Karki sake ki taɓata Hassatu, ke wai baƙya tausayin yarinyar nan ne kullum duka dai duka dai, gata abu ba abuba ko jikin kirki ta gagara yi saboda masifarki”.      Ran Umma a ɓace ta ce, “Inna nagaji da al'amarin Nimrah a gidan nan, tun gama karin kummalonta fa na aiketa sayen mai gidan Inna Yalwa sai yanzu take dawo min da galon ɗin babu man babu kuɗin, dan iskanci kuma ta shigo ta faɗa min yanda akayi shine ta laɓe a zaure har tana shirin dukan Lawwali dana aika ya nemo min ita. Wannan wace irin rayuwa ce, jiba jikinta daga gani dambe taje tayi yarinya kamar wata namiji”.        “Koma dai miye dukan ai ba shine magani ba addu'a ce, sannan kowane yaro da irin ƙuruciyarsa”. Inna tai maganar tana ƙwace Nimrah a hannun Umma. Dole ta sakar mata ita, tanaji tana gani ta wuce da ita sashensu aka barta da takaici, sai sake bada wasu kuɗin tayi aka sayo mata wani man. Ba kuma ta sake saka Nimrah a idonta ba sai dare da babanta ya dawo gidan.... >>>>>>★<<<<<<           Sai da suka je sallar azhar massalaci suka dawo sannan ya koma sashensu. Ƴammatan ɗazun kawai ne a falon, suna ma jin motsinsa suka shiga rige-rigen faɗawa bedroom ɗin kwanansu. Sai dai hakan bai hanashi fahimtar suna a gidan ba har yanzu. Sai da ya shige ɗakinsa ɗaya daga cikinsu ta fito cikin sanɗa ta shiga bedroom ɗin matar gidan. Tana zaune a bakin katafaren gadonta da yaji shinfiɗa ta alfarma kamar yanda jikinta ke cikin kwalliya. Ɗakin ya haɗu matuƙa, komai tsaf babu wani tarkace. Waya ce a kunnenta alamar magana take da wani, sai dai ganin yanda ƙanwar tata ke tsaye a bakin ƙofa fuska a marairaice ya sata ɗan kauda wayar a kunnenta ta rufe speaker ɗin da hannu.          “Miya faru?”.      “Aunty ya dawo fa, dan ALLAH kije ki bashi haƙurin”.      Hararta ta ɗanyi da faɗin, “Naji. Fita ki bani waje.”    Sai da ta tura baki gaba sannan ta juya fuuu ta fita. Ita kuma tai ƙaramin tsaki tana janye hannunta. “Mommy Please ina zuwa, wai ya dawo sashen. Bari naje kin san shi da baƙar zuciyar tsiya, duk yanda mukai zan kiraki. Amma dan ALLAH ki kwantar da hankalinki babu inda zasuje”.      Banji mi akace mata daga can ba, ta dai yi ɗan shiru alamar saurare kafin ta yanke kiran ta ajiye wayar. Gaban ƙaton mirror ɗin ɗakin taje, ta ɗauka wasu turare ta ƙarama jikinta tare da mouch freshener sannan ta fito. Dining ta nufa ta ɗauki wani ƙyaƙyƙyawan basket ƙarami da aka shirya abinci a ciki ta nufi ɗakinsa. Shigowarta dai-dai da fitowarsa a bayi jikinsa na raɓar ruwa farar fatarsa tayi wani fayau sai towel ɗaure a ƙugunsa. Tabbas Zak-Shadow murɗaɗɗen mutum ne bana wasa ba, dan ko wasu ƴan wrestling ɗin albarka. Sarai yaji sallamarta da motsinta, amma yay biris ko kallon ƙofar baiyi ba yama wuce bakin gado abinsa yana ɗaukar wayarsa dake a bed side drawer tana vibration. Kiran ya ɗaga tare da kai wayar kunnensa. Dai-dai lokacin ta ƙaraso wajen itama bayan ta ajiye basket din acan saman table dake a tsakiyar kujerun ɗakin. A hankali ta manna jikinta da bayansa, ta zagayo da duka hannyenta biyu, ɗaya a ƙirjinsa ɗaya a saman shafaffen cikinsa mai manyan layukan six-pack.       Sai ko daya ɗan lumshe ido saboda yanda ta fara zagaya hannun a jikin nasa, sai dai ya dake abinsa, yana cigaba da wayarsa hankali kwance. Bai kuma ajiye ba sai da ya kammala. Yana cireta a kunnensa yay ƙoƙarin janye jikin nasa daga riƙon datai masa, sake ƙanƙameshi tai cike da shagwaɓa ta furta, “Please my Cool one, I really miss you wlhy. I'm so sorry, dan ALLAH kada kaimin hukunci da laifin daba nawa ba. Bance kazo dan na ɓata maka rai ba”.         A hankali ya ɗan saki huci, batare da yayi maganar da take son yayin ba yasa hannu ya cire hannayenta dake a jikinsa. Da sauri ta dawo ta gabanshi ta rungume shi tsam-tsam, tare da sakar masa kuka. Karo na farko ya ɗan ciji gefen lips ɗinsa, shiru kamar bazai kulata ba sai kuma a hankali ya ɗaura duka hannayensa biyu akan bayanta shima ya zagayeta yana sake matseta. Cike da farin ciki ta sake ƙanƙameshi da bashi kissis masu zafi a saman ƙirji, kafin ta ɗago tai ɗiɗɗishe da ƙafafunta dan ya fita tsawo kawai ta haɗe lips ɗinsu waje guda.       (Ehem-ehem nai gyaran murya dan ganin al'amarin babbane), dan kuwa tuni ya ɗagata cak ya ɗora a gadon ta yanda tsahonsu yay dai-dai, tun abun nasu na iya tsayen ana sumbatar juna har takai suka zube a gadon gaba ɗaya...........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 38_ __________________ 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH?mode=ems_copy_t *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF 'YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........A wahale ta kalla agogon dake bangon ɗakin, ƙarfe shida saura fa na yamma. Wani irin ciwo ƙasusuwanta ke mata, tun kusan ɗaya da rabi bawan ALLAHn nan bai barta ta huta ba, sallar la'asar ma a ɗakin yayi ta, duk da yanda yaga tayi laushi tun ɗazun bai raga mata ba har sai da ta fara masa kuka da roƙo da magiya, a hankan ma sai da ya mula dan kansa...      Fitowarsa a bayi ya katse mata tunani, ɗaure yake da towel yana tsane jiki da wani, suna haɗa ido ta tura masa baki. Nashi bakin ya ɗan taɓe yana ɗauke ido a kanta shima. Sai da yaje gaban mirror cikin muryarsa data koma can ƙasa ya furta, “Ki tashi ki gyara jikin ki raguwa kawai. Ki damu mutum yazo-yazo sai yazo kuma kiyita raki”.            Cikin sake tura baki ta ce, “Kai dama ai baka da tausayi wani lokacin, amma idan bani ɗinba ma wazai iya da kai. Kuma ni ALLAH bazan iya tashi ba, bakaji ƙasusuwana ba kamar ana sassarawa fa”.        “Da sauƙi ma tunda sarawa ce ba niƙawa ake ba”. Ya bata amsa cike da gatse.        Bata sake cewa komai ba, dan so take ya sauka a fushin nasa yabar ƙannenta su cigaba da zama a gidan. Shima bai sake magana ba ya gyara jikinsa tare da saka kaya. Ita dai tana binshi da kallo harya kammala. Zuciyarta kuwa wani ƙara cika take da soyayyar sa, tasan samun miji irinsa ba ƙaramin morewa bace. Gaban gadon yazo ya tsaya hannayensa a cikin aljihu yana kallon fuskarta dake a marairaice, ita ko ta kasa kallon cikin idonsa. Shekara ta goma sha suke da aure, amma har yanzu bata iya kallon tsakkiyar idon Zak-Shadow duk da wayewarta da matsanancin soyayyar da take masa, to ƙarshen wayewa ma tun tana shekara biyu a duniya aka tafi da ita UK, ba kuma ta taɓa zuwa Nigeria ba sai a shekarun girma kuma a lokacin sukai aure. Takan ji ya mata kwarjini da cika mata waje a duk sanda yake a gabanta, wani lokacin ma tafi sakewa da shi a waya fiye da kasancewa a face-to-face....         Ɗagatan da yay ne cak ya katse mata tunani, kamar wata babyn wasa duk da kuwa ita ba ramammiya bace jikinta a mulmule yake da ƴar ƙibarta sai dai bamai yawa ba. Hannayenta ta zagayo a wuyansa tana mai kwantar da kanta a ƙirjinsa. A haka ya shiga da ita cikin bayin ya dire cikin jacuzzi. Ƙasa-ƙasa cikin raɗa da wani salon soyayya irin ta manya yana wani kalar shinshinar wuyanta daya sakata lumshe idanunta tsam-tsam ya furta.        “Kiyi amfani da ruwa mai zafi sosai zai daina taguwar Zak... Sarkin raki” dai-dai nan ya sakar mata ƴar sumba a cikin kunne data sakata zabura. Yanda ta ƙanƙame jikinta ya sashi sakin wani lallataccen murmushi na ganin dama, cike da takunsa na zarra da jarumta ya bar mata bathroom ɗin gaba ɗaya har lokacin da ƙaramin murmushin a lips ɗinsa, ƙyawawan idanunsa kuwa sun wani shige ciki sosai jan cikinsu yafi yanda suke akoda yaushe. Sai wani luuu yake da su yana buɗewa a gajiye...      Gaban mirror ya koma ya saka turare kaɗan ya fice a ɗakin gaba ɗaya dan yana son zuwa gidan su Imran gaida iyayensa..... <<★>><<★>><<★>>           ƘAUYEN BANKAURA      Rakwacammm!! Ɓarin bazata ya karaɗe kunnen Umma dake tsakar gida tana aiki. Da sauri ta kalla ƙofar ɗakin, tare da ƙwala kiran sunan Nimrah da tasan tana ciki. Shiru taƙi amsawa. Umma tai ƙwafa da faɗin, “Nice nake kiranki kina min shiru ko, shike nan ALLAH ya baki sa'a na shigo ɗakin nan jikinki ne zai gaya miki.”       Tsulum ta fito jikinta fututu da garin tuwo ko fulawa. Suna haɗa ido da Umma sai ta fashe da kuka tana ɗaga yatsa sama bayan ta lashesa akan harshe.          “Umma na rantse bani nai miki ɓarin nan ba, ɓeran ɗakinki ne......” kuka ya ƙwace mata. Rasama abin cewa Umma tayi, kawai ta cigaba da kallonta. Itako tana ƙara ƙarfin kukanta da rantsuwar ba ita bace ɓera ne yay ɓarin nan. Dai-dai nan Babanta dake bayi ya fito. “Kaiya-kaiya lafiya dai kuwa? Uwa kin san bana son wannan shashancin kukan banzar fa. Mi akai miki?”.        Ran Umma a ɓace ta ce, “Sai anyi mata. Ko ita tayi ai ta iya kukan iskanci. Kuma wlhy yau babu mai hanani dukanki a nan gidan. Fulawar mutane kika ɓarar min daga kawowa ai musu mirjin taliya, bayan a sama na sakata saboda sanin halinki”.         “Na rantse ɓera ne, Baba kace karta dake ni, ai dai ɓeran yafi ta kamo ta daka”. Nimrah ce ke maganar cikin uhun kuka bayan ta rugo tazo jikin Babanta ta ɓuya. Kansa kawai ya girgiza da faɗin, “ALLAH ya shiryeki Uwa, al'amarinki ya fara bani tsoro, yanzu kiyi laifi amma tsabar shaƙiyanci kice wai ɓera ne? Shekaran jiya fa haka kika ɓarar da mangyaɗa Inna ta hana a taɓaki da Kawunki Tanimu, yanzu kuma kayan mutane, sana'ar kike so uwar ki ta daina?”.         “Baba na rantse ɓera n.....”    Bummm!!! Abinda Umma ta jeho mata ya daki bakinta. Ai data buga wani tsallen ihu ta zube ƙasa saita fara birgima da faɗin wai Umma ta cire mata bakinta. Haushi ya ƙara turniƙe Umma tazo kanta da tsumagiya ta fara zuba mata a jiki, da ƙyar Baba ya kwaceta. Sai ga Inna ta shigo itama tana sababi, dan a duniya idan kana son ganin tujararta to ka taɓa Nimrah a gidan nan, shiyasa ma take wani iskancin da hujja. Maimakon taima Umma kaɗai faɗa sai ta haɗa harda Baba wai basa son Nimrah. Su dai haƙuri suka koma bata.... Da Nimrah Inna ta tafi sashenta, acan ta lallasheta ta bata nera ashirin wai ta sayo awara da kunu gidan Zinaru. Aiko da farin ciki ta ɗauki kwano ta tafi, gidan Zinaru mai awara da gidansu akwai ƴar tazara kaɗan, dan gidansu Nimrah yana cikin gidajen ƙarshen gari, sune na ƙarshe ma sai jeji babu gidaje a bayansu sai wasu ƙauyukan. Har tabi ta cikin gari ta canja hanya ta koma ta bayan gida tabi wai tafi sauri. Tafe take tana shan majina da doke-doken abubuwa da karan dake hannunta. Wani lokacin ma har yara ƴan uwanta idan ta gamu dasu sai dai kaji ta zuba maka duka, kafin ka rama ta zura da shegen gudu. Gata ƴar sirit babu ƙiba sai tsayi.             Taje birtalin da zata fita a bayan gidan ta koma hanyar gari sosai ta hango wasu mutane zaune a ƙasan wata ƙatuwar bishiyar mangwaro dage wajen. Humm Nimrah neman magana ake gaya muku, sannan Nimrah faɗi ba'a tambayeka ba. Fasa tafiyar tai ta koma hanyar inda mutanen nan ke a mangwaro. Babu zato sukaji ƴar muryarta na faɗin, “Suwaye ku?”.      Da wani irin sauri duk suka juya suna kallonta, sai mutum ɗaya da bai juya ba sai ma runtse ido da yayi tare da jan hiraminsa dake kan wuya da sauri ya rufe fuskarsa alamar baya son ta ganshi, kuma tabbas ta sanshi ne shiyyasa yayi haka. A hasale wani zai mata magana na kusa da shi ya hanashi ta hanyar riƙe masa hannu ya matse. Murmushi yayi mata tare da faɗin, “Yarinya miya kawoki nan?, mu baƙi ne”.      Fuska a ya yamutsa, maimakon kula zancensa na farko sai catai, “Baƙi? A bayan gari”.        Sosai mamakin shegen wayonta ya bayyana a kan fuskokinsu. Wanda yay maganar dai ne ya sake mata murmushi. Ya ce, “Eh zamuje ƙauyen Garjalle ne”.       Batace komai ba, sai ma ido data zubama jakunkunan gabansu, sai kuma ta koma kallon wanda ya rufe fuskarsa. Ganin yanda ta zuba masa ido yasa wanda yay mata magana ɗazun ɗakko naira hamsin ya miƙa mata. “Kinga ƴar Baba amshi wannan ki wuce gida kada a nemeki”.     Kuɗin ta zubama ido, sai kuma ta girgiza kanta tana kamo gefen kallabinta da aka kulle ta nuna masa. “Bana so, nima Inna ta bani zanje sayen awara ne”.        “Yauwa to maza kije ki sayo kada ta ƙare”.    Harta juya zata wuce sai kuma ta dawo. Ta ce, “Kai Baba to miye a wannan ƙaton jakan da yawa? Wannan kuma miyasa ya rufe fuskarshi ko bashi da lafiya?”.         Babu wanda a cikinsu baiji kamar ya hamɓare yarinyar nan ba. Amma dai wanda ke amsata ya daure ya ce, “Eh baida lafiya. Jakun kuna kuwa mangwaro ne muka zuba”.       “Ai yanzu ba lokacin mangwaro ba ne”.      Ta amsa tana sake matsosu. Tsawa na ɗazun ya daka mata dan ya kasa haƙuri, “Ke wuce ki bar nan komu yanka ki mai shegen surutun tsiya, ƴar firit dake sai sa ido kamar aljana”. Ganin ya ƙare maganar yana jawo wani ɗan icce a kusa da shi da gudu tabar wajen kuwa. Sai da tai nisa daga nesan tana hakki ta juyo ta ce, “Ku! In ALLAH ya yarda sai kura ta cinye ku masu jajayen ido irin na fatalwa”.      Daga haka ta sake zurawa a guje. Takaici ya saka wanda yay mata tsawar nan ciro wata ƴar mitsitsiyar bindiga ya saita ta. Cikin sauri wanda ya rufe kansa da hirami ya kaɓar da bindigar yana yaye hiramin da girgiza masa kai alamar karya aikata wannan kuskuren.          “Mi kake nufi ko kana da alaƙa da ita ne?”.     “Babu ruwanka da koma ya nake da ita, ka duba mana yarinya ce ƙarama dududu bata wuce shekara bakwai da wani abu ba. Sannan a tsarinmu bamuyi haka da ku ba ai. Babu cutar da yara, babu cutar tsoffi”.         “Kai baƙauyen banza anƙi abi dokar taka, kodan kaga mun biyo ta hannunka ne kake tunanin bazamu iya aikin da kammu ba. Kada ka manta kuɗi muka biyaka kai mana komai. Sannan da kake kiranta yarinya ai a yarintar tata tasan rashin kunya ma manya ko. To na rantse maka duk inda naga yarinyar nan a garin nan sai na fasa mata kai kuwa”.         Da sauri mai hiramin nan ya kalla Ogan tawagar, kafin ma yayi magana ogan ya ce, “Kaga manta da shi, babu abinda zai mata kasan shi dai da zuciyar tsiya. Kamar yanda mukai alƙawari da kai tun farko babu canji, bazamu taɓa yara da tsoffi ba. Kai dai kaje ka fara mana aikin tantance yara mazan da muke so. Zuwa jibi ka tabbatar aikinka ya kammala zuwa dare zamubi gida-gida mu tattaresu waje guda. Ga kayan aikinka nan da kuɗaɗenka zaka iya tafiya”.       Kansa kawai ya jinjina, sai kuma ya miƙe. “Bazan tafi da waɗan nan kayan ba yanzu, sai magriba zan dawo ɗauka.”      “Baka da case Goga”. Ogan ya faɗa yana bashi hannu. Daga haka ya gyara hiraminsa ya zagaya wata hanyar ɓadda kama ya koma cikin gari..........✍🏼      (Lallai cakwakiya, to wanene wannan 🤔? Yaya batun wanda yace sai ya kashe Nimrah? Kuna ganin zai ƙyaleta kuwa🤔🥲😳. Hummm kudai muje kawai, dan ba'a fara komai ba ma. Cakwakiya ce iya cakwakiya a cikin littafin nan🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️). _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 39_ __________________ *_Kuyi hakuri dani, ni kaina bana gane kai na saboda uzurirrika da suka zagayeni wlhy. Amma ina sha ALLAHU ina gab da kammalawa na dawo da hankalina gaba ɗaya kanku. Ina muku fatan alkairi gaba ɗaya 😘😘😘😘😀🙏_* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Hajiya Nimrah kam dai koda ta bar wajen gidan sayen awara ta nufa, koda ta sayo yaran gidansu data samu acan gidan awarar sunzo saye suka janye ra'ayinta suka tafi tare ta cikin gari bata dawo ta bayan gidan ba. Ta samu Umma na murza taliya, dan wannan itace sana'arta. Tuni Bana ya sayo mata wata fulawar ta murza a maimakon wadda Nimrah ta zubar, wannan ma ta wasu ce take murzawa a yanzu. Nimrah ta zauna kusa da ita tana shan majina da buɗe kwanon awararta.        “Umma kalla, Baba Zinai ta zubo min da yawa”.     Batare da Umma ta kalleta ba ta ce, “Kin gode. Sai ki tashi ki cire wannan majinar da kike faman sha ki wanke hannu sannan kizo kici dan nasan a fitarki kaf tarkacen garin nan sai da kika taɓa”.        “To”.      Ta faɗa cike da abin arziƙi ta tashi tayi duk yanda Umma tace. Harda ɗebo ruwa a moɗa cikin randarsu. Tazo ta ajiye ta kaiwa zaune. Kamar wadda aka tsikara ta ce, “Umma kinga ko, da zanje ta bayan gida nabi, a gonar Baban Zakiru naga wasu mutane da yawa zaune, idanunsu jajaye kamar na fatalwa. Hadda jakunkuna manya sun ajiye, wai sukace min ƙauyen Garjalle zasu je......”        Kallonta Umma tai a karo na farko, sai kuma ta ɗauke kai cikin rashin ɗaukar zancen da muhimmanci ta ce, “To uwar soki burutsu zaki fara baƙin surutun naki ba. A gidan uwarwa ake ganin wata fatalwa da rana. Ɗauki awararki kici bana son magana”.      Baki ta tura sosai, kamar zatayi kuka ta ce, “Na rantse da gaske nake Umma. Kuma har wajensu naje ma, har naga wani mai irin kayan......”         “ALLAH idan baki min shiru ba sai na fasa maki baki, koki tashi ki wace wajen Inna in damuna zakiyi.”      “Mi kuma tayi za'a fasa mata baki? Bayan ɗazu kika gama dukanta”.    Baba dake shigowa ya faɗa. Sannu Umma tai masa sannan ta ce, “Ta isheni da surutu ne. Wai taga fatalwa ko a gidan uwarwa ake ganin wata fatalwa”.       Shi abin ma dariya ya bashi, ya kaɗa kai kawai yana ƴar dariyar da faɗin, “Uwa sarkin magana, Zakanyar Kawu Tanimu, in dai zance ne a bar miki abinki”.         “Baba banyi ƙarya ba fa, kuma harda mai irin kayan......”      Murfin kwano da Umma ta jawo ya sakata saurin dafe bakinta dan tasan kaɗan daga aikinta ta kwafɗeta da shi. Shima Baba sai ya shige kawai yana murmurshi.. koda Nimrah taga Umma da Baba sun ƙi sauraren labarinta na fatalwoyi sai ta surare ta koma sashen kakarta Inna. Acan ta fara bata labari, sai dai anyi rashin sa'a itama Inna ta kwaɓeta batare data maida hankali a zancen ba ta ɗauka soki burutsinta ne kawai data saba. Daga ƙarshe ma korota tayi daga sashen akan ta tafi ta bata waje barcin zatayi. Daga haka Nimrah ta fice cikin yara suka kama wasa. Can kamar an tsikareta taba yaran labari suma, abinka da ƙuruciya sukace ƙarya ne, sai ta dage akan suje ta nuna musu. Aiko haka suka haɗa gayya suka fita bada sanin iyayen ba bayan gidan.      Tafiya takanas babu ko gargada ta kaisu har wajen mangwaron nan dake cikin gonar Baban Zakiru kamar yanda ta faɗs, sai dai a yanzu babu kowa wajen mutanen sun tashi sai robobin ruwa da suka sha da takardun nama, wata ledar ma ba'a cinye naman ba. Haka sukaita tsincewa suna ci, suka tattaro robobin ruwan dana lemo suka dawo gida. Yawancin iyayen sun gansu da waɗan nan robobin ruwa dana lemo, amma sai basu tambayesu daga ina ba saboda a wasu lokutan kawunsu Tanimu kan raba musu dan su dinga zuba ruwan zuwa makaranta, shima kuma yana zuwa dasu ne daga birni.             Da yamma gab da magriba Umma ta gama aikin tuwon dare. Ruwan data ɗumama ta ɗiba taima Nimrah dake ta damunta da surutu tana cin gyaɗa wanka. Ta shafa mata mai ta saka mata kaya. Tuwon Inna data zuba a langa ta saka a botiki ta tura gaban Nimrah ɗin. “Ki ɗauki tuwon Inna kikai mata, sai ki dawo ga miyar nan itama zan saka miki a wannan botikin ki ɗauka ni zan shiga wanka bana son a kira magriba, saura kuma dan ALLAH kiyi abinda ban saki ba, ALLAH bazaki bini gidan Malam ba in har kikai min wata ɓar nan”.          “To Umma, ALLAH ba abinda zanyi, dan ALLAH kada kice bazaki je dani ba, ina son na gaida Malam da Iya”.     Nimrah ta faɗa cikin tsalle-tsalle tana daukar botiki. Ita kuma Umma ta ɗauki ruwan wankanta ta shige bayi tana faɗin, “In da kinso ganinsu ai ƙafarki tasan inda suke”. Nimrah da bataji mi Umman ta faɗa ba ta ɗauki tuwon Inna ta fita cike da murna zasu gidan Malam, (Malam dai shine mahaifin Umma, babban malami ne a yankin kuma dattijon arziƙi da kowa ke girmamawa) koda Nimrah ta shiga sashen Inna babu kowa, dan dama ita kaɗaice a sashenta tunda kishiyarta ta rasu sai dabbobinta. Ɗaki ta shiga ta ajiye mata kwanon tuwon ta fito, ta sake komawa sashensu ta ɗakko miyar ma ta kawo. Harta juya zata tafi ta hango ƙwayayen kazar Inna dake akurkin jikin katanga gab da fita a sashen. Kwana tayi ta koma wajen akurkin ta duƙunna ta ɗauki ƙwai ɗaya ta saka a botikin hannunta, sai kuma tayi ɗan tsai kamar mai lissafin sauran ƙwayayen, hannu tasa ta ƙara ɗaukar ɗaya, ta ce, “Ni ɗaya Umma ɗaya. To Baba fa, shima bari na ɗaukar masa, idan Inna taji harda shi akaci ai bazata dake shi ba tunda yayi babba sosai.” tana maganar tana leƙa cikin akurkin duba wasu ƙwan. Sai dai maimakon ganin ƙwari taci karo da wata jaka. Hannu tasa ta jawo jakar. Tare da faɗin, “Lah Inna har cikin jaka take ɓoye ƙwai, aiko saina ɗibawa Babana da Kawu”. Tana maganar tana kici-kicin buɗe jakar, sai dai ta kasa. Abinka da yaro tana jiyo maganar Inna ta yayimi jakar ta jefa a botikin ta ɗauka da gudu ta shige bayi, sai da Inna ta shigo ta shiga ɗakinta Nimrah ta fito da gudu nan ma ta fice zuwa sashensu da wannan ƴar jaka da zato ta ke ita ƙwai ne Inna ta ɓoye a ciki.       Lokacin da take shigowa sashensu Umma ta shige ɗaki dan anata kiran sallar magriba. Anan tsakar gida ta ajiye botikin da jakar duka ta nufi ɗakin gayama Umma takai wa Innar tuwon. Koda ta faɗa mata sai tace taje tayo alwala suyi salla su tafi. Cikin farin ciki ta fito, dan tasan koba komai zatayi wasa da ruwa ai. Sai da ta gama facaccalinta kuwa sannan ta tafi ɗakin tayi sallar. Ta mance da batun ƙwai taci tuwo suka tafi gidan Malam. Kafin su dawo ta ɓingire barci, sai goyota Umma tayi ma. Sanda Baba ke shigowa gidan ta jima da yin barci.       Misalin sha ɗaya na dare Umma da Baba sun gama cin abinci da hira Umma ta fito kaye-kaye tsakar gida sai ga Tanimu ya shigo sashen da sallama. Amsa masa tayi, tana murmurshi da faɗin, “A'a kawun Nimrah baka kwanta ba?”.         “Wlhy kuwa ban kwanta ba Yaya, nace bari nazo nai muku sallama dan in sha ALLAHU gobe zan koma birni. Amma sai yamma zan wuce da safe dai zanje hayi wani ɗaurin aure, daga can nake son nabi wasu abokanmu da zasu zo ɗaurin auren suma daga birni.”        “Kai kawun Nimrah da wuri haka, wannan karon ai baka daɗe mana ba, kwata-kwata bakafi sati biyu ba”.      “Wlhy naso yin sati uku ne fa, to ganin mota a sauƙaƙe yasa zan wuce kawai. Amma bazan jima ba nanda ƙarshen wata zan dawo yin dashen albasar nan.”           “Ato da gaskiyarka, ALLAH to ya kaimu. Ka shiga Yayan naka na ciki ai, bari nima na ƙarasa kaye-kaye dan karnuka na shigo mana da dare”. Amsawa yay da to yana shigewa, ita kuma ta cigaba da tattare kayan tsakar gidan. Ciki harda botikin nan da Nimrah ta sakawa jaka a ciki. Batare da Umma ta damu da miye cikinsa ba ta rufe shi da murfinsa dan dama tana kwaɓin fulawar taliya ne a ciki idan zata murza. Ɗaki ta shiga da su ta ajiye, daga haka ta zauna suka cigaba da hira da Baba da Tanimu.... ★>>>>>★<<<<<★              Tunda ragamar jejin ta koma hannunsa a daren jiya duk ya kasance a tsarguwa. Ko barcin kirki baiyi ba, dan haka kawai yake jin wani abu mai nauyin gaske a zuciyarsa. Ga yawan faɗuwar gaba dake samunsa. Bafa yau ne karo na farko da Zak-Shadow ke barin jejin shugabanci ya koma hannunsa ba, amma sai yake jin na wannan karon da girma sosai.       Wajen misalin ƙarfe uku na dare barci ya gagaresa gaba ɗaya, sai kawai ya tashi. Wayar sadarwa ya ɗauka, yay kira kai tsaye ga dukan Captains dake cikin rundunar, cikin bada umarni ya buƙaci ganinsu. Basu ko ɓata lokaci ba, dan kafin ƙarfe huɗu na asuba sun tattaru a sansanin nasu. Meeting Major Imran yay da su na minti talatin kawai, kafin biyar na asuba ya sallamesu kowa ya nufi komawa sansaninsa.... ★A lokacin da Major Imran Abbas ke zaman wannan meeting da Captains ne yaran ƙungiyar duhu suka samu damar kutsa kai cikin wasu sansani kamar yanda suke iso tun farkon dare. Mataki na farko da suka fara amfani da shi shine datse na'urorin sadarwa dake cikin sansani uku. Cikin bazata ƙarfe biyar dai-dai na asuba matasan jaruman sojojin na ƙoƙarin gabatar da al'awalar shiga sallar asubahi, wanda basa sallar na ƙoƙarin amsar duty kawai sukaji saukar harbin kan mai uwa da wabi.     Tabbas duk wanda bai zama jami'in tsaro ba bai san minene tashin hankali da ainahin jarumtar mazan ƙwarai ba. Cikin abinda baifi minti biyu ba sojojin nan sun rikiɗe maida raddi, hatta waɗanda suka sami harbi bata ciwon suke ba sam balle zubar jinin da suke yi. Lokacin da Captains ɗinsu suke dawowa wajen ƙarfe biyar da wasu mintina wasa yayi wasa, domin kuwa waje ya hargitse hargitsewa irin ta MAZAJEN FAMA. Cikin tashin hankali Captains ɗin sukai ƙoƙarin kai rahoto ga sauran sansani ta hanyar wayoyin sadarwa, amma abin mamaki duk basa aiki. Makircin masu makirci yayi tasiri kenan bisa ƙaddarar UBANGIJI.     Ba wannan bane hari na farko da suka taɓa fuskanta, amma wannan kam ya girgiza hazo sakamakon tsahon shekaru uku kenan babu wani damuwa har suna jin sun gama nasara akan azzalumai, domin kuwa shiri suke na barin jejin a cikin wannan shekarar ganin zaman lafiya ya samu a yankin fiye ma da yanda ake fata..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* 40 ........Gari ya ɗan fara hasken dake bayyana safiya, Major Imran daya kasa zaune ya kasa tsaye na a bakin ruwa yana zubama tsuntsayen nan dawa tamkar yanda sukeyi shi da Zak-Shadow wani irin nishi ya fara tasiri a cikin kunnen sa. Kowane yanayi soja mai ankarewa ne akan aikinsa. Cikin sauri ya ajiye robar dawar yana waige-waige da ƙara buɗe kunne saitin inda yake jin nishin. Tabbatar da wajen ya sashi zabura tare da ciro bindiga a jikinsa yaja ya ɗana, cikin sanɗa da jarumta ya tunkari wajen. Dai-dai yana isowa gab aka ƙara jan nishin da ƙarfi tare da hankaɗa ciyayin wajen. Soja ne ya bayyana jikinsa kace-kace da jini, da ƙyar yake iya ambaton, “Commandos, help us! We need you here! Where are you?.”.         Ai Major Imran baima San ya zabura kansa ba. Cikin tashin hankali yakai duƙe gabansa yana mai kamashi gaba ɗaya...         “Soldier! What happened? Report now! Are you okay?.”.     “Sir! Hari, hari aka kai mana a kusurwar ƙofar kudanci, sun mana ɓarna, sun datse na'urar sadarwa, shiyasa muka kasa isar da sanarwa......”      Ya kasa ƙarasawa saboda aman jini da yake yi. Bayyana tashin hankalin da Major Imran Abbas yake ciki ɓata lokaci ne. Sai dai da yake soja-soja ne babu alamar rawar jiki ko ɗimuwar zahiri. Da kansa ya ɗauki sojan nan a hannunsa ya juya nasu sansanin....      Zamu iya cewa wannan shine mafari, mafarin tashin hankali na bazata da masu makirci suka ɗauki kwanaki suna shiryawa da daidaita wannan gaɓar domin aiwatarwa ya tabbata. Ba ƙaramar ɓarna akaima sansani ukun nan da aka kaima hari ba. Gashi an yanke musu na'urorin sadarwa ta yanda har Headquarter sun gagara kai rahoto balle sanar da Zak-Shadow halin da ake ciki. Sai misalin ƙarfe goma sha ɗaya aka samu damar fita da waɗanda suka jikata, sai mutane shida da tun asubahin ma sun rasu, sojoji huɗu ƴan ta'addan biyu...... >>>•>•>•<•<•<<<         Tunda ya fita sallar magriba sai ƙarfe tara saura suka shigo gidan shi da Ammar dake maƙale da shi, dan shima gab da magriba ya iso daga Zaria inda yake karatu. Bai haɗu da Dadan nasu ba sai a masallaci bayan sun fito sallar magriba. Sosai suke so da ƙaunar Zak-Shadow, dan shi suka buɗe ido suka gani kuma suke kallo a matsayin uba. Ba sunan Dada da suke kiran shi ne kawai girmamawar da suke masa ba. Hatta umarni idan ya basu ko saka doka akan abu ko hanasu yin wani abu duk son da sukema abunnan sun barshi kenan har abada. Dan sunyi imanin bazai hanasu abinda zai amfane su ba, ba kuma zai sakasu yin abinda zai cutar da su ba.          Komai na hidimar rayuwarsu: ci, sha, ilimi, lafiyarsu da duk wani abu da akema ɗa ɗan gata shi da Mammah ne sukai musu a rayuwa. Taya zasu gagara masa biyayya su zama butulu. Sun tabbatar soyayyar da Dada ke musu soyayya ce irin ta ƴaƴa da mahaifi. Babu abinda zasu biya shi da shi sai addu'a da fatan shima ALLAH ya bashi tashi zuri'ar, dan rashin haihuwar nan tasu na damun kowa kawai dai basa magana ne...           Tunda suka baro gidan su Imran surutu kawai yake zuba masa. Shi ko Zak-Shadow nashi murmurshi, sai lokaci-lokaci yake jefa magana a taƙaice. Hakan baya damunsu, dan duk wanda yasan Dadan su yasan bamai yawan magana bane. Sam ba miskili bane, amma bai da yawan surutu ko dariya. Idan yaso hirarsa kuwa zakaji yanayi da Mammah sosai kamar bashi ba. To suma sukan ɗan samu kanshi wani lokacin ya biye musu idan yana jin nishaɗi..        Gaba ɗaya kowa na falon har matarsa da ƙannenta. Dama Aunty Ummi da Aunty Mommy da tun ɗazun suna gidan tare da shi. Aunty Mimi ce sai yanzu ta iso, ɗazun sanda Biebah ta kirata sun fita da mijinta anguwa. Suna yin sallama kuwa ta taso a guje cike da farin ciki tana faɗin, “Oyoyo Dada ta rungumeshi”.      Kansa ya girgiza kawai tare da ɗan bubbuga bayanta. “Ke dai baƙya girma ko”.      Ɗagowa tai tana dariya da kamo hannunsa cikin nata ta riƙe. “Dada in dai a gabanka ne ina nan ƴar yarinyata Autarka, dan ma wannan ɗan buƙulun yazo ya ragen farashin autar ne da waccan yarinyar”.     Tai maganar tana hararar Ammar da Biebah. Ramawa Ammar ɗin yayi shima, “Sai ki haɗiyi ƙwallon mangwaro ki suma, dole dai a ce da mijin iya baba ai. Muma autocin nan dai ne ko Auta”.        “Yes Yayana”.    Biebah ta amsa masa tana ma Mimi gwalo.       “Dada ka gansu ko, shiyasa idan baka nan bana son zuwa gidan nan na daɗe”.             Murmushi yayi kaɗan shi dai, sai kuma ya shafa kanta da faɗin, “Ki daina lulasu, ke yanzu ai kin girmi ƙuruciyarsu. Kalleki fa da yara har biyu”.      Fuskata ta ɓoye a jikin hannunsa, dan ita kunya take ji ma ace ta haihu. Shima bai sake cewa komai ba yaja hannunta suka ƙarasa cikin falon. Tashi Yaya Bilal yay ya bashi kujera da yake, ya koma kusa da Mammah, dan shi dama ɗan shagwaɓar Mammah ne, ya girma amma bai san ya girma ba. A ƙasa Ammar da Mimi suka zauna kusa da ƙafafunsa, duk sun riƙe masa hannaye kamar wasu ƙananun yara ko zai gudu ya barsu. Biebah tai ƙwaɓa-ƙwaɓa da fuska kamar zatai kuka ganin sun tsare ko ina bata samu wajen zama kusa da Dada ba. Gefensa ya nuna mata da ido, basa iya zama a kujera idan yana kan kujera har su Ja'afar kuma, amma bazata iya kuma ƙin bin umarninsa ba, dan haka ya taho saɗaf-saɗaf kamar munafuka ta zauna a hannun kujerar da yaken.         Dai-dai nan Mommy ta fito a kitchen ɗauke da kofi akan tray ƙarami. “Oh ni, duk kunzo kun wani dabaibayeshi kamar ku kaɗaine da Dadan.”       “Kema dai ƙya faɗa Mommy”. Cewar Aunty Ummi tana harararsu. Murmurshi Mammah tayi, yayinda matarsa dake cike fam da kishi da takaici kamar ba ƴan uwansa ba ta ɗan taɓe baki. Mugun haushin wannan soyayyar da yake nunawa ƴan uwansa take. Ta taɓa suɓutar bakin nuna masa abin yayi yawa, daya zuba mata wani mummunan kallo ai bata sake kwatantawa ba.         Bilal ya ce, “Dada dan ALLAH sati biyu zakai mana ko? ALLAH muna missing ɗinka muna son muyita kallonka, idan kana nan gidan yafi daɗi”.        Sai da ya amshi mug ɗin shayin da Mommy ta kawo masa ya kai baki kaɗan sannan ya amsa Bilal ɗin. “Kuyi haƙuri Bilal, lokaci na zuwa da zan zo na zauna tare da ku na baku dukkan lokaci na. Nima ina jin farin ciki a duk sanda nake tare da ku”.       Sosai maganarsa ta shige su da saka su jin ƙaunarsa na ratsasu. Naneeha data ɗan zuba masa ido ya kalla, sai kuma ya kauda kansa. Falon ya ɗanbi da kallo tare da faɗin, “Ina Mu'azz!”.          Biebah ta ce, “Dada yayi barci, ya gaji da jiranka ya ɓingire”.      “Da wuri haka”.   Ya faɗa a taƙaice. Mammah dake duba wani littafin addini ta ce, “Wannan ɗan naka ai ruwa-ruwa ne. Ina ga dai sojan zaka maidashi ko zai canja.”          Dariya sukayi su duka. Banda shi daya ɗan murmusa kawai. Haka suka cigaba da hira cike da nishaɗi, duk da shi tashi maganar bamai yawa bace, sai dai sun sha murmushi dan su kam yana musu murmushi ba kamar a waje ba. Kasancewar duk anan su Aunty Ummi ma zasu kwana wannan hira bata tashi ba sai kusan ƙarfe ɗayan dare. A hakan ma sai da Mammah tace su barshi yaje ya kwanta, dan su basu ƙi a kwana ana hira suna ganin Dada ba.       Tuni Nabeeha da ƙannenta dama sun koma can sashen nasu tun wajen 11. Dan haka ya fito, sai Ammar da Bilal da sukai masa rakkiya har ƙofar sashen nasa sai da ya shiga sannan suka koma...          Ganin haske alamar batai barci ba kai tsaye ɗakinta ya nufa a karo na farko tun isowarsa gidan. Zaune kuwa ya sameta tana waya, ta canja kayanta zuwa na barci da sukai mata ƙyau sosai. Idanunsa a kanta yay sallama cike da nutsuwarsa. Idanu ta ɗago a hankali ta kalleshi, sai kuma ta kawar tana yin sallama da wanda suke wayar. Dai-dai tana ajiye wayar yakai zaune kusa da ita, kasancewa a sofa take zaune. Ganin kallon daya zuba mata cike da tsarguwa ta ce, “Mummy na gaishe ka”.          “Na gode”.    Ya faɗa a taƙaice. Kanta ta jinjina masa itama, sai kuma ta matso kaɗan ta kwantar da kanta a kafaɗarsa, hannunsa ta kamo ta saka nata a ciki. Mintuna kusan biyu suna a haka shiru, sannin hirarsa sai ya gadama ya sata ɗaga kai tana kallon ƙyaƙyƙyawar fuskarsa, idanunsa a lumshe suke tamkar mai barci, amma tasan ba barcin yake yi ba. Dan haka ta ɗan matsa hannunsa tare da faɗin, “My Cool”.       “Uhhmm”.    “Kayi barci ne”. Maimakon amsa mata sai ya buɗe idon kawai yana kallonta. Kasa jurewa tai ta ɗan risinar da nata tana sauke numfashi. Cikin jin shakkar faɗar abinda ke bakinta ta cigaba da matsa yatsun hanun nasa, kafin a ɗarare ta ce, “Dan ALLAH wannan karon ka yarda muje muga likitan nan mana. Ta hakanne zamu fahimci idan wata matsala ce a tare damu mu tashi mu nema magani. Shekara goma sha fa ba kwana goma sha bace My D. Dan ALLAH kai baka jin wani abu a ranka idan ka kalla ƙannenka da yaransu? Ga su Ja'afar suma zasuyi nasu auren, nan da shekara ɗaya sai kaga duk suma da yaransu. Haka kake son suma matansu suzo a bayan bayana su haihu ina kallo....”          Shiru ya mata yaƙi tankawa. Sai hakan ya ƙara ƙular mata da zuciya, dan haka yake mata a duk sanda ta kawo masa batun zuwa ganin likita. Kuka ta fashe masa da shi mai ratsa zuciya. Kafin ta yunƙura fuu ta miƙe da nufin bar masa wajen, batare daya kalleta ba shima ya riƙo hannunta, tare da fisgota ta faɗo jikinsa gaba ɗayanta. Kici-kici ta fara nason tashi tana ƙara ƙarfin kukanta, amma riƙon da yay mata da hannu ɗayan nan kawai ta gagara tashin. Ganin ba iya ƙwatar kan nata zatai ba da gaske sai kawai ta kwantar da kanta a ƙirjinsa ta cigaba da raira masa kukan.Tsawon lokaci suna a hakan idanunsa a rufe tamkar bai san tanayi ba, ganin ba dainawa zatai ba ya ɗagata a jikin nasa ya miƙe da nufin bar mata ɗakin gaba ɗaya.........✍🏼 *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 41_ __________________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LkEgiP5qOEo9YDYjaeZLLc?mode=ems_wa_t✍️✍️ Assalamu Alaikum my people dafatan kunanan cikin aminci sunana ummuh sayyeed yar mutan Chadian traditional medicine center Zaria dealer in all kinds of magungunan mata turarukan wuta sudaniss dilka skin care products at home my people bazamafa a kwai zafafan promo damukeyi in Sha allahu zuwa on 15 zamugama sannan gareku Yan Kano free ne kayanki zasuzo miki amma fa karyazo bayan mungama promo kuce kyauta ne aa zakibiya kudi nagode takuce yar mutan Chadian mai gyaran ciki dawaje 💃💃 please banda maza,❌maza❌ In kinada matsala wadda zamu iya taimaka miki 09065504546 Ga PRODUCTS DINMU KAMAR HAKA MAGANIN SANYI TSUMIN BOM MADARAR TABAJE GORON TULA SYRUP ZUMAR SHADAMATSIN GARIN YAUKAYAUKA EMERGENCY GARIN KINFI KAZA DADI SIRRIN MALLAKAR KASA SIRRAN GIDANKI DAHUWAR KAZA DAHUWAR CICCIBI DAHUWAR YAN SHILA HMM BAZASU IRGUBA INA GODIYA SOSAI MY PEOPLE 🥰🥰 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Zaram tasha gabansa, sai dai ta gagara kallonsa kamar yanda shi yake kallonta. Zuciyarta na mata ƙuna da raɗaɗi, shawarwarin mahaifiyarta na bata ƙwarin gwiwa ta ce, “Haysam kana saka min shakku a zuciyata da jin yarda akan maganganun mutane. Kodai baka son haihuwa ne kamar yanda kowa ke faɗa?”.          Ya daɗe bai ji abinda ya sokar masa zuciya kamar kalamanta ba. Cikin wani irin yanayi mai girman gaske ya zuba mata idanu yana mata wani irin kallo mai zafin gaske. Zuciyarsa kuwa tuni ta yinƙuro ta tokare maƙoshinsa. Ya tabbata in dai ya buɗe baki akan bata amsar kalamanta zai iya gaya mata mai zafin gaske da zata ninka wadda ta gaya masa sau dubu. Dan haka sai kawai ya zagayeta ya fice a ɗakin gaba ɗaya.       Fashewa tai da wani irin kuka tana kaiwa ƙasa ta zube. Jifa ta fara yi da duk abinda ya tare mata gaba. Babu abinda ke ƙara ingiza fushinta sai kalaman mahaifiyarta. Tabbas ta yarda gaskiya Momy ke faɗa akan mijinta. Dan ita kanta a wasu lokutan takan zauna taita tunani game da al'amarinsa. Yanda yake mutum mai yawan buƙatar iyali miyasa idan ya tafi wajen aikinsa in ba ita ta takura masa da magiyar yazo tana missing ɗinsa ba dan kansa baya shiryowa yazo dan yin hakan. Sannan ko zuwan yayi idan ba ita da kanta ta kawo masa kanta ba bazai nema ba. Da tana ɗauka tsabar girman kansa ne ke sashi yin hakan. Sai da mahaifiyarta ta fara fargar da ita ne akan kodai yana neman mata ne sannan ya ɗan fara taba tunaninta, sai dai zuciyarta bata amince ba tana wasi-wasi dan tasan sa da ƙyanƙyami. Amma zuwa yau zuciyarta kamar ta fara jin aminci da wannan zance, musamman idan ta tuna maganar wasu ƙawayenta da kance ta tashi tsaye akan mijinta dan wasu sojojin akwai son matan tsiya, shiyasa ma basu cika son haihuwa ba dan kar aima ƴaƴansu abinda sukema wasu.           Waɗan nan tunane-tunane Nabeeha ta cigaba da tasirantarwa a wannan dare suna ƙara tunzurata da rikita mata sissafi. Koda ta sake kiran mahaifiyarta ta gaya mata yanda sukayi da mijin nata sai ita kuma ta sake tabbatar mata hasashensu ya zama gaskiya dai, Zak-Shadow baya san haihuwa a gaske. Kuma tabbas dole ta miƙe tsaye da bincikensa dan ta tabbatar shin baya neman mata. Ai ko haka ta ƙara hawa ta zauna. Da safe har ya shirya ya fito bata leƙashi ba. Sai shine ya shigo ɗakin nata.         Yanda ta faffasa abubuwa kawai ya tsaya yana kallo, kafin ya maida idanun kanta. Tana kwance a kan gado da waya a hannunta. Sarai kuma ta ji shigowar tasa amma tai biris. Uffan baice mata ba ya juya ya fice a ɗakin. Sai ta raka bayansa da harara tare da jan tsakin daya shiga kunnensa a bazata, dan ya juyone da nufin dawowa ɗakin ya mata magana. Cak ya tsaya tamkar wanda akai ma tsawa, sosai fuskarsa tayi masifar sake haɗewa fiye da yanda take, idanunsa sun wani juye alamar zuciyar ƴan maza ta motsa, dan ni kaina na tsorata addu'a kawai nake kar yace zai koma ɗakin. Ganin ya bar wajen ya sani sauke ajiyar zuciya.      Sashen Mammah ya nufa, a kallo ɗaya kuma ta fahimci ransa a ɓace yake. Sai dai batayi magana ba saboda ƙannensa. Shima cikin dannewa da haƙuri da ALLAH ya bashi ya fuskanci ƴan uwansa ya ajiye batun Nabeeha gefe..... >>>>>★<<<<<         Gaba ɗaya wannan yinin su Major Imran sun yishi ne akan ƙafafunsu wajen binciken son sanin su wanene suka kawo musu wannan harin, ta wani ɓangare kuma hankalinsa a tashe yake matuƙa akan son samun Zak-Shadow kafin zancen harin da aka kai musu ya kai Headquarter asan baya jejin tunda yayi fita ne irin ta sirri. Amma har wani daren bai samu mafita ba. Sai dai sun sake shiri na musamman akan kowane sansani dama jejin gaba ɗaya. Dama haka wannan munafukai ke buƙata, wato karkatar da hankalin su Imran ɗin, sun ko samu nasara zamuce, dan ana cikin sallar isha'i suka sami nasarar kai hari a ƙauyuka uku. Bankaura dake babban ƙauye na wannan yankin, sai wani ƙauye da ake kira Gangare, sai kauyen Marke.      Wannan sabon tashin hankali ne da waɗan nan ƙauyuka basu taɓa fuskanta ba a baya, dan rikicin shekarun baya daya faru a sauran ƙauyukan ne banda nasu. Ruwan fitar harsasai da ƙarar tashin nakiya ce ta fara jan hankalin wasu a yaran su Imran. Cikin gaggawa wani haziƙin matashin soja ya silalo yabaro inda suke da bayi da nisa da ƙauyukan ya sanar da Imran. Ai babu ɓata lokaci ya zabura da wasu tawaga suka nufi wannan waje. Ƙauyen Gangare suka fara shiga kasancewar shine farko. Tun a farkon shiga suka fara cin karo da gawarwakin mutane. Hankalinsu ya tashi dan sun fahimci al'amarin da lallai babba ne. Ai babu wani maganar ɗaga ƙafa suka buɗe ma yaran su Dagger wuta, nan fa sabon wasa ya koma tsakaninsu, mutanen gari kuwa tashin hankali yasa sun watse cikin jejin, wasu kuma a cikin gidajensu suka samu wajen ɓuya.      Matuƙar bata kashi akasha a wannan dare, kowane ɓangare sun gama jigata musamman mutanen gari da sukafi fuskantar ƙalubale, an kashe mutane da yawa, a wannan ƙauye. Ba'a samu lafawar wannan hargitsi ba sai zuwa ƙarfe shida da rabi na asuba gari ya fara haske, daga ƙarshe dai su Dagger suka gudu, an kashe wasu a cikinsu suma, an kama mutane biyu kuma, kamar yadda wasu a cikin yaran su Imran suma aka ji musu ciwo, sai dai soja ko ɗaya bai mutu ba. Sojoji na tattara mutanen da suka jikkata Imran ya samu waya ta wani da aka kashe, gefe ya koma ya shiga neman layin Zak-Shadow, a lokacin kusan ƙarfe tara na safiya. A kuma dai-dai wannan time ɗin ne Zak-Shadow yake a sashen Mammah tare da ƴan uwansa bayan ya baro nashi sashen da ɓacin ran matarsa.      ★ Bilal ne yaga wayarsa na haske, dan shi hankalinsa ya tafi kan magana da Mammah.       “Dada kamar ana kiran wayarka”.    Bilal ɗin ya kalla, sai kuma ya juya yana kallon wayar dake a gefensa. Baƙuwar number ce, shi kuma baya ɗaga baƙuwar number. Dai-dai nan kiran ya katse, har zai ɗauke kansa sai kuma wani kiran ya sake shigowa a karo na biyu, cikin takaici ya ɗauki wayar zai kashe gaba ɗaya dan zuciyarsa sam babu daɗi...            “Ya kamata dai ka ɗauka kasan waye”.     Maganar Mammah ta dakatar da shi daga kashe wayar, cikin bin umarni ya ɗaga tare da sakawa a hansfree. Jigatacciyar muryar Imran ta daki kunnensa, “Imran ne Sir!.........”          Wayar ya ɗauka yana miƙewa tare da cireta daga hansfree ɗin gaba ɗaya. Cikin wata irin razananniyar murya ya ce, “What! Shine sai yanzu kuke sanar dani. Imrannn!!!”.       Yanda ɗakin ke amsawa da amon muryarsa yay matuƙar tada hankalin ƴan uwansa, a zafafe ya yanke kiran yana mai isowa gaban Mammah. Kai tsaye ya ce, “Mammah zan wuce akwai matsala”.            “Ya rabbi, miyake faruwa?”.      “Ba lafiya Mammah, hari aka kai mana. Kiyi haƙuri zamuyi waya”.    Daga haka ya fice daga falon kamar wani yunwataccen zaki. Hankalinsu a tashe duk suka miƙe suna kallon juna, sai kuma duk sukayo waje suma. Dai-dai nan yake fitowa daga sashensa da jaka a hannu, sai hular mashin ɗinsa. Gaban Mammah yazo ya ɗan rungumeta, ta shafa kansa tana mai masa addu'a, dan yanayinsa kawai ya tabbatar mata al'amarin babba ne sosai. Hakama ƙannensa a tare suka zo suka rungumesa tare da masa addu'a. Da sauri yabar wajen ganin su dukansu suna faman sharar hawaye, har Mammah duk jarumtarta sai da ta kauda kai gefe, yana hawa ƙaton mashin ɗinsa da in yana tafiya baka jin ƙara Bilal ya zabura ya nufi gate da gudu ya buɗe masa. Ai ko a guje ya fice daga gidan shima, dan ji yake kamar ya rufe ido ya gansa a jejin... Ganin kowa ya fito babu Nabeeha ƙanwarta ta tafi da gudu tana buga mata ɗaki da kiranta.     “Aunty!. Aunty! Ki buɗe dan ALLAH Dada fa zai tafi”.     Wani irin dukan zuciyar Nabeeha kalmar zai tafin tai a karo na farko. Cikin sauri ta diro a gadon da take kwance. Yanzu fa taji yana buga mata ƙofa da kiran sunanta tai banza da shi, a zatonta kan maganar jiya ne yazo ko fitinarsa ce ta motsa, duk da tasan kome yake ji idan yana fushi zai iya danne abinsa ya haƙura, shiyasa taƙi buɗewa. Tana buɗe ƙofar ƙanwarta taja hannunta kawai suka fito, sai dai rashin sa'a suna fitowa tsakar gidan ana rufe gate alamar harya wuce. Sharrr hawayen da suka cika mata ido suka shiga rige-rigen zubowa, sai kawai jikinta ya kama rawa har tana neman faɗi sai da ƙanwarta ta riƙeta. Ciki suka koma, dan su ma su Mammah sun shige nasu sashen. Bedroom Nabeeha ta shige tana mai fashewa da kuka, dan ita duk tunaninta abinda tayi jiya ne da ƙin buɗe masa ƙofa a yanzu ya fusata shi.          “Aunty dan ALLAH ki daina kukan nan, kimasa addu'a kamar yanda sauran ƴan uwansa ke masa. Dan ita yafi buƙata a garemu baki ɗaya”.          “Ismat bazaki gane ba, laifina ne, nasan nina fusatashi ya tafi. Miyasa daya buga ban buɗe masa ƙofar ba....”       “Anya haka ne kuwa Aunty. Kamar fa kiransa akai daga wajen aiki inaga wani abu ne ya faru”.       “Wajen aiki?”.   “Tabbas haka ne Aunty, amma ki bincika wajen su Mammah”.          Hawayenta ta shiga sharewa da sauri. Sai kuma ta jawo wayarta ta shiga kiran number ɗinsa. Amma harta katse bai ɗaga ba. Ta jera masa fin kira goma no answer, sai ta sake fashewa da kuka tana yin jifa da wayar, ALLAH ma ya sota bata faɗi ƙasa ba Ismat ta cafe..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 42_ __________________ https://wa.me/+23408067422528 Kina son rage kiba ba tare da kin daina cin abunda kike so sannan ba tare da kinyi gudawa ba? To kimin magana domin samun hanyoyi da zaki rage kiba ba tare da kinsa wahala ba. Ko kuma matsalar gashi ce ke damunki, ko rashin tsahon gashi ne, shima muna da solution dinsa. Ko kuma fatar ki tana lalacewa ne a sanyin? Muna da ingantaccen man da zai gyara miki kafafunki ko kuma kamar ta jarirai. Ko kuma kafarki ce take kaushi a sanyin nan muna da ingantaccen mayuka Ko kuma man gyaran fata kike so da zai gyara miki jikinki a sanyin Nan ?duk muna dasu ba tare da kinsa wahala ba sannan 100% natural ne. Yar uwa idan ma bangaren samun kudi shima kike nema shima duk zamu koya miki. Kedai kawai ki mana magana domin karin bayani. https://wa.me/+23408067422528 “Shin Ke uwa ce, kina son samun kuɗi ba tare da kin fita kin bar ’ya’yanki a gida ba?” ko kuwa ke student ce kina son samun karin kudin shiga ko kuma ma dai kawai kison karin side hustle ne Tare da Oriflame, za ki iya yin kasuwanci daga wayarki a gida. Ba tare da kin fita ba. Mata da yawa sun riga sun farga da wannan Kasuwanci kuma suna moriya dashi sosai, suna making kudi daga gida, kuma ke ma za ki iya sannan bayan ribar ki zaa biyaki salary a karshen wata. ko kuma kina son yin siyayya for personal use ne ba tare da anci riba dake ba ga link nan a kasa zaki iya register da kanki it's free👇 https://shop.oriflame.com/NG-salmaibrahimismail/3M3HmQWe __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Mahaukacin gudun da yay a hanya, wanda UBANGIJI ne kawai ya tsaresa kusan ƙarfe biyu na rana ya iso cikin jejin. Tun daga sansanin farko da aka kaima hari a daren shekaran jiya ya fara cin karo da tashin hankali, dan gaba ɗaya sansanin a hargitse yake, an fasa tantunan da harsasai tako ina huji ne, ga karnuka nan kusan huɗu kwance a mace an harbesu. Shiru babu kowa alamar mazaje nakan aiki. Sansaninsu ya ƙarasa da sauri, tuni ƴan tsirarun sojojin da ke a sansanin suka tareshi tare da miƙa gaisuwa.        Ajiye mashin ɗinsa yay a wajen da yake ɓoyewa, tare da canja kayansa zuwa uniform ya zubama bindugu biyu bullets sannan ya fice. Kai tsaye inda baradan karnukansa suke yaje ya buɗesu. Ai ko suna ganinsa suka fara wani mahaukacin haushi. Bayan mota dake fake irin ta sojoji dake shiga kowane kwazazzabo saboda ƙarfin tayoyi ya buɗe musu duk suka shiga, shima ya zagaya gaba inda aka buɗe masa kusa da mazaunin driver, cikin sauri wanda zai tuƙa shin ya fice a wajen a guje zuwa ƙauyen Gangare inda su Imran suke.        Da tarin gawarwakin mutanen garin fin arba'in ya fara cin karo su Imran sun taresu a waje guda. Sai sojojin da suka samu raunuka ana duba su da wasu a jama'ar gari da suma suka sami raunukan. Garin tsit mutane duk sun ɓuya, sai su sojojin kawai da kallo guda zai tabbatar maka duk a jikace suke, wasu suna gyara bindiga, wasu kuma suna ta duba ƙananun raunikan jikinsu.        Motar na tsayawa duk suka miƙe. Tare da ƙamewa suka sara masa. Yayinda Captains ɗinsa suka iso gabansa da sauri, ilahirin fuskokinsu suma na nuna gajiyawa da damuwa.           Zak-Shadow da idanunsa sukayi ja, muryarsa cike da ƙarfi da zafi idonsa akan Major Imran Abbas ya furta, “Na bar sansani na kwanaki biyu kawai, amma ku kai sakacin da komai ya rushe haka? What the hell is this?! Are you ladies or soldiers?!”. Yanda yay maganar idanunsa na sake rikiɗewa kamar garwashin wuta yay matuƙar hargitsasu. Kowa ya kasa magana, dan babu ma mai wannan zarran bare gigin, garama Major Imran, dan haka a yanzu ma shine yay magana. Cikin matuƙar girmamawa Major Imran dake tsaye a kusa da shi jikinsa da kura, ya ce, “I'm sorry sir. Mun yi iya ƙoƙarinmu. Amma mun ji kamar makiyan suna sanin duk motsinmu ne kafin mu yi. Kamar ana gaya musu abin da muke shiryawa ne kai tsaye. Sannan hari ne na bazata. Mun rasa haɗin sadarwa tun daren shekaran jiya. An kai hari biyu lokaci guda a Arewa da Yamma. Sojojinmu sun watse, mun rasa mutane da yawa. Wannan dalilin ne ya janye hankalinmu da sansanin mu, ashe shiri ne na musamman, hari ne na kauda hankali aka kaima sansanin nan shine ainahin target ɗinsu”. Sosai zuciyar Zak-Shadow ke hanƙoro a cikin ƙirjinsa, wani irin raɗaɗi da zafi mai ƙuna yake ji a ransa. Dan ya fahimci bayanin Imran fiye da yanda yayi masa shi, tabbas yaji a ransa dole ne harin ya kasance shiryayye, sannan an tsarasa ne ta hanyar amfani da fitarsa a jejin. Sanin fitarsa kuwa dole tana da nasaba da munafiki a cikinsu. Dan Imran bazai taɓa aikata wannan kuskuren a gareshi ba. Da rinannun idanunsa masu saka tsinkewar zuciya ya juya yana ƙarema sojojin da duk suka nutsu kallo. Nazarinsu yake ɗaya bayan ɗaya. Ya daka tsawa yana zagaya tsakaninsu, yana kallonsu kamar zai cinye su da idanun. Wasu daga cikin sojojin suka sunkuyar da kai, wasu suka tsaya cak saboda tsoro.      “Wanda ya ɗauki nauyin ƙasarmu ba zai yi wasa da jinin mutanenmu ba!, dan kuwa duk soja na gaskiya ɗan ƙwarai ne kuma ɗan jalak ne. Yanda ya shiga da ƙarfin zuciya, haka yake karɓa da ƙarfin imani, sannan ya sadaukar da dukkan gaskiya. Ku sani duk wanda na gano yana fitar da wani sirri namu komai ƙanƙantarsa wlhy sai ya ɗanɗana kuɗarsa da mafi girman hukunci. Zan gano shi, ko da kuwa yana tsakanin ku kuma mafi kusa da ni. Dan haka tun kafin guri ya ƙure masa stand up! Fix this mess now!”.       Shiru kake jin wajen ya ɗauka kowanne yana kallon kasa. Har kana iya jin bugun zuciyoyinsu dake kai kawo a ƙirazansu. Ya ɗan ja numfashi mai zafi shima, yana kallon garin da ya rikice. Sai ya sake daka musu tsawa cikin murya mai zurfi, wacce ke cike da takaici da iko, “You call this a village? Pathetic!” Janye idanunsa yay daga kansu ya fara taku a hankali yana kallon gawarwakin bayin ALLAH da basu taka ma kowa ba balle zubarwa amma aka musu irin wannan kisan zalunci. A wannan lokaci Zak-Shadow ya fahimci cewa ba kawai yaƙi da makiya yake yi ba, akwai wani babban yaƙin da munafukan cikin gida da haɗarinsu yafi na waje. Cike da zafin zuciya ya juyar da kallonsa zuwa sama, inda hayaƙi ke hargitsewa cikin iska. Ya rufe idonsa na ɗan lokaci, a saman lips ya furta, (Wannan ba yaƙi da bindiga bane kaɗai. Babban yaƙi ne duhu). Idanun ya sake buɗewa a kansu ya sake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, yanzu kam cikin ɗan sauƙaƙa zafinsa amma da ɗaga murya da ƙarfin soja ya cigaba da faɗin, “Kun bar harin bazata guda ɗaya ya rikita ku haka? Kuna nunama shashashu masu dattin kai su masu ƙarfi ne akan karfinku why?! Why? My Soldiers! Why?”. Suma ji sukai gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi, kalamansa na ratsasu da sake ƙarfafasu da zaburar dasu. A tare suka sara masa tare da faɗin, “I'm sorry Sir!”. Iska ya ɗan furzar, cikin tsawa da sake zaburarwa ya ce, “Ku tattara mutane a bama ƴan uwansu su musu wanka ayi jana'iza, zamu mayar da martani kafin gari ya waye!” A tare suka amsa cikin murya mai rawar tsoro da ƙwarin gwiwa: “Yes, sir!” Shima cikin ƙara ƙarfafawar ya ce, “Move! Let’s show them what real soldiers look like!” Nan masa suka sake faɗin “Yes sir!” a tare.               ★ Zak-Shadow baifi mintuna goma sha biyar ba jiragen sama na soji masu saukar angulu suka fara sauka a kauyen, yayinda sojoji ke shiga gida-gida suna fito da mutane kamar yanda ya bada umarni, a wannan fitowar kuwa sai gashi an zaƙulo yaran Dagger har uku da suka ji rauni suka ɓuya cikin wasu gidaje.          “You see! Kuna nan zagaye da gawarwaki maƙiyanku na fake a cikin al'ummar da kuke bawa garkuwa. Abin takaici abin a kamaku da duka.         Ƙasa duk sukai da kawunansu musamman Captains da Major Imran. Yayinda shi kuma ke ƙara hasala, ji yake kamar ya dawo da hannun agogo baya ya goge wannan zuwa gida nashi. Duk da ya san zamansa a jejin bazai hana komai ba matsayinsa na mutum kamarsu, amma yana jin kamar shine sanadin komai, kamar anyi amfani da tafiyar tasa ne aka tsara komai.           An kwashe sojojin da suka raunata da wasu a mutanen gari da suma suka ji raunuka. Gawarwakin kuwa aka shiga gidaje da su akai musu wanka aka shiryasu cikin likafanin da su Zak-Shadow suka bayar. Haka aka jera su reras abin tashin hankali akai musu salla su arba'in da uku. Harda su Zak-Shadow akai sallar, sannan aka haɗasu a babban rami guda ɗaya da aka haƙa.        Tuni rahotanni sun fara fita ga jama'ar gari, dan har sallar da sojojin sukama gawarwakin sai da aka nuna. Hankali ya matuƙar tashi, zantuka suka fara kai-kawo barkatai, dana gaskiya dana ƙirƙira. Yayinda anan cikin jeji su Zak-Shadow suke sabon shiri. Dan sun bar ƙauyen Gangare bayan an zuba sojoji tako ina suka shiga ƙauyen marke da shi ma aka kaima harin duk a daren jiya. Anan ɗin ma akwai sojojin, sannan harin baiyi tsamari kamar na Gangare ba, dan ba'a rasa rai ko ɗaya ba. Wanda suka jikata kuwa an kwashe su zuwa asibiti cikin birni kamar na Gangare.       Suna cikin ƙauyen Marke suka sami rahoton gaggawa daga sojojinsu cewar a ƙauyen Bankaura an rasa yara matasa har guda hamsin da wani abu maza da mata. Cikin tashin hankali Major Imran da Zak-Shadow suka ɗauki hanyar ƙauyen Bankaura tare da wasu sojoji. Suna shigowa ana kiran sallar magriba. Sun sami garin a hargitse, iyayen ƴaƴa nata koke-koke cikin matsanancin tashin hankali. Tun ba'aje da nisa ba Zak-Shadow ya fahimci koma yaya ne ba'akai ga fita da yaran a garin ba sai dai wasu a ciki. Sannan dole-dole akwai bakin wasu a garin, dan wannan tarko ne na da ɗan gari akanci gari.      Tuni yasa sojoji suka zagaye duka ƙofofin shiga da fita na garin. Tun a daren suka fara bincika wasu gidaje daki-daki. Binciken daya sa aka fara zaƙulo wasu makamai a wani gida an ajiye ƙarƙashin gadon matar gidan. Ta kuma rantse akan bata san wanda ya ajiyesu ba, kuma ko miji bata da shi ALLAH yay masa rasuwa sai yaranta huɗu duk bama masu wani girma ba. Amma babban an haɗa da shi a yaran da aka sace dudu kuma bai wuce shekara sha biyar ba.      Kasancewar an sake haɗa musu na'urar sadarwa a yammacin yau cike da bada umarni Zak-Shadow yasa a kawo musu wasu na'urorin, dan tabbas akwai magana a cikin wannan ƙauyen na Bankaura ƙwarai da gaske. Sojoji sun cigaba da shiga gidaje, inda bincike ya ƙara tsauri matuƙa hatta inda bakai zato ba a gidan ka sai an bincika kuwa. Wannan kuma umarni ne daga oga kwata-kwata, wato Lt. Col Haysam Abdul-rasheed Shehu (Zak-Shadow), ba kuma sojojin ne kaɗai keyi ba harda baradan karnukansa da suka samu training mai wahalar gaske dako su sojojin bazasu nuna musu komai ba.... <<<<★><★>>>>         Duk wanda ya kwana ya tashi a garin bankaura in dai ya kai shekarun banbance rayuwa da mutuwa barci sai dai ɓarawo ya ɗaukesa amma bana zahiri ba. Waɗanda ma aka ɗaukewa yara sun kwana ne suna kukan tashin hankali. Da asubahi sai sojoji ne sukai kiran salla, dan babu wani mai kiran salla daya fita balle liman ko mamu. Kai sallar ma a cikin gidaje wasu basuyita ba sai da rana ta haska.           Anan kuwa mituniyarku Nimrah sarkin rikici da ire-irenta dama barcinsu suka sha hankali kwance. Tana farkawa ma ta fito tsakar gida abinta wai zata wanke ido, sai da Umma ta kamata da ƙyar ta maida ɗaki. Kuka ta fara da tirje-tirjen ita yunwa take ji, “Umma ki barni naje gidan Iya mai koko na sayo”.        Baba ne ya kamata ya zaunar kusa da shi, cikin lallashi ya ce, “Uwa kiyi haƙiri, idan yunwa kike ji a saka miki fura kisha da ƙuli, yau iya mai koko bata koko dan garin namu ba lafiya”.          Cikin rashin fahimta Nimrah tace, “Baba zazzaɓi akeyi?”.      Kafin ya bata amsa sojoji suka shigo gidan. Dan sai yanzu ne aka iso ta bangaren gidajen su. Gida ne gidan yawa, dole sojojin suka kasu kowane ɓangare.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 43_ __________________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JuUwr2QU7XMEYXZ7L7 Mmn surayya me kayan kamshi Ina amaran da uwayan gidan tou kumatso kusa Mmn surayya ta gwangwaje ku da kayan kamshi munada Turaran wuta na danal banat Kajiji Turaran kaya watau abbasiyya Kabbasa spray Humra Kwallacca Uwa uba Ina kuyarda yadda xaki hadasu Zaku iya samuna ta wannan number wayar kamar haka👇 08103143517 Ina katsina Ina aika kaya ko ina. __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Kaf gidan sai da kowa ya fito tsakar gida suka fara bincike a kowane sashe. Nimrah uwar magana sai son sakin zance take yi Umma ta toshe mata baki da hannu. Sojan dake bincike a sashensu ne ya fara fitowa hannunsa ɗauke da botiki, gaban shugaban su ya ƙaraso dake tsaye inda kowa na gidan yake...         “Mun samu bullets da yawa a nan ɓangaren”.     Yay maganar dai-dai yana ajiye bitikin gaban ogan ya fiddo jakar dake ciki. Wani irin bugawar zukata Baba da Umma suka samu a tare. Musamman da Captain Musa ya buga tsawa da faɗin, “Suwaye masu wannan sashen?”.        Rikicewa Umma da Baba suka sake yi, a take suka fara rantsuwar su basu san da jakar bama a sashen nasu. Zaram Nimrah dake kallon jakar ta ce, “Umma kwai ne a ciki fa”. Sai kuma ta zabura gaban sojan tana cigaba da faɗin, “Kai Baba ɗan sanda ƙwan Inna ne a ciki ka ɓoye kada ta gani ta dake ni”.       Yanda tai maganar ƙasa-ƙasa cikin raɗa tana cacumar jakar ta maida a botikin yasa sojojin zuba mata ido, sai kuma Captain Musa ya kai duƙe gabanta ya riƙo hannunta, jikin ƙafarsa dake tsugunne ya jingina ta, fuskarsa da murmurshi ya ce, “Ƴata miye sunanki?”.        Kai tsaye ta ce, “Zakanyar Kawu Tanimu”. Kaɗan ya rage yay dariya, dan yanda tai maganar, amma sai ya danne ya ce, “Bayan Zakanyar Kawu Tanimu sai wane suna kuma?”. Ta ce, “Naja'atu. Nimrah. Uwa. Sunana da yawa”.     Murmushi Captain Musa yayi yana jinjina kansa da shafa kanta. “Sunayen kuwa masu daɗi, kamar yanda kike mai ƙyau kema. Kince ƙwayayen Inna ne a cikin wannan jakar? Ya akai ke kika sani?”.        Inda mutanen gidansu suke ta kalla, ganin duk ita suke kallo ta kauda kanta da kai ɗan bakinta wajen kunnen Captain Musa cikin raɗa ta ce, “Jiya da Umma ta aikeni kai mata tuwo naga ƙwanta a akurkuki shine na ɗauka nasa a botikin, to sai ban ɗaukama Baba ba shima da Kawu ta dawo, shine na ɗakko duka jakar dan karta kamani, kaga ai zata iya zaneni ni kuma bana son duka”.        Kanta ya ƙara shafawa yana murmurshi, sai kuma ya miƙama sojan dake kusa da shi hannu. Da sauri ya miƙa masa waya. Danne-danne yay ya kai kunnensa yana miƙewa tsaye, hannunsa ɗaya riƙe da nata. Sai da ya ƙame kamar yana a gaban ogan da ya kira sannan ya ce, “Sir mun sake samun harsasai da adadinsu zai kai dubu biyu a wani gida”.     Banji mi akace masa daga can ba, yanda dai ya ɗan buga ƙafa da sake ƙamewa ya ce, “Yes Sir!”. Zai baka tabbacin umarni aka bashi. Daga haka ya sauke wayar ya miƙama yaran nasa. Idonsa ya maida ga mutanen gidan da sukai tsuru-tsuru cikin matsanancin tashin hankali. “Wacece Inna? Tare da iyayen yarinyar nan?”.       ALLAH sarki su Umma duk sun ƙara gigicewa, musamman Inna da al'amarin ya haɗa da tsufa, tuni ta jiƙe jikinta da fitsari, jikin sai rawa yake yi sai da Umma ta kamata. Gefe aka maida su, babu jimawa Zak-Shadow ya shigo gidan baradan sojoji kusan huɗu biye da shi. Ƙamewa sojojin sukai a tare, suka sara masa. Hannunsa dake dunƙule kawai ya ɗan miƙar alamar amsa girmamawarsu. Fuskar nan kam ba sauƙi babu sassauci. Dan su kansu mutanen gidan su Nimrah shigowar tasa sake gogitasu tayi, kai da gani kasan BARADAN MAZA ne da kansu ba saƙo ba. Duk rashin tsoron Nimrah tana haɗa ido da shi da sauri ta koma bayan Captain Musa ta ɓuya tana ɗan leƙosa kaɗan da ido ɗaya.        Zak-Shadow ya bi duk mutanen gidan da kallo irin na nazari, kafin ya ɗauke kansa ya maida ga sojojinsa, a nan ne ya hangi Nimrah dake ɓoye jikin ƙafafun Captain Musa.        Da sauri Captain Musa ya shiga yima Zak-Shadow bayanin tattaunawar sa da Nimrah cikin harshen turanci. Sai da ya gama tsaf yana saurarensa sannan ya maida dubansa ga Nimrah. Abin mamaki a karo na farko yay mata wani ɗan murmushi, sai kuma ya muƙa mata hannu da muryar lallashi ya ce, “Zo Baby girl”.        Kalmar Zo ɗin kawai ta fahimta, ta kuma san kiranta yake, dan haka ta maƙe kafaɗa alamar a'a, dan bata taɓa cin karo da mutumin daya bata tsoro da cika mata waje irinsa ba, ko babanta mutum ne mai sanyi hali da rashin hayaniya, bai taɓa dukanta ba, idan yaga Umma ma zata daketa shike cetonta. Haka ma Kawu Tanimu da kowa ke ɗaukarsa masifaffe a gidan, ita sangartata yake ko laifi tai baya dukanta. Risinawa Captain Musa yayi ya gwargwaɗa mata magana a kunne kamar yanda tai masa ɗazun. Karo na farko ta ɗago tana kallon Zak-Shadow. Sai kuma cike da ƙuruciya tace ma Captain Musa, “Da gaske baba ɗan sanda?”.         Kai Captain Musa ya jinjina mata yana murmurshi. Kallon Zak-Shadow Nimrah ta sake yi, ganin har yanzu yana murmurshi sai ta nufesa da sauri. Hannu ya saka ya ɗauketa gaba ɗayanta, ɗaukar da ta saka Umma kallonsa hankali tashe. Wani mugun waro idanu tayi a kansa, jikinta da bakinta na ɗan rawa cikin suɓucewar harshe ta ce, “Bawan ALLAH kai ne?”.       Ganin wanda take kallo take maganar yaran sojin suka daka mata tsawa, sai lokacin shi Zak-Shadow ma fahimci da shi take, karo na farko ya dubeta, kai tsaye kuwa ya gane ta, dan dama tunda ya kalla Nimrah zuciyarsa ke yi kamar yasan fuskarta, ashe kamanin mahaifiyarta ne. Hannu ya ɗagama sojan da ke mata tsawa, ita kuma duk ta firgice dan gani take harbeta sojan zaiyi. Zak-Shadow baiyi magana ba sai kallonsa daya maida kan Nimrah Ummanta kamar zatayi kuka. Cikin son kawar mata da hankali ƙasa-ƙasa ya ce, “Muje ki nuna min inda ƙwan Inna yake mu kwaso sauran ma, duka zan baku shi ke da mamanki”.        Hawayen da take riƙewa na zubo mata ta ce, “To kace Kada Baba ɗan sandan can ya bugar min Umma na”.          “Bazai bugeta ba ai”.     Captain Musa ya faɗa cike da lallashinta shima. Sun motsa zasu tafi tace ita sai da Ummanta, babu yanda suka iya da wannan mulkin mallaka na Nimrah dole akabi yanda take so. Umma ce ta kaisu har sashen Inna, Zak-Shadow kam na ɗauke da Nimrah har yanzu. Sai da suka isa sashen ne ya sauketa ya riƙe hannunta, babu ko gargada ta kaisu inda akurkukin Inna suke jere da yawa dan tana kiwon kaji, zabbi sosai har ma da agwagi.         Cikin bada umarni Captain Musa ya dubi yaransu uku dake biye da su, ai cikin sauri suka shiga bincike akurkayen ɗaya bayan ɗaya. Aiko abin mamaki daban tsoro sai ga abubuwa ana zaƙulowa. Ai tuni an shiga fancake komai dake sashen Inna, itama kuma an taso ƙeyarta. Baiwar ALLAH kuka take tana ƙari da rantsuwar bata san da wannan ajiya ba sam. Hasali ma bata san Nimrah ta ɗauki waccan jakar ba, ta dai ga an ɗiba mata ƙwai biyu, ta kuma san itace ke mata haka, wani lokacin ta kai cikin kajinsu wani lokacin tace zata soya taci.         Ba ɓangaren Inna kawai ba gidan gaba ɗaya aka shiga masa filla-filla, yayinda aka tattare mazan kaf waje ɗaya, aiko mata da yara nata kuka. Bincike yay bincike har cikin rijiyar gidan da rumbuna ba'a bari ba, an ko samu abubuwa da yawa da sukafi na sauran gidaje da aka samu, kuma abin mamaki an rarrabasu a ɓangarori da dama ta yanda baka isa cewa tunda a sashen wane aka gani ba shine ya ajiyesu. Dole dai aka tattara su Baba da ƙanensa da yayunsa duka su kusan goma sha shida mazan gidan, idan ka cire Tanimu da yay tafiya a jiya da safe kowa yana nan.       An bar wasu sojoji a gidan dan tabbas suna buƙatar tsaro, dan dole ne akwai mai alaƙa da su Dagger a gidan, idan kuma suka ji an samu kayan da ke gidan zasu biyo sahu na ganin sun ɓadda mai alaƙar da su ko ɗaukar wani mataki...       <<•>><<•>>•<<•>>          Kwanaki biyu kenan su Baban Nimrah na hannun su Zak-Shadow. Hatta Kawu Tanimu daya wuce birni anje an taho da shi. An kuma samu wasu tsirarun yara cikin waɗanda aka kwasa a garin a wani gida, sauran kuwa da alama an riga an fita da su. Har yanzu waɗan nan ƙauyukan suna zagaye ne da sojoji, musamman gidan su Nimrah dake cikin haɗari fiye da kowane gida a ƙauyen Bankaura, sai gidaje huɗu da suma aka samu makamai da yara tara cikin wanda aka sata.         Tun waccan ranar Zak-Shadow bai sake shigowa ƙauyen ba dan yayi busy sosai, bincike suke babu wasa shi da su Imran da sabbin jami'ai da aka ƙaro musu. Yayinda su Captain Musa da sauran Captains ke aikinsu bisa jajircewarsu da yaran soji tako ina a cikin jejin. Yanzu ma sunzo yin wani sabon bincike ne a nan cikin gidan su Nimrah ɗin ta hanyar zanen hannun kowa, suma mazan gidan dake hannunsu duk an ɗauka acan sansani.          Sun sami Nimrah na darzar kuka da birgima ita bazataci garin kwaki da Umma ta jiƙa ba shinkafa zataci. Umma kuwa ta zuba mata ido kawai tana kallo dan tashin hankalinta yafi ƙarfin rigimar Nimrah. Ba ita kawai ba duk macen dake gidan tana cikin tashin hankalin tafiya da mazansu da sojoji sukayi, ga yara babu su babu labarinsu dan har yanzu ba'a samo su ba. Imran sarkin son yara da tausayi ne ya zo har inda Nimrah take bori ya ɗagata cak batare daya damu da yanda tai buɗu-buɗu cikin ƙasa ba. Shi dai Zak-Shadow kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa, sai da tai wani furuci ma Umma ya juyo a karo na biyu ya ɗan kalleta.           Cikin kuka Nimrah ta sake maimaita, “Kuma sai naje na kira fatalwoyin bayan gida masu jan ido su saka ki a jakarsu su tafi dake tunda bazaki dafa shinkafa ba”.       Mutane irin su Zak-Shadow nada wata baiwa ta tsarta da saurin tsarguwa. Sannan inda suna a gaɓar aiki basa raina abu komai ƙanƙantarsa koda ga waye yazo. Imran nama Nimrah murmushi da faɗin, “Yi haƙuri Baby kada ki kira ma Mama fatalwa in dai shinkafa ce ina da ita zan baki....”        Zak-Shadow daya ƙaraso inda suke idonsa akan Nimrah da tunda ta hango yana tahowa ta ƙanƙame Imran da lafewa a jikinsa dan tsoronsa take ji. Yana isowa ta sake ɓoye fuskarta sosai a jikin Imran ɗin. Kai kawai Zak-Shadow ya ɗan girgiza, kafin ya saka hannu a aljihu ya ciro Dabino da yake yawan ci dan yana matuƙar son shi, zai iya ci miki dabino yasha ruwa matsayin abinci. Ɗan hannunta ya kamo ya saka mata, a karo na farko ta ɗan ɗago cike da shakka ta kallesa tare da hannun nata. Murmushi ya mata kamar ranar, sai ta tashi da ƙyau tana dariya cike da farin ciki.........✍🏼 Tunda aka ba Nimrah dabino aiko za'a sha labarin fatalwoyin bayan gida kenan, yau zamu san mai ɓoye fuska.🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️😂        _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 44_ __________________ *🔥 RASH BEAUTY WORLD 🔥 duniyar kayan mata masu kyau da arha ,Ina masu son kaya na kyan gani, amma basu son tsada? To, *ki daina nema!* Rash Beauty World ta zo miki da komai: *👗 Abaya masu kyau na zamani Egypt/dubai* 👜 *Bags masu kyau* *👠 Takalma masu ɗaukar ido* 💍 *Jewelry masu ƙyalli kamar na sarauta* 🍽️ *Kayan Kitchen masu amfani da kyau* *Koma da Naira kaɗan za ki yi shopping kamar sarauniya!* 👑💃 ✅ Farashi mai sauƙi ✅ Kayamasu quality ✅ Fast delivery *Shiga group dinmu yanzu kiga sabbin kaya ,Kayanmu masu kyau ne kuma farashi mai sauƙi! Kar ki bari a baki labari don samun kayayyaki masu inganci* 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/GzcU1TcAem21oJedkisrhj?mode=wwt *RASH BEAUTY WORLD – Inda kyawu da araha suka haɗu!* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Hannu ya miƙa mata shima yana cigaba da murmushin nasa dai, babu musu ta tafi wajensa. Cikin wayo da dabara ya tambayeta miye fatalwa? Yaushe ta ganta kuma?. Yo har a gayama Nimrah zance, ba'a tambayeta ba ma faɗa take balle wannan harda cin hanci aka bata. Ai tsaf ta shiga bama Zak-Shadow labarin fatalwoyin bayan gida. Koda yace zata kaishi ya gani? Sai ta bashi amsa da, “Ai sun gudu tun ranar, koda na raka su Fatsima ma da sukace zasu gani babu kowa sai dai mun samo jarkoki harda nama”.       (Anzo wajen) Cewar Zak-Shadow a zuciya. Dabino ya sake cirowa a aljihu ya bama Nimrah, sannan ya fita da ita su Imran biye da shi ransu fal mamakin al'amarin wannan yarinya. Ranar fa da taimakon ALLAH da wayon nan nata suka gano makamai na ban mamaki a gidan, yau kuma ga wata sabuwar magana da tabbas tunda sukaga oga ya maida hankali akai tana da muhimmanci. Tsaf Nimrah ta dinga nuna musu hanya har cikin gonar nan da taga mutanen ranar da take kira fatalwoyi. A kallon farko kuwa sojojin suka fahimci gaskiyar zancenta. Dan har yanzu akwai alamar mutane sun zauna. Sauran takardun nama da yaran basu ɗauka ba saboda an cinye suna wajen duk da iska ta ɗan ɗaukesu sun matsa, sai kashi a gefe dake nuna alamar na gardawane da kufan fitsari da akayi, ɓawon ƙwai da akaci da sauran sigari da akasha.       Nimrah na cin dabinonta ta nuna wani waje tana kallon Zak-Shadow. “Baba ɗan sanda, kuma anan naga wani mai irin kayan Babana zaune shima ya rufe fuskarsa saboda tsoron fatalwoyin”.        “Babanki?”.    “Eh mana”. ta faɗa cikin shiririta tana cin dabinonta.           Kallon kallo akai tsakanin Zak-Shadow da Imran. Imran ya maida hankalinsa kan Nimrah, cike da wayo ya ce, “Shine kuma baki masa magana ba?”.        “Ai tsoro naji na fatalwoyin, kuma ya rufe fuska fa, shima kaga ai tsoron su yake ji ko baba ɗan sanda?”.       “Miyasa baki faɗama mamanki ba?”.      “Na faɗa mata ita da Inna sukace na cika surutu, shine na gayawa su Fatsima sukace ƙarya nake, niko na rakosu harnan fatalwoyin kuma har sun gudu”.       Wani irin cije baki Zak-Shadow yayi, zuciyarsa na hasaso masa tabbas akwai ɓoyayyen al'amari akan mahaifin yarinyar nan. Barin wajen sukai suka koma can gidan su Nimrah. A karo na farko Zak-Shadow ya buƙaci zama da Umma dake cikin tashin hankali tunda suka fita da Nimrah, sai dai ganin sun dawo ta shiga sauke ajiyar zuciya a jajjere. Dan haka ma koda Zak-Shadow ɗin ya nema suyi magana bata musa ba. Tabarma ta ɗakko ta kawo ƙarƙashin inuwar ceɗiya dake a sashen nata. Dan haka kawai take jin girman mutumin nan a ranta tun randa suka fara haɗuwa shekarun baya. Bai musa ba ya zauna shi da Imran. Ita kuma zata zauna ƙasa yace ta ɗakko wata tabarmar. Ɗaki ta koma ta ɗakko tabarma ta shinfiɗa itama ta zauna.      Shiru wajen ya ɗauka kafin ta motsa baki cike da ƙarfin hali ta ce, “Kayi haƙuri da abinda nayi ranar, ban san kuskure bane ba. Wlhy farin ciki ne kawai ya kamani na ganinka saboda tun wancan shekarun da muka haɗu nai maka alƙawarin baka abinda na haifa sai nake yawaita mafarkinku a barci na. Kullum kuma cikin addu'ar ganin ba haifi namijin da zan baka ba nake, amma har yanzu ALLAH bai cika min burina na ba”.        Karo na farko Zak-Shadow ya kalleta, kai tsaye ya furta, “Ina abinda kika haifa wancan karon?”.      Cikin sauke ajiyar zuciya ta kalla Nimrah dake wasa da ƙasa gefensu kaɗan, “Itace waccan da kuka fita da ita ɗazun”.       Daga shi har Imran kallon Nimrah sukai suma. Imran dake murmushi ya ce, “Masha ALLAH, ALLAH ya albarkaci rayuwarta. Minene sunanta?”.       “Naja'atu, amma muna kiranta Nimrah saboda sunan mahaifiyar maigidana ce.”      Ɗan huci Zak-Shadow yayi kaɗan, ƙasa-ƙasa ya ce, “ALLAH ya rayata”. Sai kuma ya cigaba da faɗin, “Ranar tace miki taga fatalwa a bayan gida, miyasa baki saurareta ba?”.           “Nimrah nada surutu sosai, shiyasa nakan ƙwaɓeta da irin waɗan nan abubuwan saboda tarbiyyarta matsayinta na mace”.      “Hakan ba laifi bane, amma yana da ƙyau idan yaranmu sukazo mana da maganar abinda ba kasafai ake zancen sa a cikin al'umma ba mu basu lokacinmu, idan na gyara ne mu gyara musu, ko muyi musu ƙarin bayani ta yanda zasu fahimci abin a yanda yake. Idan ba haka ba zasuje su faɗa a inda bai dace su faɗa ɗin ba, maybe ya cutar da su, ko kuma ya zama na cutarwa ga kowa. Yanzu kamar ita zancen fatalwa data kawo miki mutanen da sukai muku ɓarna da ɗibar yaranku ta gani a wannan ranar, da kin saurareta da kin fahimci abinda take magana akai, koda bazaki iya ɗaukar mataki ba zaki iya faɗawa maigari, kinga kin taimaki garinki da al'ummar garin. Saɓanin haka kuma kinga sakamakon daya kawo.”         Ba ƙaramin tashi hankalin Umma yay da bayanin Imran ba. Ta zubama Nimrah ido da har yanzu ke wasa hawaye na silalo mata. Imran ya sake katseta da faɗin, “Minene sana'ar mahaifinta?”.         “Manomi ne kamar sauran mazan garin, sai sana'ar kifi da yake yi kuma”.      “Ɗanye?”.    “Eh, harda soyayye, a can yara yake zama, duk zagayen ƙauyukan nan shi kaɗai ne ke wannan sana'ar shiyasa yake samun kuɗi sosai dan wajensa ake zuwa a saya ƙauye-ƙauye dake kusa damu”.          “Ƙarfe nawa yake fita da kayan sana'ar tasa?”.     “Sai da yamma bayan la'asar. Dan haka yake jimawa bai shigo gida ba sai irin sha biyu haka, wani lokacin kuma baya kaiwa musamman idan Tanimu ƙaninsa na gari, dan yakan amsheshi shi kuma ya dawo gida”.         “Shi Tanimun miye sana'arsa?”.    “Shima yana noman ne, amma yana fita balaguro cikin birni. Yaro ne mai ƙoƙari sosai, dan kusan cigaban dake yankin ƙauyukan nan namu duk da taimakonsa da tsayawarsa aka samesu.”       “Kamar mi da mi?”.   “Kamar makarantu, asibiti, wutar lantarki. Shi ne yayta wayar da kammu har muka saka yara a makaranta musamman mata da mukaƙi da farko.”          “Idan yaje birni yakan daɗe ne?”.     “Baya wuce wata uku yake zuwa gida yay kamar sati biyu ko uku sai ya koma”.       “Shida mijinki waye yafi wani kuɗi?”.           “To bana ce ba, dan shi samun namiji ba kai tsaye mu muke iya ganewa ba anan. Amma su duka kowa na samu gwargwadon iko, sai dai shi Tanimu mutum ne mai hidima ga ƴan uwansa gaskiya. Shi ko mai gidana in banda mu da Innarsa babu nauyin kowa a kansa”.        “A wannan zuwan da Tanimu yayi gida kwanansa nawa a garin?”.      “Bai wuce sati ɗaya ba”.   “Yana taya maigidanki zama wajen kifinsa kamar yanda ya saba?”.     “Eh yana taya shi”. “Kwana huɗu da suka wuce ina maigidanki ya je?”.           “Yaje Gangare ɗaurin auren ƴar wani abokinsa”.     “Ƙarfe nawa ya dawo?”. “Da daddare ne sosai gaskiya dan har munyi barci ma?”.        “Tunda kika aureshi, kin taɓa kama shi da wani laifi?”.      “A'a gaskiya, shi mutum ne mai haƙuri da rashin son magana. Tun a rayuwar samartaka ma ban taɓa jin ance ga abokin faɗansa ba. Koni aka ɓatawa rai na tashi da nufin yin faɗa ko ramawa yakan zauna yayta bani haƙuri da hanani.”        “Kasancewar sana'ar dare yake yi yana zama a gida tare da ku ya yini?”.     “A'a gaskiya, yin haka zai iya zama abin magana mu anan balle gidan yawa, yakan fita kamar kowa amma yana shigowa gida musamman lokacin cin ɗumame da kuma in an gama abincin rana”.       “Zamu iya ganin kayan sakawarsa?”.       Ɗan shiru tayi a karo na farko ta kasa amsa Imran a wannan karon, sai da Zak-Shadow ya ce, “Karki damu ba wani abu bane”.      Ajiyar zuciya ta ɗan sauke. Kafin ya miƙe ta shiga ɗaki, babu jimawa ta fito da akwatin ƙarfe babba. A gabansu ta ajiye sa, Imran ya ce ta buɗe da kanta. Buɗewar tayi tana fiddo kayan ɗaya bayan ɗaya, gaba ɗayansu basufi kala bakwai ba, duk yadi ne irin na mai ƙaramin ƙarfi. Bayan ta gama gaba ɗaya yace ta maida, ta kawo masu datti suma. Haka ta miƙe ta ɗebo su, suna ɗaure a cikin zaninta, harda nata dana Nimrah. Nashi suka saka ta ware, nata ma haka, sai na Nimrah da sukafi duk nasun yawa.        “Zaki iya lissafa min ranakun da duk kuka saka waɗan nan kayan?”.       Da yake basu da yawa sai tace zata iya. Da nata ta fara, sai nashi. Ta ɗakko kala na huɗu tai ɗan shiru tana kallon kayan, a karo na farko ta kallesu, sai kuma tai ƙoƙarin ajiye kayan batare da tayi magana ba”.         “Miyasa zaki ajiye?”.     “Na manta ranar daya saka waɗan nan gaskiya, shiyyasa zan ajiye gefe kozan tuna kafin na gama”.        “Ya yi cigaba”.   Cigaba da lissafa sauran kala ukun da suka rage tayi. Imran zai yi magana Zak-Shadow ya katsesa ta hanyar yi mata nunin ta ɗauki kayan ta koma da su. Ƙoƙarin kwasa tai harda wanda ya ware ɗin nan yace ta barsu. Haka ta barsu ya kwashe sauran. Tana barin wajen Zak-Shadow yay kiran Nimrah. Da gudu kuwa tazo, ya kama hannunta ya zaunar a kusa da shi, sai kuma ya jawo kayan baban nata gabansu ya ajiye.           “Kalla wannan kayan na waye?”.      Cikin wasa tace, “Babana”. “Yaushe ya saka su a jikinsa?”.     “Na manta”.   “Tuna dai, kamar na ranar da kikaga fatalwoyi ne a bayan gida fa”.      Kayan ta zubama ido kamar mai son tuno haka. Sai kuma ta kalli Zak-Shadow. “Eh-eh irinsu ne wanda ya rufe fuska ya saka”.      “Dami ya rufe fuskar?”.   “Bansan sunan abin ba, amma Babana na saka irin shi shima”.      “Jeki ɗakko min na gani”.   Da gudu ta tashi zuwa ɗakinsu. Umma dake tsaye tana kallon su hankalinta ya fara tashi, zata bi bayan Nimrah Imran ya hanata. Kusan mintuna uku kuwa sai ga Nimrah da hiramin Babanta ta dawo. Karɓa Imran yayi, ya ce, “Kin tabbatar shine wannan?”.      Kai ta jinjina musu kawai. Imran ya kalla Zak-Shadow, kai ya jinjina masa. Shima sai ya jinjina nashi yana ɗaukar kayan ya fara bincikar aljihunnan jikin wando da rigar. Ana farko ya ciro kuɗi ƴan ɗari biyar bandir biyu sabbi, ɗayan ya ciro wata takarda ƙarama a nannaɗe. Gaban Zak-Shadow ya ajiye kuɗin, sannan ya warware takardar.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 45_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Layukan waya ne a ciki har huɗu. Suma ajiyesu Imran yayi, sai kuma ya juya yana kallon Umman Nimrah dake kallon kuɗin da mamaki, dan ita kam bata san da su ba sam, kai kayan ma ta kasa tuna randa mijin nata ya sakasu a jikinsa....        “Ko zamu iya ganin wayarki?”.     Ajiyar zuciya ta ɗan sauke na katsewar tunaninta, ta girgiza masa kanta. “Banda waya”.         “Mijinki fa?”.     “Shima baida ita, sai dai ranar yake cemin yana son ya saya mana ni da shi, zai ba Tanimu ƙaninsa idan zai dawo sai yazo mana da ita. To ban sani ba ko ya ba Tanimu sautin a randa zai tafi”.        “Kota wani baki taɓa gani a hannunsa ba?”.     “Eh to sai ta matar Tanimu, itama kuma sai in Tanimun ya kira dan suyi magana take kawo mana, ta kuma kaima Inna. Daga ba wannan ba ban taɓa ganinsa data kowa ba, kai gidan nan ma duka daga Tanimu sai matarsa keda salula”.        Zaki iya faɗa mana abokan mijinki da kike yawan ganinsu tare, har suke zuwa gidan nan”.            “Abashe ne kawai abokinsa. Kuma ALLAH yay masa rasuwa watanni goma sha ɗaya kenan. Kowa da shi kawai ya sanshi tun yana saurayi”.      “Ina ne gidan Abashen?”. “Da nan makwaftanmu ne, amma yayi sabon gida sun koma can farkon gari shekara uku kenan?”.         Kai kawai Imran ya jinjina mata, sai kuma ya juya yana kallon Zak-Shadow da duk ke nazartar tambayoyin da Imran kema Umman Nimrah da amsar da take bashi. Canja harshe Zak-Shadow yayi, cikin harshen turanci yace, “Dole a sake sabon bincike a gidan nan. Kayi kiran Captain Musa yanzun nan”. Daga haka ya miƙe ya fita yana latsa wayar hannunsa alamar zai yi magana da wuni...       Kandala matar Tanimu dake laɓe tun shigowar su Zak-Shadow a bayan katangarta data raba sashensu dana su Umman Nimrah na ganin su Imran sun fita itama tabar wajen saɗaf-saɗaf. Sai faman tafa hannaye take da riƙe haɓa irin na gulma. Magana ce ke tsikarar mata uwawu gashi babu damar fita kai gulma maƙwafta, ta gagara zaune ta gagara tsaiwa. Zuwa can dabara ta faɗo mata, wata ƴar dusa data shanya akan rumfar dabbobinta ta ɗauka ta juye a roba. Sashen ɗayar facalarsu da mijinta da su Tanimu ke uba ɗaya ta nufa. Tun daga farkon shiga ta ce, “Ramma ga dusa, naji kina jaje ɗazun na gagara tashi ne na miƙo muki ita tun ɗazun ina fama da ciwon kai”.      Ramma da tasan batai jajen dusa ba ita dai ta buɗe baki zatai magana. Da sauri Kande ta ƙyafta mata ido alamar tai shiru. Sai ko ta wayance itama ta ce, “Kai aiko na gode. Tun ɗazun dabbobina ke kuka na rasa tudun dafawa”.           Ƙasa-ƙasa Kande tace, “Ramma akwai matsalafa a gidan nan”.      “Matsala ai dama cikinta muke Kande. Yau kwana biyu mazanmu na can a hannun sojoji”.        “Ai inaga gaskiya ta kusa bayyana, ALLAH ya kusa ƙwato mana su. Tun ɗazun wannan bahagon sojan da kallon fuskarsa kawai tashin hankali ce yazo gidan nan. Naga ya ɗauki waccan yarinyar ƴar gori ya fita da ita, tunda kuma suka dawo suka tsare uwarta da tambayoyi tana basu amsa, har kayan sakawar Yaya mai kifin aka sakata ta ɗakko suka zazzage, naga sun fiddo kuɗi sabbi fil ƴan ɗari biyar, da layin waya. Kin kuma san bashi da waya ai. Gashi can sun sake fita dai....”         Ramma dake zazzare ido ta ce, “Mun shiga uku Kande, kar dai ana zaton wuta a maƙera a ganta a masaƙa”.      “To aiko da alama can ɗin take. Yo ai biri yayi kama da mutum, ki kula a kwanakin nan basa shan koko kullum sai shayi da burodi, ranar ƴar naba su Laminu labari wai sunci tsire da daddare babanta ya sayo. Ke dama ki kiyayi mutum sumu-sumu wlhy abin tsoro ne. Randa Tanimu zaiyi tafiyar nan da daddare yake gaya min ya ranci kuɗi a wajensa har dubu arba'in, naita mamaki har ina jin haushi, ashe-ashe kuɗin bana ALLAH bane”.       “Kande ni abinda ban gane ba anan. Kenan dai shine ya kawo mana wannan masifar da aka samu shekaran jiya cikin gidan nan?”.           “A to ke da mi kike tunani, shine mana. Dan bala'i ya rasa inda zaije ya ajiye sai ɗakin tsohuwarsa, yanzu da wannan abun daya kashe mutane a Gangare ne a ciki tunda ance fashewa yake shi ai kinga shike nan ya kasheta ko yama ɗiyanta asara. Maganinta itama, badai tafi sonshi da ƴarsa ba kamar shi kaɗai ta haifa, mai mata wahala daban wanda take riritawa daban”.      Salati kawai Ramma take tana ƙarawa, dan maganar ta girgizata matuƙa. Kasancewar ita babu wani jin haushin su Umman Nimrah a ranta ita tausayinta ne ma ya kamata wlhy. Ka daɗe baka haihu da mutum ba sanda kuma ALLAH ya fara baku ace ga wannan masifa mutum nayi, ga yarinya mace, idan wannan magana ta fita wazai aureta a wannan garin basu da ba'a manta abin gori.... <<<<<•>>>>>       A ɓangaren su Imran mintuna talatin ba'ai ba Captain Musa ya iso da wata tawagar soji, da karnuka. Sai da suka miƙa gaisuwa ga Zak-Shadow dake a ƙofar gida har yanzu yana waya sannan suka shiga cikin gidan. Kamar yanda ya bada umarni haka sojojin nan keyi, bincike ake mai zafi da yafi na farko har a jikin bango da ramin ɓeraye ba'a bari ba. Kai saida takai hatta ledar ƙasan ɗakin Umman Nimrah sai da aka kwaye gaba ɗaya, da ledar sama da akai kamar silin. Cikin filos ba'a bari ba. A ɗayan ɗakinsu da take ajiye-ajiyen kayan aiki da icce sai randunan ruwa sai da aka fidda komai. Wani guri ne ya nuna kamar an tona aka maida ƙasa aka rufe Zak-Shadow yace a tone shi shima. Haka suka shiga tonawa kuwa, abin mamaki sai ga tunkunyar ƙasa, ana buɗe murfinta sai ga kuɗi masu yawa a ciki kusan cike. Nan fa aka shiga fiddosu bandir-bandir sabbi ƙal.  Hakama a cikin ɗakin Umma an ƙara samo kuɗi cikin katifar rimi ta gadon da yake kwana, harda wayoyi har biyu. ALLAH sarki Umma zuwa yanzu kuka take sosai, hakama Inna sai surutai take kamar wadda ta zautu. Tana son baban Nimrah sosai fiye da sauran yaranta musamman yanda bashi da yara sosai ɗin nan. Duk da kuwa Tanimu yafi ƙyautata mata da yi mata hidima a rayuwa, shi baƙin halin matarsa ne yasa bata sakewa da shi, itako Umman Nimrah tana mata abu kamar ƴarta. Idan ma ta nema abu Baban Nimrah ɗin bai mata ba ita takanyi a madadinsa batare da Innar tasan ba shine yayi ɗin ba.      Bincike na biyu shine gidan abokinsa mai rasuwa Abashe, inda su Zak-Shadow suka gane shine gidan matar nan mai yara marayu da suka fara samun abubuwa tace ita kuma bata san da su ba. Ashe kuwa da gaske bata sani ɗin ba. Dan sai yanzu ne da zance ya kai ya kawo akan lamarin Baban Nimrah ɗin ta tuna ya kawo musu hatsi kusan sati ɗaya kenan, da yake tunda mijinta ya rasu haka yaketa ɗawainiya da ita da yaran babu gajiyawa, randa ya kawo hatsin yace babban yaronta da yaci sunansa suke kira da Aboki yaje ya amso musu kifi. Tabbas taga yaron nata da bako bayan ledar kifi, koda ta tambayesa sai yace mata Baba ne ya bashi ajiya yace zai amsa ranar kasuwar Gamau. Itako bata maida hankalin sanin minene a ciki ba yaron ya shiga da bakko ɗin ɗakinta ya ajiye. Bako ta sake tunawa ba sai yanzu ma.       Gari fa ya ɗauki sabon tashin hankali. Dan duk wanda keda alaƙa da Baban Nimrah sai da aka kamashi a wannan yinin, hatta wajen kifinsa da inda yake zuwa sari a can cikin local government ɗinsu sai da aka bibiya. Zuwa dare sai ga ƴan uwansa na nan gidansu duk an sakko, sai dai banda Tanimu dan basu gama bincike a kansa ba. ALLAH sarki Umman Nimrah idan ka ganta abin tausayi, wuni ɗaya duk ta susuce ta fita a hayyacinta. Dan zuwa dare ma zance ya gama baje gari dan ma akwai sojoji da sukai musu takunkumin hana yawo barkatai ƴan uwanta sukazo suka tafi da ita harda Nimrah bisa umarnin mahaifinta dattijon arziƙi, babban malami ne a yankin ma ba garin kawai ba, dan bazasu so abin kunyar da mijinta ya aikata ya shafeta ba, musamman da matan gidan suka fara mata habaice-habaice da yada magana a kai-kai ce bisa jagorancin Kande matar Tanimu data fara yaɗa maganar, dan ma dawowar mazan gidan ya sata komawa tai laƙwas ganin babu nata mijin itama....   >>>>>><<<<<<<      A sansanin su Zak-Shadow cikin tantin Imran da bai cika zama ba ake tsare da su Baban Nimrah, zuwa safiya ake son fita da su daga jejin zuwa birni, ana ƙara tantance wanda basu da alaƙa da al'amarin ne musamman waɗanda aka tattaro yau da rana. Kwanaki na uku kenan bayin ALLAHn nan su Zak-Shadow basuyi barcin rabin awa ba. Yaransu da manyansu tsaye suke akan ƙafafunsu. Kai ko abincin kirki basa ci sai ƴaƴan itatuwa. Duk mai imani ya gansu sai ya tausaya musu.         Amma a haka muda muke kwance a gidajenmu muci mu ƙoshi mu kunna tv muyi kallo, mu hau gado muyi barci har muke iya zagin jami'anmu da kallonsu muce basa aiki. Musani ganin jami'an dake ofisoshi zaune, da wanda ke yawo akan hanya suna nuna wasu halayya mara ƙyau bashike nufin mun rasa zakaƙuran jarumanmu dake cijin jeji daban-daban suna gumiruzu akanmu ba. Akwai irinsu Zak-Shadow da su Imran da yawa da bamu san da su ba, sai dai ALLAH ya saka musu da alkairi kawai zamuce.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 46_ __________________ https://wa.me/+23408067422528 Kina son rage kiba ba tare da kin daina cin abunda kike so sannan ba tare da kinyi gudawa ba? To kimin magana domin samun hanyoyi da zaki rage kiba ba tare da kinsa wahala ba. Ko kuma matsalar gashi ce ke damunki, ko rashin tsahon gashi ne, shima muna da solution dinsa. Ko kuma fatar ki tana lalacewa ne a sanyin? Muna da ingantaccen man da zai gyara miki kafafunki ko kuma kamar ta jarirai. Ko kuma kafarki ce take kaushi a sanyin nan muna da ingantaccen mayuka Ko kuma man gyaran fata kike so da zai gyara miki jikinki a sanyin Nan ?duk muna dasu ba tare da kinsa wahala ba sannan 100% natural ne. Yar uwa idan ma bangaren samun kudi shima kike nema shima duk zamu koya miki. Kedai kawai ki mana magana domin karin bayani. https://wa.me/+23408067422528 “Shin Ke uwa ce, kina son samun kuɗi ba tare da kin fita kin bar ’ya’yanki a gida ba?” ko kuwa ke student ce kina son samun karin kudin shiga ko kuma ma dai kawai kison karin side hustle ne Tare da Oriflame, za ki iya yin kasuwanci daga wayarki a gida. Ba tare da kin fita ba. Mata da yawa sun riga sun farga da wannan Kasuwanci kuma suna moriya dashi sosai, suna making kudi daga gida, kuma ke ma za ki iya sannan bayan ribar ki zaa biyaki salary a karshen wata. ko kuma kina son yin siyayya for personal use ne ba tare da anci riba dake ba ga link nan a kasa zaki iya register da kanki it's free👇 https://shop.oriflame.com/NG-salmaibrahimismail/3M3HmQWe __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........*_01:am_*      Zama a duhu tamkar ɗabi'a ce ta wannan ƙungiya, musamman a lokacin yin meeting. A yau ɗin ma da zaman nasu ya kasance na gaggawa ba kowa da kowa bane a falon. Ogansu ne kawai sai Black Spider da yaronsu Dagger. Dagger bawani muhimmanci ne da shi a wajensu ba face KAREN FARAUTA. Dan kuwa suna kwance ne yana musu yaƙi da horar da yaran mutane a tafarkin hatsabibanci. Shike da yaran dake musu haƙar ma'adanan yankin Bankaura da sauran ƙauyukan wajen da adalinsu suka samar da ƙungiyar ga'addaci da zata janye hankalin mutane daga ma'adanan saboda kafawa da tsarewar jaruman jami'an ƙasar sukayi irin Zak-Shadow. Kuɗi kam suna sakarma Dagger ta yanda yake sake ruɗuwa da zama a rufewar idon sai da ƙasarsa da yankinsa hankali kwance batare da jin yana aikata kuskure ba ma. Shima kuma yana amfani da kuɗin wajen ɗibar ƴaƴa a cikin tafiyar cikin sauƙi saboda ƙarancin tallafi daga matasan ta hanyar ayyukan yi akoda yaushe.       Ogan nasu daya kasance bamai yawan magana ba sai baƙar mugunta taf cikinsa ya wani zuƙi ƙaton sigarinsa yana ma Dagger wani kallo mai kama da raini ƙo ƙasƙanci ne ma oho masa. Amma kasancewar eyeglass ne a idonsa shi Dagger ba gani yake ba. Cikin harshen da suke magana da shi cike da isa da ƙasaita ya ce, “Kana nufin kazo gaya mana bazaka iya ba saboda banzan can ya kama maka yara?”.        “Ko ɗaya sir! Ai ko kura ta rame tafi ƙarfin wawason namun jeji. Waye wani Zak-Shadow ballantana yaransa. Ina son naji ne ko akwai hanyar fitar da su a hannunsa? Ko kuma mu kashe su kawai kafin ya kaisu cikin birni kamar yanda yake shiri, amma ku sani dukansu da aka kama sunada matuƙar amfani a tafiyar mu, musamman ma mutumin nan na Bankaura, dan mutumin nan yanada manyan sirrikanmu da bani da tabbacin idan yaji wuya bazai tona ba kamar yanda yay sakacin da ƴar iskar matarsa ta buɗe mana aiki. Na matar tasa ma bai ɓata min rai ba, wannan shegiyar yarinyar mai kama da ƴar aljanu, tun randa ya haɗu da su Ganuwa ashe ƴarsa ce ya ɓoye musu......”         “Kaga hakan na nufin da saninsa tazo wajen....”     Black Spider ya faɗa cikin fushi da ɓacin rai.        “Bana jin haka oga, domin kuwa Ganuwa ya tabbatar a bazata yarinyar tazo musu. Kuma yana ganinta ya rufe fuska. Sai dai ina yin zargi ɗaya, uwarta ce ta turota danta tabbatar mata shine, dan bana raba ɗayan biyu tare yarinyar take da uwarta ita ta laɓe.”     “Idan ko haka ne baka buƙatar wani umarni anan. A kashe matar tasa da ƴar gaba ɗaya. Shima bama buƙatarsa ya gama aikinsa”.            “An gama Sir! Dama wannan umarnin kawai nake jira. Sai dai a majiya mai ƙarfi na samu labarin ɗazun iyayenta sunzo sun ɗauketa a gidan. Tana gidansu. Babanta kuma shine hatsabibin malamin nan daya hana mu rawar gaban hantsi a farko.”      “Duka ahalin nata a kashe su. Dan bamu zo ƙasarku dan wasa ba, buƙatarmu ta lokaci ce muna kammala ɗiba zamuyi gaba. Duk wanda yace kuma zai tari gabanmu koda uban waye sai mun kawar da shi ya koma ƙasar takawarmu a hanyar samun cikar wannan burin. Kar su wuce gobe...”      Yay maganar ƙarshe da umarni yana barin falon gaba ɗaya, ba kowa bane face oga kwata-kwata. Shima miƙewa Black Spider yayi yabi bayan oga, hakan ya tabbatar ma da Dagger sun gama da shi. Ji yay kamar ya harari bayansu, amma ya kanne. Sai dai ƙasan zuciyarsa yana jin wani nauyi da shi kansa yakan kasa tantancewa. Shin ɗan sauran ɓurɓushin kishin ƙasar ne a wajen kokuwa takaicin dukiyar da mutanen ke samu ne su ana ɗan tsakura musu ke son saka masa jin hassadarsu... <<•>>•<<>>•<<•>>        Asubar fari wani irin hayaƙine ya turniƙe illahirin garin Bankaura da in kai wasa ganin gabanka ma zai iya maka wahala. Ga wani irin rigugi da ke tashi mai matuƙar saka razani a zukata duk wani mai rai. Kai da kaji amon kasan sautine dake fita daga bindigogi ko wasu nau'in makamai masu fashewa. Kasancewar asubahi ce barcin da mafi yawan mutane basa samu saboda tsoro a farkon dare yanzu gabanin asuba duk ya kadasu sun ɓingire. Hakan yasa shiru yayi yawa tako ina gaba ɗaya jejin ya ɗauki sautin da har saƙon ya isa cikin kunnuwan su Zak-Shadow.        Ai ko shine ya fara fitowa a tantin da ake tsare da su Baban Nimrah sakamakon tuhumar da ya saka ake musu tun daren jiya, dan yafi son samun dukkan bayanan da yake buƙata kafin ya miƙasu hannun hukumar bincike gudun samun matsala. Jin fa al'amarin na gasken-gaske ne dan har wani jijjiga jejin keyi saboda azabar fashewar gurneti ya zabura cikin wani irin rawar jikin jarumta. Kafin cikin gigitacciyar muryarsa ya furta, “Are you soldiers or a bunch of jokers?!!?”.       Gaba ɗaya sansanin ya amsa da faɗin, “No, Sir! We are Soldiers, Sir!!”.     Cikin ƙanƙanin lokaci wajen ya rikice da ƙarar gudunsu ta yanda suke rige-rigen shigewa motocin yaƙi, wasu dokuna, wasu mashina. Wasu kuma suka ƙara zagaye tantin da su Baban Nimrah suke dan kar ya zaman irin takun ranar ake son maimaita musu. A janye hankalinsu can gaba ɗaya nan kuma aka musu kwaf ɗaya. Saboda sun kula koma wace ƙungiyace wannan da ƙarfinta take.        Sojojin na isa garin ya ƙara hargitsewa da musayar wuta, tsawon awa ɗaya a wannan yanayin kafin sautin ya fara lafawa sai kukan yara da mata ya fara fitowa..         A dai-dai lokacin jirage masu saukar angulu na soji suka fara isowa suma. Cikin ƙanƙanin lokaci suka zagaye ƙauyen musamman ta yankin da abin yafi ƙarfi. Sosai tsakkiyar gidan Malam Hamisu mahaifin Umman Nimrah yayi kaca-kaca da jini, yayinda gawarwaki kusan biyar na maza ke kwance. Ta gefe kaɗan ƙyaƙyƙyawan dattijo ne mai cikar kamala ma'abocin furfura da dogon gemu durƙushe a ƙasa da Handcuffs a hannunsa da aka maida ta baya wani soja na ƙoƙarin kunce masa amma da alama al'amarin yaci tura dan kamar an kulle handcuffs ɗin da wani kwaɗon sirri. Idanu kawai kyakkyawan tsohon ya zubama gawarwakin ƴaƴansa da su Dagger suka kashe yana kallo hawaye na bin kamilalliyar fuskarsa ta girma da kwarjini. Ta gefe kaɗan matane da yara da zasu iya kaiwa adadin talatin da ɗoriya. Suma dai kukan suke sosai wasu har sunayi tamkar zasu shiɗe.         Fitowar Zak-Shadow daga cikin ƙaton gidan na ƙasa mai sassan da yawan gaske da zai tabbatar maka family house ne na waɗan nan mutane ya saka sojin dake zagaye da mutanen shiga sara masa cikin nuna girmamawa a garesa. Kansa kawai ya jinjina musu yana yamutse fuskarsa da tai kaca-kaca da jini ta yanda ko iya gane ainahinsa ba'ayi sosai. Hakama farar rigarsa da wandonsa na sojoji duk sun ɓaci. Cikin bada umarni yay nuni da gawarwakin dake a yashe a ƙasa tare da tsohon nan.        Da sauri ɗaya daga cikin yaran nasa ya furta, “Sir za'a fara gaba da su ne?”.      Maimakon yin magana yanzun ma kansa kawai ya jinjina. Basu damu ba, domin sun san shi mutum ne mara son yawan magana. Sai da suka gama kwashe gawarwakin da aka saka a cikin wasu ledoji sannan aka samu nasarar kunce handcuffs ɗin hannun dattijon nan. An kama shi da nufin miƙarwa dan jikinsa rawa yake a bazata kawai ruwan harsasai suka fara sauka a jikinsa. Gaba ɗaya wajen ya rikice, Zak-Shadow da yaransa suka fara dube-duben ta ina harsasan ke fitowa, yayinda wasu sukai kansa akai ƙoƙarin riƙoshi da hanashi kaiwa ƙasa daya tafi zai zube.      Kukan yaran nan da mata ne ya ƙara ƙarfi. Yayinda wasu a cikinsu suka miƙe da gudu zasu nufesa, amma sai sojojin suka hana hakan ta hanyar shan gabansu. Dai-dai nan wani taƙadari cikin yaran Dagger ya buɗe ƙaton dirom ɗin dake tsakar gidan ya fito yana dariya. A take sojoji suka ɗana bindugu, masu tunanin yin fata-fata da namasa har sun ɗana kunamin bindugun nasu ya turo Umman Nimrah gabansa bindiga a kanta daya ɗora mata. Sai lokacin su Zak-Shadow suka fahimci shine yayi harbin ta cikin drom ɗin kenan.       Cikin bada umarni da kaushin harshe Major Imran ya furta, “Idan kana son tsira da sauran abinda ya rage maka na numfashi ka ajiye bindigarka”.      Dariyar shaƙiyanci yayi, ga fuska ya shafe da baƙin abu ko gane kalar fatarsa balle kamaninsa ba'a iya yi. Da yanayin shaƙiyanci ya amsa ma Imran da, “An gaya maka goro na kasa a duniyar da har nake son ya ƙare na ƙirga riba da jari balle na damu da rayuwata. Kama bar wahalar da kanka, jinin wannan matar halattacene a wajena dan koba komai zanyi jihadi kashe mata mai tona asirin mijinta.”      Ya faɗa yana ƙara danna kan bindigar a kan Umma dake hawaye tana kallon Zak-Shadow da zuciya ta kume ƙirjinsa, yanda kawai zai fasa kan tsinanne yake yi. Aiko tamkar wani abin siddabaru babu ma wanda ya kula da sanda ya ja kumar bindigar hannunsa ƴar mitsitsiya balle ɗagawar hannunsa sai saukar Bullet akan shegen, dan shi ɗin ƙwarraren maharbi ne kowa ya sani kuma. Kasancewar shi kuma ɗan iskan ya riga ya ɗana kunamar bindigar hannunsa a wuyan Umman Nimrah tun ɗazun harbin da akai masa ya tafi baya sai kawai yatsarsa ya motsa harsashin ya fita ya shige jikinta.       Kusan tare Zak-Shadow da Imran suka zabura kanta. Sai dai kafin su dire ma ita ta dire a ƙasa rikica. Cikin matsanancin gigita Imran ya riƙota yana jijjigata da gwala kiran sunan Captain Musa. Murmurshi tayi mai ɗaci da ciwo hawaye na zubowa ta gefen idanunta dai-dai da malalowar jini a hannun Zak-Shadow da ya kai hannu shima zai riƙota Imran ya rigashi, sai ya kasa ƙarasawa da hannun kuma ya kasa janyewa. Da ƙyar ta iya sake yin wani murmushin tana juya idannunta da ƙyar akan Zak-Shadow... A dai-dai nan shima munafukin nan mafi kusanci da Zak-Shadow ya katse videon daya ɗauka a wayarsa yana ɗan sakin munafukin murmurshi nasara guda biyu..........✍🏼           _Wato a duniyar nan ALLAH ka rabamu da maƙiyi mai fuska biyu. Kunga wanda zai nuna maka soyayya a gaban idonka a bayan idonka yafi kowa ɓataka da aibantaka ba ƙaramin azzaluminka bane. Wannan shegen na tsaneshi tun kan aje ko ina. Duk wanda yake tare damu a zahirin rayuwa da baɗini da wata manufa ya rabbi ka rusashi kafin shi ya ruguza mu😭😭🙏._ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 47_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Kai Zak-Shadow ya shiga girgizama Umman Nimrah idanunsa na wani irin jirkicewa. Ya motsa lips zaiyi magana ta girgiza masa kai itama.. “Karka damu, a yanzu nafi buƙatar mutuwa akan rayuwar da zata cigaba da tunamin wanene mijin aurena. Rayuwar da zata cigaba da tunamin rasa ƴan uwa biyar da mahaifana a dalilin mijin aurena. Na godema ALLAH da ban koma gareshi ba sai da nasan wanene mijin aurena. Ba zan aibanta shi ba, amma ni da shi da ƴarmu tilo zamu haɗu gaban mai rarrabe ayyuka da gaskiya. Ban samu cikar burin haihuwar ɗa namiji da nai alƙawarin baka ba, amma zan damƙa maka AMANAR ƴata ɗaya tilo da kaf duniya dakai kaɗai na yarda. Dan ALLAH ka raineta tamkar yanda nake fata rainonta, ka bata ilimin addini dana zamani. Ka raini zuciyarta da jarumta irin taka da tausayi da hidima ga al'umma. Ko da wasa kada ka sanar mata ainahin halayyar mahaifinta, dan Alhamdullah Babana ya bata rubutun mantawa da shi a zuciyarta na har abada, ina kuma roƙon yay mata tasirin da bazata taɓa tunashi ɗin ba, amma ko ya cigaba da rayuwa har lokacin girmanta, ina son ta tashi da sanin shi mataccene tun tana da ƙuruciya, ma'ana ka sanar da ita ita ɗin marainiya ce gaba ɗaya ta rasa uwa da uba tun tana ƙarama. Sannan bana son tai amfani da sunansa a matsayin uba. Dan ALLAH ka riƙe min AMANAR NAJA'ATU NIMRAH, na yarda da kai bazakaci amanar dukkan alfarmata ba. Roƙo na ƙarshe har abada kada ka bar waɗanan mutanen suyi sukuni da walwala a wannan duniyar. Ka addabesu, ka zame musu KIƊA A RUWA MAI TADA HANKALIN DO...... D......”      Ta kasa ƙarasawa saboda yanda numfashinta ke fisga. Da ƙyar ta sake jawo shi da furta, “N...Nimr... Na ɗakin Inn...nta a cikin kwalla Inn...a ta ɓoyeta. Dan ita suka fara ne... Nema su ka..she. ƙin... Nu nata da mukai yasa suka kashe Innata da ƴan uwan....a. Sunyi alƙawarin kuma sai sun kashe ta, ina tsoron kada su cigaba da bibiyar rayuwarta dan ALLAH ka kula da it.....a AMANA”.      Harshenta ya riƙe ta kasa cigaba da maganar. Ga Captain Musa ya ƙaraso da yaran soji zasu ɗauketa a saka cikin jirgi likita ya bata taimakon gaggawa. Amma ina wannan tafiyar mai girma ce, kuma ta har abada ce ga Umman Nimrah. Hannu Imran ya ɗaga musu da ƙyar, yayinda Zak-Shadow ya motsa lips ɗinsa da ƙyar ya shiga ambato mata kalmar shahada. Idanun kan sunyi wani irin masifar juyewa jajur. Cikin aminci UBANGIJI akan lips itama ta dinga maimaita duk abinda ya ambata ganinta na juyewa zuwa ga UBANGIJI, amma kuma har lokacin Zak-Shadow ɗin kawai take kallo. A haka idanun suka kafe alamar rai dai yayi halinsa.        A mamakin kowa gefe Zak-Shadow ya maida kansa kawai. Kaudawar da kowa yafi zargin hawaye ne suka cika masa ido. Duk da kuwa kowa yasan kuka ba ɗabi'arsa bace. Musamman idan sukai dubi da kalolin tashin hankalin da suka gani a rayuwar aikin soja da tafi wannan har a ƙasashen ƙetare. Komai baice ba ya miƙe kawai, yayinda Imran yaja ɗankwalin kanta ta rufe mata fuska tare da shimfiɗeta a wajen.        Koke-koken mata da yaran ya ƙaru sosai, matan sun kai su goma sha bakwai, dukansu kuma matan yayyen Umma ne da ƙanne, sai yaransu. Inda Zak-Shadow ya nufa Imran yabi da kallo, a ɗakin da suka sami nasarar fiddo tsohon nan ne, nan ne kuma Umma tai nuni da Nimrah na'a ciki. Captain Musa ne biye da shi. Basu fi mintuna uku da shiga ba kuwa suka fito Captain Musa ɗauke da ƙatuwar ƙwalla irin ta mutanen da mai hoton murtala. Da alama ɗakin da suka shigan da duhu dan harda fitila a hannunsa da suka haska. Murfin kwallar ya buɗe, sai ga Nimrah a ciki da alama ma a sune take. Riga ce doguwa a jikinta ƴar kanti, tayi face-face da jinin Inna dan sanda suka harbi Inna ɗin jinin ya fallatsawa Nimrah. Karon farko Zak-Shadow daya zubama cikin kwallar juyayyun idanunsa ya kauda kansa saboda isowar Imran wajen. Cikin girmamawa ya nuna matan da yaran dake wani irin kuka mai ban tausayi. “Sir! Suma za'a wuce da su ne?”.         Kansa ya jinjina masa da bin jejin da kallo. Sai kuma ya duƙa tare da saka hannu cikin kwallar ya ɗakko Nimrah gaba ɗayanta, kafin ya furta, “Alamu sun nuna basu kaɗai bane. Dan yara mata ne sukafi yawa anan, mazan basu wuce shekaru uku-uku ba. Dole ne akwai wata tawagar yara mazan gidan ɓoye a cikin jejin nan mutanen nan sun ɗiba”.       “Tabbas nima ina hasashen hakan Sir. Musamman idan mukai la'akari da furucin tsohon da yace adadin jikokinsa maza sunfi matan yawa”.       Shiru yay yana nazarin maganar Imran ɗin. Yayinda idanunsa ke bin mata da yaran da kallo a tsanake. Sosai kukan da suke ke taɓa masa ƙasan zuciya. Amma da yake ƴan mazan mazane na gaske babu alamar hakan a saman fuskarsa. Sai ma ɗauke idanunsa yay cikin bada umarni yace a sakasu a mota. Sosai ihunsu da karuruwa ta ƙara ƙarfi. Ɗauke kansa yay tare da yima Imran magana ƙasa-ƙasa.     Kai Imran ya jinjina masa, shi kuma ya wuce jikin motar da yazo a kai ya saka Nimrah a baya ya kwantar. Imran dake bin matan da kallo nuni yay da yara kusan goma ya ce a fito da su. Bayan ya raɗama Captain Musa magana a kunne shima. Cikin gamsuwa Captain Musa ya matsa yayma sauran nasu magana shima. Aifa take suka ɗaura bindigu akan yaran.       Ihun iyayen ne ya sake ƙarfi, yayinda suke roƙon kar a kashe musu yara dan ALLAH. A kausashe Imran ya furta “Idan har bakwa buƙatar rasasu suma ku sanar mana ina sauran ƴaƴanku suke? Barazanar mi sukai muku suka kwashe su?!!”.          Shiru sukai alamar matuƙar jin tsoron yin magana. Dan kuwa takunkumi akai musu ta ƙarƙashin ƙasa akan idan suka faɗa a bakin ransu su duka. Takaici da ɗacin daya mamaye maƙoshin Zak-Shadow ya daka musu tsawa. Yanda amon muryarsa mai matuƙar saka razani ta ratsa jejin ya saka su sake shiga razani. Tuni wata tsohuwa ta fara bayani jikinta na rawa. “Iya muke nan muka rage a gidan. Dan da yawan yaranmu maza suna birni neman kuɗi. Wasu kuma sun gudu bamu san inda suke ba”.       Shi ɗin jami'in tsaro ne na soji mai matuƙar fiƙrah da kaifin basira. Yayi matuƙar sanin aikinsa ta yanda ko'a furucin baki yakan iya tantance na gaskiya da akasinsa. Dan haka kai tsaye ga gane ya kuma fahimci tsohuwar a tsorace take. Batare da ta sake cewa komai ba yay nuni da a saki yaran. Ai a guje suka shiga komawa wajen iyayensu wasu har suna tintsirawa a ƙasa suna tashi.      Fitowa su Zak-Shadow sukai ƙofar gida, aka bar yaran sojoji kusan goma sha a ciki tare da su. Mizai faru, mintuna goma su Imran basu ƙulla da fitowa a gidan ba dan suna tattaunawa ne kawai sukaji tarwatsawar abu mai ƙarfi ta yanda su kansu sai da suka zabura gefe dukansu.      Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, ashe duk wannan abun dake faruwa bomb ne ɗaure a jikin ɗaya daga matan gidan, shiyyasa suka kasa faɗar inda sauran yaransu dasu Dagger suka ɗiba a jiyan suke. Gaba ɗaya kuma ya tarwatsa gidan da matan, da yaran, da sojojin da aka barsu da su su wajen ashirin. Wannan da shine tashin hankali ba'a sanya maka rana. Dan ba gidan ba hatta gidajen makwaftansu dake lafe a gida hankula a tashe tako wace kusurwa sun tarwatse. Sai dai kaga mutum yay sama an dawo da shi ƙasa a tarwatse, wasu ma sasan jikin duk a rarrabe.       Wannan abu ya zafafi Zak-Shadow da fusatashi, dan kuwa tunda ya damƙa Nimrah a hannun Imran sai kawai yay sabuwar ɗammarar aiki da kansa ba umarni ba. Yaƙi da karan kansa ba jiran yara ba. Hankalin su Captain Musa ya tashi ganin yay wani hatsabibin tsalle ya shige motar yaƙi mai zazzage maƙiya da gurneti suka san ran ƴan maza ya ɓaci. Aiko da gasken ya ɓacin, kuma ranar yaran Dagger sun tabbatar ya ɓacin. Dan da karfin ikon ALLAH a maimakon Captains shi da kansa ya jagoranci runduna guda a cikin jejin suka dinga zaƙulo yaran daga. Wani mahaukacin kisa yake musu mai cike da fushi da baƙin ciki. Gaba ɗaya wannan yinin Zak-Shadow baiyi tsayuwar awa ɗaya ba da sunan hutu. Ga sojoji an sake ƙaro masa. Lungu da saƙo ya dinga zaƙulosu, dan kuwa bai gushe ba zai da ya gano sabon wajen haƙar ma'adanan daya sashi fahimtar dan su aka haddasa wannan sabon tashin hankalin na kwanakin nan. A take ya saka sojojinsa suka rufe wajen haba ɗaya... Zakusha mamaki idan nace muku duk wannan abun da ake munafukin nan bai gaji da ɗaukar video a wayarsa ba, dan cikin aljihun riga ta gaba ta sakata cike da dabara, duk kuma inda Zak-Shadow ya sanya ƙafa yana biye, hasalima shine ɗauke da wayar sadarwa a baya da jakar harsasai yana ɗurama Zak-Shadow a bindiga... <<<<<>>>>>>        Kwanaki huɗu cir su Zak-Shadow na yaƙi a wannan yanki. Sun ci nasarar zubar da yaran su Dagger zubarwa mai muni, a ƙarshe kuma Zak-Shadow ya kama Dagger da hannunsa kamar yanda yay alƙawarin cikin awanni ɗari da yardar ALLAH. Sai ko UBANGIJIN ya yarje masa ya kuma tallafa masa kafin cikar a wannan ya cafke Dagger ɗin.. Ta ko ina ƙasa ta ɗauki labari akan kama Dagger da Zak-Shadow yayi da hannunsa. Da yanda ya jagoranci wannan yaƙi na tsawon kwanaki shida da kansa ba zaman bada umarni ba shi da Major Imran. Ta ko'ina gidajen tv dana rediyo zance su kawai kake ji. Dan kuwa sun nuna matuƙar jarumta da mazantaka na murƙushe ƙungiyar duhu da ƴan barandan data tara irinsu Dagger. Sai dai abinda Zak-Shadow da al'ummar ƙasa basu sani ba. Murƙushe su Dagger kashe maciji ne kawai batare da dare kansa ba. Saboda su Dagger sunan karnukan farauta kawai suke amsawa, manyan mafarutan na gefe suna kallon komai dake faruwa suma.      Duk da hankulan shugabannin ƙungiyar duhu a tashe yake da kama Dagger ɗin da daƙile aikinsu na haƙar ma'adanai a karo na biyu da duk Zak-Shadow ya taka rawar gani wajen cin nasa a kansu a gefe ɗaya suna jin nasarar mallakar yaran da suka saka aka satar musu dake a hannunsu. Duk da kuwa Zak-Shadow da kansa ya ƙwaci yara kusan talatin a wata maɓoya dake cikin jejin bayan ya tarwatse yaran Dagger da suma ke a wajen. A yanzu yaran dake hannunsu basu wuce ashirin ba, sai na ƙarshe da suka ɗiba a gidan iyayen Umman Nimrah da suma ɗin dai Zak-Shadow ya kafa ya tsare akan nemansu da fatan dawo da su...........✍🏼          _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 48_ __________________ *🔥 RASH BEAUTY WORLD 🔥 duniyar kayan mata masu kyau da arha ,Ina masu son kaya na kyan gani, amma basu son tsada? To, *ki daina nema!* Rash Beauty World ta zo miki da komai: *👗 Abaya masu kyau na zamani Egypt/dubai* 👜 *Bags masu kyau* *👠 Takalma masu ɗaukar ido* 💍 *Jewelry masu ƙyalli kamar na sarauta* 🍽️ *Kayan Kitchen masu amfani da kyau* *Koma da Naira kaɗan za ki yi shopping kamar sarauniya!* 👑💃 ✅ Farashi mai sauƙi ✅ Kayamasu quality ✅ Fast delivery *Shiga group dinmu yanzu kiga sabbin kaya ,Kayanmu masu kyau ne kuma farashi mai sauƙi! Kar ki bari a baki labari don samun kayayyaki masu inganci* 👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/GzcU1TcAem21oJedkisrhj?mode=wwt *RASH BEAUTY WORLD – Inda kyawu da araha suka haɗu!* __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........“Wai wannan tsinannen mutumin aljani ko mutum?”.       Viper ya faɗa cikin yaren da suke amfani da shi, muryarsa na fita da ɗaci da zafin yanda yake jin tsabar tsanar Zak-Shadow.           “Mutum ne Viper, sai dai uwarsa ta haifa mana bala'i da masifa ne kawai wlhy.....”      “Ni ma ta gaskiyar Viper ban yarda mutum bane ba sam. Duba fa yanda yake wajiga burukanmu, a karo na biyu ya sake rushe nasarar mu. Taya zamuce mutum ne? Idan ko har mutum ne shi ɗin shugaban matsafa ne matsiyac.....” ya gagara ƙarasawa saboda hawayen da suka zubo masa sharr. Haka yake da baƙar zuciyar tsiya, shiyasa suke kiransa da suna Black Spider. Kukan nasa kuwa tamkar ya ƙara tunzurasu ne, musamman oga da har yanzu baice komai ba tun ɗazun. A karo na farko yayi gyaran murya, hakan yasa duk suka bashi hankalinsu, Black Spider mai kuka ya share hawayensa.        Da kaushi murya oga Jush ya ce, “Silence. Plan c will begin now. Bana buƙatar Dagger da duka yaransa da aka kama a raye. Zamu sake sabon tsari daga yau. Shi ko tunda yace zai iya wasan zamu zuba. A yanzu ba wasan mutuwa bane ba, wasan gasa masa aya a tsakkiyar tafin hannu ne. Zai rayu, sai dai rayuwa mafi raɗaɗi da ƙasƙanci a idanun ƴan ƙasar tasa dake kambamashi da zuga jarumtarsa. Mu DODANNI ne da KIƊA A RUWA BAYA TADA HANKALIN MU. Zamu ɓoye shi a indanunsa da kunnuwansa zasu cigaba da jin kukan mutanen ƙasar tashi, ya cigaba da kallon gudanar jininsu a cikin ƙasa tamkar kwata ɗin yanka dabbobi. Zakuma mu ɗiba arziƙin ƙasar tasa, kuma ƴaƴan ƙasar tasa ne zasu zama bayinmu masu haƙa, masu kuma kashewa”.       Raff!! Raff!! Raff!! Kake jin tafi na tashi ga sauran members. Sun san waye ogansu, sun kuma yarda da shi ɗari bisa ɗari. Dan daga faro tafiyar nan zuwa yanzu bai taɓa faɗa bai cika musu ba. Matuƙar nutsuwa kuwa kalaman nashi suka basu, har suna ji a ransu Zak-Shadow tamkar sauro ne yanzu a dakin kwanansu da baya buƙatar magani sai net kawai domin killacewa. Ga damar shan jini ya samu, amma babu karfin fita domin tsira da rai...      Sun rufe taronsu da zancen fara horar da sabbin yara da zasu maye gurbin Dagger. Yaran kuwa yaran nan ne da suka rage a hannunsu da suka sace. Daga haka taron ya tashi kowa ya kama gabansa rai fes.. <<•><•>><•><<•><•>>             A lokacin da can ƙungiyar duhu ke ƙoƙarin haɗa GUDU DA WAIWAYE... anan ɓangaren mazan fama bisa umarnin General ne aka turke Zak-Shadow domin duba lafiyarsa. Dan da farko ya dage akan baya buƙata, duk da kuwa ko'a zahiri jikinsa akwai ƙananun raunika na gumurzun da aka sha, banda cizon ƙwarin cikin jeji kala-kala da farar fatarsa ta kasa ɓoye wa. Shi kansa ba ganin likitan ne baya buƙata ba, hankalinsa da tunaninsa nakan Mammah da ƴan uwansa da matarsa ne gaba ɗaya. Dan ya tabbatar sunfi kowa shiga tashin hankali akan abinda ke faruwa, musamman daya kasance a kwana na uku da hargitsewar yaƙin har an sanar da mutuwarsa, mutuwar da ta ɗauki hankalin mutane sosai duk da kuwa ba daga bakin jami'an soji sukaji ba ko makusantansa, hasalima wani ɗan media daɗi ne ya zauna ya tsara labarin da komai, cikin sa'a kuwa ya samu karkatowar hankulan mutane a kansa har wasu gidajen jaridu wajen saurin son ace su suka fara kawo zancen suka fara yaɗawa. Da yake mutane jininsu a farce yake na son jin yaya Zak-Shadow ke ciki saboda randa ya saka sulken yaƙi da kansa kafafen yaɗa labarai masu girma da sanin yakamata sun sanar cike da alfahari. Shiyyasa fitar batun mutuwar tasa yaso yin tasiri sai da hukumar soji suka ƙaryata hankulan mutane ya kwanta aka cigaba da binsu da addu'ar samun nasara.        Alhamdullahi UBANGIJI kuwa ya amsa wannan addu'oi tunda nasara ta samu. Duk da wasu sojojin sun rasa rayukansu wasu sun rasa wani sashe na jiki. Musamman Captains da aka rasa kusan guda uku da suka sha gwagwarmaya. Imran ma ya samu harbi a ƙafa, kamar yanda shima Zak-Shadow ɗin ya samu harbi a hannu ta gefen kafaɗa, sai dai da kansa ya cire harsashin ya kuma cigaba da gwagwarmaya, sai kuma a yau ne da komai ya lafa aka sake masa treating ɗin wajen yanda ya kamata... <<<<<•>>>>>        Kamar kuwa yanda Zak-Shadow yay hasashe akan tashin hankalin su Mammah hakanne. Dan kuwa tun ranar da ya bar gidan ba kowa ya sake barci mai daɗi ba. Hatta su Ma'aruff dake ƙasar Chaina kawo kaya tunda Bilal ya sanar musu a ranar da Dadan ya ɗauki ɗammarar yin yaƙin da kansa suka tattara komai suka dawo gida cikin tashin hankali. Dan a duk sanda Dada yay irin wannan zuciyar ta saka sulken yaƙi ba ƙaramin ɗagawar hankali suke samu ba, gani suke kamar za'a kashe musu shi a tarnaƙin yaƙi. Sai dai Alhamdullah UBANGIJI na bashi kariya da nasara koda kuwa zai samu wani rauni mai girma, iyaka yayi jiyya ya miƙe ya koma filin daga. To amma wannan karon sai suka ji zukatansu sun karaya sosai.       Mammah kanta mai ƙoƙarin ƙarfafasu da shanye tata damuwar a wannan karon itama a raunane take, amma maimakon zaman kuka da ɗaga hankali sai ta maida hankali ga addu'a da sadaka, hakan ya ƙarfafa zukatan su Bilal suma suka nutsu wajen gayama UBANGIJI kukansu da fatan nasara ga Dadansu. A randa kuwa akace an kashe shi ɗin nan yanke jiki Mimi tai ta faɗi, jini ya ɓalle mata abinka da mai ƙaramin ciki, hakama sauran babu wanda bai kusa suma ba saboda tarwatsawar zukata. Sai dai Alhamdullah abin bai nisa ba sukaji gaskiyar zance aka koma hawayen farin ciki.      Yau kuwa suna jin fitowar su daga jejin kowa ya kasa zaune ya kasa tsaye. Tuni suka bar gida zuwa Headquarter tun ma kafin su Zak-Shadow ɗin su iso Abujan, dan an sanar zai wuce gida ya huta tare da yin jiyya. Suna a cikin barrak ɗin jirgin soji mai saukar angulu daya ɗakko su Zak-Shadow ya sauka, sai dai basu samu ganinsa ba aka shige dasu ciki saboda yanayin da yake ciki na ganin jiri a dalilin jinin daya zubar sosai. Su Imran kuwa dama yau kwanansu huɗu kenan a asibitin cikin barrak ɗin.      Har bayan magriba basu ji sun gaji da zaman ba, zuwa lokacin ma Uncle Nasiru ya iso shima. Shi da mahaifin Imran ne suka samu ganawa da Gen. Dan son jin yaya Haysam ɗin na raye kuwa?. Cikin mutuntawa Gen yay musu bayanin da sukaji gamsuwa da kwanciyar hankali, ya kuma basu haƙuri da tabbatar musu in sha ALLAHU zuwa gobe za'a basu damar ganin shima Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu ɗin da muƙarrabansa dake a raye dan sunga Imran dama kullum ma suna zuwa dubashi, sannan a sanar da wanda suka rasa rayukansu... Wannan bayani ya saka su Uncle Nasiru lallaɓa su Mammah komawa gida, sai dai a gidan ma jigum-jigum sukayi babu mai wata walwalar kirki balle jira. Abinci kuwa babu wanda ya nema balle tunanin ci. Nabeeha matarsa kuwa data dinga kuka acan da dagewar acan zata kwana har sai ta ganshi koda suka dawo gidan Mammah bata barta komawa sashenta ba, sai ta taho da ita nan sashensu a bedroom ɗinta. Sosai take jin tausayin Nabeeha ɗin a ranta duk da kuwa ita ta haifi Haysam, ita tafi cancanta aji tausayi da yarda tafi kowa jinraɗaɗi da tashin hankali. To amma mata da miji sai ALLAH, musamman auren soyayya irin na Nabeeha da Haysam, dan tsantsar soyayyar da Nabeeha kema Zak-Shadow a bayyane take ƙwarai da gaske, bata iya ɓoyeta agaban kowa har da ita mahaifiyarsa ma. Shiyasa a wasu lokutan da Nabeeha kan nuna kishinta akan ƙannensa Mammah takanyi murmurshi ne kawai. Haka suma ƙannen nasa basa iya ɓoye kishinsu a kanta wani lokacin, musamman ma idan yazo gidan da nufin yin ƴan kwanaki kowanne najin shine yafi cancanta da samun lokacinsa fiye da ɗayan ɓangaren. Ita dai tana musu addu'a da fatan haɗin kai, dan koba komai itama Nabeeha tasu ce tunda jinin Uncle Nasiru ce, Uncle Nasiru kuwa ya cancanci kowace irin ƙauna da girmamawa a garesu baki ɗaya.         Washe gari ma basu sami damar ganin su Zak-Shadow ba. Dan allurar barci ake musu saboda su sami isasshen hutu na rashin wadataccen barcin kwana da kwanaki da suka sha. Musamman ma shi uban tafiya commandor ɗin yaƙin da ko bai faɗa ba a kallo ɗaya zaka fahimci a jigace yake da son barci, hasalima shine ya saka shi ganin jirin da har suka iso yana ciki.       Kwanaki uku cir kuwa suka sami wadataccen barci da nutsuwa yanda ya kamata. Dan basa ganin kowa babu mai ganinsu sai likitoci da wasu manyan soji da ke ɗan zama da su a duk sanda suka ɗan farka musamman a lokacin salla. Suma basa wuce mintuna talatin suke fita su barsu. A kwana cikon na huɗu tunda safe iyalan Mammah kaf suka kammala shirin komawa cikin barrak da su Zak-Shadow ke kwance a asibiti. Mota uku sukayi dan babu wanda ya yarda aka barshi a gida har ƙannen Nabeeha. Ganin sammakon nasu ga ƴan jarida da suma suka matsu da son jin halin da su Zak-Shadow ke ciki dan su isar ma al'umma sai General da kansa ya bada umarnin a kaisu ɗakin da Zak-Shadow yake.      Nabeeha ce gaba-gaba wajen shiga, cikin takaici Mommy ta balla mata harara da jan ƙaramin tsaki. Ja'afar dake gefenta da shima takaicin Raihana dake nuna kamar ta fisu son Dadan ya kume, ƙasa-ƙasa ya furta, “Itafa ji take kamar tama fimu sonshi mtsowww”.         “Kabar ƴar wahala Yaya J. Ai mu da ita kar tasan kar ce. Dan wannan da ace ta samu Dada yanda take so wlhy sai ta rabamu da shi ma”.     “Ita ɗin banza”. Cewar Ma'aruff ƙasa-ƙasa shima. Dai-dai nan suka ƙarasa shigewa ɗakin. Shi kaɗai ne a ciki duk da kuwa babban ɗaki ne an kuma zuba komai a ciki na more rayuwa kamar ba ɗakin asibiti ba. Babu wanda zuciyarsa bata sosu a cikinsu da ganin yanda Nabeeha taje ta maƙalƙalesa ba. Haba wannan rashin kunya har ina bayan tasan Mammah na tare da su.        Shi kansa Dadan da alama bai san harda su ba, tunda sai da ta shigo da fin minti ɗaya da rabi saboda gudun da tayi sannan suka ƙaraso. Suna yin sallama yay ƙoƙarin janyeta daga jikinsa, ita ko sai ƙara mannewa take har Momy da Ja'afar ɗin dake a gaba suka fara shigowa suka gansu. Magana yay mata data sakata sakinsa na dole, sai dai cike da takaici da baƙin ciki ta watsama su Mommy ɗin harara. Basu kulata ba, dan basa son koda wasa Dada ya fahimci suna TAKUN SAƘA da matarsa akan soyayyarsa.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 49_ __________________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LkEgiP5qOEo9YDYjaeZLLc?mode=ems_wa_t✍️✍️ Assalamu Alaikum my people dafatan kunanan cikin aminci sunana ummuh sayyeed yar mutan Chadian traditional medicine center Zaria dealer in all kinds of magungunan mata turarukan wuta sudaniss dilka skin care products at home my people bazamafa a kwai zafafan promo damukeyi in Sha allahu zuwa on 15 zamugama sannan gareku Yan Kano free ne kayanki zasuzo miki amma fa karyazo bayan mungama promo kuce kyauta ne aa zakibiya kudi nagode takuce yar mutan Chadian mai gyaran ciki dawaje 💃💃 please banda maza,❌maza❌ In kinada matsala wadda zamu iya taimaka miki 09065504546 Ga PRODUCTS DINMU KAMAR HAKA MAGANIN SANYI TSUMIN BOM MADARAR TABAJE GORON TULA SYRUP ZUMAR SHADAMATSIN GARIN YAUKAYAUKA EMERGENCY GARIN KINFI KAZA DADI SIRRIN MALLAKAR KASA SIRRAN GIDANKI DAHUWAR KAZA DAHUWAR CICCIBI DAHUWAR YAN SHILA HMM BAZASU IRGUBA INA GODIYA SOSAI MY PEOPLE 🥰🥰 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Cike da girmamawa da soyayyar da suke masa suka zagaye gadon kowanne idanu cike da hawaye, shi ko ya zuba musu ido kawai daga zaunen da yake bayansa jingine da fillo. Sanye yake da wando da riga masu taushi kalar army green na barci. Duk da fatarsa tayi duhu sosai saboda wahalar yaƙi ga raunikan jikinsa hakan bai hana kamilar fuskarsa fitar da hasken kwarjini da bayannanniyar nutsuwarsa da kamun kai ba. Karo na farko ya sakar musu ƙaramin murmushi.         “Miye haka kunzo kun zagaye ni kamar masu shirin min tambayoyin kabari?”.       A tare suka saki murmushi suma suna share hawayensu, sai kuma suka shiga rungumeshi abin sha'awa su takwas ɗin duka sukai masa runfa. Yayinda kukan Mimi da Biebah ya ƙara ƙarfi. Kansa kawai ya girgiza, tare da ɗan buga bayan Ammar da Ummi da sukafi kusa da shi. Cikin lallashi ya furta, “It's okay guys! I'm here. Kun san dai bana son kuka. Ina Mammah?”.        Kamar jira suke ya nema Mammah ɗin suka wani dare daga jikinsa Mammah dake tsaye a farkon shigowa ɗakin ta bayyana cikin idanunsa. Yunƙurawa yay zai sauka ta girgiza masa kai. Shi mutum ne mai tsananin girmama iyaye da basu darajarsu koda a gaban waye. Baya wasa da al'amarin Mammah a rayuwarsa ako wane yanayi....           “Kaida ke fama da kanka ina zaka sauka”.    Cewar Mammah tana ƙarasa shigowa ɗakin idanunta akansa. Ƙasa-ƙasa ya ɗan murmusa, koda ta kai zaune a gefen gadon kusa da ƙafafunsa sai yay salute ɗinta. Ƙaramar harara tayi masa, harar data saka murmurshinsa ƙara faɗaɗa ƴan uwansa kuwa na dariya. Da ido yay ma ƙanen nasa alamar suma suyi, ai ko sai suka wani ƙame tare da sara mata a tare.      Mammah dake girgiza kai ta ce, “ALLAH ya shiryeku to. Da alama na fara zama kakarku kuma”.      Ma'aruff ya ce, “Mammah ba haka bane, kin san masu iya magana sunce UWAR RAGO akema JAJE, UWAR GWANI kuwa sai dai ai mata SAMBARKA.”          “Wannan zance haka yake Yaya M.”    Cewar Bilal yana kashe masa ido ɗaya.        “ALLAH ya shuryeku”. Mammah ta sake faɗa tana sake maida hankalinta kan Zak-Shadow daya risinar da kai yana gaisheta.             “Yaya jikin naka?”.      “Alhamdullahi Mammah bana jin ciwon komai, kawai dai sun so riƙeni anan ɗin ne suma”.      “Yin hakan shine dai-dai ai. Ga jiki duk raunika ace ba'a jin komai kuma.”       Ɗan murmurshi kawai yayi, ta gefen yana kallon yanda Nabeeha ta haɗe fuska, dan tunda ƙannen nasa suka zagaye shi ta koma gefe. Sai su Ismat ƙannenta suka koma gefenta suma duk suka maƙale. Idanunsa ya ta janye, zuciyarsa na masa babu daɗi. Ya jima da fahimtar matar tasa bata son ƙyaƙyƙyawar alaƙarsa da ƙanensa, kai wani lokacin ko tare da Mammah ta ganshi suna hira sai fuskarta ta canja, ya rasa gane ma'anar hakan da take yi. Bayan ita bai taɓa nuna damuwar zaman ƙanenta tare da su ba, dan ko babu ita zai riƙe zuri'ar Uncle Nasiru a duniyar nan duk da kuwa Ismat ce kasai tashi biyun ƴaƴan ƙanwar mamarta ne...       Shigowar Uncle Nasiru da Baban su Imran da Hajiyarsu, sai matar Uncle Nasiru ɗin da yaranta, dan itama dai yaranta biyar da shi a gidan yanzu, kuma suma duk sun tasa ba laifi. Idan aka haɗa dasu Nabeeha da ƙanenta biyu yaransa takwas shima a duniya. Cikin girmamawa Zak-Shadow ya gaida su, dan kallon iyaye yake musu su duka. Yana kallon Uncle Nasiru tamkar Abiy a gefensa, iyayen Imran kuwa suma sun zama iyaye a gareshi, dan suma suna masa abu irin na ɗan da suka haifa, shiyyasa zuminci ne mai ƙarfi a tsakanin waɗan nan zuri'a uku a yanzu.       Sun jajanta masa, tare da jinjina da addu'a bisa ga namijin ƙoƙarin da sukayi da jarumtar murƙushe waɗan nan mutane da bayyanar ta'addancinsu ke tada hankalin al'umma. A wannan yanayin Imran da zuwa yanzu shi ya fara takawa dan kwanansa na takwas kenan shi a barrak ɗin tun randa aka harbesa aka kawosu ya shigo tare da wasu soja biyu. Sai Nimrah riƙe a hannunsa tayi fes da ita, sai dai tayi zuru-zuru alamar rashin sakewa da damuwa bayyane akan ƴar fuskarta.       Kamar yanda Zak-Shadow ya zuba mata ido haka kowa a ɗakin ita yake kallo, yaran sojin suka ƙame cike da girmamawa ga Zak-Shadow, sannan sukai gaisuwa da tambayar jikinsa. Kai ya jinjina musu kawai. Imran ma ɗan ƙamewa yay alamar nuna girmamawar, kawai Zak-Shadow ɗin ya balla masa harara. Bakuna su Ma'aruff suka gumtse suna dariya ƙasa-ƙasa, suko su Mammah murmushi duk sukayi. Imran ya gaishesu, suka tambayi nasa jikin shima duk da kuwa kullum suna shigowa dubashi tun ma kafin a kawo su Zak-Shadow.         A karo na farko Zak-Shadow dake kallon ƙafar Imran ɗin ya ce, “Yaya kafar taka?”.       “Alhamdullah saura kaɗan ya rage, dan shekaran jiya na fara takawa sosai. Yaya jikinka kaima?”.             “Ni lafiyata Lau, kawai anso takura min ne anan”.      Ƴar dariya Imran yayi, sai kuma ya jawo hannun Nimrah data noƙe gefe tayi kicin-kicin da fuska kamar zata fashe da kuka. Kusa da Zak-Shadow ya matso da ita yana faɗin, “Yanzu su Yusuf suka kawota, itama yau aka sallameta a asibiti”.          Hannu ya miƙa mata a karo na farko, sai kuma ya ɗaga kai yana kallon su Yusuf ɗin yaran sojin dake tare da Imran. Cikin girmamawa suka ƙara ƙamewa, sannan wanda aka kira Yusuf ya ce, “Sir! Yau da safe suka sallameta gaba ɗaya, bayan an tabbatar babu wata matsala a tare da ita a yanzu. Sai dai sunce lokaci-lokaci zata iya dinga tsintar kanta a yanayin tsorata ko firgici, dan haka za'a cigaba da kaita tana ganin likita da amsar magani”.          Kansa ya ɗan jinjina, “Sauran yaran fa?”.     “Duk suna cikin ƙoshin lafiya da kulawa ta musamman ga Captain Ayuba, dan tun ranar su aka miƙasu can hannun jami'an gwamnatin jiharsu. Da ita kaɗai muka taho nan Abuja bisa umarnin Major Imran”.        “Zaku iya tafiya”. Kawai ya faɗa bayan ya jinjina kansa. Sai da suka ƙara Sara masa da salute shi da Imran ɗin duka sannan suka juya suka fita. Babu dai wanda yayi magana a ɗakin kowa yana kallon Nimrah da son jin ƙarin bayani a bakin Zak-Shadow ɗin ko Imran. Sai dai suma duk sunyi shiru. Sai da aka kusan mintuna biyu sannan Zak-Shadow yay ma Nimrah magana a karo na farko.          Idanunta dake tara ƙwalla ta zuba masa batare data amsa ba, sai kuma ta fashe da kuka da faɗin, “Baba ɗan sanda nika kaini wajen Ummana. Bana son nan”.        Kallonta kawai yake yi shi dai, sai Imran ne cikin lallashi ya duƙo yana mata magana. Kafaɗa ta maƙe masa. “Ni dai bana son nan”. Ta sake faɗa tana ɓarkewa da kuka harda fara buga ƙafa, ƙarshe ma ta zube ƙasa zata fara musu borin data saba yima Ummanta a Bankaura. Zak-Shadow bai ma san ya daka mata tsawa ba.            “Kika mana bori anan sai na karya ƙafafunki, maza tashi”.     A mugun razane ta miƙe jikinta na rawa, ta gumtse baki domin hana kukan dake son kufce mata fita. Imran zai riƙota rawar jikinta ta ƙaru.  A karo na farko Mammah dake kallonsu kamar kowa na ɗakin tai ƴar gyaran murya, sai kuma cikin lallashi ta miƙe ta ɗauki Nimrah cak ta ɗaura a saman cinyarta. Rungumeta tayi a jikinta. Kamar kuwa tana jira sai ta ƙanƙameta ta fashe da kuka. Cikin dabara irin ta uwa Mammah ta dinga shafa kan Nimrah da bayanta har barci ya ɗauke ta a haka. Dai-dai lokacin kuma likitan dake kula da Zak-Shadow ya shigo. Dole kowa ya miƙe domin tafiya.      Mammah dake kallon ƙyaƙyƙyawar baƙar fuskar Nimrah dake barci ta ce, “Gashi tayi barci, ko nan kusa da kai za'a kwantar da ita ne?”.         “A'a Mammah ku tafi da ita gida, dama nan za'a kawota”.       Babu wanda a ɗakin bai kalla Zak-Shadow mai maganar ba, idan ka cire Imran dake normal. Tsulum Nabeeha ta ce, “Gida kuma D. A dalilin mi? Ina iyayenta da baza'a kaita wajensu ba sai gidan mu?”.       Bashi da niyyar bata amsar tambayoyinta. Dan haka Imran ya katse shirun da faɗin, “Kuyi haƙuri idan ya samu lafiya zakuji bayanin komai a kanta.....”       “Bayani kamar ya? Kai miyasa baza'a kaita naka gidan ba to? Ko dole shike da alaƙa da ita?”.      Naneeha ta sake maganar cikin rufewar idanu. Dan tana da matsanancin kishi na tashin hankali. Shiyasa ko ƴan uwan Zak-Shadow take jin kishi idan sun raɓe shi. Matar mahaifinsu Uncle Nasiru kanta saboda kishin uwarsu basa ko gaisheta, shiyasa da suka shigo ma ko kallonta basuyi ba balle ƴaƴanta duk da kuwa bata haɗa zama da uwarsu a gidan su ba, tunda sai da ta fita a dalilin auren Nabeeha da Zak-Shadow ɗin sannan ya aureta. Da aka sasanta su ta dawo tace bazata koma ba sai ya saki matar tasa, shiko yace tai zamanta, shi da matarsa mutu ka raba dan yana samun kwanciyar hankali a wajenta fiye da sanda yay rayuwa da ita. Hakan ya ƙara mata tsana a wajen su Nabeeha ɗin, ita ko ta kame kanta daga garesu sai dai su zageta a bayan idonta, agaban ta kam babu dama dan shakkarta ma suke yi... Ganin mugun kallon da Zak-Shadow ya watsama Nabeeha ɗin Mammah ta katse yunƙurin Imran na son sake magana. “Ya isa haka, kumuje kawai ga likita na jiranmu fa”.      Kowa yunƙurawa yay da niyyar tafiya banda Nabeeha data cika tai fam. Sai ma yunƙurowa tai zata sake magana Uncle Nasiru ya daka mata tsawa. “Ba'a isa dake ba kenan ko Nabeeha?”.        Hawayen da suka cika mata idanu ne suka silalo, ta ce, “Amma Abbah....”     “Bana buƙatar ji, wuce muje”.   Yanda yay maganar babu wasa balle sassauci ya sakata raɓashi ta wuce tana waiwayen Zak-Shadow dako kallonta bayayi. Suna gama ficewa yaja tsaki mai ƙarfi yana mai zamewa ya kwanta. Ayyanawa yake a ransa Yaya zai yi da baƙin kishin Nabeeha shi kam? Dan yayi imanin tunda ta fara da haka ba ƙaramin badaƙala zaman yarinyar nan zai kawo ba a wajensu. Shi kuma babu gudu babu ja da baya akan yarinyar nan, yanda ya amshi amanarta a hannun mahaifiyarta in sha ALLAHU zai riƙe koda ransa zai zama fansa a wajen bata kariya........✍🏼        (🤔To babbar magana).    _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 50_ __________________ 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 https://chat.whatsapp.com/DMCa4TXOqV712jNc1UBBRH?mode=ems_copy_t *_GYARA SHINE MACE_* *_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF 'YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_* 🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾 *_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 07069711327 *Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula, Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍 Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍 Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃 Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai , Mmn Yusuf likitar Mata💃😍 Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃 Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃 Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin gari Kalolin tsumi Zumar dabino Zuma Mai rubutu Zumar goron Tula Zumar ridi Dahuwar kaza Dahuwar zabo Dahuwar zuciya Dahuwar ciccibi Dahuwar tsoka Tara Dahuwar Yan shila Dahuwar kwai Mai rubutu Turaren mallaka Turaren Mara Turaren tsugunno Turaren k'irji Shuumar humra HATSABIBI turare Hatsabibiyar humra Matan gaske Maltinat Mata Shayin Mata Tsumin kankana Sirrin tafin k'afa Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a Akwai hadin farinjini na matar aure Akwai kwallin mallaka Zoben mallaka Set na Jigidar mallaka *Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻 07069711327 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍 Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 07069711327 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Iska kaɗan Imran ya furzar yana kallon fuskar Zak-Shadow daya lumshe idanu. “Zak.. gaskiya akwai matsala, tunda har matarka ta fara nuna damuwa akan yarinyar nan”.       Shiru kamar bazai tanka ba, sai kuma ya buɗe idanunsa da har sun ɗan sake kaɗewa akan Imran ɗin. “Saboda itace mai aure na?”.           “Humm bazaka fahimta ba, kasan mata da kishi, bana son maimakon riƙe amanar da bani da haufi a kanka wajen riƙewa al'amarin ya koma wani abu daban. Taya kake tunanin zata riƙe yarinyar nan a wannan yanayin data fara nunawa?”.       “Sai ta kasheta ai, ince dai ƙarshen kishin nasu kenan ko. Mtsoww, ni kada ka ɓata min rai ma”.     Shiru Imran yay bai sake magana ba, amma tabbas shi yasan akwai rigima. Dan kishin Nabeeha ba ɓoyayye bane ga kowa. Tunda har akan ƴan uwansa da Mammah ba ɓoyewa take ba. A haka likita ya dawo ya duba Zak-Shadow ɗin, ganin ya ɗakko allurar barci ya dakatar da shi.        “Ka sallame ni kawai”.   Cikin girmamawa sojan likitan ya ce, “Kayi haƙuri Sir ko zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu ne, dan jikinka na buƙatar hutu sosai”.        Wani kallo ya watsa masa kawai. Da sauri likitan yace, “I'm sorry Sir”.   Murmurshi Imran yayi a karo na farko. Sai kuma ya kalla likitan. “Karka damu ka sallame shi kawai, idan baiji dai-dai ba sai ya dawo”.       “Okay Sir”. <<•>>°<<•>>°<<•>>           A ranar aka sallami Zak-Shadow daga asibiti. Shi mutum ne mai adalci da duba na ƙasa da shi akan komai daya dace. Dan haka maimakon tafiya gida ya samu hutun jiyya da aka basu sai ya koma jihar da ƙauyukan su Bankaura suke ƙarƙashinta ya duba sojojinsu da aka kwantar a asibiti. Ba ƙaramin tashin hankali ya shiga ba da ganin irin ɓarnar da akai musu. Dan sojoji da yawa sun jikkata. Hakama ya shiga har inda aka killace gawarwakin waɗan da suka rasa ransu, ciki harda Captain Musa. Lokacin daya ɗora idanunsa akan Captain Musa sai da suka sake juyewa, Captain Musa jarumin soja ne  ɗan amanarsa, ya taka rawar gani matuƙa akan wannan yaƙin, babu abinda zasu masa sai addu'a. Lokaci ɗaya aka harbesu da Major Imran, shi da yake kwana ya ƙare tun a jejin ya rasu, shi kuma Imran ya suma.          Bayan ya gama zagaya su kaf daga asibitin cikin barrak inda sojojin suke su, babban asibitin jihar ya nufa itama. Nan ko mutanen ƙauyukan ne da suma suka samu raunuka. Kamar yanda yay fata suna samun kulawa ta musamman daga gwamnati, akwai kuma jami'an sojinsu a tare da su, da ƴan sandan farin kaya. Suma ya dubasu. Daga nan ya wuce sansanin da aka samawa waɗan da suka tsira. Ganin yanda aka barsu a wulaƙance sai a tsakar wajen suke kwana damma zafi ne ransa ya ɓaci.      Dama akwai zaman da zasuyi da Gwamnan jihar da shi da wasu manyansu a washe gari. Ai gaba ɗaya ya tattara takaicinsa ya ajiye har zuwa lokacin zaman. Daga sansanin cikin jejin da nasu sansanin yake suka koma. Komai ya lalace, sai dai anata kafa sabbin tantuna an kuma kawo wasu rundunar sojojin dan bazai yiwu abar yankin a haka babu tsaro mai ƙarfi ba. Har dare suna a cikin jejin, dan har cikin ƙauyukan Bankaura, Gangare, da Marke sai da suka shiga. Anan dama abubuwan sukafi tsamari musamman Bankaura a ƙarshe-ƙarshe. Dan an musu ɓarna matuƙa da zasu daɗe basu maida gurbinta ba. Har a yau ana zaƙulo gawarwaki a cikin jejin da ƙauyen Bankaura irin na wanda suka ɓuya a wasu wajejajen suka kasa fita. A lokacin da suka wuce ta ƙofar gidan su Nimrah ya kwashe mintina uku yana kallon gidan da tuna abubuwan da suka faru tun daga farkon zuwan su Imran da sanda yay kiransu. Randa Nimrah tai musu zancen falawa har zaman da sukayi da Ummanta. Rayuwa kenan, cikin abinda baifi sati huɗu ba komai ya lalace, dan gidan ya rurrushe sosai sakamakon bomb da yaran Dagger suka tayar musu suma tamkar gidan iyayen Umman Nimrah. Shiyasa suma baya jin akwai wani sauran zuri'ar data rage, idan kuwa sun rage to ƙalilan za'a samu kuwa a ciki, suma yara ne ko wanda basa a garin al'amarin ya faru.         Tunda suka baro jejin zuwa masaukin da aka bashi a cikin barrak na jihar wanka kawai ya iya yi ya zauna yana wasu rubuce-rubuce, bayan ya kammala kuma ya hau salloli. Bai kwanta ba sai da yay sallar asubahi. Zuwa ƙarfe goma dole ya farka dan suna da meeting da zasu zauna da Gwamna akan harkar tsaro.      Amintaccen yaron nan nasa, kuma munafukinsa a bayan fage da tunda ya iso yake nane da shi ya kira a waya. Babu jimawa ya iso. Bayan miƙa gaisuwar girmamawa tamkar wani mutumin arziƙi kansa a ƙasa ya ce, “Sir! Akwai abinda kake buƙata ne?”.      Batare da Zak-Shadow ya dubashi ba ya miƙa masa wata ƙaramar takarda da ATM ɗinsa. “Kaje Boutique ka sama min kayan da zanyi amfani da shi. Saura ka ɓata min lokaci”. Ya ƙarashe maganar ƙarshe cikin dakewarsa da rashin ɗaukar raini.         “I'm sorry Sir, bazan daɗe ba in sha ALLAHU”.     Zak-Shadow bai sake tanka masa ba, hasalima ya ɗauke kansa ya koma gaban takardun da yay ta rubutu a daren jiya.           Koda Ojo ya fito sai ya harari ɗakin da Zak-Shadow yake, kafin ya kalla ATM ɗin daya bashi da takardar mai ɗauke da pin ɗinsa ya taɓe baki. Baiyi yunƙurin komai ba sai da ya fita a barrak ɗin gaba ɗaya. Nesa sosai ya samu waje ya tsaida mai mashin ɗin daya ɗakko shi. Sauka yayi ya bashi kuɗin, ya samu ƙasan wata bishiya ya zauna. Kamar yanda ya saba kai duk wani motsi da bayanan Zak-Shadow ga iyayen gidansa yanzun ma haka yay kira ya rattafa bayani. Tun daga dawowar Zak-Shadow a jiya har komawarsu jejin nan da ƙauyukan, da takardun da yaga ya baza a ɗakin daya kwana.     Daga can wanda yake gayawar ya ce, “Su kayan daya aikeka ka saya na miye?”.        “Sakawa zai yi sir! Sai dai kamar akwai inda zasuje shi da wasu manyanmu dan jiya bayan mun dawo barrak ɗin sunyi wani ƙaramin meeting su uku”.         “Na baka daga nan zuwa awa ɗaya, nasan ina zai je. Idan ba haka ba kada ka kirani. Sannan ka sani, dolene a yanzu sanya idonka yafi na baya, dan mun rasa yara biyu a wannan tafiyar, an kashe ɗaya, ɗaya na cikin wanda aka jima rauni a asibiti”.       “Babu wata damuwa Sir, komai kuke buƙata zanyi fiye da hakan, kada ka manta na shiga rigar soja ne kawai saboda aikin ku badan zama soja ba. Shiyyasa ma a yaƙin nan ban yarda na cusa kaina a halaka ba”.           “Good! Da kake tuna hakan. Yaushe zai koma Abuja?”.      “Bani da cikakken bayani akan hakan shima, amma nasan bazai jima ba tunda yana ƙarƙashin hutun jiyya ne shi da aminin nashi dama sauran Captains ɗin mu. Dan shi kaɗai ma yazo jiyan alamar akwai abinda yazo yi, duk da dai nasan shi mutum ne azababbe akan aiki shiyyasa ake shan wahalar cimmas cikin sauƙi”.           “Mtsoww! Zai kuwa gane kuransa a wannan karon”. Daga haka ya yanke kiran. Ojo dake dariyar mugunta zaram ya miƙe yana cire layin daya saka a wayar tasa yay kira, ya maida ainahin layinsa da kowa ya sani sannan ya sake tare mashin ya hau ya tafi aiken Zak-Shadow. ★Kai sojan da Zak-Shadow ya saka ya biyo bayansa ke ɗawa tamkar ƙadangare, sai da ya ga mashin ɗin da Ojo ya hau yayi ɗan nisa sannan ya tare wani shima ya hau. Bayan Ojon yasa suka bi, sai dai bai sauka a mashin ɗin ba lokacin da suka iso inda ya sauka a nashi mashin ɗin ya shige wani Boutique. Har yace mashin ɗin ya juya sai kuma yace ya dakata, suna nan kusan mintuna ashirin Ojo ya fito cikin sauri yana kallon agogon hannunsa. Mashin ya sake tarewa ya haye. Yanzun ma sakawa sojan yay suka cigaba da bin bayansa, sai dai ganin ya sauka a ƙofar gate ɗin barrak ɗin shi kuma sai ya sauka can nesa ya biya mai mashin ɗin ya ƙaraso da kafa.        Bai nufi masaukin Zak-Shadow ba har sai da ya tabbatar Ojo ya kai masa kayan ya baro ɗakin sannan. Cike da girmamawa yayi knocking, Zak-Shadow ya bashi izinin shiga. Cikin ƙamewa da sarawa ya ce, “Sir! Duk inda yaje tare mukaje da shi ina biye......” tsaf ya labarta masa komai da ya gani ya kuma ji daga Ojo. Wani kalar zuba masa ido Zak-Shadow yayi, dan tabbas zuciyarsa ta girgiza. Saboda daga jiya zuwa yau ne kawai ya ɗarsa zarginsa akan Ojo, zargi kuma ba irin wanda ya samu bayani ba a yanzu. Dan kuwa shi zargin ma da yakema Ojon daban, abinda yaji a yanzu daban. A take wata ƴar zufa ta taru masa a goshi, idanun nan suka shiga juyewa. Da wata irin tsatstsaurar murya ya furta, “Ka tabbatar da abinda ka faɗa?”.          “Yes sir! Duk abinda na faɗa maka shine gaskiya, zaka iya saka wani binciken bayan ni ma domin tabbatar wa”.         Wani irin amsa kuwwa sunan Ojo ya shiga yi a kunnen Zak-Shadow da brain ɗinsa, har yana ma jin kamar wata juwa-juwa na neman ɗibarsa. Ojo fa, yaron daya bama yarda mai girma bayan Imran, dan ko sauran amintattun yaransa basu kai Ojo ɗin ba ciki kuwa harda shi wannan Yusuf ɗin daya kawo masa bayani akan Ojo ɗin yanzu. Lallai babbar magana, ashe kamar yanda yayi hasashen yaƙin nasa biyu ne na cikin gida dana waje hakan take.       >>•<>•<<>•<<>•<<          Har Zak-Shadow suka isa gidan gwamnati al'amarin yaronsa Ojo na masa kai-kawo a zuciya. Da ƙyar ya iya dannewa suka tattauna sosai akan abinda ya dace. Bai gusaba kuwa sai da ya sakko zancen ƴan gudun hijira da aka bari a wulaƙance. Babu wani tsoro ko shakka kuma ya nuna ma gwamna idan fa akai sakacin barinsu a wulaƙance to za'a iya fuskantar ƙalubale mai girma da yafi wanda ake kai a yanzu. Amma basu muhallin zama da tattara yaransu a saka a makarantu a samawa matan sana'ar yi da sauran mazan da suka rage shine babban gata garesu dama al'umma baki ɗaya.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 51_ __________________ https://vm.tiktok.com/ZSHcfQFhUuBVU-MpLRV/https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg==Wa.me/+2348140002981 Instagram https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg== Assalamu alaykum mutanen Sokoto Da kewaye Shin Ko kunsan cewa DIJAS DELICACY ashirye take Domin faranta ranku a bukukuna Da kowani irin even? Kama Daga samosa, doghnut, spring rolls meat pie, birthday cakes Da sauransu Bata tsaya anan ba tana amsar orders koda yaushe. Inda samosa kike nema frozen Ko fried duka tana dasu akan 3k 10pcs and she bakes daily🥰 Bata tsaya anan ba GA masu son gyaran jikinsu wata skin care tana siyarda best skin care products Kama Daga face wash, face cream,body butter, shower gel dadae sauransu tana aeka Kaya a kowani gari cikin aminci Da yardar allah GA no. Dinta kiyi saving Domin samun naki was.me/+2348140002981 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Duk da yanda yake maganar kai tsaye ta sosa zuciyar gwamna haka ya danne, dan harga ALLAH wani irin kwarjini da cika waje Zak-Shadow ɗin yay masa. Ya jima yana jin labarinsa da jarumtarsa a wajen yaransa musamman kwamishinan tsaro a tsakanin wannan rikicin, amma bai taɓa tunanin mutumin fa ya wuce yanda ake labarin nasa ba. Cikin danne abinda ke ransa da nuna aminta da zancen Zak-Shadow ɗin ya tabbatar masa zai yi ƙoƙarin yin abinda ya dace in sha ALLAHU daga yau zuwa gobe ma. Dan ya fahimci hukumar sojin ma wani girma na musamman take bashi.         Sun ƙara tattaunawa akan batun ƙara sojoji a cikin jejin kafin meeting ɗin ya tashi. A gidan Gwamnatin sukai sallar azhar, daga nan sukai zaman cin abinci da gwamna wanda Zak-Shadow yaƙi cin komai a wajen. Wannan ba sabon abu bane, dan duk wanda ya sanshi yasan ba'a ko'ina ake bashi abu yaci ba. Dan komai nashi da tsari. Kai da yawansu zasu iya ratsuwar basu taɓa ganin ya zauna cin abinci a gaban kowa ba. Idan zai ci abinci yakan killace kansa ne yaci a nutse.        Hakan da yayi ma ya ƙara saka jin shakkarsa a zukatan jami'an gwamnatin da akai zaman hadda gwamnan kansa. Dan bayan barowar su Zak-Shadow gidan gwamnatin sai da sukai ƴar gulma akan girman kan Zak-Shadow yayi yawa. Acewarsu yana Lieutenant Colonel kawai yana wannan isar da izza inaga ya zama General watarana, ai kowama ya shiga uku. Acewarsu wannan tsaf zai iya assasa juyin mulki a ƙasa.     Oho shi baima san sunayi ba, dan daga gidan gwamnatin airport ya wuce zai wuce Abuja. Jirginsu yana gab da tashi ma. Acan ya samu Ojo na jiranshi, shi ya saka ya saya masa tickets harda shi. Bai tsara matakin ɗauka akan Ojon ba, amma ya ƙudira sake jansa a jikinsa fiye da da saboda wani dalili nashi. Mintina baifi goma da zuwansa airport ɗin ba jirginsu ya ɗaga. Tafiyar da bata gaza awa ɗaya ba suka sauka birnin tarayya.       Anan airport suka rabu da Ojo, shi ya wuce barrak shi kuma ya samu su Ma'aruff sun zo ɗaukarshi. Cike da farin ciki suka rungumeshi kuwa. Ojo dake binsu da kallon ƙurilla ya miƙama Ja'afar ƴar briefcase ɗin Zak-Shadow ɗin dake hannunsa. Kafin ya ƙame tare da sara masa. Hannu kawai ya ɗaga masa batare daya kallesa ba, amma yana lure da kallon ƙurillar da yake ma su Ja'afar ɗin. Kaɗan ya cije lips ɗinsa, a ransa yana raya (Yaro tsaya matsayinka kada zancen ƴan duniya ya ruɗe ka. Dan in kace zaka tsalla gonar zuri'ata zan yanka maka kazar wahala ne kuma sai ka figeta da sili-silin gashi). A zahiri kam bayan mota da Ma'aruff ya buɗe masa ya shiga ya zauna. Suma duk gaba suka shiga Ja'afar yaja motar suka kama hanyar gida. Gaba ɗaya sun cika masa kunne da surutu kamar wasu ƙananun yara, shi dai yana jinsu da kunne kawai, wani lokacin kuma yakan yi murmurshi ko girgiza kai da faɗin, “ALLAH ya shiryeku” a taƙaice. A haka suka ƙaraso gidan.... (((★)))★(((★)))            Zantukan Ojo kaf sunje kunnen oga Jush shugaban ƙungiyar duhu. Dan haka ya tara meeting na gaggawa ga members ɗin ƙungiyar. Dama dukkan motsinsu a tsakanin nan a cikin meeting ɗin suke kala-kala. A duk sanda ya bada umarni babu mai wasa wajen amsa kiransa. Dan haka a yanzun ma cikin gaggawa suka gama hallara. Kowa da kowa yazo idan ka cire Dagger da dama ba akowane zama suke zama da shi ɗin ba sai suna buƙatar hakan saboda a wajensu sunan karen farauta kawai yake amsawa. Saɓanin kowanne zama yau oga ne ya fara magana kafin ma su tambayi dalilin zaman.          Sai da ya fara kunna musu recording ɗin muryar Ojo da aka tura masa duk suka saurara. Batare da jiran cewar wani a cikinsu ba ya cigaba da faɗin, “Zamu rushe wasu ɓangarori na plan c”.       Gaba ɗayansu kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu, cikin alamar tambayar juna a yanayin kurame suke ɗan jujjuya hannayensu. Wasu ko na ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki irin na suma basu gane ba. Oga Jush dake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya yay ƙaramar gyaran murya daya dakatar da gungunan nasu dake tashi a ɗakin. Tsitt sukayi gaba ɗaya, tare da maida hankali kansa.        Sai da yaja sakanni cike da shan ƙamshi sannan ya cigaba da magana. “Kamar yanda na faɗa bama buƙatar wasu ɓangarori na plan c kwata-kwata saboda na fahimci wani abu a yanzu”.         “Kamar mi kenan oga?”.     “Muna buƙatar su Dagger a raye. Dan haka Viper ka dakatar da plan ɗinmu na tura masu kashesu”.           “Yanda kace haka za'ai Sir. Amma miyasa kace hakan? Bayan kasan zaman mutanen nan a raye hannun sojojin nan komai zai iya faruwa, ciki kuwa harda sanin mu su wanene. Musamman haɗarin yafi girma akan Dagger da shi ya sammu. Gara ma sauran su Dagger ɗin suka sani”.        Tabbas zancenka a kan hanya yake kuma kana kan dai-dai Viper. Amma abinda nake son ku tuna ba ko yaushe ake iya kama tsuntsu ta baki ba, dan wani tsuntsu ba hatsi yake ci wajen ƙoto ba ababen cikin ruwa ne abincinsa. Ba kashe Dagger ne mafita ba, yin amfani da shi wajen kama mutumin nan ta wuya shine ya dace”.       Sake kallon kallo suka shiga yi, dan su sam basu wani fahimci komai ba. Cike da izza Mr Specter sarkin ƴan girman kai tamkar ogan nasu ya furta, “Na fahimci abinda kake nufi Oga, kuma nayi na'am da wannan tsarin. Kai tsaye ma ni har wani ƙyaƙyƙyawan tunani yazo min”.       Karo na farko Oga Jush ya saki murmurshi idonsa akan Mr Specter, shiyyasa yake matuƙar son shi, dan shima akwai kwanya. Yana wani jinjina kai da lumshe idanu da buɗewa a lokaci guda ya ce, “Yes Mr Specter muna saurarenka, wane tunani kayi?”.         Wani ƙarin girman kai Mr Specter yaji, dan haka ya gyara zamansa yana ajiye ƙatuwar sigarin hannunsa a ɗan bowl ɗin da yake tara tokar. “Sir ina ganin wannan sabon shirin zai dace da yin jifa da karan farautarmu a jikin fatsar da zata kamo mana wannan babban kifin. Ina nufin wannan yaron Ojo, dan aikinsa na ƙyau sosai, sai dai gaggawa zata hana masa yin doguwar tafiya dan Zak-Shadow ba sakarai bane”.        Murmurshi mai faɗi Oga Jush ya sake saki, sai kuma ya shiga tafama Mr Specter, dole suma sauran suka zama ƴan bin yarima akasha kiɗa kawai. Sai da sukai na fin sakan goma sha biyar sannan suka sarara. Oga Jush ya ce, “Lallai ka gane mi nake nufi a sabon shirin mu na ɓangaren haggu. Na ɓangaren dama kuwa lokaci yayi da tafiyarmu zata gayyato manyan babba da jaka na ƙasar nan, hakan ne kawai zai bamu damar farauto kifin cikin ruwa dake gadarar shi ISHA'U DUTSE NA RIMI ne BAKA FARGABA, to amma a ƙarshe shima ai yace SAI NA RUWA ko”.        A karo na farko saura ma suka fahimci darasin Ogan nasu, dan a tare suka kece da dariyar mugunta da na hango nasara. Sun sake tattauna abinda ya dace musamman akan fara horar da sabbin yara da maye gurbin Dagger a cikin yaransa da su Zak-Shadow basu kama ba da gaggawa, sai al'amarin Ojo da shima dole su gaggauta, daga haka taron ya watse zukatansu fes..... <><><><><><><>             Tun shigowarsu harabar gidan Zak-Shadow ya zubama baƙuwar motar dake fake a dai-dai ƙofar sashensu idanu. Koda Ja'afar ya kammala parking a inda ya dace har Ma'aruff ya fita ya buɗe masa sashen da yake hankalinsa nakan motar dai, a karo na farko shima Ma'aruff ɗin ya juya ya kalla motar, sai kuma ya juyo batare da jiran tambaya ba ya ce, “Dada motar Momyn su Ismat ce, jiya tazo da yamma itama”.        Kauda idanun nasa yay daga kan motar, batare da yace komai ba ya miƙama Ma'aruff ɗin wayoyinsa biyu. Ja'afar ma daya riga ya fito can gefen ya buɗe ya ɗauki briefcase ɗinsa. A tare suka rufe motar, sai kuma suka kalli juna suna murmushi ganin ya nufi sashen Mammah. Da sauri sukabi bayansa sun ɗan tafa kowa ya janye hannunsa yana yarfarwa da ƙoƙarin danne dariya duk a lokaci guda, sai kuma akai sa'a Dadan ya juyo zai kallesu ganin basu biyo shi ba. Da sauri suka gimtse fuskoki tare da zabura inda yake. Shaƙiyancin Ja'afar da Ma'aruff babu wanda bai sani ba, dan haka ma ya juya abinsa ya cigaba da tafiya suna take masa baya.        Sallamar su ta saka Mu'azz dirowa a kujera da gudu yayo ƙofa, cike da farin ciki yake faɗin, “Oyoyo Dada na”.         Guntun murmushi Zak-Shadow yayi, tare da tsayawa cak har Mu'azz ɗin ya ƙaraso inda yake ya rungumeshi. Kan yaron ya shafa, dai-dai shima Ja'afar na kai masa rankwashi da faɗin, “Ɗan iya kenan, wato Dadanka ma kai kaɗai, ai mu riƙo aka kawomu gidan naga”.      “Ai rankwashin da yafi wannan ya kamata kai masa”. Cewar Ma'aruff yana harar Mu'azz shima. Baki Mu'azz ya tura yana sake maƙale Zak-Shadow, dan in dai muguntar Uncle ɗin nasa biyu ne ya saba da ita a gidan. (Mu'azz ɗan Aunty Ummi ne, mahaifinsa ya rasu tun yana a ciki, dan watan Aunty Ummi ɗin bakwai da aure mijin nata ya rasu, ba kowa bane face yayan Imran, rasuwar ta gigitata dama ahalinsa da su su Zak-Shadow ɗin, har takai ta shiga wani yanayi na ciwo dole aka dawo da ita gida, a haka ta ƙarasa rainon cikin ta haifeshi. Ko bayan haihuwar tasa ma ansha fama da ita kafin ALLAH yasa ta koma dai-dai ta cigaba da shayar da shi, sai dai rainonsa gaba ɗaya Mammah da Mimi ne sukayi shi, har ya kai yaye. Ta jima a gida bata sake wani auren ba kusan shekara biyar dan tama koma karatu, sai da Zak-Shadow yay mata jan ido sannan. Ƴan gidan su Imran basu taɓa nuna kwace Mu'azz ba a hannunsu, sun san yana samun dukkan gata anan gidan, sai dai kuma suma hakan baya hana suyi masa nasu gatan. Dan haka Mu'azz shine jika na farko a gidan tunda har yanzu matar Dada Nabeeha bata haihu ba duk da kuwa tare akai bikinsu da Ummi ɗin a lokacin. Gashi a gidan sabon aurenta har ta sake yara biyu).        “Dada! Nima kaga Mammah ta kawo min sabuwar ƙanwa. Sunanta Nimrah”. Mu'azz yay maganar yana raba jikinsa dana Dada. Bai jira amsarsa ba ya bar wajen da ɗan gudu. Inda Nimrah take maƙure a tsakanin kujera tunda sukai sallama ta tashi ta buƴa a wajen dan har yanzu bayan Mammah da Mu'azz ɗin taƙi sakin jiki da kowa a gidan. Hannunta ya kamo cike da farin ciki ya ce, “Nina taso ga Dadana da nake baki labari yazo”.       Kafaɗa Nimrah ta maƙe alamar bazataje ba. Da damuwa a fuskar Mu'azz ya juya inda su Dada suke tsaye har yanzu yana kallon su. “Dada kaji wai bazata zo ba”.     Maimakon Zak-Shadow ya basu amsa sai ya shiga takawa a nutse har inda suke..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 52 __________________ https://vm.tiktok.com/ZSHcfQFhUuBVU-MpLRV/https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg==Wa.me/+2348140002981 Instagram https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg== Assalamu alaykum mutanen Sokoto Da kewaye Shin Ko kunsan cewa DIJAS DELICACY ashirye take Domin faranta ranku a bukukuna Da kowani irin even? Kama Daga samosa, doghnut, spring rolls meat pie, birthday cakes Da sauransu Bata tsaya anan ba tana amsar orders koda yaushe. Inda samosa kike nema frozen Ko fried duka tana dasu akan 3k 10pcs and she bakes daily🥰 Bata tsaya anan ba GA masu son gyaran jikinsu wata skin care tana siyarda best skin care products Kama Daga face wash, face cream,body butter, shower gel dadae sauransu tana aeka Kaya a kowani gari cikin aminci Da yardar allah GA no. Dinta kiyi saving Domin samun naki was.me/+2348140002981 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Duk da yanda yake maganar kai tsaye ta sosa zuciyar gwamna haka ya danne, dan harga ALLAH wani irin kwarjini da cika waje Zak-Shadow ɗin yay masa. Ya jima yana jin labarinsa da jarumtarsa a wajen yaransa musamman kwamishinan tsaro a tsakanin wannan rikicin, amma bai taɓa tunanin mutumin fa ya wuce yanda ake labarin nasa ba. Cikin danne abinda ke ransa da nuna aminta da zancen Zak-Shadow ɗin ya tabbatar masa zai yi ƙoƙarin yin abinda ya dace in sha ALLAHU daga yau zuwa gobe ma. Dan ya fahimci hukumar sojin ma wani girma na musamman take bashi.         Sun ƙara tattaunawa akan batun ƙara sojoji a cikin jejin kafin meeting ɗin ya tashi. A gidan Gwamnatin sukai sallar azhar, daga nan sukai zaman cin abinci da gwamna wanda Zak-Shadow yaƙi cin komai a wajen. Wannan ba sabon abu bane, dan duk wanda ya sanshi yasan ba'a ko'ina ake bashi abu yaci ba. Dan komai nashi da tsari. Kai da yawansu zasu iya ratsuwar basu taɓa ganin ya zauna cin abinci a gaban kowa ba. Idan zai ci abinci yakan killace kansa ne yaci a nutse.        Hakan da yayi ma ya ƙara saka jin shakkarsa a zukatan jami'an gwamnatin da akai zaman hadda gwamnan kansa. Dan bayan barowar su Zak-Shadow gidan gwamnatin sai da sukai ƴar gulma akan girman kan Zak-Shadow yayi yawa. Acewarsu yana Lieutenant Colonel kawai yana wannan isar da izza inaga ya zama General watarana, ai kowama ya shiga uku. Acewarsu wannan tsaf zai iya assasa juyin mulki a ƙasa.     Oho shi baima san sunayi ba, dan daga gidan gwamnatin airport ya wuce zai wuce Abuja. Jirginsu yana gab da tashi ma. Acan ya samu Ojo na jiranshi, shi ya saka ya saya masa tickets harda shi. Bai tsara matakin ɗauka akan Ojon ba, amma ya ƙudira sake jansa a jikinsa fiye da da saboda wani dalili nashi. Mintina baifi goma da zuwansa airport ɗin ba jirginsu ya ɗaga. Tafiyar da bata gaza awa ɗaya ba suka sauka birnin tarayya.       Anan airport suka rabu da Ojo, shi ya wuce barrak shi kuma ya samu su Ma'aruff sun zo ɗaukarshi. Cike da farin ciki suka rungumeshi kuwa. Ojo dake binsu da kallon ƙurilla ya miƙama Ja'afar ƴar briefcase ɗin Zak-Shadow ɗin dake hannunsa. Kafin ya ƙame tare da sara masa. Hannu kawai ya ɗaga masa batare daya kallesa ba, amma yana lure da kallon ƙurillar da yake ma su Ja'afar ɗin. Kaɗan ya cije lips ɗinsa, a ransa yana raya (Yaro tsaya matsayinka kada zancen ƴan duniya ya ruɗe ka. Dan in kace zaka tsalla gonar zuri'ata zan yanka maka kazar wahala ne kuma sai ka figeta da sili-silin gashi). A zahiri kam bayan mota da Ma'aruff ya buɗe masa ya shiga ya zauna. Suma duk gaba suka shiga Ja'afar yaja motar suka kama hanyar gida. Gaba ɗaya sun cika masa kunne da surutu kamar wasu ƙananun yara, shi dai yana jinsu da kunne kawai, wani lokacin kuma yakan yi murmurshi ko girgiza kai da faɗin, “ALLAH ya shiryeku” a taƙaice. A haka suka ƙaraso gidan.... (((★)))★(((★)))            Zantukan Ojo kaf sunje kunnen oga Jush shugaban ƙungiyar duhu. Dan haka ya tara meeting na gaggawa ga members ɗin ƙungiyar. Dama dukkan motsinsu a tsakanin nan a cikin meeting ɗin suke kala-kala. A duk sanda ya bada umarni babu mai wasa wajen amsa kiransa. Dan haka a yanzun ma cikin gaggawa suka gama hallara. Kowa da kowa yazo idan ka cire Dagger da dama ba akowane zama suke zama da shi ɗin ba sai suna buƙatar hakan saboda a wajensu sunan karen farauta kawai yake amsawa. Saɓanin kowanne zama yau oga ne ya fara magana kafin ma su tambayi dalilin zaman.          Sai da ya fara kunna musu recording ɗin muryar Ojo da aka tura masa duk suka saurara. Batare da jiran cewar wani a cikinsu ba ya cigaba da faɗin, “Zamu rushe wasu ɓangarori na plan c”.       Gaba ɗayansu kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu, cikin alamar tambayar juna a yanayin kurame suke ɗan jujjuya hannayensu. Wasu ko na ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki irin na suma basu gane ba. Oga Jush dake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya yay ƙaramar gyaran murya daya dakatar da gungunan nasu dake tashi a ɗakin. Tsitt sukayi gaba ɗaya, tare da maida hankali kansa.        Sai da yaja sakanni cike da shan ƙamshi sannan ya cigaba da magana. “Kamar yanda na faɗa bama buƙatar wasu ɓangarori na plan c kwata-kwata saboda na fahimci wani abu a yanzu”.         “Kamar mi kenan oga?”.     “Muna buƙatar su Dagger a raye. Dan haka Viper ka dakatar da plan ɗinmu na tura masu kashesu”.           “Yanda kace haka za'ai Sir. Amma miyasa kace hakan? Bayan kasan zaman mutanen nan a raye hannun sojojin nan komai zai iya faruwa, ciki kuwa harda sanin mu su wanene. Musamman haɗarin yafi girma akan Dagger da shi ya sammu. Gara ma sauran su Dagger ɗin suka sani”.        Tabbas zancenka a kan hanya yake kuma kana kan dai-dai Viper. Amma abinda nake son ku tuna ba ko yaushe ake iya kama tsuntsu ta baki ba, dan wani tsuntsu ba hatsi yake ci wajen ƙoto ba ababen cikin ruwa ne abincinsa. Ba kashe Dagger ne mafita ba, yin amfani da shi wajen kama mutumin nan ta wuya shine ya dace”.       Sake kallon kallo suka shiga yi, dan su sam basu wani fahimci komai ba. Cike da izza Mr Specter sarkin ƴan girman kai tamkar ogan nasu ya furta, “Na fahimci abinda kake nufi Oga, kuma nayi na'am da wannan tsarin. Kai tsaye ma ni har wani ƙyaƙyƙyawan tunani yazo min”.       Karo na farko Oga Jush ya saki murmurshi idonsa akan Mr Specter, shiyyasa yake matuƙar son shi, dan shima akwai kwanya. Yana wani jinjina kai da lumshe idanu da buɗewa a lokaci guda ya ce, “Yes Mr Specter muna saurarenka, wane tunani kayi?”.         Wani ƙarin girman kai Mr Specter yaji, dan haka ya gyara zamansa yana ajiye ƙatuwar sigarin hannunsa a ɗan bowl ɗin da yake tara tokar. “Sir ina ganin wannan sabon shirin zai dace da yin jifa da karan farautarmu a jikin fatsar da zata kamo mana wannan babban kifin. Ina nufin wannan yaron Ojo, dan aikinsa na ƙyau sosai, sai dai gaggawa zata hana masa yin doguwar tafiya dan Zak-Shadow ba sakarai bane”.        Murmurshi mai faɗi Oga Jush ya sake saki, sai kuma ya shiga tafama Mr Specter, dole suma sauran suka zama ƴan bin yarima akasha kiɗa kawai. Sai da sukai na fin sakan goma sha biyar sannan suka sarara. Oga Jush ya ce, “Lallai ka gane mi nake nufi a sabon shirin mu na ɓangaren haggu. Na ɓangaren dama kuwa lokaci yayi da tafiyarmu zata gayyato manyan babba da jaka na ƙasar nan, hakan ne kawai zai bamu damar farauto kifin cikin ruwa dake gadarar shi ISHA'U DUTSE NA RIMI ne BAKA FARGABA, to amma a ƙarshe shima ai yace SAI NA RUWA ko”.        A karo na farko saura ma suka fahimci darasin Ogan nasu, dan a tare suka kece da dariyar mugunta da na hango nasara. Sun sake tattauna abinda ya dace musamman akan fara horar da sabbin yara da maye gurbin Dagger a cikin yaransa da su Zak-Shadow basu kama ba da gaggawa, sai al'amarin Ojo da shima dole su gaggauta, daga haka taron ya watse zukatansu fes..... <><><><><><><>             Tun shigowarsu harabar gidan Zak-Shadow ya zubama baƙuwar motar dake fake a dai-dai ƙofar sashensu idanu. Koda Ja'afar ya kammala parking a inda ya dace har Ma'aruff ya fita ya buɗe masa sashen da yake hankalinsa nakan motar dai, a karo na farko shima Ma'aruff ɗin ya juya ya kalla motar, sai kuma ya juyo batare da jiran tambaya ba ya ce, “Dada motar Momyn su Ismat ce, jiya tazo da yamma itama”.        Kauda idanun nasa yay daga kan motar, batare da yace komai ba ya miƙama Ma'aruff ɗin wayoyinsa biyu. Ja'afar ma daya riga ya fito can gefen ya buɗe ya ɗauki briefcase ɗinsa. A tare suka rufe motar, sai kuma suka kalli juna suna murmushi ganin ya nufi sashen Mammah. Da sauri sukabi bayansa sun ɗan tafa kowa ya janye hannunsa yana yarfarwa da ƙoƙarin danne dariya duk a lokaci guda, sai kuma akai sa'a Dadan ya juyo zai kallesu ganin basu biyo shi ba. Da sauri suka gimtse fuskoki tare da zabura inda yake. Shaƙiyancin Ja'afar da Ma'aruff babu wanda bai sani ba, dan haka ma ya juya abinsa ya cigaba da tafiya suna take masa baya.        Sallamar su ta saka Mu'azz dirowa a kujera da gudu yayo ƙofa, cike da farin ciki yake faɗin, “Oyoyo Dada na”.         Guntun murmushi Zak-Shadow yayi, tare da tsayawa cak har Mu'azz ɗin ya ƙaraso inda yake ya rungumeshi. Kan yaron ya shafa, dai-dai shima Ja'afar na kai masa rankwashi da faɗin, “Ɗan iya kenan, wato Dadanka ma kai kaɗai, ai mu riƙo aka kawomu gidan naga”.      “Ai rankwashin da yafi wannan ya kamata kai masa”. Cewar Ma'aruff yana harar Mu'azz shima. Baki Mu'azz ya tura yana sake maƙale Zak-Shadow, dan in dai muguntar Uncle ɗin nasa biyu ne ya saba da ita a gidan. (Mu'azz ɗan Aunty Ummi ne, mahaifinsa ya rasu tun yana a ciki, dan watan Aunty Ummi ɗin bakwai da aure mijin nata ya rasu, ba kowa bane face yayan Imran, rasuwar ta gigitata dama ahalinsa da su su Zak-Shadow ɗin, har takai ta shiga wani yanayi na ciwo dole aka dawo da ita gida, a haka ta ƙarasa rainon cikin ta haifeshi. Ko bayan haihuwar tasa ma ansha fama da ita kafin ALLAH yasa ta koma dai-dai ta cigaba da shayar da shi, sai dai rainonsa gaba ɗaya Mammah da Mimi ne sukayi shi, har ya kai yaye. Ta jima a gida bata sake wani auren ba kusan shekara biyar dan tama koma karatu, sai da Zak-Shadow yay mata jan ido sannan. Ƴan gidan su Imran basu taɓa nuna kwace Mu'azz ba a hannunsu, sun san yana samun dukkan gata anan gidan, sai dai kuma suma hakan baya hana suyi masa nasu gatan. Dan haka Mu'azz shine jika na farko a gidan tunda har yanzu matar Dada Nabeeha bata haihu ba duk da kuwa tare akai bikinsu da Ummi ɗin a lokacin. Gashi a gidan sabon aurenta har ta sake yara biyu).        “Dada! Nima kaga Mammah ta kawo min sabuwar ƙanwa. Sunanta Nimrah”. Mu'azz yay maganar yana raba jikinsa dana Dada. Bai jira amsarsa ba ya bar wajen da ɗan gudu. Inda Nimrah take maƙure a tsakanin kujera tunda sukai sallama ta tashi ta buƴa a wajen dan har yanzu bayan Mammah da Mu'azz ɗin taƙi sakin jiki da kowa a gidan. Hannunta ya kamo cike da farin ciki ya ce, “Nina taso ga Dadana da nake baki labari yazo”.       Kafaɗa Nimrah ta maƙe alamar bazataje ba. Da damuwa a fuskar Mu'azz ya juya inda su Dada suke tsaye har yanzu yana kallon su. “Dada kaji wai bazata zo ba”.     Maimakon Zak-Shadow ya basu amsa sai ya shiga takawa a nutse har inda suke..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 53 __________________ https://vm.tiktok.com/ZSHcfQFhUuBVU-MpLRV/https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg==Wa.me/+2348140002981 Instagram https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg== Assalamu alaykum mutanen Sokoto Da kewaye Shin Ko kunsan cewa DIJAS DELICACY ashirye take Domin faranta ranku a bukukuna Da kowani irin even? Kama Daga samosa, doghnut, spring rolls meat pie, birthday cakes Da sauransu Bata tsaya anan ba tana amsar orders koda yaushe. Inda samosa kike nema frozen Ko fried duka tana dasu akan 3k 10pcs and she bakes daily🥰 Bata tsaya anan ba GA masu son gyaran jikinsu wata skin care tana siyarda best skin care products Kama Daga face wash, face cream,body butter, shower gel dadae sauransu tana aeka Kaya a kowani gari cikin aminci Da yardar allah GA no. Dinta kiyi saving Domin samun naki was.me/+2348140002981 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Duk da yanda yake maganar kai tsaye ta sosa zuciyar gwamna haka ya danne, dan harga ALLAH wani irin kwarjini da cika waje Zak-Shadow ɗin yay masa. Ya jima yana jin labarinsa da jarumtarsa a wajen yaransa musamman kwamishinan tsaro a tsakanin wannan rikicin, amma bai taɓa tunanin mutumin fa ya wuce yanda ake labarin nasa ba. Cikin danne abinda ke ransa da nuna aminta da zancen Zak-Shadow ɗin ya tabbatar masa zai yi ƙoƙarin yin abinda ya dace in sha ALLAHU daga yau zuwa gobe ma. Dan ya fahimci hukumar sojin ma wani girma na musamman take bashi.         Sun ƙara tattaunawa akan batun ƙara sojoji a cikin jejin kafin meeting ɗin ya tashi. A gidan Gwamnatin sukai sallar azhar, daga nan sukai zaman cin abinci da gwamna wanda Zak-Shadow yaƙi cin komai a wajen. Wannan ba sabon abu bane, dan duk wanda ya sanshi yasan ba'a ko'ina ake bashi abu yaci ba. Dan komai nashi da tsari. Kai da yawansu zasu iya ratsuwar basu taɓa ganin ya zauna cin abinci a gaban kowa ba. Idan zai ci abinci yakan killace kansa ne yaci a nutse.        Hakan da yayi ma ya ƙara saka jin shakkarsa a zukatan jami'an gwamnatin da akai zaman hadda gwamnan kansa. Dan bayan barowar su Zak-Shadow gidan gwamnatin sai da sukai ƴar gulma akan girman kan Zak-Shadow yayi yawa. Acewarsu yana Lieutenant Colonel kawai yana wannan isar da izza inaga ya zama General watarana, ai kowama ya shiga uku. Acewarsu wannan tsaf zai iya assasa juyin mulki a ƙasa.     Oho shi baima san sunayi ba, dan daga gidan gwamnatin airport ya wuce zai wuce Abuja. Jirginsu yana gab da tashi ma. Acan ya samu Ojo na jiranshi, shi ya saka ya saya masa tickets harda shi. Bai tsara matakin ɗauka akan Ojon ba, amma ya ƙudira sake jansa a jikinsa fiye da da saboda wani dalili nashi. Mintina baifi goma da zuwansa airport ɗin ba jirginsu ya ɗaga. Tafiyar da bata gaza awa ɗaya ba suka sauka birnin tarayya.       Anan airport suka rabu da Ojo, shi ya wuce barrak shi kuma ya samu su Ma'aruff sun zo ɗaukarshi. Cike da farin ciki suka rungumeshi kuwa. Ojo dake binsu da kallon ƙurilla ya miƙama Ja'afar ƴar briefcase ɗin Zak-Shadow ɗin dake hannunsa. Kafin ya ƙame tare da sara masa. Hannu kawai ya ɗaga masa batare daya kallesa ba, amma yana lure da kallon ƙurillar da yake ma su Ja'afar ɗin. Kaɗan ya cije lips ɗinsa, a ransa yana raya (Yaro tsaya matsayinka kada zancen ƴan duniya ya ruɗe ka. Dan in kace zaka tsalla gonar zuri'ata zan yanka maka kazar wahala ne kuma sai ka figeta da sili-silin gashi). A zahiri kam bayan mota da Ma'aruff ya buɗe masa ya shiga ya zauna. Suma duk gaba suka shiga Ja'afar yaja motar suka kama hanyar gida. Gaba ɗaya sun cika masa kunne da surutu kamar wasu ƙananun yara, shi dai yana jinsu da kunne kawai, wani lokacin kuma yakan yi murmurshi ko girgiza kai da faɗin, “ALLAH ya shiryeku” a taƙaice. A haka suka ƙaraso gidan.... (((★)))★(((★)))            Zantukan Ojo kaf sunje kunnen oga Jush shugaban ƙungiyar duhu. Dan haka ya tara meeting na gaggawa ga members ɗin ƙungiyar. Dama dukkan motsinsu a tsakanin nan a cikin meeting ɗin suke kala-kala. A duk sanda ya bada umarni babu mai wasa wajen amsa kiransa. Dan haka a yanzun ma cikin gaggawa suka gama hallara. Kowa da kowa yazo idan ka cire Dagger da dama ba akowane zama suke zama da shi ɗin ba sai suna buƙatar hakan saboda a wajensu sunan karen farauta kawai yake amsawa. Saɓanin kowanne zama yau oga ne ya fara magana kafin ma su tambayi dalilin zaman.          Sai da ya fara kunna musu recording ɗin muryar Ojo da aka tura masa duk suka saurara. Batare da jiran cewar wani a cikinsu ba ya cigaba da faɗin, “Zamu rushe wasu ɓangarori na plan c”.       Gaba ɗayansu kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu, cikin alamar tambayar juna a yanayin kurame suke ɗan jujjuya hannayensu. Wasu ko na ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki irin na suma basu gane ba. Oga Jush dake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya yay ƙaramar gyaran murya daya dakatar da gungunan nasu dake tashi a ɗakin. Tsitt sukayi gaba ɗaya, tare da maida hankali kansa.        Sai da yaja sakanni cike da shan ƙamshi sannan ya cigaba da magana. “Kamar yanda na faɗa bama buƙatar wasu ɓangarori na plan c kwata-kwata saboda na fahimci wani abu a yanzu”.         “Kamar mi kenan oga?”.     “Muna buƙatar su Dagger a raye. Dan haka Viper ka dakatar da plan ɗinmu na tura masu kashesu”.           “Yanda kace haka za'ai Sir. Amma miyasa kace hakan? Bayan kasan zaman mutanen nan a raye hannun sojojin nan komai zai iya faruwa, ciki kuwa harda sanin mu su wanene. Musamman haɗarin yafi girma akan Dagger da shi ya sammu. Gara ma sauran su Dagger ɗin suka sani”.        Tabbas zancenka a kan hanya yake kuma kana kan dai-dai Viper. Amma abinda nake son ku tuna ba ko yaushe ake iya kama tsuntsu ta baki ba, dan wani tsuntsu ba hatsi yake ci wajen ƙoto ba ababen cikin ruwa ne abincinsa. Ba kashe Dagger ne mafita ba, yin amfani da shi wajen kama mutumin nan ta wuya shine ya dace”.       Sake kallon kallo suka shiga yi, dan su sam basu wani fahimci komai ba. Cike da izza Mr Specter sarkin ƴan girman kai tamkar ogan nasu ya furta, “Na fahimci abinda kake nufi Oga, kuma nayi na'am da wannan tsarin. Kai tsaye ma ni har wani ƙyaƙyƙyawan tunani yazo min”.       Karo na farko Oga Jush ya saki murmurshi idonsa akan Mr Specter, shiyyasa yake matuƙar son shi, dan shima akwai kwanya. Yana wani jinjina kai da lumshe idanu da buɗewa a lokaci guda ya ce, “Yes Mr Specter muna saurarenka, wane tunani kayi?”.         Wani ƙarin girman kai Mr Specter yaji, dan haka ya gyara zamansa yana ajiye ƙatuwar sigarin hannunsa a ɗan bowl ɗin da yake tara tokar. “Sir ina ganin wannan sabon shirin zai dace da yin jifa da karan farautarmu a jikin fatsar da zata kamo mana wannan babban kifin. Ina nufin wannan yaron Ojo, dan aikinsa na ƙyau sosai, sai dai gaggawa zata hana masa yin doguwar tafiya dan Zak-Shadow ba sakarai bane”.        Murmurshi mai faɗi Oga Jush ya sake saki, sai kuma ya shiga tafama Mr Specter, dole suma sauran suka zama ƴan bin yarima akasha kiɗa kawai. Sai da sukai na fin sakan goma sha biyar sannan suka sarara. Oga Jush ya ce, “Lallai ka gane mi nake nufi a sabon shirin mu na ɓangaren haggu. Na ɓangaren dama kuwa lokaci yayi da tafiyarmu zata gayyato manyan babba da jaka na ƙasar nan, hakan ne kawai zai bamu damar farauto kifin cikin ruwa dake gadarar shi ISHA'U DUTSE NA RIMI ne BAKA FARGABA, to amma a ƙarshe shima ai yace SAI NA RUWA ko”.        A karo na farko saura ma suka fahimci darasin Ogan nasu, dan a tare suka kece da dariyar mugunta da na hango nasara. Sun sake tattauna abinda ya dace musamman akan fara horar da sabbin yara da maye gurbin Dagger a cikin yaransa da su Zak-Shadow basu kama ba da gaggawa, sai al'amarin Ojo da shima dole su gaggauta, daga haka taron ya watse zukatansu fes..... <><><><><><><>             Tun shigowarsu harabar gidan Zak-Shadow ya zubama baƙuwar motar dake fake a dai-dai ƙofar sashensu idanu. Koda Ja'afar ya kammala parking a inda ya dace har Ma'aruff ya fita ya buɗe masa sashen da yake hankalinsa nakan motar dai, a karo na farko shima Ma'aruff ɗin ya juya ya kalla motar, sai kuma ya juyo batare da jiran tambaya ba ya ce, “Dada motar Momyn su Ismat ce, jiya tazo da yamma itama”.        Kauda idanun nasa yay daga kan motar, batare da yace komai ba ya miƙama Ma'aruff ɗin wayoyinsa biyu. Ja'afar ma daya riga ya fito can gefen ya buɗe ya ɗauki briefcase ɗinsa. A tare suka rufe motar, sai kuma suka kalli juna suna murmushi ganin ya nufi sashen Mammah. Da sauri sukabi bayansa sun ɗan tafa kowa ya janye hannunsa yana yarfarwa da ƙoƙarin danne dariya duk a lokaci guda, sai kuma akai sa'a Dadan ya juyo zai kallesu ganin basu biyo shi ba. Da sauri suka gimtse fuskoki tare da zabura inda yake. Shaƙiyancin Ja'afar da Ma'aruff babu wanda bai sani ba, dan haka ma ya juya abinsa ya cigaba da tafiya suna take masa baya.        Sallamar su ta saka Mu'azz dirowa a kujera da gudu yayo ƙofa, cike da farin ciki yake faɗin, “Oyoyo Dada na”.         Guntun murmushi Zak-Shadow yayi, tare da tsayawa cak har Mu'azz ɗin ya ƙaraso inda yake ya rungumeshi. Kan yaron ya shafa, dai-dai shima Ja'afar na kai masa rankwashi da faɗin, “Ɗan iya kenan, wato Dadanka ma kai kaɗai, ai mu riƙo aka kawomu gidan naga”.      “Ai rankwashin da yafi wannan ya kamata kai masa”. Cewar Ma'aruff yana harar Mu'azz shima. Baki Mu'azz ya tura yana sake maƙale Zak-Shadow, dan in dai muguntar Uncle ɗin nasa biyu ne ya saba da ita a gidan. (Mu'azz ɗan Aunty Ummi ne, mahaifinsa ya rasu tun yana a ciki, dan watan Aunty Ummi ɗin bakwai da aure mijin nata ya rasu, ba kowa bane face yayan Imran, rasuwar ta gigitata dama ahalinsa da su su Zak-Shadow ɗin, har takai ta shiga wani yanayi na ciwo dole aka dawo da ita gida, a haka ta ƙarasa rainon cikin ta haifeshi. Ko bayan haihuwar tasa ma ansha fama da ita kafin ALLAH yasa ta koma dai-dai ta cigaba da shayar da shi, sai dai rainonsa gaba ɗaya Mammah da Mimi ne sukayi shi, har ya kai yaye. Ta jima a gida bata sake wani auren ba kusan shekara biyar dan tama koma karatu, sai da Zak-Shadow yay mata jan ido sannan. Ƴan gidan su Imran basu taɓa nuna kwace Mu'azz ba a hannunsu, sun san yana samun dukkan gata anan gidan, sai dai kuma suma hakan baya hana suyi masa nasu gatan. Dan haka Mu'azz shine jika na farko a gidan tunda har yanzu matar Dada Nabeeha bata haihu ba duk da kuwa tare akai bikinsu da Ummi ɗin a lokacin. Gashi a gidan sabon aurenta har ta sake yara biyu).        “Dada! Nima kaga Mammah ta kawo min sabuwar ƙanwa. Sunanta Nimrah”. Mu'azz yay maganar yana raba jikinsa dana Dada. Bai jira amsarsa ba ya bar wajen da ɗan gudu. Inda Nimrah take maƙure a tsakanin kujera tunda sukai sallama ta tashi ta buƴa a wajen dan har yanzu bayan Mammah da Mu'azz ɗin taƙi sakin jiki da kowa a gidan. Hannunta ya kamo cike da farin ciki ya ce, “Nina taso ga Dadana da nake baki labari yazo”.       Kafaɗa Nimrah ta maƙe alamar bazataje ba. Da damuwa a fuskar Mu'azz ya juya inda su Dada suke tsaye har yanzu yana kallon su. “Dada kaji wai bazata zo ba”.     Maimakon Zak-Shadow ya basu amsa sai ya shiga takawa a nutse har inda suke..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 54 __________________ https://vm.tiktok.com/ZSHcfQFhUuBVU-MpLRV/https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg==Wa.me/+2348140002981 Instagram https://www.instagram.com/dijas_delicacy_?igsh=MWp3MThqcXlsZXB2eg== Assalamu alaykum mutanen Sokoto Da kewaye Shin Ko kunsan cewa DIJAS DELICACY ashirye take Domin faranta ranku a bukukuna Da kowani irin even? Kama Daga samosa, doghnut, spring rolls meat pie, birthday cakes Da sauransu Bata tsaya anan ba tana amsar orders koda yaushe. Inda samosa kike nema frozen Ko fried duka tana dasu akan 3k 10pcs and she bakes daily🥰 Bata tsaya anan ba GA masu son gyaran jikinsu wata skin care tana siyarda best skin care products Kama Daga face wash, face cream,body butter, shower gel dadae sauransu tana aeka Kaya a kowani gari cikin aminci Da yardar allah GA no. Dinta kiyi saving Domin samun naki was.me/+2348140002981 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Duk da yanda yake maganar kai tsaye ta sosa zuciyar gwamna haka ya danne, dan harga ALLAH wani irin kwarjini da cika waje Zak-Shadow ɗin yay masa. Ya jima yana jin labarinsa da jarumtarsa a wajen yaransa musamman kwamishinan tsaro a tsakanin wannan rikicin, amma bai taɓa tunanin mutumin fa ya wuce yanda ake labarin nasa ba. Cikin danne abinda ke ransa da nuna aminta da zancen Zak-Shadow ɗin ya tabbatar masa zai yi ƙoƙarin yin abinda ya dace in sha ALLAHU daga yau zuwa gobe ma. Dan ya fahimci hukumar sojin ma wani girma na musamman take bashi.         Sun ƙara tattaunawa akan batun ƙara sojoji a cikin jejin kafin meeting ɗin ya tashi. A gidan Gwamnatin sukai sallar azhar, daga nan sukai zaman cin abinci da gwamna wanda Zak-Shadow yaƙi cin komai a wajen. Wannan ba sabon abu bane, dan duk wanda ya sanshi yasan ba'a ko'ina ake bashi abu yaci ba. Dan komai nashi da tsari. Kai da yawansu zasu iya ratsuwar basu taɓa ganin ya zauna cin abinci a gaban kowa ba. Idan zai ci abinci yakan killace kansa ne yaci a nutse.        Hakan da yayi ma ya ƙara saka jin shakkarsa a zukatan jami'an gwamnatin da akai zaman hadda gwamnan kansa. Dan bayan barowar su Zak-Shadow gidan gwamnatin sai da sukai ƴar gulma akan girman kan Zak-Shadow yayi yawa. Acewarsu yana Lieutenant Colonel kawai yana wannan isar da izza inaga ya zama General watarana, ai kowama ya shiga uku. Acewarsu wannan tsaf zai iya assasa juyin mulki a ƙasa.     Oho shi baima san sunayi ba, dan daga gidan gwamnatin airport ya wuce zai wuce Abuja. Jirginsu yana gab da tashi ma. Acan ya samu Ojo na jiranshi, shi ya saka ya saya masa tickets harda shi. Bai tsara matakin ɗauka akan Ojon ba, amma ya ƙudira sake jansa a jikinsa fiye da da saboda wani dalili nashi. Mintina baifi goma da zuwansa airport ɗin ba jirginsu ya ɗaga. Tafiyar da bata gaza awa ɗaya ba suka sauka birnin tarayya.       Anan airport suka rabu da Ojo, shi ya wuce barrak shi kuma ya samu su Ma'aruff sun zo ɗaukarshi. Cike da farin ciki suka rungumeshi kuwa. Ojo dake binsu da kallon ƙurilla ya miƙama Ja'afar ƴar briefcase ɗin Zak-Shadow ɗin dake hannunsa. Kafin ya ƙame tare da sara masa. Hannu kawai ya ɗaga masa batare daya kallesa ba, amma yana lure da kallon ƙurillar da yake ma su Ja'afar ɗin. Kaɗan ya cije lips ɗinsa, a ransa yana raya (Yaro tsaya matsayinka kada zancen ƴan duniya ya ruɗe ka. Dan in kace zaka tsalla gonar zuri'ata zan yanka maka kazar wahala ne kuma sai ka figeta da sili-silin gashi). A zahiri kam bayan mota da Ma'aruff ya buɗe masa ya shiga ya zauna. Suma duk gaba suka shiga Ja'afar yaja motar suka kama hanyar gida. Gaba ɗaya sun cika masa kunne da surutu kamar wasu ƙananun yara, shi dai yana jinsu da kunne kawai, wani lokacin kuma yakan yi murmurshi ko girgiza kai da faɗin, “ALLAH ya shiryeku” a taƙaice. A haka suka ƙaraso gidan.... (((★)))★(((★)))            Zantukan Ojo kaf sunje kunnen oga Jush shugaban ƙungiyar duhu. Dan haka ya tara meeting na gaggawa ga members ɗin ƙungiyar. Dama dukkan motsinsu a tsakanin nan a cikin meeting ɗin suke kala-kala. A duk sanda ya bada umarni babu mai wasa wajen amsa kiransa. Dan haka a yanzun ma cikin gaggawa suka gama hallara. Kowa da kowa yazo idan ka cire Dagger da dama ba akowane zama suke zama da shi ɗin ba sai suna buƙatar hakan saboda a wajensu sunan karen farauta kawai yake amsawa. Saɓanin kowanne zama yau oga ne ya fara magana kafin ma su tambayi dalilin zaman.          Sai da ya fara kunna musu recording ɗin muryar Ojo da aka tura masa duk suka saurara. Batare da jiran cewar wani a cikinsu ba ya cigaba da faɗin, “Zamu rushe wasu ɓangarori na plan c”.       Gaba ɗayansu kallon kallo suka shiga yi a tsakaninsu, cikin alamar tambayar juna a yanayin kurame suke ɗan jujjuya hannayensu. Wasu ko na ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki irin na suma basu gane ba. Oga Jush dake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya yay ƙaramar gyaran murya daya dakatar da gungunan nasu dake tashi a ɗakin. Tsitt sukayi gaba ɗaya, tare da maida hankali kansa.        Sai da yaja sakanni cike da shan ƙamshi sannan ya cigaba da magana. “Kamar yanda na faɗa bama buƙatar wasu ɓangarori na plan c kwata-kwata saboda na fahimci wani abu a yanzu”.         “Kamar mi kenan oga?”.     “Muna buƙatar su Dagger a raye. Dan haka Viper ka dakatar da plan ɗinmu na tura masu kashesu”.           “Yanda kace haka za'ai Sir. Amma miyasa kace hakan? Bayan kasan zaman mutanen nan a raye hannun sojojin nan komai zai iya faruwa, ciki kuwa harda sanin mu su wanene. Musamman haɗarin yafi girma akan Dagger da shi ya sammu. Gara ma sauran su Dagger ɗin suka sani”.        Tabbas zancenka a kan hanya yake kuma kana kan dai-dai Viper. Amma abinda nake son ku tuna ba ko yaushe ake iya kama tsuntsu ta baki ba, dan wani tsuntsu ba hatsi yake ci wajen ƙoto ba ababen cikin ruwa ne abincinsa. Ba kashe Dagger ne mafita ba, yin amfani da shi wajen kama mutumin nan ta wuya shine ya dace”.       Sake kallon kallo suka shiga yi, dan su sam basu wani fahimci komai ba. Cike da izza Mr Specter sarkin ƴan girman kai tamkar ogan nasu ya furta, “Na fahimci abinda kake nufi Oga, kuma nayi na'am da wannan tsarin. Kai tsaye ma ni har wani ƙyaƙyƙyawan tunani yazo min”.       Karo na farko Oga Jush ya saki murmurshi idonsa akan Mr Specter, shiyyasa yake matuƙar son shi, dan shima akwai kwanya. Yana wani jinjina kai da lumshe idanu da buɗewa a lokaci guda ya ce, “Yes Mr Specter muna saurarenka, wane tunani kayi?”.         Wani ƙarin girman kai Mr Specter yaji, dan haka ya gyara zamansa yana ajiye ƙatuwar sigarin hannunsa a ɗan bowl ɗin da yake tara tokar. “Sir ina ganin wannan sabon shirin zai dace da yin jifa da karan farautarmu a jikin fatsar da zata kamo mana wannan babban kifin. Ina nufin wannan yaron Ojo, dan aikinsa na ƙyau sosai, sai dai gaggawa zata hana masa yin doguwar tafiya dan Zak-Shadow ba sakarai bane”.        Murmurshi mai faɗi Oga Jush ya sake saki, sai kuma ya shiga tafama Mr Specter, dole suma sauran suka zama ƴan bin yarima akasha kiɗa kawai. Sai da sukai na fin sakan goma sha biyar sannan suka sarara. Oga Jush ya ce, “Lallai ka gane mi nake nufi a sabon shirin mu na ɓangaren haggu. Na ɓangaren dama kuwa lokaci yayi da tafiyarmu zata gayyato manyan babba da jaka na ƙasar nan, hakan ne kawai zai bamu damar farauto kifin cikin ruwa dake gadarar shi ISHA'U DUTSE NA RIMI ne BAKA FARGABA, to amma a ƙarshe shima ai yace SAI NA RUWA ko”.        A karo na farko saura ma suka fahimci darasin Ogan nasu, dan a tare suka kece da dariyar mugunta da na hango nasara. Sun sake tattauna abinda ya dace musamman akan fara horar da sabbin yara da maye gurbin Dagger a cikin yaransa da su Zak-Shadow basu kama ba da gaggawa, sai al'amarin Ojo da shima dole su gaggauta, daga haka taron ya watse zukatansu fes..... <><><><><><><>             Tun shigowarsu harabar gidan Zak-Shadow ya zubama baƙuwar motar dake fake a dai-dai ƙofar sashensu idanu. Koda Ja'afar ya kammala parking a inda ya dace har Ma'aruff ya fita ya buɗe masa sashen da yake hankalinsa nakan motar dai, a karo na farko shima Ma'aruff ɗin ya juya ya kalla motar, sai kuma ya juyo batare da jiran tambaya ba ya ce, “Dada motar Momyn su Ismat ce, jiya tazo da yamma itama”.        Kauda idanun nasa yay daga kan motar, batare da yace komai ba ya miƙama Ma'aruff ɗin wayoyinsa biyu. Ja'afar ma daya riga ya fito can gefen ya buɗe ya ɗauki briefcase ɗinsa. A tare suka rufe motar, sai kuma suka kalli juna suna murmushi ganin ya nufi sashen Mammah. Da sauri sukabi bayansa sun ɗan tafa kowa ya janye hannunsa yana yarfarwa da ƙoƙarin danne dariya duk a lokaci guda, sai kuma akai sa'a Dadan ya juyo zai kallesu ganin basu biyo shi ba. Da sauri suka gimtse fuskoki tare da zabura inda yake. Shaƙiyancin Ja'afar da Ma'aruff babu wanda bai sani ba, dan haka ma ya juya abinsa ya cigaba da tafiya suna take masa baya.        Sallamar su ta saka Mu'azz dirowa a kujera da gudu yayo ƙofa, cike da farin ciki yake faɗin, “Oyoyo Dada na”.         Guntun murmushi Zak-Shadow yayi, tare da tsayawa cak har Mu'azz ɗin ya ƙaraso inda yake ya rungumeshi. Kan yaron ya shafa, dai-dai shima Ja'afar na kai masa rankwashi da faɗin, “Ɗan iya kenan, wato Dadanka ma kai kaɗai, ai mu riƙo aka kawomu gidan naga”.      “Ai rankwashin da yafi wannan ya kamata kai masa”. Cewar Ma'aruff yana harar Mu'azz shima. Baki Mu'azz ya tura yana sake maƙale Zak-Shadow, dan in dai muguntar Uncle ɗin nasa biyu ne ya saba da ita a gidan. (Mu'azz ɗan Aunty Ummi ne, mahaifinsa ya rasu tun yana a ciki, dan watan Aunty Ummi ɗin bakwai da aure mijin nata ya rasu, ba kowa bane face yayan Imran, rasuwar ta gigitata dama ahalinsa da su su Zak-Shadow ɗin, har takai ta shiga wani yanayi na ciwo dole aka dawo da ita gida, a haka ta ƙarasa rainon cikin ta haifeshi. Ko bayan haihuwar tasa ma ansha fama da ita kafin ALLAH yasa ta koma dai-dai ta cigaba da shayar da shi, sai dai rainonsa gaba ɗaya Mammah da Mimi ne sukayi shi, har ya kai yaye. Ta jima a gida bata sake wani auren ba kusan shekara biyar dan tama koma karatu, sai da Zak-Shadow yay mata jan ido sannan. Ƴan gidan su Imran basu taɓa nuna kwace Mu'azz ba a hannunsu, sun san yana samun dukkan gata anan gidan, sai dai kuma suma hakan baya hana suyi masa nasu gatan. Dan haka Mu'azz shine jika na farko a gidan tunda har yanzu matar Dada Nabeeha bata haihu ba duk da kuwa tare akai bikinsu da Ummi ɗin a lokacin. Gashi a gidan sabon aurenta har ta sake yara biyu).        “Dada! Nima kaga Mammah ta kawo min sabuwar ƙanwa. Sunanta Nimrah”. Mu'azz yay maganar yana raba jikinsa dana Dada. Bai jira amsarsa ba ya bar wajen da ɗan gudu. Inda Nimrah take maƙure a tsakanin kujera tunda sukai sallama ta tashi ta buƴa a wajen dan har yanzu bayan Mammah da Mu'azz ɗin taƙi sakin jiki da kowa a gidan. Hannunta ya kamo cike da farin ciki ya ce, “Nina taso ga Dadana da nake baki labari yazo”.       Kafaɗa Nimrah ta maƙe alamar bazataje ba. Da damuwa a fuskar Mu'azz ya juya inda su Dada suke tsaye har yanzu yana kallon su. “Dada kaji wai bazata zo ba”.     Maimakon Zak-Shadow ya basu amsa sai ya shiga takawa a nutse har inda suke..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 55_ __________________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LkEgiP5qOEo9YDYjaeZLLc?mode=ems_wa_t✍️✍️ Assalamu Alaikum my people dafatan kunanan cikin aminci sunana ummuh sayyeed yar mutan Chadian traditional medicine center Zaria dealer in all kinds of magungunan mata turarukan wuta sudaniss dilka skin care products at home my people bazamafa a kwai zafafan promo damukeyi in Sha allahu zuwa on 15 zamugama sannan gareku Yan Kano free ne kayanki zasuzo miki amma fa karyazo bayan mungama promo kuce kyauta ne aa zakibiya kudi nagode takuce yar mutan Chadian mai gyaran ciki dawaje 💃💃 please banda maza,❌maza❌ In kinada matsala wadda zamu iya taimaka miki 09065504546 Ga PRODUCTS DINMU KAMAR HAKA MAGANIN SANYI TSUMIN BOM MADARAR TABAJE GORON TULA SYRUP ZUMAR SHADAMATSIN GARIN YAUKAYAUKA EMERGENCY GARIN KINFI KAZA DADI SIRRIN MALLAKAR KASA SIRRAN GIDANKI DAHUWAR KAZA DAHUWAR CICCIBI DAHUWAR YAN SHILA HMM BAZASU IRGUBA INA GODIYA SOSAI MY PEOPLE 🥰🥰 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Da mugun ƙarfi Colonel ya buga desk ɗinsa yana mai zazzaro idanu da ture takardun daya gama karantawa, cikin ƙaraji ya furta, “Lt. Col. Garba! Kana da hankali kuwa zaka kawoma mutane wannan maganar banzar. Ko gaskiya ne maganar da ake faɗa akan kana kishi da Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed ne?”.        “I'm sorry sir! Wannan shati faɗi na mutane ne kawai da son haddasa fitina. Dan kawai abinda ya faru tsakanina da shi a NDA na ƙuruciya sai a kalli abu mai muhimmanci irin wannan matsayin rashin jituwa. Sir nifa soja ne, yana da ƙyau na fargar da hukumata ɓarna idan naga zata afku balle ma irin wannan. Sannan ban kawo shi gareka kai tsaye ba sai da na tabbatar, ina kuma da shaidu sosai da suma suka gani kuma akayi a gabansu a cikin yaransa”.          Idanu kawai Colonel Galadima ya zubama Lt. Col Garba. Sai kuma ya sake jawo takardun yana sake dubawa ɗaya bayan ɗaya. Sosai zuciyar ke rawa, dan kuwa duk wanda ya kwana ya tashi yasan ƙwazo da gaskiyar Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu, sai dai isa cewa zai yi rejecting ɗin wannan report ɗin batare da bincike ba. Karo na farko ya zari tissue ya goge gumin daya tsatstsafo masa a goshi. Cikin bada umarni yace da Lt. Col. Garba, “Okay zaka iya tafiya”.       Ba haka Lt. Col. Garba yaso ba, amma sai ya miƙe cikin nuna jimami ya fita a office ɗin. Koda ya fita Colonel yafi minti sha biyar yana sake duba report ɗin kafin ya haƙura ya miƙe da takardun a hannu zuwa office ɗin Brigadier General, dan bashi da hurumin cigaba da riƙe report ɗin a wajensa dole ya kaisa sama saboda maganar babba ce sosai. Bayan an bashi izinin shiga ya ƙame tare da salute duk a lokaci guda. Brigadier General Abraham Yohana daketa rubuce-rubuce batare daya ɗago ba yay masa nuni da kujera. Zama Colonel yayi, cike da girmamawa ya ajiye file ɗin hannunsa gaban Brigadier General.        “Sir wata babbar magana ce da ake buƙatar dubata da gaggawa”.    Karo na farko Brigadier General ya ɗago yana kallonsa, sai kuma ya maida kansa ga rubutunsa a taƙaice ya ce, “Mike faruwa Colonel Galadima?”.           “Report ne muka samu akan Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu game da wannan rikicin daya jagoranta.”      Batare daya ɗago ba ya ce, “Ba ɗazun aka gama meeting da ministan tsaro a fadar shugaban ƙasa ba akan karrama shi, shi da duk wanda akai yaƙi da bizne waɗanda aka rasa. Kuma harda kai ka sani”.           “Hakane sir! Amma fa al'amarin na neman canjawa ne. Dan wannan report ɗin na nuni da Lt. Col Haysam Abdul-rasheed Shehu da hannunsa akan shirya komai daya faru, hasalima shugaban ƴan ta'addan dake hannun jami'an bincike ya tabbatar da shima yana cikin ogans......”      A fusace Brigadier General ya katse Colonel. “Wace kalar banzar magana ce wannan. Haysam!? Haysam! Dai? Za'ace yana tare da ƴan ta'adda?”.          “Wlhy sir nima abin ya girgizani matuƙa. Amma ka duba ka ga report ɗin dai. An kawo shi ne tun daga jihar da abin ya faru. Kuma banan kawai ba har gidan gwamnati ya isa”.       File ɗin Brigadier General ya ɗauka ya shiga dubawa. Cikin ɓacin rai yay wurgi da takardar yana faɗin, “Impossible. Har abada Haysam bazai taɓa koda ɗagama ƴan ta'adda ƙafa ba balle haɗa hannu da su. Wannan ma zancen banza ne, ba kuma Haysam ake son ɓatama suna ba hukumar mu ake son ɓatama suna”.           Shi kansa Colonel Galadima abinda zuciyarsa ke bashi kenan. Amma harga ALLAH zuciyarsa ta tsorata, dan ya fahimci wannan shiri ne mai ƙarfi da girma. Musamman idan akai dubi da yanda aka shirya report ɗin kansa..          Cikin ƙanƙanin lokaci takardar ta gama zagaye Headquarter ɗin. Babu shiri manyan suka haɗa meeting na gaggawa. Sai dai ko farawa basuyi ba kira ya samu General na kuma gaggawa daga ministan tsaro bisa umarnin shugaban ƙasa dake son ganinsa da gaggawa a gidan gwamnati cikin sa'oi biyu kawai. Dole yabar nasu meeting ɗin akan Lieutenant General ya jagoranta. Shi kuma ya wuce amsa kiran shugaban ƙasar...... <><><><><><><>          Yanda Nabeeha ke ribzar kuka ba ƙaramin sake zafafa zuciyar Mammah take ba. Amma ta danne cikin bada umarni tace ma Ma'aruff.      “Kira min Dadan ku”.   Sai da ya watsama Nabeeha da Momynta harara sannan ya miƙe. Shima Ja'afar dake a wuya miƙewar yayi. Ammar kam da shigowar shi falon kenan baiji maganganun da Momyn Nabeeha ta faɗa ba tsaye yay daga bakin kofa kawai yana kallon Nabeeha ɗin. Har Ma'aruff na neman bugeshi. Kauce masa yay ya fita. Ja'afar ma ya shiga kitchen yana kai waya a kunnensa. Bayan gaisuwa ya zayyanema Uncle Nasiru daya kira komai dake shirin faruwa a gidan. Ba ƙaramin tashi hankalin Uncle Nasiru yayi ba da jin ɓacin rai, cikin sauri yace gashi nan zuwa gidan. (Shima dai Uncle Nasiru yanzu a nan Abuja yake, dan anan yake aiki, kuma anan cikin anguwar yake zaune dan da ƙoƙarin Zak-Shadow ma ya samu filin daya gina gidan, dan haka basu da nisa da su sosai).       Ja'afar na yanke wayar ya kira Imran shima. Shima rai ɓace ya ce, “What! Yarinyar nan nada hankali kuwa?”.          “Yaya dama ai mahaukaciyar ce kune baku fahimta ba. Wlhy badan mutuncin Uncle Nasiru ba yau sai na fasa mata baki na karyar ƙafar uwar tata”.        “No. Ba wanda ya aikeka kai kuma. Gani nan zuwa gidan nima”. Daga haka ya yanke kiran...         A lokacin da can zaman meetings ya ɓarke akan Zak-Shadow da alama nan wata sabuwar ƙurar ke shirin tashi saboda baƙin kishin matarsa Nabeeha da rashin hankalin uwarta dake bata goyon baya saboda wani burinta na banza da wofi. Kasancewar Ma'aruff ya iske Dadan su na wanka sai da ya jirashi, dan haka kusan lokaci ɗaya suka shigo falon Mammah da Uncle Nasiru. Suna zama Imran na shigowa. A can kuwa Biebah dake kitchen tana aiki taji komai tuni ta fice can baya tana kuka ta kira Aunty Ummi da Aunty Mommy da ma Aunty Mimi ta gaya musu abinda ke shirin faruwa. Ai tuni suma kowa ya ɗakko hanyar zuwa gidan. Yo ubanwa ya isa taɓa musu Dada a zauna lafiya ba'atada yaƙin duniya na uku ba. Ai wlhy Mammah ce kawai keda wannan isar, itama dan uwa ce babu yanda zasuyi da ita. Duk wannan abin dake faruwa Bilal baya gidan, ya tafi saka Nimrah a islamiyyar su Mu'azz, boko ma in sha ALLAHU gobe-gobe za'a kaita. Dan tunda Mammah ta gama jin komai a wajen Zak-Shadow ta yanke shawarar a yau ɗin nan za'a saka Nimrah islamiyya gobe boko ko hakan zai sa ta saki jikinta. Dama gashi anyi sa'a cikin satin nan aka koma hutu kuma zangon farko ne.            Tunda Zak-Shadow ya shigo falon yaji zuciyarsa ta sake zuwa wuya. Da ƙyar ya iya daurewa ya gaida Uncle Nasiru ya samu kujera ya zauna, tare da jingina bayansa ya lumshe idanunsa kawai yana sauraren zagin da Uncle Nasiru kema Nabeeha da ke neman komawa faɗa tsakaninsa da Momynta data saka baki. Sai da Mammah ta basu haƙuri da nuna musu kuskuren abin kunyar da suke neman yi agaban yara sannan sukai shiru kowa na huci.      Dai-dai nan Imran ya shigo da sallama shima. Kai tsaye ya ƙaraso falon dan shima ɗan gida ne, har bedroom ɗin Mammah shiga yake. Yanzu ma sai da ya gaida su ita da Uncle Nasiru da Momyn Nabeeha su Ma'aruff suka gaisheshi shima. Da ido Mammah taima su Ma'aruff ɗin umarnin fita a falon. Badan sun so hakan ba suka fita. Amma sun san duk rintsi Mammah bata maganar data shafi Dada a gabansu in har bata farin ciki bace, amma a ganinsu wannan tasha banban ai, sai dai duk da haka an kora su waje.           Bayan gama fitarsu da rufe ƙofa suka koma jikin windows suka maƙe, dan sun fi son jin komai yanda zasu ci ƙaniyar Nabeeha da lasisi. Mammah da bata san suna laɓe ba kai tsaye ta maida kallonta ga Zak-Shadow.     “Muhammad”. Ta kira sunansa kamar yanda ta saba. Idanunsa da suka rine ya buɗe, sai kuma ya gyara zamansa cike da girmamawa ya amsa mata.         “Miya haɗaka da matarka haka da zafi har kake zaginta da korota daga ɗakinka cewar zaka daketa”.      A karo na biyu ya ɗan juya ya kalli sashen da Nabeeha take manne da Momynta, sai kuma ya dawo da kallonsa ga Mammah. Ƙaramin murmurshin takaici yayi, mamakin wannan ƙarya ta Nabeeha na cizonsa, amma sai ya danne, cike da girmamawa ya ce, “Tazo min da wata maganar banza ne akan yarinyar nan da kuka taho da ita daga asibiti Mammah”.          “A gani na ai bayani ya kamata kai mata ba kakkausan lafazi ba.....”      “Miye wani kakkausan lafazi zagi dai.”      Momyn Nabeeha ta katse Mammah a hasale.       “ALLAH kika ƙara magana sai kin bar falon nan”. Cewar Uncle Nasiru yana nuna Momyn Nabeeha. Itama a hasale ta ce, “To ubana”.       “Dan ALLAH kuyi haƙuri Yaya”. Mammah ta faɗa cikin tausasawa, sai kuma ta cigaba da faɗin, “Muhammad ita yarinyar wacece a wajenka? Ƴar waye? Miyasa kazo da ita nan?”. Ta jera masa tambayoyin duk da kuwa ita ya mata bayanin komai ɗazun..         Iska ya furzar mai ɗacin gaske, dan haka Imran yay saurin faɗin, “Mammah bara nai muku bayanin komai”.        “Ai bakai aka tambaya ba”.    Momyn Nabeeha ta faɗa tana hararar Imran.     A hasale Uncle Nasiru ya ce, “Shine kuma zai bada amsa, kai Imrana faɗi muna jinka. Kai Imran ya jinjina ma Uncle Nasiru yana gyara zama. Yayin da a jikin Windows su Ja'afar kejin kamar su tsallako falon su daki bakin Momyn Nabeeha, dan zuwa yanzu suma su Aunty Ummi sun iso, tuni kuma su Ma'aruff sun musu bayanin komai dan haka suka nema wajen maƙewa suma ayi komai da su.        “Wannan yarinya sunanta Naja'atu, amma iyayenta na kiranta Nimrah saboda sunan kakarta taci...........” tsaf Imran ya zayyane musu komai, sai dai banda ainahin halin da mahaifinta ke ciki, hasalima kamar yanda Umma ta roƙa sai ya sanar musu mahaifinta ya rasu a rikicin kamar mahaifiyar tata. Ba ƙaramin daɗin hakan da yayi Zak-Shadow da Mammah sukaji ba. Dan ita Mammah komai sai da Dadan ya sanar mata bai ɓoye ba.      Cikin damuwa sosai Uncle Nasiru ke jimanta al'amarin, da tsakanin jin tausayin Nimrah a ransa. Amma a mamakin kowa sai ji sukai Nabeeha ta ce, “Wlhy ban yarda ba, Imran kai dama ai munafuki ne nasani, tun ba yau ba nasan ba ƙaunata kake yi ba. Banda ma rainin hankali in har da gaskene abinda ka faɗa ɗin ai ba ita kaɗai bace aka kashewa iyaye, miyasa su sauran yaran kuka barsu can ita kuka taho da ita nan. Ba sai ku barta acan camp ɗin ba kamar sauran. Ni wannan labarin ƙanzon kuregen bazan taɓa yarda da shi ba, dan dama na jima ina zargin ana cin amanata, idan har ana son na yarda ba ƴarsa bace sai dai muje asibiti ai musu gwaji shi da ita.....”          A matuƙar fusace Zak-Shadow ya miƙe, cikin buɗaɗɗiyar muryarsa dake fita da kaushi da ɗaci ya nuna Nabeeha, “Baki isa ba, kinyi kaɗan wlhy. Kije labarin ƙaryar aka baki, kuma ana cin amanar taki kiyi duk abinda zakiyi, dan ke baki isa sakani yin abinda banyi niyya ba wawiya kawai”.       A fusacen itama ta miƙe tana kuka, kai da ka ganta kasan kishi ne da zuga suka rufe idannunta, itama cikin ƙaraji ta ce, “To wlhy kuwa sai dai mu rabu, dan nima baka isa na cigaba da zama da kai ba. Jaka ka ɗauke ni ko dabba?, shekara da shekaru ina fama da kai muje muga likita akan matsalar haihuwa amma kaƙi saboda kasan mi kake shiryawa, kaje ka ajiye wata ƴar iska a jeji kana dadiro da ita ku haihu dan yanzu an kasheta ka ɗakko ƴar ka kawo gida mu shaƙi iska ɗaya da ita, mu kwanta muhalli ɗaya da it.....”      Tasss! Tasss!!! Kake jin saukar mari har biyu a kan fuskarta irin mai gigitarwar nan, ai ko ƙara ta ƙwalla, dai-dai da miƙewar Momyn ta ta riƙeta tana shiga tsakkaninta da Uncle Nasiru mai marin........✍🏼 Gaskiya ƙawata Nabeeha baki ƙyauta ba, ya zaki mana haka kuma😳😏.        _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 56_ __________________ https://chat.whatsapp.com/L3BXH7JYlBRHIkFRiOjeW3?mode=ems_copy_t UMMU KHALIFA COLLECTION Ina Mata Yan kwalisa ina mata masu san kayan ado kamar Egyptian abaya sleeping drees kids were shos bags musk dahara original. To kukanku yazo karshe domin ummu khalifa sun zo muku da duk wadannnan kayan dierct suke order dinsu daga Egypt zuwa gida Nigeria kaidai kawai kashiga link dinsu domin gani ya kori jiii.. Ba nan ummuh khalifa suka tsaya ba suna nemawq mutane visa masu shaawar shugowa kasar ta Egypt karatu ko yawon bude ido ko kasuwanci ku tuntubeta a number dinta +201017018846/07048811474/ KO kuma shafinta na tiktok https://vt.tiktok.com/ZSU1F __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........“Miyasa zaka mareta? Naga akan gaskiyata take dai ai? Sai a daki yarinya a hanata kuka. Idan yasan yana da gaskiyar mizai sa yaƙi yarda suje suyi gwajin?”.      Cikin kuka Nabeeha ta ce, “Momy ki barshi ya kasheni, Abba ka kasheni, dama mun san ai ba son mu kake ba yanzu, shi da yay laifin ka kasa yimasa magana saboda kana tsoronsa sai ni, sai ni da nake da gaskiyata za'a tauye ni......”       Wani marin ya ƙara kawo mata, dan yama kasa magana saboda abinda ya tsaya masa a maƙoshi. Da sauri Momyn tata dai ta sake tarewa. “Wlhy bazaka sake dukanta ba”.           Mammah da al'amarin ya girmi kanta ma sai yanzu ta iya ɗaga baki da ƙyar tace ma Uncle Nasiru, “Dan ALLAH Yaya kayi haƙuri ya isa hakan, duka ba shine mafita ba, ku barta ta huta ta huce dan yanzu shaiɗan yayi tasiri a zuciyarta. Sannan kuma tunda gwajin take so ni zan masa magana zaije suyi, ba shike nan sai a zauna lafiya ko”.      A gatsine Momynta ta ce, “Da dai yafi kam”. Taja hannunta suka nufi ƙofa. Gagara sake yin magana kowa yayi a falon, dama Zak-Shadow tunda ya gama yaɓa mata zancen farko ya koma can dining ya zauna, yaƙi fita ne dan kar ya ɓatama Mammah rai, Uncle Nasiru kuma yaga kamar ya raina shi, dan kallon uba yake masa. Amma ya tabbatar ya cigaba da zama inda Nabeeha take zai iya fara kai mata duka a karo na farko na rayuwarsu, shiyasa ya zaɓi komawa can ya zauna ɗin...      Salatin da Mammah ta saki ita da Imran a lokaci guda ya sashi buɗe idanunsa ya kallo falon, ai baima San ya miƙe ba da sauri ganin Imran ya taro Uncle Nasiru alamar faɗuwa zai yi. Ganin Uncle Nasirun na neman sumewa ya ƙarɓi ruwan da Mammah ta miƙo da sauri, ɓalle murfin yay kawai ya zuba a hannu yana kaiwa duƙe shima ya shafa a fuskar Uncle Nasiru. Nannauyan numfashi ya kawo mai ƙarfi, sai kuma ga hawaye....          “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, dan ALLAH Yaya ka kwantar da hankalinka. Wannan fa ba wani abun tashin hankali bane ba. Komai mai sauƙi ne, tunda ma ALLAH ya kawomu zamanin da ake gwaje-gwajen sai a godema UBANGIJI ko. A kuma je ayi dan itama ta samu nutsuwa da kwanciyar hankali.”       “A'isha bazai je ba”.   “A'a dan ALLAH Yaya kada kace haka, ita masalaha a rayuwa babu abinda ya kaita daɗi da sauƙi balle ma a rayuwa irin ta aure, itama yana da ƙyau a bata hakkinta kodan cire zargi, kasan bazan iya bijirema umarninka ba, amma dan ALLAH ko sau ɗaya ne ka bani damar nan na roƙe ka”.         Yunƙurawa yay zai tashi, Zak-Shadow da Imran suka taimaka masa. A kujera suka maida shi, yay shiru tsawon lokaci, wata irin nadamar auren Momyn Nabeeha yake ji da zama da ita ba tsawon shekaru, wlhy badan ƴar uwarsa bace jininsa mafi kusa da har nadamar haɗa zuri'a yayi da ita. Matar nan itace babban ƙalubalensa na rayuwa, yasha wahala a hannunta a zamansu na turai, dan gaba ɗaya ta fanɗare masa ta saka yaransu fanɗare masa. Shiyasa ma ya yanke shawarar dawowa gida Nigeria. Ko batun saƙo da yake turama su Mammah ɗin da bai zuwa daga baya abokin nashi yazo ya gaya masa gaskiyar itace ta hana, ta dinga amsa tana rabawa uku ta bashi kaso ɗaya ta ɗauki biyu...       Imran ne ya katse masa tunani da faɗin, “Uncle kayi haƙuri nima ina bayan Mammah, ka bari aje ai gwajin kawai kodan samun zaman lafiya da cire zargi, itama yarinyar kaga zata rayu cikin salama”.         “Imrana.....”    “Dan ALLAH Uncle”. Imran ya sake katsesa. Kallon Zak-Shadow Uncle Nasiru ya ɗanyi, sai tausayinsa ya sake kama shi da kunyarsa mai tsanani, dan tabbas ya cutar da shi da har ya bari aka aura masa Nabeeha bayan yasan bata da isashiyar tarbiyya. Tabbas Haysam magajin Abdul-rasheed ne tako ina, dan ko a halayya da dattako da sanin ya kamata bai bar komai na mahaifinsa ba, kawai dai shi Abdul-rasheed mutum ne mai faranfaran da yawan magana, saɓanin Haysam mai shiru-shiru da ƙarancin fara'a a fuska idan ba shi yaso ba. Amma kowa ya shaida mutum ne mai haƙuri da kawaici..... ••><••><••><••     Da ƙyar Mammah da Imran suka ci ƙarfin Uncle Nasiru ya yarda da batun gwaji, shi dai gogan bai sake tankawa ba. Yayinda can ƙanensa ke cike tab a waje. Dan sanda Momyn Nabeeha ta fita da ita yanda suka zuba musu idanu a fusace sai da sukaji hantar cikunnansu ta motsa, shiyasa da sauri suka wuce su zuwa sashen su Nabeehan.        Bayan sallar Magriba da aka kira Mammah tasa Biebah zuwa ta sanar musu su fito za'a asibitin. Koda suka fito a tsakar gida suka iske Mammah ta fito, Uncle Nasiru dama bai shiga ciki ba bayan dawowarsu massalacin. Hakama Imran da Zak-Shadow dake can gefe Imran ɗin na lallashinsa. Cike da gadara Momyn Nabeeha tace kuma sune zasu zaɓi asibitin da za'aje. Nan ma Uncle Nasiru zai yi magana Mammah tai saurin cewa sun amince ayi hakan. Takaici kamar zai kashe Uncle Nasiru da Zak-Shadow, amma dole sukai shiru aka tafi asibiti. Ita da ƴarta motar ta suka shiga. Su ko suka shiga mota ɗaya. Imran ke tuƙi, Uncle Nasiru a gefensa. Mammah da Zak-Shadow suka shiga baya Nimrah da Bilal ya dawo da ita tana barci a cinyarta, dan har yanzu barcin takeyi. Motar ta ce gaba tasu a baya. Cike da kulawa da lallashi Mammah ta kamo hanun Zak-Shadow a cikin nata, dan ta tabbatar zuciyar ƴan mazan na nan na tafasa a ƙirji, saboda umarninta ne kawai zai je gwajin nan.      Aiko tabbacin a zuciyen yake ko motsi baiyi ba koda ta riƙe hannun nashi. Idanunsa kuma a rufe har suka iso asibitin daya kasance privete ne, babban asibiti ne kuma da akeji da shi a Abuja. Abinka da maganar kuɗi ko zaman mintina goma basuyi ba likitan da zasu gani ta basu izinin shiga. Nimrah da tun zamansu wajen ta farka tana lafe jikin Mammah Imran ya miƙama hannu. Mammah ta kalla, sai ta mata murmushi da faɗin, “Jeki kinji, ai yanzu zaku dawo ina nan ina jiranki”.      Kai ta jinjina Mammah, sannan ta miƙama Imran ɗin hannu ya sakko da ita. Da ƙafafunta ta taka har ƙofar Office ɗin, sai a lokacin kuma uban gayyar ya miƙe saboda maganar da Mammah tai masa. Nabeeha da itama sai yanzu uwarta ta kamata ta miƙar ta harari bayansa tana murguɗa baki, hakama Momynta da harara ta rakashi. Suna zuwa ƙofar ɗakin inda Imran ke tsaye tsagal Nimrah mai bakin magana da barci ya fara sakinta ta ce, “Baba ɗan sanda kanka ke ciwo ne?”.      Yanda tai maganar idonta akan Zak-Shadow ya saka Imran yin ƙaramin murmushi, shiko idanu kawai ya zuba mata ya ƙi magana. Yayinda Mammah da Uncle Nasiru ke murmurshin maganar tata, nan kuma Nabeeha da Momynta ji suke kamar su shaƙe shegiyar yarinyar. Nimrah bata haƙura ba ta matso kusa da Zak-Shadow, kamar zatai kuka tana kallon fuskar tasa dai ta kama hannunsa, “Baba ɗan sanda akwai zafi sosai ko? Kada kayi kuka kaj.....”       “Ke dan ubanki yima mutane shiru!!!”.     Nabeeha ta daka mata tsawa. A mamakinsu ko irin ma ta tsorata nan sai ma ƙuri datai mata da idanu ba shakka ba girgiza. Aiko ji Nabeeha tai ta sake hasala, ta fige hannunta tayi kan Nimrah zata daka, sai lokacin ta sake matsawa jikin Zak-Shadow sosai ta rungume ƙafafunsa tana ɓoye fuskata. “Wayyo Baba ɗan sanda kace Kada ta dakeni, bana son duka bana so....”      Jin shiru ba'a daketan ba tai shiru, sai kuma ta ɗan leƙo fuskarta taga miya faru. Nabeeha ta gani tsaye cak tana huci kamar zakanya. Sai dai bata san miya tsaidata ba. Abinda kuwa bata sani ba wani shegen kallo Zak-Shadow kema Nabeeha ɗin daya sakata dakatawar. Imran shi ya katse yanayin da faɗin, “Bismillah ku shiga”.         Ƙwafa Nabeeha tayi da watsama Nimrah harara, ƙasa-ƙasa ta ce, “Sai na kasheki shegiyar yarinya ƴar zin....”. Bata ƙarasaba Momynta taja hannunta suka shige. Shima cikin lallashi Imran yay masa magana da ido, bai tanka ba ya kama hannun Nimrah suka shiga, Imran biye da su.       Da Imran kawai doctor ya gaisa, koda ya miƙama Zak-Shadow hannu yi yay kamar bai ma gansa ba. Shima doctor ɗin sai ya sake nutsuwa dan ya fahimci waɗan nan mazan bana wasan yara bane ba. A ɗarare ya juya ga Momyn Nabeeha yana tambayarta mike tafe da su.      Ganin Momyn Nabeeha zata fara wani ƙalƙale-ƙalƙalen magana da iyayin ƴan bariki Imran ya katseta kai tsaye yay ma likitan bayanin abinda suke buƙata. Doctor yaga ba wajen wasa bane dandanan ya ɗauka waya yay kiran wani. Kafin kace mi an musu dukkan abinda ya dace anan cikin office ɗin nashi batare da sunje lab ba. Dukkan abinda ya kamata anyi musu, duk da dai ansha badaƙala da ihu lokacin yima hajja Nimrah nata gwaje-gwajen. Bayan an kammala komai doctor yace results sai nan da kwana biyu.         “Bazai yiwu mu sameshi a gobe ba doctor. Abin na gaggawa ne Please”.   Momyn Nabeeha ce mai maganar, doctor yay ɗan jimm, sai kuma ya jinjina kai. “Okay ba damuwa hajjaju ai kece. Zuwa yamma zan kira ki”.         “Ai ni da zai yiwu ma zuwa 12 nake so, dan goben zuwa 1 inada meeting da first lady, kuma sai dare zamu fito”.       Bakin doctor a washe ya ce, “Shike nan yanda kike so haka za'ayi, zan yi ƙoƙarin hakan”.       “Na gode”.    Ta faɗa tana kama hannun Nabeeha suka fito, dama Zak-Shadow tuni ya fice da Nimrah. Sai Imran ne kawai aka bari, gama nazartar alaƙar dake tsakanin doctor da Momyn Nabeeha ya sashi tsayawar kuma. Sai da suka fice sannan doctor ya kallesa. “Ranka ya daɗe akwai sauran wani abu ne?”.         “Mai muhimmanci ma kuwa. Naga akwai alaƙa tsakaninka da su, to ka sani idan ɗigo ya canja a cikin result ɗin da muke buƙatar gani kayi kuka da kanka. Suna Major Imran Abbas.”      Daga haka Imran yay ficewarsa a office ɗin shima yabar likita da baki buɗe na firgici da mamaki. Dan a kwanakin nan babu sunayen dake amsa kuwwa a kafafen yaɗa labarai dana sada zumunta kamar Major Imran Abbas da Zak-Shadow da sauran Captains ɗin da akasha wancan gumurzun..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 57_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ...........A inda suka bar su Mammah nan Zak-Shadow daya fara fitowa riƙe da hannun Nimrah suka samesu ita da Uncle Nasiru. Kallonsa kawai Mammah keyi cike da tausayi, dan tasan ransa a matuƙar ɓace yake, yana dannewa ne saboda umarninta. A kujerar kusa da ita ya zauna. Dan wani ɗan jiri-jiri yake ji, haka yake idan ransa yakai ƙololiwar ɓaci, dan mutum ne shi mai haƙuri amma yana da fushi sosai musamman akan gaskiyarsa. Yana kaiwa zaune Nimrah ta sake matsawa kusa da shi ta manne a jikinsa saboda hararar da Nabeeha da Momynta da suka fito ke mata. Hakan kuwa sai ya ƙara ƙona ran Nabeeha, dan babban baƙin cikinta itafa ka raɓar mata miji ne, cikin ƙunƙuni ta ce, “Banda ma ana son raina hankalina Momy, jiba yanda mayar yarinyar nan ke nane masa tabbacin ta masa sani na haƙiƙ....”            “Malama ya isheki haka”.     Karon farko Imran da fitowarsa kenan daga office ɗin shima ya faɗa a fusace, dan shi kam ya tsani nacin magana. Haukan Nabeehan ya fara isarsa shima. Ya tabbatar shi kansa Zak-Shadow ɗin darajar Mammah kawai yasa shi ƙyaleta. Hararar Imran tayi cike da jin baƙin ciki da tsanarsa. Tsigit Nimrah ta ce, “Baba ɗan sanda tana harararka” kafin wani yace wani abu ta cigaba da faɗin, “Kuma sai na rama maka, ai ido bai fi ido ba”. Tako ballarama Nabeeha harara harda riƙe ƙugu, dan tagaji da hararar da Nabeehan ke mata tun ɗazun itama. Mi Imran da Uncle Nasiru zasuyi ba dariya ba, Mammah kanta sai da ta murmusa kaɗan. Shi kansa uban gayyar idanu ya zuba mata. Kafin ya kai hannu ya matso da ita kusa da shi, kallonsa tayi a ɗan tsorace, dan ta zata faɗan hararar da taima Nabeehan zai mata, dan haka tai ƙoƙarin son goge laifinta kamar yanda take ma Umma a gida idan tasan tayi ba daidai ba. A bazata kawai yaji saukar ɗan hannunta akan goshinsa. “Baba ɗan sanda har yanzu kanka na ciwo ne?”.        Yanda sanyin hannun nata da zazzaƙar muryarta suka ratsa kunnensa sai ya sake zuba mata idanunsa kawai, yama kasa mata faɗan da yay niyya ɗin. Itama kallonsa take ƙiri cikin ido kamar ba ita ba. Ji yay bazai iya shareta ba, balle ma shi mutum ne mai son yara sosai, hannun nata kawai ya kamo ya riƙe cikin nashi, tun fitowarsu gida a karo na farko yayi magana yana gyara mata ɗan baby hijjab ɗin jikinta. “Karna ƙara jin bakin nan yayi magana, babu ƙyau rashin kunya.” ya faɗa cikin gargaɗi yana ƙoƙarin miƙewa.           Da sauri ta saka hannu ta rufe bakinta, ɗayan hannun nata kuwa na riƙe a cikin nashi. Suma su Mammah miƙewa sukai ita da Uncle Nasiru suna murmushi, dan sun fahimci Nimrah zata fara sakin jikinta da su kenan, da alama kuma yarinyar akwai surutu da tsiwa..... <<>><<>><<>><<>>            “Wannan shine gidan Sir!”.     Matashin ya faɗa cikin karyayyen harshensa fuska cike da murmushi. Shima Dabo murmurshin yayi masa, tare da zaro kuɗi da zasu iya kaiwa dubu biyu ya bashi. “Nagode sosai, amma ko zaka bani number ɗinka, dan in na kammala abinda nake na kiraka ka fita dani koda nayi dare”.      Ɗan jimm matashin yayi yana gyara zamansa akan mashin ɗinsa, dan haka Dabo yay murmushi a karo na biyu. “Karka ji tsoron komai, ni bamai cutarwa bane ba”.           “Kayi haƙuri sir, kasan yankin namu ne sai a hankali, ana mana ƙwacen mashina musamman da dare a hanyar tamu shiyasa kaga nayi shiru, amma badan ina tunanin zaka cutar dani ba”.       “Ayya na fahimta. Shike nan ba damuwa nagode sosai kaje kawai”.      “A'a bara na baka number ɗin, sai dai idan dare yayi sosai sai dai na baka haƙuri dan ina jin tsoro bazan iya fita da kai ba”.            “Na gode”.      Bayan Dabo ya amshi lambar mai okada ya ɗan tsaya a ƙofar gidan yana waige-waigen da ƙarema wajen kallo. Garin ƙauye ne sosai, dan gidaje ma ɗai-ɗai suke. Gidajen duk babu wata katanga irin dai gini ne na yankin. Sai da ya ɗan furzar da iska kafin ya taka steps ɗin barandar ya haye kanta, dai-dai ƙofar dake rufe ya tsaya tare da fara knocking. Yayi fin sau uku sannan akazo aka buɗe. Cikin masa kallon rashin sani tsohuwar data buɗe ƙofar ta ce, “Waye kai? Wa kake nema?”.        Tsaiwa Dabo ya gyara, cikin girmamawa ya sanar mata shi baƙo ne, kuma ma'aikacin soja, yazo wajensu ne akan wani Ojo”.             Dan danan yaga fuskarta ta canja, jikinta har rawa ya ke ta kamo hannunsa tana faɗin, “Ojo! Kai soja ne?, kasan inda yarona Ojo yake? Da gaske kaga Ojo na? Shigo-shigo maza shigo ciki”. Ciki ta turashi, ta maida ƙofar ta rufe. Falo ne madaidaici da wasu ruɓaɓɓun kujeru a ciki, sai ƙaramar tv akan katakon tv stand. Sai da ta jawo wani ƙyalle ta saka masa a kujerar sannan ta sake jan hannunsa alamar ya zauna. Baiyi musu ba ya zauna, jikinta har rawa yake ta nufi wata ƙofar tana cigaba da maimaita masa kalmar sannu da zuwa data kasa daina faɗa. Karo na farko yabi falon da kallo, har idanunsa suka sauka akan hotunan dake saman tv ɗin falon manne a bango. Guda kusan huɗu ne, ɗaya mata da miji ne suna da ƙuruciya, kamaninta yasa ya gane itace duk da ta tsufa a yanzu. Sai na biyu mutumin kusa da ita ɗinne dai shi kaɗai da kayan sojoji, sai uku yara biyu matasa masu kammani da juna matuƙa, wanda kai tsaye yaga kamanin Ojo a tare da yaran duk da sanda akai hoton suna ƙananu sosai. Sai na ƙarshe zai iya cewa Ojo ɗin ne da kayan soja....      Dawowar tsohuwar ya katse masa tunani da nazartar hotunan. Ruwa ta ajiye masa da faɗin, “Fara shan wannan bari naje na kawo maka lemo nan kusa”.         Hannunta ya kamo da murmushi dan harta yunƙura zata bar wajen. “A'a Mama ruwan ma ya isheni, yi haƙuri ki zauna magana zamuyi ne”.      Cikin damuwa ta ce, “Ko kaima kana tsoron cin abun hannuna ne? Kaima ance maka ni mayya ce ko....”      Hawaye suka shiga sakko mata. Da sauri ya shiga bata haƙuri da lallashinta, da ƙyar ta tsagaita kukan bayan ya tabbatar mata shi babu wanda ya sanar masa komai a kanta.          “Ka tabbatar?”.      “Yes Mama”.   “To kasha ruwan”. Danta samu kwanciyar hankali ya ɗauki ruwan yasha sosai tare da mata godiya. Sannan ya fara magana cike da nutsuwa da kulawa. “Mama kamar yanda na faɗa miki ni soja ne, nazo garin nan ne kuma takanas saboda ke. Sai dai kafin na faɗa miki dalilin zuwana ina son nasan wanene Ojo a wajenki?”.         Cikin jinjina kai da sauke tagwayen ajiyar zuciya ta ce, “Ojo ɗana ne, shi ɗin twins ne shi da ɗan uwansa, suna kamanni da juna sosai ta yanda koni wani lokacin suna ruɗani bana gane su. Su biyu kawai muka haifa, babansu soja ne, an kashe shi shekaru masu yawa, lokacin su Ojo nada shekara goma-goma. Bayan mutuwarsa nasha wahala akan rainon su Ojo, dan babu mai taimaka min, haka na dinga noman Togo da doya ni kaɗai ina biya musu kuɗin makaranta. Bayan sun gama Secondary Ojo yace yana son zama soja kamar mahaifinsu. Na tsorata sosai da hakan saboda a aikin aka kashe babansu, duk yanda na lallaɓa Ojo yaƙi saurarena yace shi dai yana so, dole na barshi. Shiko ɗan uwansa Jeo baice yana son komai ba, dama na masa maganar komawa karatu sai yace ba yanzu ba. Ban matsa masa ba na barshi. Bayan tafiyar Ojo saina fahimci Jeo ya fara rashin ji da yawo da abokan banza suna bin yaran ƙauyen nan. Na zaunar da shi nai masa faɗa amma bai saurareni ba, sai ma ya koma ba kullum yake kwana a gida ba sai randa yaso, canjawar halayensa na damuna sai dai babu mai taimakona ya masa faɗa sai na haƙura. A haka Ojo ya dawo gida cike da farin cikin zama soja bayan wani lokaci, nima duk da bana so na tayashi farin ciki, yayi kwanakinsa ya sake komawa, a lokacin shima Jeo ya shirya yabar ƙauyen nan wai zai yi karatu. Tun daga nan ban sake ganinsu ba su duka sai bayan shekara biyu Ojo yazo min da wata yarinya wai da zai aura. A lokacin ne ya gyara min gidan nan ya zuba min wannan kujerun da komai masu ƙyau ya ajiye min kayan abinci da kuɗi. Kwanansa goma sai ga Jeo shima yazo, gaba ɗaya Jeo ya canja min a yanda na sanshi, ya zama wani iri da shi, babu tarbiyyar dana basu ko ɗaya a tare da shi. Ni da Ojo mukai masa faɗa sosai, yay mana alƙawarin duk zai daina abinda yake yi Ojo ya ɗauki kuɗi ya bashi shima. Daga nan ya ɗauki budurwarsa suka tafi yace min sai nan da wata uku zai sake zuwa dan yanzu an masa canjin wajen aiki ne ma, na musu addu'a suka tafi suka bar Jeo anan, sai da ya ƙara kwana biyu ya lallaɓa ni ya amshi abinda Ojo ya bani sannan shima ya koma......” ta fashe da kuka sosai, da ƙyar Dabo ya lallasheta ta cigaba da faɗin, “Tun daga lokacin ban sake ganinsu ba su duka biyun. Nayi kuka nayi nema harna gaji, nayi addu'a an tayani amma babu wanda ya dawo. Tun mutane na tausayina har suka daina suka fara kirana mayya, wai na sayar da jinin ƴaƴana ne dan ni nayi rayuwa mai yawa”.         Ba ƙaramin tausayin tsohuwar nan bane ya sake mamaye Dabo ba. Haka ya dinga lallashinta harta tsagaita kafin ya cigaba da mata tambayoyi.      “Amma Mama kafin Ojo ya tafi bai gaya miki inda aka mai dashi aiki ba?”.       “Bai gaya min ba, kawai yace min arewa ne”.      “Shima Jeo babu wanda ya sake sanar miki ya ganshi?”.            “Wani abokinsa ya taɓa gaya min wai sunje har inda Ojo ke aiki shi da Joe, amma basu ganshi ba akace yana kan aiki, daga nan suka dawo, shi sai ya samu hanyar barin ƙasa zuwa turai, akan shima Jeo zai biyoshi daga baya, sai dai Joe bai bishi ba daya tambayi wanda yayi musu hanyar sai yace shi tun ranar bai sake ganin Joe ba ma”.        “Yanzu ina abokin nashi?”.     “Ya koma turai, dama yazo tafiya da Mamansa ne. Ga gidansu anan bayana kaɗan harma ya rushe saboda babu kowa”.        “Mama kince kamanin Joe da Ojo mai tsanani ne har mutane basa banbance su, kema wani lokacin suna ruɗar dake. Amma da wane irin banbanci kike banbance su a sauran lokaci?”.       Ɗan shiru tayi na wani lokaci, kafin ta nisa tana jinjina kai.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 58_ __________________ Ina mata ma'abota ado da kwalliya maryam's all-in-one emporium ta tanadar muku Mayafai masu kyau da aminci kama daga plain chiffon veils masu kyau kamar daga Egypt suka sauko🥰 jersey scarfs , beaded and stoning veils, Chantilly, 2D to 10D Turkish veils Dubai d.s Kuma abun farinciki muna bada sari da siyan dai dai ina Kano Ina tura kaya ko'ina cikin Aminci da yardar Allah ga number ta 09064960666 https://chat.whatsapp.com/FfaJ30ZOz8NHazD2ZwtzAd?mode=wwt A cikin duniya ta gayu da burgewa mayafi shine ya ke daukaka ado da aji Maryam's all-in-one emporium 09064960666 Kano Anan ne gayu yake tarar da qawa. Ki more hadaddun Mayafan mu da suka hada da Plain chiffon veils (soft & flowy) Italian Chantilly veils (pure elegance Jersey Veils (comfort meets class) Lafaya and many more. Each piece tells a story of grace, crafted for women who understand beautyin simplicity.🤍 🖤 Premium quality 💛 Affordable luxury 🖤 Available in elegant shades 💛 Delivery 🚚 duk inda kike a fadin duniya Ba mayafi kawaii kike bukata ba you deserve a statement of class.👑 Wholesale group https://chat.whatsapp.com/FfaJ30ZOz8NHazD2ZwtzAd?mode=wwt __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........“Jeo yafi Ojo sauƙin kan zama da mutane, dan Ojo nada saurin fushi kuma bai son mutane sosai. Dan ko aboki da wuya kaga Ojo da shi. Shi ko Jeo na kowa ne. Sannan akwai wani ɗan tabo a bayan kunnen Jeo da Ojo bashi da shi, suna jarirai wani abu ya ciji Joe a wajen shine ya zama ciwo har sai da mukaita zuwa asibiti kafin a samu ya warke da ƙyar, daga nan ne ya zama tabo, shine abu na biyu bayan waccan halayyar da nake banbance su da shi.”      Kafin Dabo ya bata amsa ta miƙe ta shiga bedroom, babu jimawa ta dawo da albom na hotuna ta miƙa masa. Amsa yay ya kuna fitilar wayarsa dan akwai ƙarancin haske a ɗakin. Gaba ɗaya albom ɗin hotunan su Ojo ne a jiki, tun suna jarirai har lokacin da Ojon yay mata gyaran gida harda budurwarsa ma kamar yanda ta faɗa, sai biyun ƙarshe shi da Jeo lokacin an kammala aikin gidan, ɗaya su biyu, ɗaya su huɗu harda budurwar Ojo da ita maman, wani kallo da Jeo kema budurwar Ojo ya ɗauki hankalin Dabo sosai. Ya jima yana kallon hoton kafin ya ajiye albom ɗin yana ɗan murmushi.        “Mama naga hotuna, na kuma gode sosai”.     “Nima na gode da kazo min da labari akan yarona, bayan shekara biyar ban sake jin komai akansa ba. Yanzu ka gaya min yana ina?”.         Samun kansa yay da yi mata ƙarya. Ya ce, “Ojo yana nan lafiya, jinsa da bakiyi ba na tsawon shekaru an turashi aiki ne wata ƙasa. Kin san mu sojoji akan aikinmu sai haƙuri. Amma ki kwantar da hankalinki yana gab da dawo wa. Yanzu ma saƙo aka sakani zuwa na kawo miki. Sai dai yanzu dare yayi, zan koma can babban garin naku na kwana zuwa safiya sai na dawo...”         “Miyasa bazaka kwana anan gidan ba?”.     Ta faɗa cikin damuwa. Daɗi ne ya kama shi dan dama abinda yake so kenan, amma sai ya danne tare da faɗin, “Karki damu Mama zanje can, anan ai sai na takura ki”.      “Ni bazaka takura ni ba, ga ɗakin su Joe kullum sai na gyara Dan Kada wani yazo a cikinsu ya ganshi da datti, na roƙeka ka kwana anan”.          “Shike nan Mama Nagode zan kwana.”     Sosai ta nuna jin daɗi da amincewarsa.... >>>>>>%<<<<<<          Imran na ƙoƙarin yin parking kiran Dabo ke shigowa a wayarsa. Bai ɗaga ba sai da ya kashe motar, Zak-Shadow dake baya ya fita ya buɗe ma Mammah dake riƙe da Nimrah, dai-dai nan shima ya fito yana ɗaga wayar da kaita kunensa. Sunan Dabo daya ambata ya saka Zak-Shadow juyowa yana kallonsa. Dai-dai kuma lokacin ake kiran sallar isha'i. Dan haka Imran yace ma Dabo ya bari su dawo salla sai suyi magana.         Ba wanda ya cema ɗan uwansa komai shi da Zak-Shadow ɗin suka fice massalaci, dama shi Uncle a gida suka ajiyeshi kafin su ƙaraso. Suna fita a gate ɗin ne motar Momyn Nabeeha ke shigowa. Ko kallon inda motar take Zak-Shadow baiyi ba suka fice. Koda aka idar da salla suka dawo gidan anan compound suka zauna. Imran yay kiran Dabo. Bugu ɗaya ya ɗauka kamar dama abinda yake jira kenan..         “Kamar dama ni kake zaman jira Dabo?”.     “Wlhy Sir a ƙage nake kamar ka sani, dan ji nake kamar nayi tsuntsuwa na ganni a gabanka.”             “An samu abinda ake so kenan?”.      “Kusan hakan sir, dan yanzu haka ina a cikin gidan su Ojo, a ɗakinsu ma mahaifiyarsu tai min masauki zan kwana”.         “Masha ALLAH Dabo, shiyasa na yarda da aikinka sosai. Yanzu ya akayi?”.      “Sir tabbas akwai alamar tambaya akan Ojo, dan kuwa ta tabbata shi twins ne, sunan ɗan uwan nasa Jeo..........” ya kwashe labari tsaff ya sanar masa. Kuma komai Zak-Shadow shima yaji saboda wayar a hansfree take. Dan haka Zak-Shadow ɗin ya amsa ya ɗan yi masa tambayoyi.          Bayan ajiye wayar ne Imran ya kalla Zak-Shadow da yay shiru alamar yana nazari. “Mika fahimta a wannan labarin Zak...?”       Shiru kamar bazai amsa ba, dan yafi minti biyu kafin ya nisa yana sake gyara zamansa. Kai tsaye ya maidama Imran tambayar da “Kai mika fahimta?”.              “Babbar alamar tambaya akan Ojo gaskiya”.      Ƙaramin murmushi Zak-Shadow yayi idanunsa na kallon wani waje daban, sai kuma ya juyi yana kallon Imran ɗin hannayensa harɗe a ƙirjinsa. “Imran dole a cikin biyu ɗaya ya kasance a tunani na. Kodai tun farko Ojo ya shiga aikin soja da manufa, ko kuma Jeo shine Ojo a yanzu”.        “What! Taya hakan zata faru Zak.. idan ma tunanin farko zai yiwu taya na biyu zai yiwu? Ta yaya Ojo zai zama Jeo? Kuma ya saka rigar soja babu tsoro har wannan shekarun baya ganosa ba?”.       “Ta yanda hasashenka ke baka bazai yiwu ba....”     Zak-Shadow yay maganar yana kai wayarsa kunne. Idanu kawai Imran ya zuba masa cike da tsoro. Dai-dai yana amsa gaisuwar da ake masa daga can a taƙaice. Cikin bada umarni ya cigaba da faɗin, “Yusuf kana ina?”.          Daga can cike da girmamawa akace “Sir! Ina barrak?”.      “Ina Ojo?”. “Tun ɗazun ya fita wai zai yi shopping saboda zaije gida gobe na hutun da muka samu”.         Ɗan jimmm Zak-Shadow yayi na sakani, sai kuma ya ce, “Daga yanzu zuwa goben duk wani motsinsa ina son na sani”.     “In sha ALLAHU sir”. Yanke wayar Zak-Shadow yayi, sai kuma ya juya yana kallon Imran dake kallonsa. “Yana barin cikin barrak a kama shi”.       Kai Imran ya jinjina masa. “Haka shine dai-dai”.     Ganin Zak-Shadow ɗin zai miƙe Imran ya dakatar da shi. “Ina zaka kuma bamu gama magana ba”.              “Miya rage?”.        “Case ɗin yarinyar nan da iyalinka”.     Murmurshi mai ƙayatarwa yayi, sai kuma ya ɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa hannayensa duka biyu na cikin aljihu. “Karka damu na gama yanke hukunci”.      Aɗan tsorace Imran ya miƙe. “Wane irin hukunci ka yanke?”. “Zaka gani a goben”. “Haysam dan ALLAH kada ka aikata abinda Mammah zataji babu daɗi. Koba komai Uncle Nasiru nada muhimmanci a wajenta shiyasa ma kaga tana iya shanye komai. Tasha faɗa a gabanmu Shine Yayanta daya rage take ma kallon uba duk duniyar nan a yanzu”.         Sosai Zak-Shadow ya zuba masa ido, sai kuma ya sake murmusawa kaɗan yana kauda su gefe. “Kafi kowa sanin waye ni, kada kai banzan tunani”. Daga haka yabar wajen. Da kallo kawai Imran ya bishi harya shige sashensa sannan ya sauke ajiyar zuciya. Addu'a yake a ransa ALLAH ya yayafama wannan masifar ruwan sanyi da wuri, dan yasan wanene Haysam idan aka ƙure haƙurinsa, ya fahimci kuma Nabeeha ta fara ɗakko hanyar ƙure haƙurin nasa a yanzu, komai kuma zai iya faruwa idan tai wasa. Da wannan tunanin ya nufi sashen Mammah domin yi mata sallama shima ya wuce nashi gida.... ★>><<>><<★             GIDAN GWAMNATI.        A Ƙaramin ɗakin taro dake ƙawace da sanyin ac da haske mai sauƙi. Shugaban ƙasa da ministan tsaro sai General da wasu manya uku ne ke zaune cikin nutsuwa da hali irin na masu girma. Babu komai a gabansu sai manyan files guda uku a teburin tsakiyarsu sai ruwa. Shiru mai nauyi ya ratsa ɗakin tun bayan gaisuwa kowa ya nutsu. A karo na farko shugaban ƙasa ya nisa cikin nuna damuwa yay ƴar gyaran muryar data sakasu sake maida hankali sosai da nutsuwa suma duk da hankalinsa akan General yake alamar shi zaima magana, “General rahotannin da suka fito daga bangaren Arewa maso yamma sun fara girgiza mana tsarin tsaro gaba ɗaya. Muna bukatar gaskiya daga gare ka, a wane hali zamu iya kira ko auna Zak-Shadow a yanzu bayan abinda kukazo mana da shi a zahiri da wanda muka gani game da nagartarsa a wannan makon har mukai zaman shirya karramawa a garesa?”.        Iska General ya ɗan furzar tare da  jan numfashi kafin ya amsa da, “Your Excellency, Zak-Shadow ba sunan da ake ambata kai tsaye a cikin runduna bane kawai. Zaki ne na gaskiya dake aiki da ZUCIYA DA ƘWANJI akan duk wanda ya tare masa gaba da sunan GIRGIZA ƘASARSA. Ni kaina shaida ne akan hakan batun yanzu ba. Amma na fahimci ana son alamta wannan nasarar tasa ne ta jiya-jiya da cewa yana da alaƙa da tsohon skasin ɓangare na Special Recon Unit, wanda aka rufe shekaru uku da suka wuce…...”       Cikin nuna fusata Ministan tsaro ya katse General da faɗin, “Kana nufin ana iya samun haɗin kai daga cikin mu ne General?”.      Cikin ɗan kausasa harshe shima General ya bashi amsa da, “Ba zan tabbatar ba, amma abubuwa na nuna akwai waɗanda ke ƙoƙari ko son ƙirƙirar wani labari daga sama a kan sadaukarwar tasa shiyasa suke son dawo da abinda ya faru jiya su haɗa dana yau dan cimma manufa.”        Cikin matuƙar fusata Minista ya sake yunƙurowa zai yi magana. Amma sai shugaban ƙasa ya ɗan buga table ɗin, hakan yasa ya nutsu yay shiru. Kai shugaban ƙasa ya ɗan girgiza, tare da yin baya ya jingina da kujera, ya fahimci ministan tsaro da Janar kowa na kan gaskiyarsa ne. Iska ya ɗan furzar tare da gyara zamansa yana duba takardar gabansa. “Rashin nuna fahimtar juna tun a farkon tafiya ba shike bada nasara ba. Ya kamata mu kula dan karkacewarmu tamkar rasa ƙashin bayan al'amarin ne kai tsaye. Wannan bincike yana buƙatar a tafiyar da shi cikin sirri da kulawa. Ba na son ƙarin jita-jita a cikin jama’a. General, zaka jagoranci wannan aikin, amma kai kaɗai zaka san asalin manufarsa. A kafa kwamitin bincike da gaggawa dan kwanaki uku ne damu rak, sai kuyi aikin haɗin gwiwa da ministan tsaro..”       Daga haka shugaban ƙasa ya miƙe abinsa. Duk miƙewar sukai suma cike da nuna girmamawa, har sai da ya fice dogarinsa biye da shi sannan suma sukai yunƙurin fitowa..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 59_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........Cikin damuwa General ya koma office, tunda ya baro gidan gwamnati babu abinda yake maimaitawa sai sunan Zak-Shadow a fili. Zama yay a kujerar office ɗinsa tare da ɗan ja numfashi mai nauyi. Dai-dai nan mutane biyu daya buƙaci gani suka shigo office ɗin.      Koda suka ƙame da sara masa alamar su zauna kawai yay musu. Cikin damuwa ya sake furzar da iska mai kauri yana kallon su. “Aikin nan ba ƙarami ba ne fa. Kuma idan rahoton da na gani gaskiya ne… to akwai wanda ya karya alkawari cikin runduna.”        Cikin matsanancin tashin hankali ɗaya daga cikin hafsoshin nashi Colonel Haydar dake gefen damansa ya ce, “Sir! duk mai hankali zai fahimci hakan musamman yanda komai ya taso da zafi. Kenan za mu sake tuntuɓar sashen Recon Unit da aka rufe a baya? Akwai tsoffin bayanai da zasu taimaka nake ga.”        Cikin ƙwafa General ya ce, “Ai mu ake hara kai tsaye ba Zak-Shadow kawai ba Colonel. Shiyyasa wannan binciken zai gudana a cikin inuwa ne kawai. Dan haka ko ɗaya daga cikin Recon Unit bai kamata ya san munayi ba. Saboda Zak-Shadow yana cikin su, idan muka motsa da ƙarfi zai iya kallonmu daga nesa duk da nasan ita gaskiya gaskiya ce.”        Ɗayan ne yay magana a yanzu cikin jinjina kai da gamsuwa. Ya ce, “Haka ne sir, zamuyi komai a yanda ya dace.”         “Wannan shine dai-dai, “Ku shirya min jerin waɗanda suka yi aiki da sashen nan a shekaru uku da suka wuce. Ina so in san inda suke, koda kuwa wasu a cikinsu sun yi murabus.”      “Yes, Sir.” <<><>>★<<><>>         Dare yayi nisa, shiru ya ƙara ratsa ko ina a garin na Abuja. A duka ɓangarori biyu na gidan daren yau yazo musu da wani yanayi ne. Sai dai kowa da manufar tasa damuwa. A ɓangaren Mammah ta maida hankalinta ne ga ibada, yayinda Nimrah ke barci ɗai-ɗai a gadon ɗakinta dan tunda suka dawo daga asibiti tana nane da ita. A can kuwa Bilal, Yaya Ma'aruff, Yaya Ja'afar da Ammar ne suka ƙule a ɗaki suna sake tattauna abinda ke shirin faruwa a gidan nasu. Tun ɗazun Mammah ta kora su Aunty Ummi gida badan sun so tafiya ba, dan haka tattaunawar ta koma a tsakaninsu su iya mazan sai kuma waya da su matan ke kiransu dan suji ko akwai wani motsi. Amma kasancewar Mammah ta haɗe girar sama data ƙasa na hana kowa damar cewa wani abu yasa su zamewa suka koma ɗakin barcinsu suna tattauna iya abinda suka ji da tunanin mi ya faru da su Mammah ɗin suka je asibiti? Sun so zungurar Nimrah ta faɗa musu tunda sunga tanada surutu amma Mammah ta kafa ta tsare ta hana yarinyar zuwa wajensu kamar tasan mi suke shiryawa.        ★Anan ɓangaren ma Momyn Nabeeha da Nabeeha ɗinne a ɗakinta sun kulle kansu suna sake tattaunawa. Dan suma tunda suka dawo gidan Momyn keta sake tunzura Nabeeha, hakan ne yasa Jiddah yin fushi tabar musu gidan ko jiran zuwan mijin nata ma batai ba. Dan ta riga ta fahimci al'amarin Momynsu a wannan karon yayi babban tasiri a zuciyar ƴar uwarta Nabeeha. Tana tafiya Momyn ta koma zaginta, sai hakan ya ƙara tunzura zuciyar Nabeeha ta ƙullaci ƴar uwar tata da sake tabbatar da ba sonta da ƙaunarta take ba daman, tunda bata kishinta bata tayata baƙin cikin abinda ke faruwa da ita. Hasalima goyon bayan mijin nata take saboda neman duwawun zama. Sai hakan ya sake jagorantarta shagaltuwa da huɗubar Momy da dake jin zafin Zak-Shadow matuƙa..        ★Zak-Shadow kam tun bayan wucewar Imran daya koma sashen ɗakinsa kawai ya shige ya rufe kansa. Shi sam ba wani shirmen Nabeeha ko abinda ke faruwa a gidan ke damunsa ba. Hasalima bai ɗauki wannan serious ba dan yama gama tsara abinda zaiyi. Damuwarsa tana ga aiki ne musamman akan al'amarin Ojo da binciken da yake yi na musamman akan ainihin son sanin shuganin ƙungiyar duhu. A yanzu ma yana tsaye a bakin tagar ɗakinsa ne, yana sanye da kayan barci farare masu sauƙin nauyi, hannunsa riƙe da kofin shayi da bai gama sha ba. Sararin samaniya datai haske fayau na gangarawar ƙarewar wata ya zubama idanu kawai. A hankali tunaninsa yabar kan Ojo ya koma ga sojojin da suka barin a sansani a halin yanzu, yana jin kewar aiki, amma a lokaci guda yana jin daɗin hutunsa da ya tabbatar zai bashi damar binciken daya kafama alƙalami..       Vibration ɗin wayarsa ne ya katse tunaninsa, ya ɗan waiwaya yana kallonta a study table, kafin ya furzar da iska kaɗan tare da takawa zuwa study table ɗin. Ɗan zubama number ɗin ido yayi na sakani harta tsinke, ba suna, amma ya tabbatar duk wanda zai kira wannan layin nasa amintacce ne a garesa. Kiran ne ya sake shigowa a karo na biyu, bai jima ba yanzu kam ya ɗaga. Sallama akai daga can, ya amsa a taƙaice tare da faɗin, “Who’s this?”.       Murmurshi akai mai sauti daga can, sai kuma a taƙaice aka furta, “Col. Faro”.          Karo na farko Zak-Shadow ya ɗan murmusa, sai kuma ya ajiye kofin hannunsa yana kaiwa zaune a kujerar study table ɗin tare da ɗan taɓe baki cikin mamaki.       “Humm kai dai bazaka taɓa canjawa ba, shi kuma wannan layin fa?”.      Ƙaramar dariya Faro yayi daga can, sai kuma ya furzar da iska kaɗan shima tare da komawa serious, yace, “Zak-Shadow Ba zan iya yin wannan kiran da wata waya ta hukuma ba”.         “Humm hankaka...”.     Sai da yay ƴar dariyar batun Zak-Shadow ɗin da ƙarasa masa da “.....baka jewar banza ba” sai kuma cikin damuwa ya ce, “Zak... Ina cikin aiki yanzu, kuma lokaci bai ƙi min yakana ba. Amma akwai wani abu da ya kamata ka sani kafin lokaci ya ƙure.”      Ɗan shiru Zak-Shadow yayi na fin sakan biyu, kafin ya sake daidaita muryarsa ya ce,  “Ina saurarenka”.       Ajiyar zuciya mai ƙarfi Faro ya saki, “Ka kula sosai Zak. Na ji ana motsi a sama. Sun buɗe fayil ɗin Shadow Recon Unit. Kuma sun haɗa sunanka da wani rahoto mai nauyi. Ban san gaskiyar sa ba, amma na ji suna cewa za a turo da Special Board daga Defence HQ domin bincike.”       Shiru ya biyo bayan maganar, sai ɗan cizar lips da Zak-Shadow keyi kaɗan-kaɗan da ƙaramin saukar numfashin Faro. Zak-Shadow ya saki murmurshi mai bala'in ƙayatarwa a hankali yana miƙewa hannunsa ɗaya a cikin aljihu, inda ya baro jikin window ɗin nan ya koma ya sake tsayawa kamar ɗazun. Kai tsaye ya furta, “Da alama ababen farauta sun fara tsallako gaɓar ruwa domin neman ceto, sai dai idan basuyi taka tsantsan ba za suyi gudun GABA KURA NE BAYA SAYAƘI. Wane ne ke da alhakin motsin?”.        “Ban sani ba, amma akwai liken tattabara a cikin runduna, Zak-Shadow naji a jikina wani na ciki ne ke aika bayanai. Ka kula sosai. Idan wani abu ya faru, kar ka bari su kama ka kai tsaye. Ka jira umarni na hukuma, amma ka sa idonka a kan mutanenka, musamman waɗanda ka fi yarda da su.”         Kai tsaye ya kamo bakin zaren, dan haka ya sake sakin murmushi mai sauti, “Faro…” Zak ya kira sunansa cikin murya mai nauyi, tare da dakewa ya cigaba da faɗin, “Karka kuskura ka tona asiri da yawa. Ka tsaya a gefe, ka bar sauran wasan a kaina”.         “Na riga na shiga Haysam, Imran kawai nake ji, dan yana da rauni akan ka. Kuma bana so a bar maka wannan wasan kai kaɗai, ko yin amfani da shi akan ka, dan girman filin da za'ayi shi ya wuce duk yanda kake tunani…” Daga haka Faro ya katse kiran daga can. Ji kawai Zak-Shadow yayi Beep… beep… line disconnected.        Tsayawa yay kawai yana kallon wayar kamar yana son ta amsa masa sauran abin faɗar dake yawo a zuciyarsa da kanta. Sai dai yasan hakan bamai yiwu bane, yasan kuma iya batun da zai iya samu daga Faro kenan, wannan ma da yaji amintaka ce da yarda, amma duk tsanani soja baya auna wajen harbi da harsashi a gaɓar share fagen wasa. Wayar ya ajiye a hankali, yana tura labulen window ɗin da ƙyau saboda buƙatar shaƙar iska mai yawa, idanunsa ya tsayar kan sararin samaniya dake rikiɗewa zuwa duhun tsakkiyar dare. A ƙasan maƙoshi fuskarsa da murmushi mai wahalar fassara ya furta, “Da alama yanzu ne za'a dawo da wasan gaskiya. Wasan da zai rarrabe shiru da amsa kuwwar masu son a shelantawa”. ((★))<>((★))          WASHE GARI....    A yau rana ce a gurin kowa kamar sauran ranaku da suka shuɗe. Sai dai ga Zak-Shadow rana ce da tazo da abubuwa kashi-kashi. Masu ban tsoro da ban mamaki har ma da ruɗani musamman ga ahalinsa dama duk wani masoyinsa.        Rashin samun isasshen barci da daddare baisa ya kwanta da safe domin yin ramuwarsa ba. Dan ana idar da sallar asubahi ya fito a masallacin kenan su Ammar zagaye da shi kiran Imran ya shigo wayarsa. Dama ya fito da wayar ne shima dan nemansa, sai kuma akai sa'a shi ya fara kiransa. Barin inda ƙanen nasa suke yay ya koma gefe, duk suka bishi da kallo rayukansu babu daɗi, dan sun kwana da damuwa. Yanzu ma sun yanke shawarar tunkararshi da batun da aketa ɓoye musun duk da sunji komai, sai dai shakkarsa ta sakasu inda-inda har Imran ya kirashi. A tare suka saki ajiyar zuciya, sai kuma suka kalla juna....                “Na kama yaron nan a daren jiya da kaina dan na kasa haƙuri”.      “Oh shittt! Imran miyasa kai hakan?”. Zak-Shadow ya faɗa cikin runtse ido.     Cikin rashin damuwa Imran ya ce, “Zak.. wannan abun dole muyisa da gaggawa, dan jiya Dabo ya sake kirana sakamakon abubuwan daya sake samu a gidan su Ojo. Shiyasa na fahimci jira har sai gobe yabar barrak mu kamashi zai iya zama matsala. Shiyasa kawai na tarfashi a wani hotel da ya je”.            “Hakan da kayi shine dai-dai, amma matsala zata iya biyo bayan hakan nayi da kanka da kayi”.        “Miyasa?”.     “Ba maganar waya bace. Yanzu dai ina ka ajiye shi?”.      “Yana cikin gidana, dan hakan ne kawai zai k.......”                “Imran!!!!! A are you madd!!!!”.       A yanda yay maganar ba Imran ba hatta su Ma'aruff sai da suka firgita. Kafin Imran ya iya cewa wani abu Zak-Shadow ya cigaba da magana cikin kaushin murya da zafafawa. “Maza ka kimtsa shi gani nan zuwa zan fiddashi. Wane irin mugun tunani da ganganci ne wannan zaka kaishi cikin gidanka? Wlhy idan ka bari wani abu ya biyo hakan da zai taɓaka sai na HUKUNTAKA Imran. Sai na HUKUNTAKA tabbas sai na HUKUNTAKA....”          Kai da kaji yanda yake magana kasan tabbas Imran yana cikin babban lagonsa da yake matuƙar tsoro da gudun abinda zai iya taɓa rayuwarsu.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 60_ __________________ https://chat.whatsapp.com/J92XqvWDRch1EJPdGDBa41?mode=wwt https://vm.tiktok.com/ZSHWHk4ULWbMN-geqJz/ This post is shared via TikTok Lite. Download TikTok Lite to enjoy more posts: https://www.tiktok.com/tiktoklite https://chat.whatsapp.com/KfkKd9vD8MrAst8i8CQDsj?mode=wwt Assalamu alaikum, Mutanen arziki Ina musu capacity😍🥰 kuna Neman Inda zaku Samu ingantattun Kaya masu kyau da quality sosai 💝 Kamar Kayan Yara Zannuwan Gado Kayan kitchen Shoes and bags Jewellery Laces, atamfa,shadda Dadai sauransu. To nesa tazo kusa, Maza Danna wannan link din domin Samun Kaya masu inganci da ƙayatarwa da idan kika saka ko ina kika shiga sai an kalleki an ƙara kallo. Ko ku nememu ta wannan number 08165751018 ❤️❤️❤️😘 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........Imran kuwa murmushi kawai yayi daga can, sai ma ya yanke wayar yana ɗan taɓe baki. Zak-Shadow nashi kenan, shi ya yarda ya shiga kowane irin haɗari dominsa, amma idan shine ya gwada yin wani abu koyaya yanzu Zak-Shadow ɗin zai tada hankalinsa. To an taɓa rayuwa haka, shi ya sadaukar da rayuwarsa a kansa shi kuma ya gagara yin hakan saboda son tashi rayuwar, bazai yiwu ba, sai dai akan koma minene ya yarda suyi mutuwar kasko. Amma bazai yarda shima Zak-Shadow ya shiga haɗari ba duk rintsi in dai yana da damar taimakonsa...         Cikakken mintuna goma ba'ai ba kuwa Zak-Shadow ya ƙarasa gidan Imran, damma sai da ya koma gida ya ɗauki mota sannan. Wata muguwar harara ya zubama Imran ɗin dake compound zaune yana jiran isowarsa, dan yasan tunda yace zai zo to zai zo ɗin. Imran yayi dariya yana tasowa, koda ya iso jikin motar da har Zak-Shadow ya fito ya bashi hannu ƙin amsa yayi. Imran ya sake murmusawa yana kamo hannun nasa sukai musabaha. Cike da tsokana ya ce, “Haba Yayan Imran ayi haƙuri. Irin wannan tada hankali haka? Kada ka manta dai ƙanin naka soja ne fa”.       Harararsa Zak-Shadow ya sake yi, a ɗan fusace ya ce, “Kana saka kanka a haɗari da iyalanka kana ɗaukar abu wasa. Imran wai miyasa baka jin magana ne?...”           “To bana ce ayi haƙuri ba dai, sannan baka bari na kai ƙarshen maganata bane ba fa. Ba wannan gidan nake nufin na kawo shi ba, sabon gidan can fa da babu kowa”.      ALLAH sarki Zak-Shadow, wata irin ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke yana runtse idanunsa da kifa kansa jikin motar. Imran ya sake yin murmushi, sai kawai yaji ƙananun ƙwalla sun taru masa a cikin ido. Shi ya sani ƙaunar da Zak-Shadow ke masa mai girma ce, shiyasa shima bai san yawan adadin da yake masa ba a rayuwa.         Sunja lokaci a haka kafin su koma inda Imran ɗin ya taso suka zauna. Ba jimawa matarsa ta kawo musu coffee. Cikin girmamawa ta gaida Zak-Shadow dan Yaya ma take kiransa. Shima ya amsa mata da kulawa yana tambayar lafiyar yara, tace suna lafiya gasu nan ma zasu zo gaisheshi. Aiko babu jimawa suka fito, su huɗu abin sha'awa mata biyu maza biyu. Dukansu kama suke da Imran ɗin. Fuskarsa da murmurshi ya buɗe musu hannayensa, suma cike da farin ciki suka zo suka shige jikin nasa. Yanda yake suna musu soyayya irin ta mahaifi haka suke masa soyayya irin ta uba da ƴaƴa. Ya tambayesu makaranta kowa yace lafiya lau, kowa kuma na ƙoƙarin bashi labarin makarantar tasa. Shi ko yana zuba murmurshi da saurarensu. Yarinya ta uku, wadda daga ita sai auta da zasu iya zama sa'anni da Nimrah ta ce, “Dada zan bika wajen Mammah”.       Kanta ya shafa da faɗin, “Makarantar fa Ruƙayyan Dada?”.          “Ni na gaji da zuwa dama”.       Murmurshi yayi har haƙoransa na bayyana, ya ce, “Babbar magana, dama ana gajiya da neman ilimi Baby na. Kinga yanzu dai kije school, na miki alƙawarin weekend zan zo da kaina na ɗaukeki dama na kawo miki ƙawa”.         Wani tsalle Ruƙayya ta saka cike da farin ciki tana ma sauran ƴan uwanta gwalo. Suma sai suka fara ƙorafi, sai da Imran ya ga zasu damesu yace su wuce su ƙarasa shiri lokaci zai ƙure ga driver na jiransu. Badan sun so ba suka wuce ciki. Shi kuma suka cigaba da tattauna abinda ya dace. Sun tsayar da shawarar bazasu kula Ojo ba sai nan da kwana uku, zuwa lokacin ya jigata yayi laushi. Dole anan Zak-Shadow yay breakfast, dan basu baro gidan ba sai 11:30, suna zuwa ya wuce sashensa yin wanka. Shi kuma Imran ya shiga wajen Mammah, in da ya samu Uncle Nasiru da Uncle Jamilu da yazo daga Bauchi, kasancewar kuɗin jirgi Zak-Shadow ya tura masa shine ya iso da wuri. Itama Mammah ganinsa kawai tayi, har ma abin ya bata mamaki, bata samu damar tambayarsa komai ba bayan gaisuwa sai ga Uncle Nasiru yazo.         Suna zaune suna hira harda su Yaya Ma'aruff da ganin Uncle Jamilu ya hanasu fita kasuwa, dan sammakon nasa da zuwan bazata ya tabbatar musu akwai dalili. Suna nan zaunen Dada ya shigo, basu ba hatta Mammah sai da ta zuba masa ido. Shi ko kamar baiga kallon da suke masan ba ya sake fiskewa abinsa. Ja'afar daya kasa haƙuri cikin ɗan sosa ƙeya ya ce, “Humm wlhy Dada manyan kaya na maka ƙyau, ka ganka kuwa kamar sabon ango...” ya ƙarasa faɗar angon a hankali.       Hararar da Dadan ya watso masa ta saka Ma'aruff rufe baki yana danne dariya, Ja'afar kam sai yay saurin haɗe hannayensa alamar ban haƙuri, su ko su Mammah duk murmurshi sukayi. Mammah ya fara gaidawa, sannan cikin girmamawa ya gaida Uncle Nasiru da Uncle Jamilu, suma su Ja'afar suka gaisheshi. Dai-dai nan kira ke shigowa a wayar Imran, ganin likitan jiya ne mai kiran yasa shi ɗagawa a wajen batare daya tashi ba, sun gaisa yay masa bayanin ga result ya fito ya za'ayi? Sai yace masa ya jirashi gashi nan zai zo ya amsa. Yana yanke wayar ya sanar musu doctor ne.      Uncle Nasiru yace, “Ai sai muje kenan?”.         “A'a Uncle bara kawai naje na amso kuyi zamanku”.      Su Ma'aruff najin haka suka miƙe wai bari su rakashi, shi ko yace suje. Daɗi ne ya kamasu, tunda dama neman hanyar jin komai sukeyi. Bayan fitarsu ne Mammah da Uncle Nasiru da Uncle Jamilu suka sake tattauna abinda ke faruwar, dan shi dama Zak-Shadow bai ma Uncle Jamilu bayanin komai ba. Sosai Uncle Jamilu ya girgiza, tare da jin tausayin yarinyar, dan yanzun kam Mammah ta buɗema Uncle Nasiru da Uncle Jamilu komai game da mahaifin Nimrah ɗin matsayinsu na iyaye. Sai lokacin ma Zak-Shadow ke tambayar tana ina?.      Mammah ta ce, “Bilal ya tafi kaita makarantar su Mu'azz, nayi mamakin ma har yanzu bai dawo ba dan tun goma suka tafi”.         Shima agogon hannunsa ya kalla dan gab ake da kiran sallar azhar, sha biyu kusan da ashirin ne. Zai yi magana sallamar su Imran ta katseshi, kowa juyawa yay yana kallonsu banda shi. Imran ya zauna, Mammah tace Ja'afar yay kiran su Momyn Nabeeha daga nan su wuce kasuwa ta sallamesu. Baki suka tura gaba su duka alamar basu so hakan ba, dan su so suke ai komai a gabansu. Amma an koresu bayan daga Dadan sai su a gidan. Babu yanda zasuyi suka fitan, shi Ja'afar yaje ya sanar ma da su Nabeeha batun kira. Dan suna falo suna breakfast da sai yanzu suke yinsa. Daga ƙofa ya tsaya ya sanar musu, bai jira amsarsu ba ya juya abinsa.       Harara Momyn tasu da Nabeehar suka rakashi da ita, yayinda Ismat ke jin kamar taje ta rungumeshi, tana matuƙar son Ja'afar, amma shi ko kallo bata isheshi ba, randa aka saka ranar aurensu tasha kuka, amma sai ta ƙara ƙarfafa kanta akan kota biyu taje. Sai da suka gama abinda suke fin minti ashirin sannan suka tafi, a zatonsu wai haƙuri Zak-Shadow zai bada ya faɗi gaskiya tunda su basu san likita ya kira ba, duk kuma Kusancinsa da Momyn bai kirata ya sanar mata komai ba saboda hargaɗin Imran. Yanda Momy ke cika da batsewa haka Nabeeha keyi, da ƙyar ta gaida Ubanta da Mammah. Momy kam babu wanda ta gaisar, sai Mammah ita ta gaidata, ta amsa kuma da ƙyar. Shima Uncle Jamilu da yake bamai damuwa bane sai ya gaisheta. Imran da Zak-Shadow kam yi sukai kamar ma basu san da shigowarsu ba, sai hakan kuma ya ƙona mata rai, a ganinta ko Imran bazai gaisheta ba ai shi ya dace Zak-Shadow ya gaisheta kodan ƴarta da yake aure.         Cikin danne takaici Uncle Nasiru yay gyaran murya tare da yin sallama. Kowa ya amsa sannan ya amshi takardar da Imran ya miƙo masa. “Ga result ya fita, doctor ya kira Imran yaje ya amso. Zamu duba sai muga mike cik.....”       A wani irin zabure Momyn Nabeeha ta ce, “Kamar ya result ya fito anje an amsa? Ke nan wani abun aka ƙulla daban, yo inba wani abu aka ƙulla ba ai banga dalilin zuwa a amso result bada saninmu ba, kuma ai can ya kamata muje asibitin shi likitan ya mana bayani idan ba wani munafunci bane kuma ko an siyesa ne banda labari”.         Babu wanda ya tanka mata, shima Uncle Nasiru baki kawai ya ɗan taɓe yana girgiza kansa. Ya kuma buɗe takarda ya fara bayanin da kowa zai gane, sannan ya ajiyeta a kan table yace duk mai buƙata zai iya ɗauka ya sake dubawa. Caraf Nabeeha ta ɗauki takardar ta duba kuwa, tunkan takai ƙarshe ta fashe da kuka wai ita wlhy bata yarda ba, sai dai in anje ansayi likitan nan ne, dan haka sai dai a sake zuwa wani asibitin a sake sabon gwaji. Yanda Momynta ke sake zugata da faɗan maganganu sai zuciyar Uncle Nasiru data Zak-Shadow ta sake hasala. Hatta Mammah dannewa kawai take tana murmushin mamaki, shi kansa Imran sai faman cizar lips yake. Sai Uncle Jamilu ne ke magana cikin lallashi da son fahimtar da Nabeeha da uwarta. Amma da alama ma ko saurarensa ma basayi.       Gani sukai kawai Zak-Shadow ya miƙe abinsa yana kallon agogo, sai kuma ya kalla Mammah da girmamawa ya ce, “Kiyi haƙuri da hukuncin dazan yanke”.        Cikin matuƙar tsoro Mammah ke kallonsa. “Wane irin hukunci kuma Muhammad? Kar ma kayi tunanin abinda zuciyata ke hasaso min”.          “Mammah wanda ya dace ne, na san kuma kema zai gamsar dake in sha ALLAHU. In dai abinda nake tunanin zakiyi hasashe ne kuma bashi bane”. Daga haka ya kalla su Uncle's ɗin. “Lokacin salla yayi Uncle's”.       Uncle Nasiru daya gama kaiwa wuya yana kallon Nabeeha data cika kunnen mutane da ihu kawai ya fisgi flowers base dake saman Centre table ya wurga kanta. Da hannu ɗaya Zak-Shadow ya cafe, yayinda kowa a falon ya waro idon tsorata, dan gilas ne flowers base ɗin, sun tabbatar idan ya sauka akan Nabeeha sai taji ciwo in ma bai fasa mata kan gaba ɗaya ba. Haƙuri Mammah da Uncle Jamilu suka hau bashi, yayinda Momyn Nabeeha ta kacame da tsiya Nabeehar na tayata da ihun kukan iskanci..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 61_ __________________ Ina mata ma'abota ado da kwalliya maryam's all-in-one emporium ta tanadar muku Mayafai masu kyau da aminci kama daga plain chiffon veils masu kyau kamar daga Egypt suka sauko🥰 jersey scarfs , beaded and stoning veils, Chantilly, 2D to 10D Turkish veils Dubai d.s Kuma abun farinciki muna bada sari da siyan dai dai ina Kano Ina tura kaya ko'ina cikin Aminci da yardar Allah ga number ta 09064960666 https://chat.whatsapp.com/FfaJ30ZOz8NHazD2ZwtzAd?mode=wwt A cikin duniya ta gayu da burgewa mayafi shine ya ke daukaka ado da aji Maryam's all-in-one emporium 09064960666 Kano Anan ne gayu yake tarar da qawa. Ki more hadaddun Mayafan mu da suka hada da Plain chiffon veils (soft & flowy) Italian Chantilly veils (pure elegance Jersey Veils (comfort meets class) Lafaya and many more. Each piece tells a story of grace, crafted for women who understand beautyin simplicity.🤍 🖤 Premium quality 💛 Affordable luxury 🖤 Available in elegant shades 💛 Delivery 🚚 duk inda kike a fadin duniya Ba mayafi kawaii kike bukata ba you deserve a statement of class.👑 Wholesale group https://chat.whatsapp.com/FfaJ30ZOz8NHazD2ZwtzAd?mode=wwt __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Imran da Uncle Jamilu dai suka lallaɓa Uncle Nasiru suka fice. Shima Zak-Shadow da baice komai ba sai ya ajiye flowers base ɗin yabi bayansu. Sunyi alwala ran Uncle Nasiru a ɓace matuƙa, sai da suka fita wajen gidan Zak-Shadow yay musu bayanin hukuncin daya yanke kawai. Abin mamaki su duka babu wanda bai sauke ajiyar zuciya ba, sannan fuskokinsu suka washe da farin ciki, barema Uncle Nasiru albarka ya dinga zubama Zak-Shadow da faɗin, “Hakan da kai shine dai-dai Haysam, ALLAH yay maka albarka ɗan halak. Babu isashen lokacin magana suka wuce massalacin dan za'a fara salla.          An idar mutane zasu fice Imran ya dakatar da su, Uncle Nasiru da Uncle Jamilu kuma suka matsa kusa da liman suna magana. Abin mamaki, abin al'ajabi da girgiza zuciya kawai sai ji su Ma'aruff dake massalacin harda Bilal daya dawo shi da Ammar suka tsaya yin salla kafin su shiga gida Nimrah kawai suka tura ta shiga sukaji ana batun ɗaura auren mai sunan Dadan su Haysam da wata wai Naja'atu Nimrah. Abinda ya sake ɗaure kansu kuwa Dada da kansa yay wakilcin auren Naja'atu, shi kuma Uncle Nasiru yay wakilcin Haysam Abdul-rasheed Shehu da suka sake tabbatar da Dadan nasu ne dai ake nufi, sai dai sun gagara kamo lissafin wacece Naja'atu.      An ɗaura aure akan sadaki naira dubu ɗari biyu. Dubu ɗari biyu mai daraja da kima a wannan lokacin na 2013, dan kuwa itace miliyan biyun wannan ƙarnin saboda taɓarɓarewar kuɗaɗen ƙasarmu. Ana gama shafa addu'a Zak-Shadow ya dinga jin kamar an zare masa jinin jiki da jijiyoyi a lokaci guda, sai yaji wani irin sanyi na shigarsa kamar wanda yake a cikin dusar ƙanƙara. Sai da takai har kowa ya fita a massalacin shi ya kasa motsawa. Aka barsu shi da Imran kawai dake kallonsa yana shu'umin murmurshi mai ƙayatarwa. Sai da yaga da gaske ba motsawa zai yi ba sannan ya kai hannun ya taɓa kafaɗarsa. “ALLAH ya sanya albarka a wannan aure, ya bamu tsawon rayuwar ganin girman Nimrah matsayin MATAR ZAKI NA.”        Ɗago idanunsa da suka kaɗe sosai yay yana kallon Imran a karo na farko, sai kuma ya lumshesu ya sake buɗewa akan Imran ɗin cikin yanayin damuwa da motsa lips kaɗan, “Imran kada kai wannan tunanin, dan ni banyi dan hakan ba, nayi ne dan waccan shashashar ta dawo a hayyacinta ta fahimci gaskiya kafin lokaci ya ƙure mata. Amma a yau ɗin nan zan yanke  wannan igiy......”               Hannu Imran ya ɗaura masa a baki yana girgiza kansa. “Karka ce haka Haysam, kada kai irin wannan tunanin. Idan ka aikata tamkar ka zalunci Nimrah ne, ka kuma ci amanar da mahaifiyarta ta baka. Wlhy ko babu wannan rikicin kai ne yafi cancanta ka auri yarinyar nan, dan ina da tabbacin zaka zame mata garkuwa kuma bargon rufin asirin da bazata samu a wajen kowa ba koda kuwa nine...”        “Imran baka da hankali ne?, yarinya ƴar shekara bakwai kake cewa na zauna da aurenta a wannan shekarun nawa? Yin hakan ma ai shine zalunci a gareta, sanda zata gama sanin kanta ma ai na gama tsofewa”.      “A'a yagalgalewa ka gama yi ba tsofewa ba, girman yaran shekara nawa ne. Bata wata shekara bakwai ɗin nan gaba kaga ikon ALLAH, sannan shi namiji har yanama nace tsufa ne?, in dai da lafiya ai ko tamanin garai ya ɗau Sweet 16. Balle kai na tabbata sanda zata kai girman baka ko cika hamsin ba. A yanzu waye zai ce ma ka cika talatin ɗin balle ace ka ɗara. Malam ajiye huɗubar shaiɗan riƙe auren nan gam in sha ALLAHU na yin alfahari ne har cikin aljanna. Fatan mu dai ALLAH ya bamu tsahon rai da lafiyar jiki”.      Rasa ma abin cewa Zak-Shadow yayi, kallonsa kawai yake da wani irin yanayi har ya kai ƙarshen zancen. Cikin girgiza kai ya ce, “Imran bazan iya ba, ko ƙannena bana ma fatan suji wannan abun kunyar ai.....”            “Hhhhh sai dai kuma wani, dan wannan kam a gaban su aka ɗaura tun daga Ma'aruff, Ja'afar, Bilal har Ammar”.        “What!?”.     “Wlhy suna massalacin nan su duka akai komai. Kana kuma bazaka iya ba, to miye abin kunya bayan koyi kayi da sunnar MANZON ALLAH mai girma ma kuwa. Dan karka manta MANZON MU ya auri Uwar Muminai Nana A'isha (RA) tana da shekara shida a duniya, ta tare gidansa tana da shekara tara, a lokacin shi kuwa yana da shekara kusan 53, to sai kuma kai ne yanzu zaka kira abin ko kallonsa da abin kunya, bayan UBANGIJI ne ya baka batare da kai kanka ka taɓa saka hakan a lissafinka ba. Wannan wata hikima ce ta UBANGIJI dan haka babu batun yin wasa da ita a gareka, kai dai kawai yi addu'a lokacin shan gara yazo”. Imran ya faɗa yana dariya da miƙewa. Sai Zak-Shadow yaji ma jikinsa ya sake zama sanyi ƙalau. Babu yanda zai yi dole ya tashi yabi Imran ɗin suka fita zuwa gida. Shigarsu kuwa ya tabbatar da cewar ƙanen nasa sunji, dan a tsakar gida ya samu su Ja'afar tsabar iskanci sun fito da speakers ɗin ɗakinsu suna kwasar rawa su duka huɗun. Abin takaici abin haushi Nimrah a tsakiyarsu ta ware itama tana rawar. Yo dama amara Nimrah da son nanaye. Yayi kansu a fusace ya hango Mammah, Uncle Nasiru da Uncle Jamilu tsaye suna musu dariya cike da farin ciki. Sai su Nabeeha dake tsaye daga ƙofar sashensu suna kallonsu kallo irin na mamaki alamar basu san mike faruwa ba sukam. Ita Nabeeha ma hankalinta akan Nimrah yake, ji take kamar ta kashe yarinyar kowama ya huta. Dan a yanzu ɗin wani sake ganin ƙyawunta tayi alamar yarinyar ta fara washewa da cima mai ƙyau da sutura, idan kuwa takai nan gaba hummm...      Yanzu ma dariya Imran yayi da faɗin, “Zakina ka sallama kawai kaji, ka barsu suyi farin cikinsu kaga ma harda tsuntsuwar taka ake cashewa.”        Rasama abin cewa Zak-Shadow yayi, sai yay ƙoƙarin juyawa da tunanin barin gidan Uncle Nasiru ya dakatar da shi. Sai lokacin ne kuma su Bilal suka gasa ma. Da gudu kuwa suka shige ɗakinsu da yake ƙofar ta wajen compound ɗin take bata falon Mammah ba. Har Nimrah zata bisu Imran yay kiranta. Tsayawa tai kuwa cak, ganin Imran sai ta taho cike da farin ciki dan kowa sai da taba labarin makarantar da aka kaita sune bata gani ba. Imran na ganin zata zo jikinsa ya nuna mata Zak-Shadow, sai ko ta juya wajensa, caraf ta riƙo hannunsa tana faɗin, “Dada!”. Dan yau Bilal ya gaya mata yanda zata dinga kiran kowa a gidan, tare da mata faɗan ta daina cema Zak-Shadow da Imran Baba ɗan sanda. Imran tace masa Uncle, Zak-Shadow tace Dada. Shine fa yanzu tace Dada ɗin.       Kallon ta yake bai ce komai ba. Bata damuba ta fara bashi labarin makarantar kuwa hankalinta a kwance, kai daga ganin yanda take farin ciki da ɗan tsalle-tsallenta kasan abin ya kai mata har ƙuryar ranta.....              <><><><><>          A lokacin da can aure ya ɗauru tsakanin Zak-Shadow da Nimrah kamar a mafarki anan Headquarter zaman meeting Janar ya sake yi a yau shi da wasu manya da kwamitin da aka naɗa zasu yi bincike akan wannan taƙaddama ta Zak-Shadow dake tsakkiyar son kaɗa musu hankali.       Meeting room ɗin yayi shiru baka jin komai sai kaɗawar fankoki da takardun da Janar ke motsawa yana a gabansa alamar yana karanta wani abu mai muhimmanci a ciki, dan fuskarsa cike take da damuwa. Gefe ya ture takardun yana ɗan furzar da iska. Sai kuma yay ma Colonel Haydar nunin yayi magana.       Zama Colonel Haydar ya gyara, cike da girmamawa ya ce, “Sir, mun tattara dukkan bayanan da suka shafi Shadow Recon tun shekaru hudu zuwa yanzu. Ga jerin ayyukansu, bayanan waɗanda suka halarta, da kuma rahoton da ya kawo tarin matsala, wato Operation Silent Echo da a yanzu ake son yin amfani da shi akan Zak-Shadow ɗin”.       Karɓar file ɗin General yayi, cikin nutsuwarsa ya buɗe shi a hankali. Hoton aiki, sunaye, jerin lokuta. Batare daya ɗago ba ya ce, “Colonel shekara uku da suka wuce, wane irin aiki ne ya jawo rufewar su a hukumance?”.          “Sir akwai zabuka uku. Amma abin da muka fi samun tabbaci a kai shi ne haɗarin da ya faru a lokacin Operation Silent Echo, an samu mutuwar fararen hula kamar a wannan lokacin, rahoto ya haifar da tsokana a wasu kafofin yaɗa labarai, sannan aka umarci a dakatar da unit ɗin don a gudanar da bincike. A lokacin an kwance wasu membobi, wasu kuma an jefa su a ayyukan waje.”        General ya ja numfashi mai ƙarfi da ɗan furzar da iska. “Shin akwai waɗanda suka je kotu ne?”.        A yanzu kam wani dake gefen Colonel Haydar ne ya amsa da “A zahiri an yi bincike a cikin gida, amma an dakatar da duk wani shari’a saboda political interference. Wasu bayanai sun ɓace daga files na asali kuma tun a lokacin.”       Idanu General ya rufe na ɗan lokaci, alamar damuwa da fushi. Amma ya haɗiye abinka da mazan fama, cikin sauƙaƙa lafazi ya furta, “Hakan na nufin idan an ɓoye bayanai har kamar haka a wancan lokacin, to kuwa wannan maganar tana nuna akwai masu ƙoƙarin kare wasu marasa gaskiya kenan. Na san Haysam, mutum ne da baya ji daɗin cutar fararen hula. Idan akwai shaida mai ƙarfi da ke nuna akasin haka mugani”.       Yanzun kam Captain Akon ne ya miƙa wata USB ƙarama, cikin girmamawa ya ce, “Ga wasu kwafin da aka samu daga tsohon kwamandan unit, sai dai ba cikakke bane, amma akwai abubuwa masu amfani da zasu taimaka. Sannan akwai sunan wani Moly Kaithan a cikin waɗanda suka amfana daga ayyukan da suka farun”.         Cikin takaici General ya ture files ɗin kaɗan, sai kuma ya bisu da kallo ɗaya bayan ɗaya. “Kada mu yarda a rarrabe mu da siyasa. Wannan bincike zai gudana cikin sirri. Zai fito ne daga ofishin mu, daga cikin runduna kuma. Kar a bari kowa ya san matakan mu. Ina sake gargaɗin kowa ya kula, dan duk wanda yay amfani da wata matsala dake tsakaninsa da Zak-Shadow yay abinda ba shine gaskiya ba zan bashi mamaki. Colonel Haydar kai ne shugaban wannan comitin a ɓangarenmu, Brigadier General ya zama Chairman na kwamitin tuhuma da bincike, koda su daga can gidan Gwamnatin sun bada nasu”..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 62_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........“Yes sir. A yanzu haka na shirya team guda uku, legal liaison, intelligence analysis, da forensics document review. Amma sir, idan har an taba goge wasu takardun fa, ba abune mai sauki ba a garemu, dan za'a iya amfani da hakan a cimmana”        “No Colonel kada mu fara da zarge-zarge. Muna bukatar gaskiya. Ka kawo mini jerin sunayen waɗanda suka yi aiki tare da Shadow Recon, waɗanda suka zauna a gida da waɗanda aka tura waje. Zan fara da hira da su.”          Cikin gamsuwa Colonel Haydar ya yi ƙasa da kai na girmamawa, “Sir, zan kawo jerin nan gobe in sha ALLAHU. Amma fa akwai ƴar matsala a waje, wasu daga cikin waɗanda aka rufe sun riga sun shiga harkar siyasa wasu kasuwanci. Wasu kuma sun yi murabus ne kawai dan kansu sun koma gefe.”       Kai General ya jinjina kawai batare da yace komai ba, sai kuma ya ɗauki fayel ɗin dake ɗauke da hoton Zak-Shadow ya zubama hoton ido ba wasu sakanni. “Zan sanar da Ministan Tsaro cewa wannan bincike zai cigaba da tafiyar a karkashinmu har zuwa wani lokaci kafin nasu ɓangaren kwamitin su shigo ciki. Dan gaskiya muna bukatar hujja a hannuwan mu kafin mu kira ko mun gayyaci kowa. Sai kuyi ƙoƙarin tattara komai daya shafi shi wannan harin na kwanaki goma tun daga farkonsa har zuwa fitowarsu a jejin. Dan zamu iya gayyatar Haysam nan da 2 to 3 days. Ina ƙara gargaɗinku ku kula”.        A tare suka amsa da “Yes Sir”. Daga haka ya fice ADC ɗinsa biye da shi.....        <<•>><<•>><<•>>       Tunda Uncle Nasiru ya fara bayanin sa jikin Nabeeha ya fara rawa, bata ma bari ya kai ƙarshe ba cikin ɗimuwa ta ce, “Abba nifa ban gane ba. Wai wane Haysam kake magana ya auri wanene...?”         Sai da Uncle Nasiru ya zuba mata harara, cikin sake tsaurara harshe ya ce, “Hausar ce kika daina fahimta kenna ko? Bayan Haysam mijinki akwai wani Haysam ɗin ne anan? Ba kince ke baƙya ji ba, uwarki kuma itace limamiyarki mai ɗoraki akan keken ɓera. Kinga yanzu ke da ita bakwa buƙatar sake gwajin likita ko ƙaryatawa tunda dai UBA baya auren ƳARSA.....”         “Amma Nasiru kai azzalumi ne? Ƴar taka za'a haɗa kai da kai a wulaƙanta?”. Momyn tace tai maganar cikin huci da miƙewa kamar zata rufe Uncle Nasiru da duka. Dan sai wani girgiza jiki take, hakan yasa kowa zuba mata ido banda Zak-Shadow dake danna waya kamar ma ba'a kansa ake bala'in ba. Dai-dai nan ihun Nimrah ya karaɗe kunnuwansu. Kusan lokaci guda Mammah da Zak-Shadow suka miƙe, hakama Imran da Uncle Jamilu. A tare su huɗun suka nufi kitchen inda suke jiyo ihun nata, shima Uncle Nasiru ya take musu baya. Babu wanda bai razana da ganin Nabeeha a kitchen ɗin ba da wuƙa a hannu, yayinda Nimrah ke can saman kitchen cabinet ta maƙale Nabeeha dake ƙoƙarin jawota na kuka da faɗin, “Wlhy sai na kasheki, shegiyar yarinya annoba mai kama da arnan jeji baƙa mummuna”.        Nimrah dake kuka cike da ihu da cika kunne ta ce, “Niba shegiya bace ba, kuma ba arniya bace muguwa mai yanka mutane. Wayyo Ummana zata yankani kizo Umma, Kawu Tanimu na....” numfashinta ya wani jaaa alamar ɗaukewa saboda kafta da Nabeeha ta sake kai mata da wuƙar cikin rufewar idanu. Hakan kuma yayi dai-dai da isowar Zak-Shadow gabanta yay ƙoƙarin janyeta amma ina UBANGIJI ya riga ya ƙaddara sai ta sami Nimrah sai ko ta shata mata wuƙa a cinya. Ya rabbi, wani irin gigitaccen ihu da Nimrah ta saki Zak-Shadow bai ma san ya wanke fuskar Nabeeha da wani wawan mari guda biyu ba a lokaci ɗaya, wajen yin taga-taga zatai baya saboda gigita shima ta sharɓeshi a hannu, saboda kaifin wuƙar sai da ta fasa rigar shaddar jikinsa ta ratsa fatarsa. Amma bawon ALLAH bata kansa yake ba, ƙoƙarin zaro Nimrah data maƙale a lungu yake yi dan yarinyar tayi ɗif alamar ta suma. Ga jini tuni ya wanke rigarta ta dai-dai cinya inda Nabeeha ta yanke ta.       Gaba ɗaya hankalin su Mammah ya gama tashi, Zak-Shadow dake rungume da Nimrah yana gama sauketa Mammah ta ɗaga rigar, ai a rikice tace, “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un” dan yanka ne babba sosai damma jini ya jiƙe ƴar cinyar tata ba'a iya ganin girmansa da zurfinsa.          “Muhammad karka sauketa muje asibiti”. Mammah ta faɗa cikin tashin hankali. Suma su Uncle Jamilu gaba ɗaya sun gama rikicewa. Hatta Momyn Nabeeha rawa jikinta yake yi, tama kasa zuwa inda Nabeehar ta kife kan kitchen cabinet itama alamar taji marin maza. Sai da suka fice Uncle Nasiru da gaba ɗaya yay sumar tsaye ya tafi taga-taga zai faɗi, da ƙyar ya iya laluben bango ya dafe. A haka ya fice a kitchen ɗin shima yabar Momyn Nabeeha da jikinta ke rawa zuciyarta kamar zata fashe. Dan kasancewar a ƙarshe tazo sai idonta ke nuna mata akan ciki Nabeeha ta yanki yarinyar, kai tsaye ta kasheta...        Acan compound ma su Ja'afar gaba ɗaya sun gigice saboda a yanda Dadansu ya fito da Nimrah shaddar jikinsa duk ta ɓaci da jini abinka da fara kawai sun ɗauka ta mutu ne.  Hankali a tashe suke tambayar miya faru? Basu sami amsar kowa ba, sai kawai suma suka fara rige-rigen shiga mota....         ★ Duk da raɗaɗin da hannunsa ke masa bata kansa yake ba, yana riƙe da Nimrah har aka gama mata ɗinki bayan an tsaida jinin da ƙyar dan anyi allura takai uku kafin aci nasara. Ya rabbi, duk mai imani dole yaji tausayin yarinyar, dan kuwa yankane bana wasa ba, gashi ya shiga sosai har ana iya ganin ƙashin ta. Su kansu asibitin da farko tsoron taɓata sukai sai da Zak-Shadow ya nema gigitasu da ihu. Dole suka dawo hayyacinsu sukai abinda ya dace. Tana sume akai komai aka gama, sannan suka farfaɗo da ita da dabarunsu. Allurar barci suka sake mata dan da ihu ta farka.       Imran ya maida Zak-Shadow dake neman miƙewa ya zaunar yana ma nurse ɗin nuni da hannunsa. Ƙoƙarin nuna shi baya buƙata yayi, dan haka Imran ɗin ya ɗaure fuska ya kafa ya tsare kuma. Dole ya haƙura ya tsaya. Nashi ma da sauƙi amma fa ya yanku shima babu laifi, sai dai bai kai ko kwatar na Nimrah ba. Amma shima duk da haka sun masa ɗinki a wajen.          Sun so riƙe Nimrah yace kawai a sallamesu za'a kula da ita a gida. Dole aka basu sallama da magunguna da dokar kawota ana dubawa suka wuce gida. Yanzu ɗin ma shine ya ɗauketa, ko'a mota tana riƙe a jikinsa har gida. Anan kuma suka tarar da tashin hankalin Uncle Nasiru, su Ismat da Biebah data dawo makaranta zagaye da shi suna kuka, sauƙin ma Biebah tai hankalin kiran matarsa, shine fa ta iso a rikice da likitansu datai kira a waya. Shine yaketa ƙoƙarin ganin nunfahsinsa ya daidaita sanda suke shigowa.     Kai sukam dai wannan family sai dai suce Alhamdullah a wannan tsakani. Ganin al'amarin zai ƙwaɓe dole aka ɗauki Uncle Nasiru zuwa asibiti. Ga kuma Nabeeha can ta kulle kanta a ɗaki tana ihun kuka da rantsuwar idan Zak-Shadow bai saki Nimrah ba sai ta kashe kanta itama. Takaici ya saka babu wanda yabi takan haukan nata sai uwarta dake magiya da lallashinta su Amima na tayata. Da ƙyar da ƙyar dai suka samu ta buɗe. Uwar ta wani rungumeta tana kuka itama wai miyasa zatai mata haka. Miye-miye dai nan sukaita surutasu.....         ★       “Tunda barci take kaje ka raba kayan nan da jikinka Muhammad, sam basu da ƙyan gani duk jini abinka da farin abu ƙara tada hankali yake”. Mammah ce mai maganar cikin damuwa da sanyi, dan kuwa babu abinda ke mata kai-kawo idan ta kallesa sai lokacin da Abdul-rasheed ke shinfiɗe a ƙasa an lulluɓa masa babbar rigar shaddarsa data jiƙe da jini.      Dama su kaɗai ne a ɗakin nata, daga ita sai shi sai Nimrah daya shinfiɗar a gado. Kansa ya jinjina yana miƙewa. Har ya fara tafiya ta sake dakatar da shi. “Dan ALLAH na roƙeka kada kace musu komai?”.       A karo na farko ya zubama Mammah hargitsatstsun idanunsa da suka mugun kaɗewa kamar wanda ya busa cocaine. Ita kanta Mammah sai da taji zuciyarta ta motsa saboda yanda idanun nasa suka koma. Magana yake son yi amma zuciyar ƴan maza tazo wuya ya ma kasa, sai kawai ta ce, “Dawo ka zauna”..         Bata jira amsawarsa ba ta taso ta kama hannunsa ta maidoshi inda ya tashi. Baya iya bijire umarninta, dan haka ya koma ya zauna kawai kamar yanda ta buƙata. Itama sai ta sauke ajiyar zuciya ita ta fita a ɗakin. Babu jimawa Ma'aruff yay sallama a ƙofar ɗakin cikin rawar murya alamar shima tsoron shigowa yake, dan sun san wanene Dadansu idan yana fushi, ya subahanallah abin babu ƙyau sam. Sum-sum ya shigo kansa a ƙasa kamar munafuki, kaɗan ya saci kallonsa yaga idanunsa a rufe suke, ƙaramar ajiyar zuciya ya sauke tare da ajiye kayan a kusa da shi kaɗan. Idanunsa cike da hawaye miryarsa na rawa kamar wani ƙaramin yaro, ba komai ya kawo hakan ba kuma sai tausayin Dada, dan duniya basa ƙaunar abinda zai taɓa musu shi.       “Kayi haƙuri Dada, ga kaya ka canja inji Mammah”.. sanin ya jishi, yasan bazaiyi magana ba kuma yasa shi fita yana share hawayen da suka sakko masa. Wlhy badan Mammah ta hana su ba yau sai sunma Nabeeha dukan mutuwa a gidan nan, kuma da bazata kwanar musu a gida ba. Amma babu yanda suka iya Mammah ta kafa ta tsare. A falo ma sauran ƴan uwansa na zaune jigum-jigum, dan har su Ummi ma sun zo gidan tuni..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 63_ __________________ https://chat.whatsapp.com/J92XqvWDRch1EJPdGDBa41?mode=wwt https://vm.tiktok.com/ZSHWHk4ULWbMN-geqJz/ This post is shared via TikTok Lite. Download TikTok Lite to enjoy more posts: https://www.tiktok.com/tiktoklite https://chat.whatsapp.com/KfkKd9vD8MrAst8i8CQDsj?mode=wwt Assalamu alaikum, Mutanen arziki Ina musu capacity😍🥰 kuna Neman Inda zaku Samu ingantattun Kaya masu kyau da quality sosai 💝 Kamar Kayan Yara Zannuwan Gado Kayan kitchen Shoes and bags Jewellery Laces, atamfa,shadda Dadai sauransu. To nesa tazo kusa, Maza Danna wannan link din domin Samun Kaya masu inganci da ƙayatarwa da idan kika saka ko ina kika shiga sai an kalleki an ƙara kallo. Ko ku nememu ta wannan number 08165751018 ❤️❤️❤️😘 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ..........Washe gari da fitinar Nimrah suka tashi a gidan. Dan tunda ta farka da asuba take ta kuka ƙafarta-ƙafarta. Haka suke zagaye da ita kowa na ƙoƙarin lallashinta. Yayinda Mu'azz ke tayata kukan shima. Sai kusan bakwai Zak-Shadow da bai san abinda ke faruwa ba ya shigo. Dan rashin samun isasshen barci a daren jiya shima yau makara yay ko sallar asuba a gida yayi ta. Dan haka sai yanzu yake fitowa daga sashensa, batare da ya ko kalla hanyar ɗakin Nabeeha ba, hasalima yayi zaton basa gidan, dan tunda suka dawo asibiti jiya baiga kowa ba tsakanin ita da uwar tasu da ƙannen nata, sai Jiddah ce ma da daddare ita da mijinta suka zo duba su tanata kuka da bashi haƙuri akan abinda ƴar uwar tata tayi.          Tun shigowarsa falon yake jin kukan Nimrah. Kai tsaye ɗakin Mammahn ya nufa shima, inda ya tadda duk ƙannensa a ciki. Kowa kuma ƙoƙarin lallashin Nimrah dake kwance jikin Mammah yake yi, amma yarinyar nan taƙi sauraren kowa sai kwarara ihu take yi. Babu wanda yaji sallamarsa sai da ƙamshin turarensa ya shiga hancinansu da gyaran muryar da yayi sannan duk suka juyo, idonsa akan ƙafar Nimrah ya amsa gaisuwarsu, suko hankulansu na'a kan hannunsa shima.         Cikin girmamawa da tsantseni ya gaida Mammah shima, tare da tambayarta jikin Nimrah data ɗan sassauta kukanta.      “Alhamdulillah, sai dai inaga dole mu koma asibiti yanzu dan tunda asuba take kukan ƙafar, inaga tana mata ciwo ne, kaima yaya naka hannun?”.        Hannun nasa ya ɗan kalla, sai kuma ya kalla ƙafar Nimrah ɗin itama. “Ni kam babu wani damuwa Mammah, itama harda rigima dai”.      “Rigima kam ai dole ce, dan tana da hujjar yinta. Wannan ciwon ba ƙarami bane ga babba ma bare ita. Babbar damuwar ma taƙi cin komai ga tea nan har ya huce taƙi sha”.         Hannu ya miƙama Biebah dake riƙe da kofin batare da yace komai ba,  ganin haka sai kawai Mammah ta miƙe tana faɗin, “To Biebah tashi ki nema na mutane abincin kari. Mu'azz tashi kaima muje kai shirin makaranta.”     Kamar zai yi kuka ya ce, “Mammah ni bazanje ba, zan zauna tare da Nina”.     Kallon da Zak-Shadow ya watso masa ya sashi sauka a gadon da sauri, sai dai idanunsa cike da ƙwalla. Murmurshi kawai Mammah tayi ta kama hannunsa suka fice. Caraf Nimrah ta ce, “Mammah ni dai ki dawo naki nake so....”        Mammah na ƙoƙarin juyowa Zak-Shadow ya watsama Nimrah harara, sai ta sake taɓe baki zatai kuka.      “Kika bari wannan hawayen suka zubo zaneki zanyi. Maza karɓa kisha. Kin zauna kinama mutane kukan banza amma bakinki baya mutuwa”.           “Ni dai dan ALLAH ka bita a hankali Muhammad, idan bazaka iya ba na dawo na bata”.     Ƙaramin murmushi yayi. “Shike nan Mammah zan bata”.      Suma su Bilal duk murmushin sukayi dan sunji daɗin ganin murmushin nashi. Shima zamansa ya gyara ya fara kai mata kofin bakinta, sai ko ta fara amsa babu musu. Sha kamar uku ta yatsine fuska tana kallonsa, ta ce, “Dada”.        “Uhhhm”.    Ya amsa mata a maƙoshi. “Kaima ƴar dabar ce ta jimaka ciwo a hannu?”.      Da mamaki ya zuba mata ido, a zuciyarsa yana ayyana (sai shegen surutu). Suko su Ja'afar dariya zancen nata ya basu, jira suke suji amsar da Dadan zai bata amma yayi shiru. Cikin kasa haƙuri Ammar ya ce, “Nimrah ƴar daba kuma?”.          “Eh Uncle Ammar”. Ta faɗa kamar yanda taji Mu'azz na kiran kowansu da Uncle ɗin. Batare da jiran cewar kowa ba ta cigaba da faɗin, “Ummana tace ƴan daba ke riƙe wuƙa da yanka mutane ai. Kaga itama ta riƙe wuƙa ta yankamu ni da Dada, Dada kaima kayi kuka data yanka ka?”.      Ta ƙare maganar tana tsatstsareshi da idanu. Rasama abin cewa yay, sai kawai ya samu kansa da girgiza mata kai. Idanu ta waro masa sosai, sai kuma ta yamutsa fuska alamar motsin da tai taji zafi. Amma bata haƙura ba sake cewa, “Kenan kai baka yi kuka ba? Kuma baya maka zafi kamar nawa?”.          Nan ma kai kawai ya jinjina mata yana kai mata kofin shayin a baki dan ta ƙyaleshi da wannan surutun nata, gashi ta wani tsatstsareshi da idannunta. Kauda kanta tai gefe, dan in surutu nacin Nimrah itafa sai ta fetsar take jin daɗi, dan yanzu ma kai tsaye ta ce, “Dada jira na gama. Kai miyasa baka jin zafin ko kaima ɗan daba ne? Dan Lawwali yace min suna ƴan daba dake yankar mutum idan aka yanke su basa jin zafi kuma basa yin kuka”.      Anya shi kam ya taɓa gamuwa da magananniyar yarinya irin wannan? A zuciyarsa yake ayyanawa, yayinda su Ma'aruff ke ƙunshe dariyar dake cinsu. Dai-dai Nimrah ta kai hannu tana taɓa hannun Zak-Shadow dake kallonta kawai Momyn Nabeeha tai sallama, kafin su amsa ta shigo Nabeeha biye da ita sai su Ismat a ƙarshe, dan ita da kanta ta tattaro su wai su duba Nimrah su bama su Mammah haƙuri. Ai a bazata Nimrah tai wani uban tsalle ta haye jikin Zak-Shadow ta ƙanƙamesa tana fasa ihu da faɗin, “Wayyo Dada ƴar daba ta sake zuwa, ɓoyeni kada ta yankamu. Wayyo Dada wayyo zata ƙara yankamu shike nan ƴar daba mai wuƙa”.       Idan kunji ana sumar tsaye to ita Nabeeha da uwarta sukayi. Dan har tsakiyar kai kalmar (ƴar daba) ɗin nan ta dakesu. Yayinda su Bilal suka kasa haƙuri shi da Ammar suka shiga kwasar dariya. Suko su Amima yanda Nimrah tai uban tsalle ne da firgita ya basu dariya. Ita ko baiwar ALLAH da gaske tsorata tayi, dan tai bala'in shigewa cikin jikinsa, ƙarshe ma rigarsa ta ɗaga ta tura kanta ciki ta duƙunƙune, ALLAH ya sota ma tun a daka tsallen farko ya riƙe ƙafar tata mai ciwo a hannunsa, da ba ƙaramin fami zatayi ba kam, maybe ma ɗinkin ya farke tunda jikin ba wani ƙwari gareshi ba fatar ƙuruciya. Ihun Nimrah ya shigo da Mammah da Biebah, sai Mu'azz da har an masa shirin makaranta.       A tsorace Mammah ta ce, “Wai mike faruwa?”.         Da ƙarfi Nimrah dake cikin rigar Zak-Shadow ta ce, “Ƴar daba ce mai wuƙa Mammah ta dawo zata yankamu ni da Dada, ku yankata Mammah kuma ku yayyankata kamar akuya”.       Duk yanda Yaya Ma'aruff da Yays Ja'afar ke dauriya a wannan gaɓar suma sai da suka dara. Sai Mu'azz ne abinka da yarinta ya hau gadon yana kamo hannunta da faɗin, “Ke Nina bafa ƴar daba bace su Aunty ne fa”.        Cikin kuka Nimrah ta ce, “Ƙarya kakeyi Ƴar daba ce, ranar ita ta yankamu ni da Dada, kuma tace saita kasheni bata sona. Muguwa! Muguwa in ALLAH ya yarda sai kin mutu yau kin haɗu da fatalwar kabari da walakiri mai ƙaton sanda”.         Cikin matsanancin ɓacin rai da kishin ganin yanda Nimrah ta shige rigar Dada, shi kuma ya wani zauna kamar gunki yana riƙe da ƙafarta kawai sai zuciya ta tokare ƙirjin Nabeeha. A zafafe ta ce, “Ubanki ne mugu ɗan daba shegiyar yarinya mayya, Momy ga abinda nake gaya miki nan kinƙi yarda kina wani muzo mu ganta...” tai maganar tana kai hannu zata damƙo ƙafar Nimrah dake hannun Dada. Abinda kuwa bata taɓa zato bane ya faru, dan kuwa caraf aka riƙe hannun nata, tana ƙoƙarin fisgewa cikin rufewar idanu Mammah ta ɗauke fuskarta da mari. Lokaci guda ɗakin yay tsitt, dan bama ita data ɗago a birkice taga Mammah ce mai marin ba hatta Zak-Shadow kansa ya girgiza, dan kowa yasan wacece Mammah akan kawaici.... Katse tunaninsu Mammah tayi, cikin faɗa ta ce, “Shin haka kike dama Nabeeha ko yanzu ne wannan halayyar banzar take neman shigarki? Wane shirme ne wannan kike yi akan yarinya ƙarama ƴar cikin ki, wadda da ALLAH ya baku haihuwa kin haifi wadda ma ta fita......”          Hannun Nabeeha Momynta ta kwace daga wajen Mammah, itama a fusace ta ce, “Haba Hajiya A'isha yada haka da girmanki? Bakiga laifin Haysam shi da ya auri ƴar cikinsa ba sai laifinta, kishiya ko jaririyace ai yin kishinta ba haramun bane balle wannan hatsabibiyar yarinyar mai kama da an haifeta a tsakiyar tasha.....”          “K! Ya isheki haka Malama!!”.     Ma'aruff ya faɗa a zafafe tamkar zai kaima Momy duka. Cikin zazzaro idanu dan shima akwai zuciya kamar Dada ya cigaba da faɗin. “K har kina da bakin cema wata ƴar tasha bayan ga ƴar tasha nan kin haifa mai yankar mutane da wuƙa, ai gaskiya Nimrah ta faɗa ƴar daba kika haifa, sannan Wlhy mahaifiyarmu ta fita cikin idanunki idan ba haka ba kuma zaki sha mamaki, dan akan Mammah da Dada komai zamu iya yi ciki harda koya muku tarbiyya dan naga tayi ƙaranci anan. Ku mi yasa baku san kawaici bane ba, idan badan Mammah ɗin ba wlhy da tun jiya mun yagalgala ku sai buzinku.”.        “Iyeee!!! Ma'aruff ni zakama rashin kunya?”.     “Anyi miki ɗin, in har zaki taɓa mana uwa duka ma zaki iya ci a hannunmu. Anata muku kawaici amma bakwa ganewa, damma kin samu ana gayawa ƴar taki gaskiya da gyara tarbiyyarta tunda ke kin kasa. Nimrah kuma ta zama matar Dada sai dai duk mai mutuwa ya mutu da baƙin ciki babu canji, wani wasan ma sai nan da shekarun girma.....”          Hannun Ma'aruff Mammah ta riƙo dan yi yake kamar zai kwashe Momyn Nabeeha da mari. “Ya isa haka”. Cewar Mammah tana janye Ma'aruff baya. Kafin ta maida dubanta gasu Nabeeha, babu alamar wasa ko sassauci a tare da ita ta nuna musu hanyar fita, “Ga hanya Hajiya Hasiba, idan kuma kuka kaini bango to zan barku da Muhammad, kun san kuma abin bazaiyi ƙyau ba. Dan na fara gajiya da tausarsa akan wannan haukar na Nabeeha. Dan ALLAH ku barmu muji da abinda ya dame mu.”       Cikin ɓacin rai itama Momyn ta buɗe baki zatai magana Mammah ta sake ɗaga mata hannu tana girgiza kanta....         “Idan bazasu fita da arziƙi ba Mammah ki barmu mu fitar da su, dan mu nan munma ishesu Dada yafi ƙarfinsu, su ɗin banza ya tanka haukarsu”.      Yanzun kam Ja'afar ne mai maganar. Jiki a sanyaye Ismat tazo ta kama hannun Momynsu dana Nabeeha, shiyyasa tacema Momy kada aje bada haƙurin nan yanzu dan tasan nacin Nabeeha da mitar tsiya, sun kuma san wanene Dada a gidan. To gashi nan shi baima ko kallesu ba su Yaya Ma'aruff na neman lakaɗa musu duka. Duk haƙurin Mammah yau an sakata tayi abinda ko da kwatance basu taɓa gani ba a tsawon rayuwar zamansu gidan kusan shekara uku..........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 64_ __________________ https://chat.whatsapp.com/L3BXH7JYlBRHIkFRiOjeW3?mode=ems_copy_t UMMU KHALIFA COLLECTION Ina Mata Yan kwalisa ina mata masu san kayan ado kamar Egyptian abaya sleeping drees kids were shos bags musk dahara original. To kukanku yazo karshe domin ummu khalifa sun zo muku da duk wadannnan kayan dierct suke order dinsu daga Egypt zuwa gida Nigeria kaidai kawai kashiga link dinsu domin gani ya kori jiii.. Ba nan ummuh khalifa suka tsaya ba suna nemawq mutane visa masu shaawar shugowa kasar ta Egypt karatu ko yawon bude ido ko kasuwanci ku tuntubeta a number dinta +201017018846/07048811474/ KO kuma shafinta na tiktok https://vt.tiktok.com/ZSU1FEkjc/ __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Duk wannan bidiri da ake fa Nimrah na cikin rigar Zak-Shadow har lokacin, sai dai ta ɗan ɗaga tana kallon komai. Sai da taga su Nabeeha sun fita ta wani sauke ajiyar zuciya kamar babba tana fitowa, hawaye shaɓe-shaɓe a fuska ta kama dariya da faɗin, “Yauwa Uncle Ma'aruff kun kori ƴan daba. Ai dama kun zaneta. Kuma in ALLAH ya yarda sai ta mutu kuraye da fatalwoyi sun cinyeta ko ɗan ƙashi bazasu bar mata ba.” shirmenta ya sakasu yin murmushi gaba ɗaya. Banda Zak-Shadow dake zaune shiru har yanzu. Sai dai Nimrah na gama fita a jikinsa ya ƙarasa ajiyeta kawai ya miƙe. Da sauri Mammah ta ce, “Muhammad ina zaka?”.       “Kiyi haƙuri Mammah”.    Abinda kawai ya iya faɗa kenan yay waje tamkar mayunwacin zaki. Kiransa Mammah keyi, dan indai yace tayi haƙuri zai aikata ba daidai bane amma ina. Daɗi ne ya kama su Bilal, dan sun san Dada aiki ne gamai ƙare ka. Mammah na yunƙurawa zata bishi su Ma'aruff suka riƙeta cike da makirci suna bata haƙuri, nan ko so suke Dada yaje yay abinda suke so kada ta hana....      (Sai daku ƙanen Dada 😂💃🏼) >>><<★>><<<         “Aiki ya faɗa”.    Cewar Mr Specter yana wata dariyar mugunta cike da nishaɗi. Suma sauran dariyar suke har oga Jush duk da kuwa shi mutum ne bamai yawan dariya ba.       Scythe ya ajiye kofin giyar daya kwankwaɗa, cike da izza ya ce, “Ka faɗi wasan Zak-Shadow”.        “Faɗuwa kan faɗuwa ma kuwa”.     Black Spider ya karɓe yana ƙyalƙyala dariya.       Viper ya cigaba da faɗin, “Ai ban taɓa zaton shegen nan zai faɗi haka cikin sauƙi ba, babu ƙarya ya wahalar da mu.”               “Ni kaina ban zato ba Viper, ashe tun da can da haka mukai da tuni labarin wani ake bashi ba. Ashema fankamar banza yake shege zagaye yake da maƙiya yana tunanin mayaƙa ne. Na rasa miyasa suka kasa kaishi ƙasa tuntuni bayan ya gama shige musu hanci tun tuni.”       “Humm bakaji mi Garba nan yace ba, Janar ɗin nasu ne ya tsaya masa ai shiyyasa, dan ko yanzu yace ya kafa ya tsare akan bayanan cikin gida da ake haɗawa wai karsu fitar.”            “Ɗan wahala, yayi ya gama shima ta kujerarsa yake yi. Hatta Ministan nan sai mun ɓarar da shi a kujerarsa”.     “Wannan dole ne ai, shi kansa uban gayyar tasu dolene mu ɓarar da shi dan na fahimci badan wannan matakin da muka ɗauka ba bazai bamu haɗin kai ba.”           “Karku wani damu kanku, duk wanda yay mana kan kara sai mun masa na itace.”     Raven ya ce, “Ni bama duk wannan ba, ɗazun fa mutum nan ke sanar dani ya rasa kowane bayani daga ɓangaren cikin yaronmu. Kuma yaro mafi kwazo dake kusa da Zak-Shadow”.        Cikin zabura Oga Jush ya ce, “Kana da hankali kuwa Raven, amma shine baka sanar ba?”.       “Kayi haƙuri sir, nima yanzu zamu shigo nan nake ganin saƙonsa. Shiyyasa ma na ɗan dakata nai kiransa a waya kafin na shigo. Amma na bashi awanni uku akan ya tabbatar yazo da labarin da kai zai iya ɗauka”.      Lokaci guda sukai ɗif, kusan mintuna biyu oga Jush ya ɗauka waya. Kai tsaye yay kiran number Garba. Aiko sai gashi ya ɗaga yana magana ƙasa-ƙasa daga can. Cikin rufewar ido Oga Jush yace, “Ina son ganinka idan ba damuwa”.         A gadarance Garba ya ce, “Bazai yiwu ba dan ina kan aiki. Ka faɗi koma miye a haka ina jinka”.     Duk da Oga Jush yaji haushi sai ya danne, a ransa yana tabbatar da zai yi maganin Garba ɗin, ya dai gama musu aikin nan. “Okay ba damuwa, na samu rahoto ne mai ƙarfi yanzu cewar cikin yaran Zak-Shadow babu wani, kuma makusancinmu ne.”       “Miye rank ɗinsa?”.   “Lieutenant.” Jimmm Garba yay alamar tunani, zuwa can ya nisa, cike da son nuna gwaninta ya ce, “Ka tura hotonsa. Duk da ina da tabbacin Ojo ne ko Rufa'i”.       Oga Jush bawani yasan sunan yaron bane ba, dan haka yace, “Okay yanzun nan za'a tura maka”. Daga haka ya ajiye wayar yana kallon Raven. “Ka kira shi yanzun nan ya tura maka hotonsa a tura masa”.       “Okay Sir”.    Raven ya faɗa yana ƙoƙarin kiran Nanu. Bugu ɗaya kuwa ya ɗaga, cike da girmamawa daga can ya ce, “Ayi haƙuri sir ina kan bincike yanzu haka”.           “Babu damuwa, zamu samu hotonsa ne?”.        “Eh za'a samu sir”.    “Tura min”.   Cikin sakanni hoton Ojo ya shigo wayar Raven. Babu ɓata lokaci kuma aka turama Garba..... <<<<<<>>>>>>>        Dariya sosai Lt Col. Garba keyi yana kallon hoton Ojo. Lallai yanzu ne wasa zai ƙara zafi kamar yanda yake so. Domin kuwa kowa yasan Ojo yaro ne makusancin Zak-Shadow matuƙa gaya. Yaransa biyu amintattu ya saka a sirri su bincika masa ina Ojo yake daga lokacin zuwa dare. Da girmamawa suka amsa masa kuwa.       Ai ko awa ɗaya basu cika ba sukazo masa da bayanin tafiyar Ojo gida. Sai dai a labari mai ƙarfi ga wani abokin Ojo shine Ojo na wani hotel ne zaune da budurwarsa bai je gida ba. Hakan yay ma Garba daɗi, da kansa ya nufi hotel ɗin neman Ojo ɗin, bayan ya saka abokin na Ojo bashi number ɗin budurwar. Dan sun gwada kiran layin Ojo a kashe.        Koda ya kirata ta sanar masa inda zasu haɗu ya sameta cikin damuwa da jin haushi. Dan a amsoshin da take bashi ya fahimci haka. Jin cewar daga fita sayo mata abu a mall ɗin kusa da hotel ɗin shine bai dawo ba yay shiru yana nazari. Kafin cikin jinjina kai yace ta bashi wayarsa.       “Da wayar ya fita ai”.   Nan ma shiru Lt. Garba yayi, sai kuma ya miƙe ya mata sallama. Bai zame ko ina ba sai ofishin ogansa, ya labarta masa komai daya samo. Murmurshi Ogan yayi da girgiza kansa, ya ce, “Baka da dama Garba, ka dai dage da kai za'a kai Zak-Shadow ƙasa”.        “Na tsaneshi ne Sir! Tun tuni da na samu dama ma da wannan hannun nawa zan kashe banza wlhy. A wannan gaɓar kam idan na bari aka ƙara masa girman da ake shirin yi zan shiga uku ne kawai, Junior ɗina ne fa a makaranta ake shirin maidawa Senior ɗina akan aiki, haba impossible nabar Haysam ya koma samana, a yanzu ma da muke mate a aiki ba ƙaramin zafin hakan nake ji ba, shiyyasa akan wannan al'amarin sai inda ƙarfina ya ƙare”.         “Zan kuwa taimaka maka kodan kwatanta alkairin da kai min nima a baya. Yanzu kaje ka samu abokin shi yaron ya kai report ma ogansu kan basu san inda yake ba, kuma gidansu an kira ance baije ba zan ƙarasa sauran aikin.”      “Okay Sir!”.    Lt. Col. Garba ya faɗa cike da farin ciki yana miƙewa. Sai da ya ƙame ya sara masa sannan ya fita. Yana zuwa kuwa abokin Ojo ɗin ya nema, ya tsara masa komai. Shi ko aboki najin zai samu tagomashin arziƙi babu wani tunani yaje ya kaima ogansu report kamar yanda Lt Garba ya tsara masa. Oga yay shiru cikin nazari, dan kuwa Ojo yana ƙarƙashin Zak-Shadow ne, shi kuma ya kamata a kaima report ɗin rashin ganin Ojon, sai dai kuma a yanzu Zak-Shadow baya kan aiki yana hutu, a gefe kuma ga tataɓurzar da ake yi a kansa ma. Daya lissafa yaga lissafin bazai dai-daita ba sai kawai ya tura report ɗin shima sama.         Tura report ɗin rashin Ojo anyi rashin sa'a ya faɗa a hannun ɗaya daga cikin membobin kwamitin bincike, wanda kuma shima sam baya ra'ayin Zak-Shadow. Aiko baiyi ƙasa a gwiwa ba ya kai ga kwamiti tare da tsatstsara zantukan da suka ja hankalinsu har suka maida hankali akan batun, tunda dama a wannan gaɓar bai kamata suyi sakaci da abu komai ƙanƙantarsa ba...       ★ Bincike ya tabbata akan neman Ojo ta ɓangare biyu koma muce uku. Domin kuwa ga ƴan ƙungiyar duhu, ga Lt. Garba, ga kuma kwamitin bincike. Al'amarin kamar wasa aka girmamashi ya zama babba. Inda a karo na farko Nanu ya haɗu da shugabannin ƙungiyar duhu saɓanin da da bai san kowa ba sai Raven. Yau kam sai gashi ƙuru-ƙuru zaune a tsakkiyarsu sakamakon memory card daya bayar wanda sai daga baya ya tuna Ojo ya bashi tun a washe garin fitowarsu a jeji.         Oga Jush dake kallon Nanu a karo na farko yayi maga cike da izzarsa. “Nanu kake ko?”.        “Eh Sir!”.    “Ka tabbatar wannan memory ɗin daga hannun Ojo ya fito?”. “Kwarai da gaske. Dan kuwa a washe garin da suka fito a jeji kasancewar kasan shi bai samu wani rauni ba ya kirani ya sanarmin yayi videos sosai a wajen yaƙin, har naita mamaki shi taya ya iya yin hakan bayan suna ta ransu, shine yace shi mahaukaci ne zai shiga yaƙi, ai yana manne da Zak-Shadow dai. Dana fahimci da gaske yake sai nace mu haɗu to na amsa. Shine yace haɗuwa bazata yiwu ba na bari sai abubuwa sun lafa, idan kuma ya samu dama zai bada saƙo ta hannun budurwarsa. Ranar kuma muka haɗu da budurwar tasa ta bani saƙon da tambayata ko nasan inda yake, nace mata a'a gaskiya, shine ma dalilina na kiran oga Raven na shaida masa, dana duba saƙon kuma banga wani abu mai amfani ba sai jiya da dare dana zurfafa nazari na sake ɗakkosu na zazzage shine na samu wannan memory card ɗin”.         Cikin gamsuwa oga ke jinjina kai, kafin ya bada damar a saka memoryn kowa yaga mike ciki. Dandanan kuwa aka saita komai da magiji, sai ga komai daya faru a jeji tare da su Zak-Shadow dalla-dalla, duk da ba komai aka ɗauka ba, wani gurin ma bai ɗauku da ƙyau ba amma sun samu wurare masu muhimmanci da suka sakasu a farin ciki mara misali. Musamman inda Zak-Shadow ke dawowa jejin, da inda ake kashe mahaifin Umman Nimrah, da inda ake kashe Umman kanta, da inda bomb ya tada gidansu da yara da sojoji a ciki. Harda randa Zak-Shadow kema su Baban Nimrah tambayoyi a cikin tanti.      Tsabar farin ciki oga da kansa yayma Nanu ƙyauta ta musamman. A take kuma suka turama wani ƙwararren masani dake wata ƙasa yay editing videon ta yanda duk iya son gano gaskiyarka baka isa tantance abinda ke ciki ba haka yake ba. Ana dawo da videon suka kalla suka sake maidashi a sabon memory card suka kira Lt. Col. Garba suka danƙa masa, akan suna son a saka memoryn a kayan Ojo. Hakan kuwa akayi, Lt. Garba ya danƙama abokin Ojo memory card ya mayar a kayansa dake cikin barrak, sannan ya koma ya kitsama ogansa batun binciken kayan Ojo, oga kuma ya ankarar da membobin kwamitin bincike. Suko dama yanzu basa wasa da abu komai ƙanƙantarsa akan wannan case, kodan matsin lambar da suke samu daga gwamnati........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 65_ __________________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Link na grp 07077532253 https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1 link. N dm https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90R3y3tCP5z&_r=1 tiktok IMZEEDVENTURE Duniyar kayan kitchen ƴan yayi dake maida mata ƴan ƙwalisa a gidajensu. Shin kuna Neman in da zaku samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa? Kayan yara masu kyau unique na yan gayu? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi GATA tanayi🥳🥳. IMZEEDVENTURE wata sabuwar duniyar ƙyale-ƙyale ce da ƙayatarwa da mata sukafi buƙata musamman ƴan ƙwalisa da son gwangwaje kawunansu harma da iyalansu. Gaji ya kori ji, garzaya ki shiga wannan link ɗin namu dai domin ganema idanunki. https://wa.me/message/TFJVQFKRUBGBJ1. Koki tuntuɓemu ta wannan layin *_+234 707 753 2253_* Muna da account aTikTok@imzeed _venture. https://www.tiktok.com/@imzeedventures?_t=ZS-90A6JG1PvXe&_r=1 Karku bari ayi babu ku,😘😘😘😘😘 Nima Bilyn Abdull tuni na antaya🏃 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Yanda hankalin su Janar ya tashi a wannan gaɓar har ba'a magana. Dan gaba ɗaya komai ya juye a yanda basa fata kuma basa zato da tsammani. Ga takurawa da suke samu daga gidan gwamnatin. Dole a karo na farko kwamitin bincike ya aikama Imran takardar gayyata. Wannan takarda kuma ta riskeshi a dai-dai lokacin da yake fitowa zai zo gidan su Zak-Shadow domin dubashi da duba jikin Nimrah. Harda matarsa, sai Ruƙayya da bataje makaranta ba jiya ta kwana da zazzaɓin mura. Ai ko tanata murna zata ga sabuwar ƙawar da Dada yace ya kawo mata.      Komai Imran bai kawo ba game da wannan takarda ta gayyata, dan tunaninsa ma ai ana kan bincike ne game da su Dagger, yasan kuma za'a iya nemansu akan hakan. Suna shigowa gidan Zak-Shadow na fitowa daga sashen Mammah a zuciye, kallo ɗaya yay ma motar Imran ya ɗauke kai zai wuce. Imran ya san Zak-Shadow sani bana wasa ba, dan haka shima a kallo ɗaya da yay masa ya fahimci akwai matsala, ko gama kashe motar baiyi ba ya ɓalle murfin ya fito, cikin hanzari da ƙarfin jini irin na masu ɗammara ya sha gaban Zak-Shadow dake gab da shiga sashensa.        Kallon kallo suka zubama juna shi da Imran ɗin. Cikin fushi Zak-Shadow ya ce, “Bani hanya”.      “Mi kake shirin yi?”.   “Zan bigeka na wuce”. “Sai dai ka bugeni ɗin, amma in dai sai na matsa ka wuce bazaka shiga sashen nan ba. Sannan ina roƙonka ka ƙara haƙuri akan wanda kayi jiya. Nasan an maka ba dai-dai ba Haysam, amma ka dubi Uncle Nasiru ko dan nagartarsa ka ƙyale yarinyar nan da halinta.”          “Kasan mita sake min ne?”.     “Kayi haƙuri indai ba wani raunin ta sake jima wani ba. Haysam Please ina ƙara roƙonka kada ka biye mata ku zama ɗaya. Ka barta ita da kanta zatai dana sani wataran”.       “Bazan iya cigaba da zama da ita ba”.     “Dan girman ALLAH kar kace haka, dan dama abinda nafi tsoro kenan fiye da komai. Kai jigo ne ga wannan gida, abinda kayi zai zama mai sauƙi wajen koyi gasu Ja'afar. A wasu lokutan idan mata suka kuskure mana, ba rabuwa da su bane mafita horasu a cikin gidan ne mafita. Karka manta kaine kake min wannan huɗubar fa. Miyasa yanzu idanunka zai rufe? Ita dai bata isa sakaka sakin Nimrah ba, ta dinga kallon yarinyar kawai a matsayin matarka duk da ƙarancin shekarunta ya isheta hukunci mai zafi da zai fi kowanne. Amma dan ka rabu da ita ai tamaci nasara kenan”.         Kallonsa kawai Zak-Shadow yake yi, amma ya gagara sake cewa komai. Sai dai har yanzu zuciyar na'a maƙoshi, bai kuma gama tantance amsar kalaman Imran ɗin ba ko ƙin amsar. Dai-dai nan Ruƙayya da basu san da zuwanta ba ta kama hannunsa cike da farin ciki tana faɗin, “Dadana nazo”.     Idanu ya lumshe a hankali, sai kuma ya juyo yana kallonta, yanda yarinyar ke masa murmushi cike da farin ciki sai shima bai san ya mata murmushi kaɗan ba, sai kuma ya ɗauketa gaba ɗaya yana sauke ajiyar zuciya. Batare daya sake kallon Imran ba ya juya sashen Mammah.       Imran ya girgiza kai yana murmurshin shima. Dan ya tabbatar badan zuwan Ruƙayyan ba da wahala ya fasa shigar. Shima bayansu yabi, dama matarsa harta shige. Ba ƙaramin farin ciki Mammah tayi da ganin Zak-Shadow ya dawo ba, ta sauke ajiyar zuciya idonta akan Imran. Dan ta tabbatar badan zuwan nashi ba za'ayi mara daɗi ne yau a gidan. Murmurshi Imran yayi shima, cikin girmamawa yay mata nunin ta kwantar da hankalinta. Cikin jinjina kai tace, “ALLAH yay muku albarka”.      Da Amin ya amsa yana hararar su Ma'aruff da suka tuttura baki alamar basu so ba, sun so yau Dadansu yaci ƙaniyar Nabeeha ne wlhy, amma Yaya Imran ya hana. Gargaɗi ya shiga musu da ido, dan haka suka haɗe hannaye alamar ban haƙuri. Daga nan suka maida hankali akan Aunty Hafsat matarsa dan ƴan gidanta ne sosai. Hasalima shi Ja'afar ƙanwarta zai aura mai suna Shariffa. Ma'aruff kuma ƙanwar su Imran ce sunanta Lailah.     Dada kam tunda ya shigo bai kula kowa ba dama, kai tsaye inda Nimrah take ya nufa, itama hankalinta nakan Ruƙayya tunda suka shigo. Itama Ruƙayyan hankalinta akan Nimrah yake. Dada na ajiyeta kuwa ta koma kusa da ita ta zauna, cike da farin ciki ta ce, “Dada itace wannan?”.     Kansa ya ɗaga mata yana kallonsu su duka, dan daga gani hali zai zo ɗaya. Sai Ruƙayya ta rungume Nimrah, cikin raɗa ta ce, “Daga yau ke ƙawata ce inji Dada”.       Cike da farin ciki Nimrah tace. Eh. Ruƙayya ta ƙara rungumeta, sai kuma ta kalla ƙafarta ta ce, “Kinji ciwo ne?”.       “Ƴar daba ce a gidan nan ta yankani da wuƙa ni da Dada”.     Furucin Nimrah ya shiga kunnen kowa a ɗakin, hakan yasa Aunty Hafsat da Imran da Mammah da sai yanzu sukaji sunan da Nimrah ke kiran Nabeeha da shi duk suka kalleta. Su Bilal kam kwashewa sukai da dariya. Imran ya ce, “Nimrah ƴar daba kuma?”.        “Eh Yaya” tace da Imran kasancewar haka taji su Ja'afar na kiransa. Caraf Ruƙayya ta ce, “K ba yaya ba Dady”.     Kallonta Nimrah tayi itama, ta ce, “Ai su Uncle Ammar Yaya suke cewa”.        Mammah tai murmurshi a karo na farko, cikin katse taƙaddamar tasu ta ce, “Nimrah su Yayansu ne, ke kuma Daddy zakice keda ƙawarki Ruƙayya ko?”.       Kanta ta jinjinama Mammah tana murmushi, sai kuma ta kalla Ruƙayya ta ce, “Shike nan nace Daddy”.      Ruƙayya tai dariya itama. Sai shirmen nasu ya burge kowa, ciki harda Dada dake sauke ajiyar zuciya kawai. Ƙarshe ma ya fice a ɗakin, Imran ya tashi ya bishi..... (())★(())★(())★(())            Bayan sallar Azhar Imran ya amsa kiran kwamiti dan dama ƙarfe biyu suka buƙaci ganinsa. Bai gayama Zak-Shadow ba ya baro gidan akan zai je wani waje ya dawo. Shima Zak-Shadow bai tambayesa ina zai je ba ya wuce cikin gida dan akwai aikin da yake so ya kammala. Zuwa gobe da safe yake so ya zauna da Ojo.      ★★★ Sojoji huɗu ne a matsakaicin ɗakin binciken da aka shiga da Major Imran Abbas, duk da kuwa yasan ɗakin ba baƙonsa bane. Cikin nutsuwarsa ya kai zaune bayan ya miƙa gaisuwar girmamawa a garesu, sai dai a zuciyarsa ya fara wasi-wasi amma ya danne..       Brigadier General Abraham Yohana ne ya fara magana. “Major Imran Abbas ka sani wannan zamane na sirri. We expect full honesty from you”. Ya ɗan ja numfashi yana jujjuya biro a yatsansa, kafin ya ɗan matsa kusa da teburin da takardun ke kai. “Before we proceed Major,” ya sake faɗa cikin murya mai sanyi sai dai cike da iko, “this is an official military inquiry. Anything you say here will be part of the record. Are you willing to cooperate fully with this Board?”      Cikin girmamawa Imran ya ce, “Yes, sir! I’ll cooperate fully”.        Takardar gabansa ya ɗan duba, sai kuma ya ɗago yana sake kallon sauran jami’an da ke gefe, kafin ya dawo da idanunsa kan Imran. “Good. Let’s start simple. A ranar 17 ga watan jiya May a ina Zak-Shadow ya kwana?”.     Ba ƙaramin dukan zuciyar Imran wannan tambaya ta bazata tai ba. Sai kawai ya samu kansa da zubama Brigadier General idanu na sakanni. A zuciyarsa hasashen miya kawo wannan tambayar yake? Brigadier General ya sake katse masa tunani da maimaita tambayar. Ajiyar zuciya Imran ya sauke. Kai tsaye ya ce, “Sir yana sansani tare damu”.        “Washe gari 18 fa?”.    Gaba ɗaya Imran ji yake kamar zai rikice, amma ya ce “Itama haka....”      “Ka tabbatar?”.   Shiru yay ya kasa cewa komai. Brigadier General ya cigaba da faɗin, “To amma miyasa kuma anan bayanansa ya saɓa da abinda ka faɗa yanzu?”. Yay maganar yana yin nuni da projector daya bada umarnin a kunna.       Ana kunnawa kuwa videon ranar da Zak-Shadow ya koma jejin bayan an kai hari na biyu garin Marke da Gangare ya bayyana. Tun daga isowarsa sansani a mashin da shigarsa mota shi da karnukansa har isowarsu Gangare da bayanin da yayi cikin ɓacin rai kan abinda ya faru, inda yace baya nan cikin kwana biyu kacal sun bari an musu irin wannan illar ya maimaita kansa yafi sau huɗu dan a sake tabbatar da ƙaryata abinda Imran ɗin ya faɗa ma.         “Har yanzu kana akan bakan ka na cewar yana nan ɗin komai ya fara faruwa?”. Lt. Col. Peter Okon ya faɗa yana tsatstsare Imran da idanu.      Shiru Imran yayi zuciyarsa na wani irin dokawa, zuwa yanzu ya fara hasaso al'amari mai girma, dan kuwa ba rami miya kawo rami. Babu dalili miya kawo ɗaukar video sirri akan su a lokacin da suke kan aiki. Imran nada haƙuri da sanyin hali, amma akan Zak-Shadow bashi da haƙuri da kawaici. Dan haka cikin tsaurara harshe a karo na farko ya ce, “Sir! Akwai makirci a wannan al'amarin kwarai da gaske. Eh naji kai tsaye zance Haysam baya cikin sansani tun daga ranar farko da aka kaima sojojinmu hari. Domin kuwa yazo ziyartar gida akan abinda ya shafesa, hakan kuma bawani abu bane a hukunce mun sani, musamman da idan mukai dubi da dalili mai ƙarfi ne ke iya saka Haysam motsawa daga sansani, sai kuma ya tabbatar babu wata matsa sannan baya iya wuce kwana biyu duk tsanani”.        “Eh muma bamuce laifi yayi ba na zuwa gidan, sai dai miyasa ba'a kai harin ba sai bayan ya tafi? Kuma yanayin harin yay dai-dai da abinda ya faru shekaru uku da suka wuce.”     Aka sake kunna wani video da aka ɗauka daga rikicin shekara uku da ta wuce, lokacin da Special Recon Unit ta jagoranci farmaki a yankin Gulmadu. Hoton ya nuna Zak-Shadow yana magana da sojoji, sai kuma a nan gaba aka ga wuta ta tashi, kamar umarnin harin daga gare shi ne.       Wani kalar rinewa idanun Imran sukayi, sai dai kafin yay magana Colonel Galadima ya ce,........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 66_ __________________ https://chat.whatsapp.com/J92XqvWDRch1EJPdGDBa41?mode=wwt https://vm.tiktok.com/ZSHWHk4ULWbMN-geqJz/ This post is shared via TikTok Lite. Download TikTok Lite to enjoy more posts: https://www.tiktok.com/tiktoklite https://chat.whatsapp.com/KfkKd9vD8MrAst8i8CQDsj?mode=wwt Assalamu alaikum, Mutanen arziki Ina musu capacity😍🥰 kuna Neman Inda zaku Samu ingantattun Kaya masu kyau da quality sosai 💝 Kamar Kayan Yara Zannuwan Gado Kayan kitchen Shoes and bags Jewellery Laces, atamfa,shadda Dadai sauransu. To nesa tazo kusa, Maza Danna wannan link din domin Samun Kaya masu inganci da ƙayatarwa da idan kika saka ko ina kika shiga sai an kalleki an ƙara kallo. Ko ku nememu ta wannan number 08165751018 ❤️❤️❤️😘 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Yanda hankalin su Janar ya tashi a wannan gaɓar har ba'a magana. Dan gaba ɗaya komai ya juye a yanda basa fata kuma basa zato da tsammani. Ga takurawa da suke samu daga gidan gwamnatin. Dole a karo na farko kwamitin bincike ya aikama Imran takardar gayyata. Wannan takarda kuma ta riskeshi a dai-dai lokacin da yake fitowa zai zo gidan su Zak-Shadow domin dubashi da duba jikin Nimrah. Harda matarsa, sai Ruƙayya da bataje makaranta ba jiya ta kwana da zazzaɓin mura. Ai ko tanata murna zata ga sabuwar ƙawar da Dada yace ya kawo mata.      Komai Imran bai kawo ba game da wannan takarda ta gayyata, dan tunaninsa ma ai ana kan bincike ne game da su Dagger, yasan kuma za'a iya nemansu akan hakan. Suna shigowa gidan Zak-Shadow na fitowa daga sashen Mammah a zuciye, kallo ɗaya yay ma motar Imran ya ɗauke kai zai wuce. Imran ya san Zak-Shadow sani bana wasa ba, dan haka shima a kallo ɗaya da yay masa ya fahimci akwai matsala, ko gama kashe motar baiyi ba ya ɓalle murfin ya fito, cikin hanzari da ƙarfin jini irin na masu ɗammara ya sha gaban Zak-Shadow dake gab da shiga sashensa.        Kallon kallo suka zubama juna shi da Imran ɗin. Cikin fushi Zak-Shadow ya ce, “Bani hanya”.      “Mi kake shirin yi?”.   “Zan bigeka na wuce”. “Sai dai ka bugeni ɗin, amma in dai sai na matsa ka wuce bazaka shiga sashen nan ba. Sannan ina roƙonka ka ƙara haƙuri akan wanda kayi jiya. Nasan an maka ba dai-dai ba Haysam, amma ka dubi Uncle Nasiru ko dan nagartarsa ka ƙyale yarinyar nan da halinta.”          “Kasan mita sake min ne?”.     “Kayi haƙuri indai ba wani raunin ta sake jima wani ba. Haysam Please ina ƙara roƙonka kada ka biye mata ku zama ɗaya. Ka barta ita da kanta zatai dana sani wataran”.       “Bazan iya cigaba da zama da ita ba”.     “Dan girman ALLAH kar kace haka, dan dama abinda nafi tsoro kenan fiye da komai. Kai jigo ne ga wannan gida, abinda kayi zai zama mai sauƙi wajen koyi gasu Ja'afar. A wasu lokutan idan mata suka kuskure mana, ba rabuwa da su bane mafita horasu a cikin gidan ne mafita. Karka manta kaine kake min wannan huɗubar fa. Miyasa yanzu idanunka zai rufe? Ita dai bata isa sakaka sakin Nimrah ba, ta dinga kallon yarinyar kawai a matsayin matarka duk da ƙarancin shekarunta ya isheta hukunci mai zafi da zai fi kowanne. Amma dan ka rabu da ita ai tamaci nasara kenan”.         Kallonsa kawai Zak-Shadow yake yi, amma ya gagara sake cewa komai. Sai dai har yanzu zuciyar na'a maƙoshi, bai kuma gama tantance amsar kalaman Imran ɗin ba ko ƙin amsar. Dai-dai nan Ruƙayya da basu san da zuwanta ba ta kama hannunsa cike da farin ciki tana faɗin, “Dadana nazo”.     Idanu ya lumshe a hankali, sai kuma ya juyo yana kallonta, yanda yarinyar ke masa murmushi cike da farin ciki sai shima bai san ya mata murmushi kaɗan ba, sai kuma ya ɗauketa gaba ɗaya yana sauke ajiyar zuciya. Batare daya sake kallon Imran ba ya juya sashen Mammah.       Imran ya girgiza kai yana murmurshin shima. Dan ya tabbatar badan zuwan Ruƙayyan ba da wahala ya fasa shigar. Shima bayansu yabi, dama matarsa harta shige. Ba ƙaramin farin ciki Mammah tayi da ganin Zak-Shadow ya dawo ba, ta sauke ajiyar zuciya idonta akan Imran. Dan ta tabbatar badan zuwan nashi ba za'ayi mara daɗi ne yau a gidan. Murmurshi Imran yayi shima, cikin girmamawa yay mata nunin ta kwantar da hankalinta. Cikin jinjina kai tace, “ALLAH yay muku albarka”.      Da Amin ya amsa yana hararar su Ma'aruff da suka tuttura baki alamar basu so ba, sun so yau Dadansu yaci ƙaniyar Nabeeha ne wlhy, amma Yaya Imran ya hana. Gargaɗi ya shiga musu da ido, dan haka suka haɗe hannaye alamar ban haƙuri. Daga nan suka maida hankali akan Aunty Hafsat matarsa dan ƴan gidanta ne sosai. Hasalima shi Ja'afar ƙanwarta zai aura mai suna Shariffa. Ma'aruff kuma ƙanwar su Imran ce sunanta Lailah.     Dada kam tunda ya shigo bai kula kowa ba dama, kai tsaye inda Nimrah take ya nufa, itama hankalinta nakan Ruƙayya tunda suka shigo. Itama Ruƙayyan hankalinta akan Nimrah yake. Dada na ajiyeta kuwa ta koma kusa da ita ta zauna, cike da farin ciki ta ce, “Dada itace wannan?”.     Kansa ya ɗaga mata yana kallonsu su duka, dan daga gani hali zai zo ɗaya. Sai Ruƙayya ta rungume Nimrah, cikin raɗa ta ce, “Daga yau ke ƙawata ce inji Dada”.       Cike da farin ciki Nimrah tace. Eh. Ruƙayya ta ƙara rungumeta, sai kuma ta kalla ƙafarta ta ce, “Kinji ciwo ne?”.       “Ƴar daba ce a gidan nan ta yankani da wuƙa ni da Dada”.     Furucin Nimrah ya shiga kunnen kowa a ɗakin, hakan yasa Aunty Hafsat da Imran da Mammah da sai yanzu sukaji sunan da Nimrah ke kiran Nabeeha da shi duk suka kalleta. Su Bilal kam kwashewa sukai da dariya. Imran ya ce, “Nimrah ƴar daba kuma?”.        “Eh Yaya” tace da Imran kasancewar haka taji su Ja'afar na kiransa. Caraf Ruƙayya ta ce, “K ba yaya ba Dady”.     Kallonta Nimrah tayi itama, ta ce, “Ai su Uncle Ammar Yaya suke cewa”.        Mammah tai murmurshi a karo na farko, cikin katse taƙaddamar tasu ta ce, “Nimrah su Yayansu ne, ke kuma Daddy zakice keda ƙawarki Ruƙayya ko?”.       Kanta ta jinjinama Mammah tana murmushi, sai kuma ta kalla Ruƙayya ta ce, “Shike nan nace Daddy”.      Ruƙayya tai dariya itama. Sai shirmen nasu ya burge kowa, ciki harda Dada dake sauke ajiyar zuciya kawai. Ƙarshe ma ya fice a ɗakin, Imran ya tashi ya bishi..... (())★(())★(())★(())            Bayan sallar Azhar Imran ya amsa kiran kwamiti dan dama ƙarfe biyu suka buƙaci ganinsa. Bai gayama Zak-Shadow ba ya baro gidan akan zai je wani waje ya dawo. Shima Zak-Shadow bai tambayesa ina zai je ba ya wuce cikin gida dan akwai aikin da yake so ya kammala. Zuwa gobe da safe yake so ya zauna da Ojo.      ★★★ Sojoji huɗu ne a matsakaicin ɗakin binciken da aka shiga da Major Imran Abbas, duk da kuwa yasan ɗakin ba baƙonsa bane. Cikin nutsuwarsa ya kai zaune bayan ya miƙa gaisuwar girmamawa a garesu, sai dai a zuciyarsa ya fara wasi-wasi amma ya danne..       Brigadier General Abraham Yohana ne ya fara magana. “Major Imran Abbas ka sani wannan zamane na sirri. We expect full honesty from you”. Ya ɗan ja numfashi yana jujjuya biro a yatsansa, kafin ya ɗan matsa kusa da teburin da takardun ke kai. “Before we proceed Major,” ya sake faɗa cikin murya mai sanyi sai dai cike da iko, “this is an official military inquiry. Anything you say here will be part of the record. Are you willing to cooperate fully with this Board?”      Cikin girmamawa Imran ya ce, “Yes, sir! I’ll cooperate fully”.        Takardar gabansa ya ɗan duba, sai kuma ya ɗago yana sake kallon sauran jami’an da ke gefe, kafin ya dawo da idanunsa kan Imran. “Good. Let’s start simple. A ranar 17 ga watan jiya May a ina Zak-Shadow ya kwana?”.     Ba ƙaramin dukan zuciyar Imran wannan tambaya ta bazata tai ba. Sai kawai ya samu kansa da zubama Brigadier General idanu na sakanni. A zuciyarsa hasashen miya kawo wannan tambayar yake? Brigadier General ya sake katse masa tunani da maimaita tambayar. Ajiyar zuciya Imran ya sauke. Kai tsaye ya ce, “Sir yana sansani tare damu”.        “Washe gari 18 fa?”.    Gaba ɗaya Imran ji yake kamar zai rikice, amma ya ce “Itama haka....”      “Ka tabbatar?”.   Shiru yay ya kasa cewa komai. Brigadier General ya cigaba da faɗin, “To amma miyasa kuma anan bayanansa ya saɓa da abinda ka faɗa yanzu?”. Yay maganar yana yin nuni da projector daya bada umarnin a kunna.       Ana kunnawa kuwa videon ranar da Zak-Shadow ya koma jejin bayan an kai hari na biyu garin Marke da Gangare ya bayyana. Tun daga isowarsa sansani a mashin da shigarsa mota shi da karnukansa har isowarsu Gangare da bayanin da yayi cikin ɓacin rai kan abinda ya faru, inda yace baya nan cikin kwana biyu kacal sun bari an musu irin wannan illar ya maimaita kansa yafi sau huɗu dan a sake tabbatar da ƙaryata abinda Imran ɗin ya faɗa ma.         “Har yanzu kana akan bakan ka na cewar yana nan ɗin komai ya fara faruwa?”. Lt. Col. Peter Okon ya faɗa yana tsatstsare Imran da idanu.      Shiru Imran yayi zuciyarsa na wani irin dokawa, zuwa yanzu ya fara hasaso al'amari mai girma, dan kuwa ba rami miya kawo rami. Babu dalili miya kawo ɗaukar video sirri akan su a lokacin da suke kan aiki. Imran nada haƙuri da sanyin hali, amma akan Zak-Shadow bashi da haƙuri da kawaici. Dan haka cikin tsaurara harshe a karo na farko ya ce, “Sir! Akwai makirci a wannan al'amarin kwarai da gaske. Eh naji kai tsaye zance Haysam baya cikin sansani tun daga ranar farko da aka kaima sojojinmu hari. Domin kuwa yazo ziyartar gida akan abinda ya shafesa, hakan kuma bawani abu bane a hukunce mun sani, musamman da idan mukai dubi da dalili mai ƙarfi ne ke iya saka Haysam motsawa daga sansani, sai kuma ya tabbatar babu wata matsa sannan baya iya wuce kwana biyu duk tsanani”.        “Eh muma bamuce laifi yayi ba na zuwa gidan, sai dai miyasa ba'a kai harin ba sai bayan ya tafi? Kuma yanayin harin yay dai-dai da abinda ya faru shekaru uku da suka wuce.”     Aka sake kunna wani video da aka ɗauka daga rikicin shekara uku da ta wuce, lokacin da Special Recon Unit ta jagoranci farmaki a yankin Gulmadu. Hoton ya nuna Zak-Shadow yana magana da sojoji, sai kuma a nan gaba aka ga wuta ta tashi, kamar umarnin harin daga gare shi ne.       Wani kalar rinewa idanun Imran sukayi, sai dai kafin yay magana Colonel Galadima ya ce,........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 67_ __________________ https://chat.whatsapp.com/DMVSa4G3a9sDd8Jjgm0mzs?mode=ems_copy_t Kin Dade kina Neman group din dazaki tallata kayanki kyauta Baki samuba to ki hanzarta shiga free advert group na EASHAS BITES AND BEAUTY domin tallata Kayanki kuyi saving number dinta domin samun shiga group dinnan akwai members Sama da 500+ aciki💃💃💃💃👇👇👇👇 wa.me/ +2348064705686 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........10:30pm    Aunty Hafsat ta kira wayar Biebah tana tambayarta ko Imran ya dawo nan gidan. Biebah ta ce, “A'a gaskiya Aunty, ni dai banga Yaya Imran ba, dan sanda na dawo islamiyya ma Dada kawai na tarar a compound zaune. Kuma Mammah tace baku jima da wucewa ba lokacin.”          “Har yanzu Dada na gidan?”.      “Eh yana nan, gashi ma tare da Mammah na bashi?”.         Kafin ma Aunty Hafsat tayi magana Dada yay ma Biebah alamar ta bashi wayar. Cikin girmamawa ta kawo masa. Sallamar da yayi ta saka Aunty Hafsat saurin gaisheshi. Ya amsa a taƙaice da tambayarta “Har yanzu bai dawo ba?”.       “Eh wlhy Yaya har yanzu, ni tsoro ma ya fara kamani. Dan sanda muke fitowa gida zamu taho nan gidan dama wasu mutane kamar jami'anku sunzo sun bashi wata takarda. Sai dai ban san ta micece ba amma naji yana ce musu zuwa 2 ɗin zai je. Daga haka ya shigo mota kuma bai sake min zancen komai ba”.            Cike da mamaki Zak-Shadow ya ce, “Takarda? kuma jami'an mu?”.      “Eh, dan ɗaya akwai wandon sojoji a jikinsa”.      “Okay ina zuwa to. Kada ki damu babu abinda zai faru”. Yanke kiran yayi batare da ya jira amsarta ba. Mammah da ke kallonsa ta ce, “Lafiya kuwa?”.          “Babu komai Mammah ina zuwa”.   Yay maganar yana miƙewa ya fita. Duk da kallo suka bishi har su Bilal. Dan suna zaune ne dama ana hira.        A waje Zak-Shadow yay ɗan tsai cikin nazari. Zancen Col Faro ne ya shiga dawo masa na jiya. Dan haka ya zaro waya a aljihu yana jinjina kai da cije lips yay kiran wata number. Ana ɗagawa daga can aka gaishe shi, a taƙaice ya amsa. Kafin ya ɗora da gaɗin, “Kaga Imran ya shigo Headquarter yau?”.          “Eh tabbas Sir! Na fito salla ni da Faruk naga motarsa ta shigo, sai dai banga fitarsa ba dan na koma office ina wani aiki”.       “Bincika min ƙarfe nawa ya fito, sannan office ya shiga ko mi?”.   “Okay sir!”. Wayar ya katse ya gyara tsaiwa, ko mintuna huɗu ba'ai ba wancan ya sake kiransa. Koda ya ɗaga sai ya fara masa bayanin daya sakashi yin cak. “Sir! Na duba har yanzu motarsa na nan. Yanzu kuma nake jin ƙus-ƙus ɗin wai zama akai da shi na musamman, a yanzu haka ma yana a ɗakin bincike”.          Shiru Zak-Shadow bai ce komai ba tsahon sakanni, sai kuma ya katse kiran yana mai furzar da huci. Yanzu kam ya fahimci komai. Dan haka yay kiran Col Faro, dan ya tabbatar a wajensa ne kawai zai ji abinda yake so. Sai da ta kusan tsinkewa ya ɗaga. Baima jira ko gaisuwa sunyi ba kai tsaye ya ce, “Imran na tare da ku?”.      Sai da Col Faro yay ɗan jim sannan cikin tsantseni ya ce, “Kada ka tada hankalinka. Na tabbatar zuwa safiya zasu barshi ya fita”.          “Bazai yiwu ba, gani nan zuwa”.      “Kayi haƙuri dan ALLAH kar kazo, dan zuwanka haɗari ne babba ga Major Imran. Ka bari muga abinda safiya zatayi. Ni kaina yanzu ina ƙoƙarin son sanin mi suka tattauna da shi ne dama zan kiraka na gaya maka. Amma zuwanka yanzu zai iya sake ɓata komai”.       Da wani irin zafin rai Zak-Shadow ya kaima motar da yake jingine a jiki naushi, batare da yace komai ba ya yanke kiran. Ya jima zuciyarsa na hanƙoro a cikin ƙirji, kafin daga ƙarshe ya danne komai ya koma wajensu Mammah. Wayar Biebah ya amsa yay kiran Aunty Hafsat. Ya ce ta kwantar da hankalinta akwai aikin da Imran keyi amma zuwa safiya in sha ALLAHU zai dawo gida. Bai jira amsarta ba kuma ya yanke. Koda Mammah ta sake masa tambaya amsar daya sake bata kenan itama. Daga nan ya musu sallama ya wuce. Tun daga nan ta sake fahimtar akwai matsala, sai dai tasan bazai faɗa ba...       Sam Zak-Shadow baiyi wani barci ba a wannan daren. Ya kwana ne akan ƙafafunsa yana salla da kuma zaman lissafe-lissafen abubuwa a taƙaice. Dan ya gama auna komai ya kuma fahimta gwargwadon hangensa. Ya auna hanyoyin kuɓuta da tsaida gaskiya yaga duk wadda yabi zai iya saka Imran a haɗari, sai kawai yay murmushi yana mai tabbatar ma kansa amsar hanyar ƙarshe kawai. Duk da ya san zai saka Mammah da ƴan uwansa a tashin hankali. Amma zai samu abinda yake so a ƙarshe koda kuwa sunci nasara a kansa shi Imran zai ƙarasa abinda yake fata kuma shi zai ci nasarar sannan zai kuɓuta. Sai kawai ya sake yarda zai sadaukar, dan ransa fansa ne ga Imran balle ma wannan harin kai tsaye nashi ne. Da wannan hukuncin ya kwana a ransa, dan haka duk wani abinsa mai muhimmanci ya killacesa waje guda a ɗakin ya kuma ajiye wasu domin Imran........ <<%>><<%>><<%>>        WASHE GARI.... 7/6/2013.            8:30am      Kamar yanda Zak-Shadow yay tsammani a wannan safiya ya samu baƙuncin ɗan aike daga kwamiti. Ya jima yana kallon takardar gayyatar mai tambarin Defence Headquarters a jiki. Sai kuma ya ɗan saki murmurshin ƙasaita. Gefe ya ajiyeta kawai ya cigaba da shan coffee ɗinsa, su Ja'afar dake kallon takardar cikin son sanin mike a ciki dan suna tare da shi ne a tsakar gida tunda suka dawo daga motsa jiki da suka bishi bayan sallar asuba. Basu koma ciki ba anan Biebah ta kawo musu coffee shine suke zaman sha har aka kawo takardar.       Ƙasa-ƙasa Ma'aruff ya ce, “Dada badai aiki zaka koma ba tun yanzu? Wlhy bamu gaji da ganinka ba, dan ALLAH ka yi kamar wata uku”.           Cikin marairaicewa Ja'afar ma ya ce, “Eh dan ALLAH Dada. Kaga ma ko warkewa fa baka gama yi ba yankan hannunka.”     Rasama mizai ce musu yayi, suko sai sake shagwaɓe masa suke kamar wasu yara ƙanana. Sai kawai ya ce, “Tom naji, ku tashi kuyi shirin kasuwa nima zan fita ne”.      Badan sun so hakan ba suka amsa da to, dan su fa idan yana gida ko fita kasuwar basa son yi, tunda duk shagunan akwai yara, su matsayin oganni ne ko sunje zaman office ne. Sai da ya tabbatar sun shige ciki sannan ya ɗauki takardar ya duba.          (Directive from the Board of Inquiry. Defence Headquarters, Abuja. Ana gayyatarka domin bayyana a gaban kwamitin bincike a yau 1:pm. Subject: Preliminary Inquiry concerning recent allegations on classified operations.        Brig. Gen. Abraham Yohana, Secretary Board of Inquiry).     Ƙasaitaccen murmushi ya sake saki mai cike da ma'anoni, sai kuma ya maida takardar ya ninke ya ajiye. Daga ƙarshe ma ya miƙe ya nufi sashen Mammah. Kusan awarsa ɗaya a sashen Mammah ya koma nashi sashen, tun faruwar rikicin Nimrah bai kuma saka Nabeeha a idonsa ba, bai kuma nemeta ba sai dai yana ganin gilmawar ƙanenta da Mamansu da bai san mitake a gidan ba har yanzu. Shi kuma bashi da lokacin tambaya ko neman ba'asi, idan taso ta dawo gidan ma da zama matsalarsu ce wannan. Yana buɗe ƙofar ɗakin nasa akan Nabeeha ya fara sauke idanunsa, tana zaune a kujerar dake kallon kofar. Kwanaki kaɗan har ta rame, ga idanu a kumbure jajur alamar cikin kuka take har yanzu. Ɗauke idanunsa yay tamkar bai ganta ba, sai ma ya hau ƙoƙarin cire kayan jikinsa hankali kwance. Ai ko ta sake ƙuluwa, zuciyarta na ƙuna da rawar murya ta ce, “Saboda kayi sabon aure kake wulaƙanta ni?”.        Babu alamar ya jita ma, dan hanyar bayi ya nufa, da sauri ta tashi tasha gabansa, ya tsaya cak yana kallonta da birkitattun idanunsa, kasa jure kallonsa tayi ita kam, dole ta risinar da idannunta tana ƙara ƙarfafa kanta ta ce, “Haysam idan kana son zama dani ka ɗauki yarinyar can ka maidata inda ka ɗakkota, ka warware tatsuniyar gizo-gizon daka ƙulla kuma”.         Ƙirjinta dake sama da ƙasa alamar da ƙyar take tattaro maganar tana gaya masa ya zubama ido, yanda takai ƙarshen zancen nata da rumtse ido sai tama bashi dariya. Amma sai ya dake abinsa kai tsaye ya ce, “To Mama Nabeeha idan naƙi fa?”.     Kamar zatai kuka dan takaicin Mama daya kirata ta ce, “Zan koyi abinda bazai mana daɗi ba ni da kai”.          Maimakon amsata zagayeta kawai yay ya wuce bayi a binsa. Wayyo jitai kamar zata haɗiyi zuciya ta mutu. Zuciyarta na bata shawarar ta jirashi wata na ingizata ta tafi kawai. Harta wuce fuuu zuwa kofa sai kuma ya dawo jikin ƙofar bayin, cikin fashewa da kuka da masifa ta ce, “Wlhy idan har baka yi abinda nake so ba nabarka har abada, mugu kawai azzalumi ALLAH ya isa ban yafe ba. Ga gidan nan na bar muku macuta”.      Daga haka ta fice fuuu. Duk abinda ya faɗa yaji, amma yay kamar bai jin ba ya cigaba da wankansa. Itako tana fita ɗakinta ta wuce, kai tsaye tace ma Momyn, “Momy muje kawai”.       Murmurshi Momy ta saki a karo na farko na cin nasara, kafin ta ce, “Yaƙi yarda kenan?”..           Bata tanka zancen ba ta ce, “Momy ni dai muje”.      Ba ƙaramin tashi hankalin Ismat yayi ba jin gidan zasu bari, ita kam ai ita za'a shukama tsiyar sakata yin nisa da masoyinta Ja'afar. Sai kawai ta sanya musu kuka da magiyar ita dai kada su tafi. Abi komai a hankali. Ai wani mari mai lasisi Momy ta bata, daga haka bata sake iya magana ba suka tattara kayansu da dama sun haɗa tun jiya Hinde ta dinga fita da su wajen mota. Tana son zuwa ta sanar ma Mammah tana tsoro, dole ta haƙura a gaban idonta Momyn Nabeeha taja mota ita da Nabeeha a gaba su Amima a baya suka wuce. Sai a lokacin ta falla zuwa sashen Mammah ta sanar mata.     Mammah zata tada hankalinta ƴaƴanta suka zagayeta da daɗin baki. Koda Zak-Shadow ya dawo sashen yin breakfast da tai masa maganar shima cikin rashin damuwa ya ce, “Mammah ba ita ta zaɓi haka ba. Ki saka musu ido kiga iya gudun ruwansu kawai yafi sauƙi. Yanda ta tafi da ƙafarta da ƙafartata zata dawo”.     Ba yanda zatai dole tai shiru.........✍🏼      Mu gayama ƴar Daba gaskiya ko muyi shiru duniya ta gaya mata 😂🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️?. _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 68_ __________________ https://chat.whatsapp.com/J92XqvWDRch1EJPdGDBa41?mode=wwt https://vm.tiktok.com/ZSHWHk4ULWbMN-geqJz/ This post is shared via TikTok Lite. Download TikTok Lite to enjoy more posts: https://www.tiktok.com/tiktoklite https://chat.whatsapp.com/KfkKd9vD8MrAst8i8CQDsj?mode=wwt Assalamu alaikum, Mutanen arziki Ina musu capacity😍🥰 kuna Neman Inda zaku Samu ingantattun Kaya masu kyau da quality sosai 💝 Kamar Kayan Yara Zannuwan Gado Kayan kitchen Shoes and bags Jewellery Laces, atamfa,shadda Dadai sauransu. To nesa tazo kusa, Maza Danna wannan link din domin Samun Kaya masu inganci da ƙayatarwa da idan kika saka ko ina kika shiga sai an kalleki an ƙara kallo. Ko ku nememu ta wannan number 08165751018 ❤️❤️❤️😘 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .......1:pm.        Duk taurin kan Zak-Shadow baya raina na gaba da shi a wajen aiki ko a shekaru na girma. Mutum ne mai tsantseni da taka tsantsan na kiyaye duk abinda baya so a masa bai yarda yayma wani ba. Zamu iya cewa kusan wannan ɗabi'ar tasa na ƙara masa nagarta da martaba a idon manyansu. Duk da suna sama da shi suma basu yarda su wulaƙanta shi ba. Dan yana musu kwarjini da cikar kamala. Kai ko haushin Zak-Shadow kake ji sai dai ka cika bakin zaginsa a bayan idonsa da ɗaukar alwashi, amma da kun haɗu ido da ido sai kaji gaba ɗaya zafin kan naka ya gudu ka koma jin shakkarsa.         Kamar yadda aka tsara, ƙarfe ɗaya da rabi na rana motarsa ta shigo Defence Headquarters cikin nutsuwa. Bayan an tabbatar da shaidarsa, aka raka shi zuwa babban zauren taron kwamitin binciken. A cikin ɗakin, akwai manyan jami’an soja shida da suka haɗa da, Brig. Gen. Abraham Yohana (Shugaban kwamiti). Col. Osama Galadima (Memba). Lt. Col. Peter Okon (Memba). Major Lami Barde (Recorder). Col. Haydar (Memba). Sai jami'an gwamnati biyu masu sa ido dake daga can gefe.       Yayi gaisuwa irinta mutuntawa kamar yanda doka ta tanada duk da kuwa akwai wanda yafi rank a wajen da wanda suke dai-dai.         “Good morning, sirs.”      A cikinsu babu wanda bai ji wani iri a zuciyarsa ba, dan muryar Zak-Shadow irin dakakkiyar muryar nan ce ta isassun maza dake fita kai tsaye kuma a dake. Sannan amonta na kama zuciya koda yana magana ne a ƙaramin sauti.       “Morning, Lt. Col. Haysam. Please, have your seat”.       Brig. Gen. Abraham ya faɗa cikin dakewar dole dan kwarjinin Zak-Shadow gaba ɗaya ya cika masa ido kamar sauran, ga fuska ya tamke babu alamar wasa kamar yanda kowa ya sanshi da ƙarancin fara'a da rashin yawan magana.       Cike da nutsuwa da ƙasaitarsa ya kai zaune inda aka nuna masa, ɗakin ya ɗan yi shiru kafin Brigadier ɗin ya maida hankalinsa ga karanta abinda ke a takardar gabansa.        Lt. Col. Haysam, mun gayyace ka nan ne domin taimaka ma wannan kwamiti da wasu bayanai kan wasu ayyukan da kai ne ka jagoranta kwanakin da suka gabata. Muna sa ran cikakken haɗin kai daga gare ka”.       Lumshe idanu ya ɗanyi kaɗan, sannan ya sake buɗesu, babu alamar wani fargaba ko damuwa a fuskar tasa ya ce, “Yes, sir. I’m ready to answer your questions.”         Kai Brig. Gen. Abraham ya ɗan jinjina yana juya takardar gabansa, sannan ya cigaba da da faɗin, “Kafin mu ci gaba, Lt. Col, muna son tabbatarwa ko kana da masaniya game da ɓacewar wani Lieutenant mai suna Ojo, wanda ya kasance cikin rundunar da ka jagoranta a aikin karshen nan daya gabata?”.         Shiru na ɗan lokaci kamar bashi da niyyar bada amsar, sai kuma yay wani ɗan malalacin murmurshi, “Yes sir! Na sani, sannan ba ɓata yay ba yana hannuna, kuma yarona ne na kusa da kowa ya sani. Wasu dalilai ne kuma yasa na riƙesa, nasan kuma yin hakan ba laifi bane a ɓangaren bincike”.       Hall ɗin ya yi shiru tamkar babu mai rai a ciki, kowanne da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa game da amsar daya fara badawa kai tsaye da babu gargada ko shakka, sun san wanene Haysam, bashi da tsoro, bai yarda ya ajiye gaskiya ba koda zata ƙwaɓe. Suko manyan jami’an da ke zaune a teburin gefe masu saka ido a madadin gwamnati kowannensu cikin matsanancin mamaki suke kallon Zak-Shadow ɗin, dan sun fahimci ya ma wuce yanda ake labarinsa ashe. Ji yanda yake bada amsa kai tsaye fuskarsa a haɗe, babu wani shakka ko tankaɗe abinda zai faɗa ɗin. Ba ruwansa da yay musu daɗi ko kar yay musu.         Brigadier General Abraham Yohana ne ya katse shirun da ɗan murmushi. Cikin son gyara tambayarsa ya ce, “Hakane, sai dai a wannan yanayin kasancewar Ojo a hannunka ya canja labarin daga bincike zuwa son kare kanka a dalilin wata gaskiya da akace ka fahimci shi Ojo ɗin zai fitar data shafeka. Shiyyasa report ya nuna inda da gaske akan tuhuma kake son kama Ojo office zaka kawo shi ba wani waje daban ba da baida alaƙa da wajen aiki. Domin kuwa an samu wasu videos a kayan Ojo da bincike ke ganin saboda shi ne ka killaceshi”.       Zak-Shadow yay wani sakaran murmurshi a karo na biyu yana ɗan kauda kansa gefe, sai kuma ya maida dubansa ga Brig. G. “Sir! I'm sorry, mizai hana muje kai tsaye ga abinda kuke buƙatar ji kawai. A lokuta da dama ana min kallon bahagon mutum, sai dai a zahiri mutane ne basa fahimtata, a komai nafi son abu kai tsaye, maida gaba baya a zance nakan kallesa kamar aikin mata ne. Dan ALLAH cikin girmamawa kawai muyi abinda ya dace”.          Cikin taushi yayi magana, amma ga mai tsatsar zuciya zasu kalli kalamansa a masu zafi. Kamar jami'an gwamnatin dake wajen da wasu a membobin zaman. Sai dai shi Brigadier General yasan Haysam sani na amana da gaskiya, shiyyasa ko kaɗan bai ɗauki kalaman nasa a komai ba face na mazan fama. Sai kawai ya murmusa idanunsa akan Zak-Shadow ɗin.         Shi ko Lt. Col Peter Okon cikin jin zafin kalaman Zak-Shadow ɗin ya ce, “Lt. Col Haysam Abdul-rasheed Shehu. An samu wasu video clips daga ayyukanka da suka gabata, musamman wanda ya faru a yankin Bankaura, wannan video clips kuma a cikin kayan Ojo amintacen yaronka aka same su kamar yanda kaji tun farko. Gasu za'a kunna maka ka gani”.       Ko kallon inda yake Zak-Shadow baiyi ba, bai kuma amsa masa ba. Koda aka kunna tvn ma yaja wasu sakanni kafin ya kai idonsa kansa. Zuciyar sa ta ɗan buga musamman a wajen harbin Umman Nimrah da mahaifinta, amma bai nuna ba. Sai dai har videon ya kai ƙarshe bai ɗauke idonsa akan tvn ba, sai da ma Brig. G. Ya ɗan buga table ɗin sannan.       Su duka ya kalla cikin idanu ɗaya bayan ɗaya, sai kuma ya ɗan yi murmurshin da su kuma ya daki zukatansu. Kai tsaye ya ce cikin murya mai ƙarfi, “Sir! Ai ban san a aikin namu harda masu ɗaukar aikin videos ba ma sai yanzu, ba zan tsaya ina kare kaina da magana kawai ba, sannan ban damu da sanin dalilin daya saka a ɗaukemu videos ɗin ba. Sai dai ko bayan na ɓata kamar yanda masu ɗaukar ko ogannin da suka saka a ɗauka ɗin ke buƙata ina so a bincika comm log ɗin mu da footage ɗin asali dan wannan edited video ne. Sannan akan Ojo ban yarda da fallasa abokin aiki ba tare da hujja ba. Mun fi son tabbatar da gaskiya kafin mu kai rahoto.” Tabbas buɗaɗɗun kalaman Zak-Shadow ba ƙaramin tasiri sukai a zukatan su Brig. G. Ba, dan haka hall ɗin yay shiru na wani lokaci, kafin Col. Haydar ya nisa cikin jimami da nauyin furuci ya ce, “Lt. Col. Haysam ka fahimci cewa wannan kwamiti ba yana tuhumar ka da laifi bane bisa son kai ko wata manufa, amma muna bukatar gaskiya. Wannan al’amari ya wuce duk abinda muke tunani. Musamman daya kasance mun samu tabbacin Ojo na hannunka kai da Major Imran”. “Sir, na san aikin soja, kuma na san kima ta fi darajar rayuwata......” “Kana nufin an shirya maka ƙarya kenan Lt. Col?”. Lt Col. Peter Akon yay maganar cikin katse Zak-Shadow yana tsatstsare shi da ƙananun idanunsa. Shima cikin ido ɗin Zak-Shadow ke kallonsa dole sai Lt. Col. Akon ɗin ya fara janye nashi, dan wani abu mai zafi ya gani a cikin idanun Zak ɗin. Amma sai ya wayance da faɗin, “Muna saurarenka Lt. Col. Haysam.” Wani shegen murmushi Zak-Shadow ya ɗan saki kaɗan, tare da janye idanun nasa ya maida kan Brig. G. Maimakon wanda yay tambayar dan tsabar yarfi. “Sir idan hakan ba shiri bane, to miye ake son ni Haysam na kira shi? Mun san akwai leak tun lokacin da muka gano Ojo yana aiki da wasu a waje. Mun tabbatar yana aika bayanai ga wani bangare a ɓoye. Mun fara bincike a kansa tare da Major Imran a yanda ya dace, gashi kuma abin na neman canja salo mai ban mamaki. Ko akwai kuskure akan abinda muka yi?”. Bring. G. Ya nisa yana gyara zama, “Tabbas kuna kan dai-dai Lt Col. Haysam, sai dai miya sa baku kai rahoto kai tsaye ba? Sannan office ya kamata Ku ajiye shi ba wani waje ba.” “Sir hakan ta faru ne because muna so mu tabbatar da gaskiya kafin mu gurfanar da shi, muna son mu kama shi da hujja mai tabbatar da gaskiya, kuma laifina ne ni kaɗai babu Major Imran a ciki”. Shiru ne ya ratsa ɗakin. Sai Brigadier General ya ɗan jingina kai ya ce cikin sanyi, Lt. Colonel Haysam, gaskiyarka zata bayyana. Amma dole ka san wannan al’amari ya kai matakin da ya wuce mu. Za a tura tattaunawar mu kai tsaye ga Chief of Defence Staff da kuma Office of the Minister of Defence. Muna so ka tsaya kan gaskiyarka, but until further notice, you are under administrative watch”. Ya ɗan yi shiru, sannan cikin murya mai nauyi ya ƙara da cewa, “Har zuwa lokacin da za mu kammala bincike, an dakatar da kai daga duk wani aiki na soja. Za ka zauna nan Abuja, kuma ba za ka iya fita daga FCT ba tare da izini daga ofishin Defence ba.” Ko kaɗan babu wani alamar damuwa a fuskar Zak-Shadow ya miƙe, ya yi salute cike da girmamawa, tare da faɗin, Yes, sir. I have nothing to hide. Na amsa. Na sadaukar da raina ga wannan ƙasa, ba zan fara gujewa gaskiya yanzu ba saboda hana maƙiya nasara, zan basu ƙafa fiye da yanda suke tunanin samu, amma a sanar da su koda ace zan ɓuya, wata rana gaskiya zata dawo dani ko ta kawo wani wanda ya fini”. Daga haka ya juya abinsa ya fita. Yana fitowa idonsa ya sauka kan Major Imran dake tsaye jikin motarsa alamar shi yake jira. Idanu suka zubama juna na wasu sakanni, kafin Zak-Shadow ɗin ya cigaba da takowa a hankali har inda Imran yake. Murmushi Imran yayi shi kuma Zak-Shadow ɗin ya hararesa. Sake murmusawa yay, cike da rashin damuwa ya furta, “Gaskiya zata fito, amma sai lokaci ya kai da yarjewar UBANGIJI”..... ((★)) A ɓangaren su Brig. G. Ƙofar na gama rufewa bayan fitar Zak-Shadow ɗaya daga cikin mambobin kwamitin Col. Haydar ya juyo yana kallon Chairman ɗin Kwamiti Brig. G. “Sir, idan har ya kasance gaskiya ne wannan makirci ne to mun shiga cikin irin abin da ba a taɓa ganin irinsa ba. Kuma hakan na nuna akwai wani bigger hand a cikin wannan abun, kuma gaskiyarka ba Lt. Col. Haysam kawai aka hara ba gidan soja ne gaba ɗaya”. Kasa ma bama Col. Haydar amsa Brig G yayi, dan shi kansa ya ɗauki zafi musamman da kalaman Haysam na ƙarshe a yanzu. Miƙewa yay cikin bada umarni yace a ɗakko masa Ojo daga inda Major Imran yace sun ɓoyeshi, daga haka ya fice, dole kowama ya miƙe har jami'an gwamnatin dake tare da su.........✍🏼 _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 69_ __________________ https://chat.whatsapp.com/DMVSa4G3a9sDd8Jjgm0mzs?mode=ems_copy_t Kin Dade kina Neman group din dazaki tallata kayanki kyauta Baki samuba to ki hanzarta shiga free advert group na EASHAS BITES AND BEAUTY domin tallata Kayanki kuyi saving number dinta domin samun shiga group dinnan akwai members Sama da 500+ aciki💃💃💃💃👇👇👇👇 wa.me/ 2348064705686 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ ........Motar shiru Zak-Shadow na murza siyarin a hankali tamkar baya so, a gefensa Imran ne zaune cikin alamu na tunani mai zurfi. A gabansu motar sojoji ce haka ma bayansu. Sai dai sukai tafiyar fin mintuna goma tsakaninsu da inda suka baro a karo na farko Zak-Shadow yay magana idanunsa akan titi.       “Ina son su Ma'aruff su dawo kusa da Mammah”.      Kallonsa Imran yayi na sakanni, kafin cikin damuwa ya ce, “Saboda mi?”.          “Saboda bazai yiwu mu duka muyi nesa da ita ba.”      “Wace irin magana ce wannan? Kai ina zaka da har zakai mata nisa?”.    Murmushi mai yalwa Zak-Shadow yayi yana sake juya sitiyarin cike da ƙwarewa, sai kuma ya ɗan kalla Imran fisha ya maida idanunsa kan titin. Kamar bazai ce komai ba dan har Imran ya fidda rai da samun amsa, kafin ya ɗan furzar da iska. Cikin komawa serious ya ce, “Imran nasan ka san abinda nake hange, kuma bana jin akwai abinda zai hanashi faruwa sai wani ikon ALLAH. Mutanen nan sun gama shirya komai kafin su tunkaremu, kuma zaka tabbatar da hakan yanzu babu jimawa. Dan haka ina son a tsaida aikin gidansu ai musu gini anan cikin gidan tunda akwai fili ta baya. Idan zai yiwu kuma a canja tsarin gidan gaba ɗaya ma har Bilal da Ammar su samu nasu kowa ya zauna a ciki. Ka fara zama da su Ja'afar ɗin kasan abinda muke da shi a ƙasa, dan naso yin hakan dama sai dai nasan lokaci ya ƙure......”      Cikin ɓacin rai Imran ya katseshi da faɗin, “Wai miye kake faɗa haka. Na gaya maka ka daina min irin wannan wasan.”        “Humm! Imran ba wasa nake ba”.    “To ka sani kuwa duk inda kake muna tare”. “Bazai yiwu ba. Dan ina son a lokaci dana ɓuya kai ka cigaba da aiki. Na ajiye maka saƙo a ɗaki na..”      Dai-dai nan suke isowa ƙofar gidan Imran inda aka ajiye Ojo. Tuni sojojin da suke tare duk sun dirga daga motocin da suke, dan haka Zak-Shadow bai kula kallon da Imran ke masa ba ya buɗe motar shima ya fita. Sai da ya ga Imran bashi da niyyar fitowa sannan ya leƙasa da faɗin, “Malam fito ka bada key mana”.      Shiru Imran ya kasa motsawa, dole Zak-Shadow ya zagaya ta inda yaken ya buɗe masa da kansa. Tamkar wanda juwa ke neman zubarwa haka Imran ya fito, yasan wanene Haysam, sani irin na ciki dabai ɗin nan. Tunda har ya ambata batun zai ɓuya akwai abinda ya gama shiryawa, wanda shi Imran yake gudu da son yaƙa. Ganin duk sojojin sunyi tsaye alamar shi suke jira da ƙyar ya iya ciro waya a aljihunsa ya shiga ƙoƙarin kiran mai kula da gidan, sai dai har kiran ya tsinke ba'a ɗaga ba. Ya sake na biyu ma haka, zai sake na uku Zak-Shadow yay ɗan murmurshi. Sai kawai ya dubi sojojin yace su ɓalle ƙofar.       Hakan kuwa akai, sun tafi da nufin ɓalle ƙofa suka sameta a buɗe. Tun a anan aka tsaya kallon kallo, sai dai basu ce komai ba suka tura gate ɗin suka shiga. A tsakar gida suka tadda mai kula da gidan a yashe, ga wayarsa da Imran ke faman kira a gefe. Tattaɓashi ɗaya daga cikin sojojin yayi, cikin sauri ya ɗago ya ce, “Baya numfashi”.          Cikin tashin hankali Imran ya iso wajen, shima ya tattaɓashi amma da gaske baya numfashi. Suna ɗagoshi sukaga alamar an dakeshi ne ta ƙeya da wani abun. A take shugaban tawagar ya basu umarnin shiga gidan, shiko Imran sai jijjiga yaron yake yana ambaton sunansa amma babu alamar rai tare da shi. Zak-Shadow na gefe tsaye kawai ya zubama Imran ido...      Cikin abinda bai fi mintuna goma ba su Zak-Shadow suka fahimci babu Ojo a gidan an fita da shi. Dan a cikin gidan a ɗakin da Imran ya tabbatar ya ajiye Ojo duk ya aɓaci da jini har ta kan stairscase da falon. Dama gidan babu komai a cikinsa. Amma duk da haka sai da sojoji suka bincike ko wane lungu da saƙo nashi. Iyakar tashin hankali Imran ya shiga, amma abin mamaki Zak-Shadow ya dake a zahiri, koda akwai wata damuwa a tare da shi ya barma ransa.      Tuni sojojin dake tare da su har sun isar da saƙo zuwa Headquarter. Ba'ai wani dogon lokaci ba aka zagaye anguwar da sojoji. Maƙwaftan dake jikin gidan duk an sakasu sun fito duk da ma sabuwar anguwa ce. Su akai taima tambayoyi suna bada amsar komai dalla-dalla. Sun tabbatar da wasu mutane ne suka zo gidan, hakan na nufin sune suka ɗauke Ojo kusan awani uku da suka shuɗe kenan, dan wasu sunga motar data shigo anguwar har cikin gidan, sannan duk sunji sanda mai kula da gidan keta ihun neman ɗauki amma tsoro ya hana su fita kasancewar su mata, ga shi kuma sunyi harbin bindiga har sau biyu.        Cikin sa'a wani saurayin yaro ya bada siffar motar kaf da lambar jikinta, daga haka suka baro gidan shi kuma yaron Zak-Shadow da Imran ɗin suka wuce da shi asibiti. Sai dai me, suna isa asibitin sai ga sojoji an saka sun biyo bayansu wai kulawar yaron zata koma ƙarƙashin ikonsu. Tun daga nan Zak-Shadow ya fahimci anzo dai-dai wajen..... <<%>><<%>><<%>>           Ɓatan Ojo ya sake hargitsa komai ta kowane ɓangare, dan hatta a cikin su jami'an sojin dake jin Zak-Shadow bazai iya aikata abinda ake zarginsa a kai ba zukatansu sun fara rawa da wasi-wasi. Sai dai a gefen zukatan nasu basa fata hakan ta kasance.        Sai dai mizai faru kuma, ana kukan targaɗe kan batun Ojo sai kuma ga na karaya ya faru, dan kuwa misalin ƙarfe biyar na yammar wani mummunan labarin ya sake isowa hukumar sojoji. Wai an harbi jirgi mai saukar angulu na sojoji dake ɗauke da su Dagger a hanyar kawosu nan Abuja. Sabon zance kenan. Cikin gaggawa aka aika jami'ai inda abin ya faru. Kuma a cikin wani ƙauye abin ya faru, har an samu mutuwar fararen hula shida wasu sun jikata. Hakama sojojin dake tare da jirgin mutum biyu a cikinsu sun rasu, sauran sun raunana. Su Dagger su goma sha uku ne, an samu gawar biyar a cikinsu, sauran takwas ba'aga ko mutum ɗaya ba, hakan na nufin an ɗaukesu kenan.      Duk da zancen bai gama bayyana ko a Headquarter ɗin ba, a yanayin nan duk wani masoyin Zak-Shadow dole ya kasance cikin jimami da fargabar abinda zai iya biyo baya, domin kuwa case ɗin su Dagger shine tushen case ɗin Ojo da ayanzu kai tsaye ake tuhumar Zak-Shadow akai.     _____________★         A Defence Headquarters kuwa, batun ɓacewar Ojo da batun su Dagger ya kai ga har gidan gwamnati. Abin mamaki, cikin ƙanƙanin lokaci aka kira taron gaggawa. (Emergency Security Council Meeting). Ba a ɓata lokaci ba, tuni manyan jami’an tsaro suka hallara cikin ɗakin taron, kowanne da fuska mai ɗauke da damuwa da jimamami, dan rashin su Dagger da Ojo kai tsaye na nuna tabbacin zargin da akema Zak-Shadow ne, duk masu bashi kariya basu da wani sauran abin faɗa. Bayan ƴan mintuna kaɗan da tattaunawa, an fito da hukunci mai nauyi. COAS ya samu umarni daga sama kai tsaye na kama Zak-Shadow. An kuma tabbatar masa a daren yau dan ba'a buƙatar wata hayaniya.     Wannan shine saƙon umarni da COAS ya samu a dai-dai wannan lokaci da agogo ke neman buga ƙarfe shida na yammaci a ofishin ministan tsaro bayan fitowarsu daga meeting room.      Shiru General Yusuf yana kallon ministan tsaro dake bada umarnin bai iya cewa komai ba na ƴan dakiku. Ya kasa ma kallon sauran takardar da ke gabansa. Sai da Ministan ya sake maimaita umarnin da baki cikin ɓacin rai, yana jaddada cewa umarnin daga shugaban ƙasa ne, sannan Janar ya furta,     “Yes, sir”.    Ya faɗa yana sauke numfashi mai nauyi tare da miƙewa ya fito. Da sauri aka buɗe masa mota ya shiga, tunda suka baro ofishin minista ya faɗa duniyar tunani. A zuciyarsa kalmomin Minista ne kawai ke maimaituwa a kwalwarsa kamar amsawa kuwwa ne a cikin kunensa. Haysam Abdul-rasheed... to be apprehended. Hankalinsa a tashe yake matuƙa, zuciyarsa na masa zafi. Duk da cewa aikin soja ya koya masa ya bi umarni ba tare da tambaya ba, wannan karon zuciyarsa ta ƙi yarda. Amma ba shi da zaɓi.       Suna isowa office shima yay kiran Director of Military Intelligence dake ƙoƙarin barin office. Amma dole shima ya yanke nasa hanzarin ya amsa kira. Tunda ya shigo office ɗin ya fahimci akwai matsala sosai, dan fuskar COAS ta nuna kai tsaye. Yayi gaisuwa cikin girmamawa. Amma COAS bai iya ya amsa da baki ba hannu kawai ya ɗaga masa. Kafin bayan sakanni biyu ya fara magana muryarsa cike da raɗaɗi, “Issue the arrest directive Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu quietly. No noise.”         Shima ba ƙaramin faɗuwa gabanshi yayi ba, ya ɗan zaro idanu waje zuciyarsa na girgiza. Sai dai kafin ma yace komai COAS ya miƙe abinsa alamar baya buƙatar wani zance. Rai a dagule ya fice daga ofis ɗin ba tare da ya tsaya da kowa ba ya bar Headquarters ɗin gaba ɗaya zuwa gidansa, kamar wanda yake guje wa wani abu da zuciyarsa ta kasa jurewa.        Bayan mintuna talatin, takardar Arrest Directive ta fita da cikakken sa hannun doka. An tura ƙungiyar jami’ai shida daga Military police da zasu kama Zak-Shadow bisa umarni, tare da amsar dukan abinda ya shafi matsayinsa.         (((*)))(((*)))      A ɓangaren Zak-Shadow da Imran sam basu sam mike faruwa ba, dan yanzu ma suke isowa gida daga asibiti bayan jam'an sojan nan sun tabbatar musu da komawar kulawar yaron a ƙarƙashinsu bisa umarni daga Headquarter kai tsaye gida suka nufa.. Sun yi ƙoƙarin kauda hankalinsu daga tashin hankali, kowa da tunanin da yake ƙoƙarin ɓoyewa, duk da shi Imran yaso su cigaba da tattauna maganar da suka fara ɗazun da Zak-Shadow ɗin, amma shi kuma yanata kaucewa sai kawai ya haƙura yay shiru shima har suka iso anguwarsu.         Zak-Shadow sai da ya kai Imran har gida sannan shima ya shiga. Bilal ne ya buɗe masa gate, dan ya fito zai je massalaci sallar Magriba da aketa kira. Shima sai yana ajiye motar bai shiga ba ya fito domin gabatar da sallar kamar yadda ya saba. Bayan idar da sallar magriba ya fito Bilal tare da shi. Labarin rigimar Nimrah Bilal ke bashi har suka iso ƙofar gate ɗinsu, hakan kuma yay dai-dai da isowar motar data saka Zak-Shadow tsayawa. Shima sai Bilal ya tsaya yana kallon motar kawai........✍️ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_🫧KIƊA A RUWA.....!!🫧_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ _Chapter 70_ __________________ https://chat.whatsapp.com/J92XqvWDRch1EJPdGDBa41?mode=wwt https://vm.tiktok.com/ZSHWHk4ULWbMN-geqJz/ This post is shared via TikTok Lite. Download TikTok Lite to enjoy more posts: https://www.tiktok.com/tiktoklite https://chat.whatsapp.com/KfkKd9vD8MrAst8i8CQDsj?mode=wwt Assalamu alaikum, Mutanen arziki Ina musu capacity😍🥰 kuna Neman Inda zaku Samu ingantattun Kaya masu kyau da quality sosai 💝 Kamar Kayan Yara Zannuwan Gado Kayan kitchen Shoes and bags Jewellery Laces, atamfa,shadda Dadai sauransu. To nesa tazo kusa, Maza Danna wannan link din domin Samun Kaya masu inganci da ƙayatarwa da idan kika saka ko ina kika shiga sai an kalleki an ƙara kallo. Ko ku nememu ta wannan number 08165751018 ❤️❤️❤️😘 __________________ *_TELEGRAM GROUP_* https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk *_WHATSAPP CHANNEL_* https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F *_TIKTOK_* https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/ *_INSTAGRAM_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv ______________________ .........Cikin nutsuwa jami'an Military Police suka fito a tsare. Babban cikinsu ya matsa kusa da Zak-Shadow cikin girmamawa da risinar da kai yayi gaisuwa.      Amsa masa Zak-Shadow yayi cikin jinjina kai batare da yace komai ba. Sai kuma ya juya yana kallon Bilal yay masa alamar ya shiga gida. Bilal da bai fahimci komai ba face abokan aikin Dadan ne sukazo maybe zasuyi magana ne akan aiki sai ya shige gida abinsa kawai.        Sai a lokacin Zak-Shadow daya sake binsu da kallo a taƙaice ya furta, “Akwai matsala ne?”.       Cikin sake risinar da kai ogan nasu ya ce, “I'm sorry Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed... by the order of the Defence Headquarters, you are under arrest. You’re to come with us quietly.”        Zak-Shadow yay shiru kawai yana kallonsa na tsawon daƙiƙu, amma bai ce komai ba. Sai kuma a nutse ya koma kallon fuskokin sauran suma da duk suka risinar da kai alamar suna matuƙar jin nauyin kallonsa ma. Sai kawai yay wani ɗan murmushi yana sauke ajiyar zuciya.       “Understood” ya furta cikin dakakkiyar murya, tare da miƙa musu hannunsa, alamar basu damar yi masa abin da suka zo yi. Wani daga cikin jami’an ya matso domin ɗora masa restraint band amma sai ya kasa. Sai ma cikin rawar murya ya ce, “I'm sorry Sir! wlhy bazan iya ba”.         Murmurshi Zak-Shadow yayi anan ma, batare da yace komai ba ya amsa da kansa ya saka....        ★★★★ Motar su Ja'afar ta iso dai-dai Jami'an MP na barin ƙofar gidan. Sukabi motocin biyu da kallo, batare da sun kawo komai a ransu ba su ma Ma'aruff ya fita ya buɗe musu gate suka shiga ciki. Idan har suka shigo gida sukan fara zuwa su gaida Mammah ne kafin su wuce nasu ɗakunan yin wanka. Yau ma kamar kullum can ɗin suka nufa. Tun a farkon shigowa suke jin surutun Nimrah da Mu'azz da Ruƙayya da bata koma gida ba. Sunayin sallama Mu'azz da Ruky sukayo kansu suna musu oyoyo. Nimrah dai babu damar tashi saboda ƙafa.       Gaishe su Bilal yayi, su ka amsa da kulawa suna tambayarsa ya aiki dan shi kam ma'aikaci ne. Fitowa Biebah dake kitchen itama tayi ta gaishesu, daga haka suka nufi ɗakin Mammah, dan in ta shiga sallar magriba bata sake fitowa sai tayi har isha'i. Har sun je ƙofa Ma'aruff ya juyo yana tambayar, “Dada fa? Ko yana sashensa?”.          Biebah ta ce, “Yaya tun ɗazun ya fita har yanzu bai dawo ba”.      Bilal ya ce, “A'a ya dawo Auta, tare ma mukayi sallar magriba. Zamu shigo gida yayi baƙi baku gansu a ƙofar gida ba?”.         Yanzu kam Ja'afar ne ya ce, “Eh muna isowa wata motar sojoji na barin ƙofar gidan, amma mu bamu ga Dada ba”.      “Maybe ya riga ya shigo ne”.   Duk sun gamsu da abinda Bilal ɗin ya faɗa, dan haka suka ƙarasa shiga wajen Mammah....        ★Bayan idar da sallar isha'i su Ja'afar sun ta baza idon san ganin Dada ya fito a masallaci shima amma shiru. Kuma sun tabbatar idan yana gida jam'i baya wucesa. Sai da kowa ya shashshare suka tabbatar dai babu shi sannan suka koma gida. Kai tsaye sashensa suka nufa, tunda sun san shi kaɗai ne yanzu Nabeeha anyi yaji.       Da knocking suka fara kafin su shiga. Sai dai ko ina shiru fitilu ma duk a rufe. Ma'aruff ya kunna fitilar falon haske ya gauraye ko ina. Sallama suka ƙara yi amma shiru babu alamar mutum. Sai kawai suka zauna a falon. Abin kamar wasa fin mintuna talatin babu motsin Dada, Bilal yaje yay masa knocking ƙofa amma shiru, dai-dai nan kiran Biebah ke shigowa wayar Bilal ɗin. Ma'aruff ya ɗaga.             “Yaya Bilal Mammah tace wai ina kuka tsaya?”.       Miƙewa Ma'aruff yayi da wayar a kunne yana amsa mata da, “Gamu nan zuwa, muna sashen Dada ne kuma da alama baya gidan”. Bai jira amsarta ba ya yanke kiran suka fito suka koma sashen Mammah. Duk sun sakankance Dada yaje wani waje ne har sunyi dinner sun dawo falo suna hira. Sai dai ganin Mammah tayi sukuku da yawa suka zagayeta da tambaya.      Ajiyar zuciya ta ɗan sauke, batare data amsa musu ba tace, “Biebah kwashe yaran nan su koma ɗaki kinga sun fara barci anan”.       Biebah ta ce, “To Mammah” tana miƙewa. Sai da ta tada Mu'azz ya wuce ɗakinsa sannan tazo ta ɗauki Nimrah takai ɗakin Mammahn ta ɗauki Ruky ma. Sai a lokacin Mammah ke amsa su Ja'afar.         “Tun ɗazun nake jin zuciyata na rawa, sannan ina jina tamkar cikin tsoro-tsoro”.      Duk kallonta suke cikin tashin hankali suma a karo na farko. Jikin Bilal a sanyaye ya ce, “Mammah wani abu ya faru ne kuma?”.       “Babu abinda ya faru Bilal, kawai dai na fahimci bayan abinda ke faruwa a gidan nan na shirmen Nabeeha kamar Muhammad nada damuwa, sai dai yana ɓoyewa. Yau kuma gashi tunda ya fita har yanzu bai dawo gida ba, bai kira kowa a waya ba, kalla agogo ƙarfe goma saura. Sannan jiya na fahimci kamar Imran bai kwana a gidansa ba shima”.           “Tabbas Mammah maganarki na kan hanya, dan kinga ɗazun da safe wasu jami'an soja sun kawo ma Dada takarda, amma sai yaƙi ya buɗe a gabanmu yace muzo muyi shirin tafiya kasuwa”.       “Nima kuma yanzu kaga da yay baƙin nan Yaya Ma'aruff cayay fa na shigo gida, bai bari sunce komai a gabana ba.”          Shiru falon yay tunanin kowa ya fara dawowa jikinsa. Kamar an saita sai ga kiran Imran na shigowa a wayar Ja'afar. Ɗagawa yay cike da zumuɗi yana gaisheshi, Imran ya amsa da kulawa yana tambayarsa lafiyar kowa, sannan ya ɗora da tambayar Zak-Shadow. Ɗan jimm Ja'afar yayi, sai kuma cikin damuwa ya ce, “Dada baya gida, muma bamu sameshi ba.”       Da mamaki Imran yace, “Baya gida kuma?”.       “Eh wlhy Yaya. Mun zata ma kuna tare ai a wajen aiki. Dan Bilal yace bayan fitowarsu a massalaci sallar magriba yayi baƙi kuma kamar jami'anku ne”.       Imran ya ɗauki sakan biyu shiru kafin yace, “Ina Bilal ɗin?”.     Wayar Ja'afar ya miƙama Bilal. Koda ya amsa sai da ya fara gaisheshi, Imran ya amsa a taƙaice ya cigaba da jeho masa tambayoyi. Ba ƙaramin rikita Imran amsar Bilal tayi ba, dan yana faɗar motar da suka zo da ita ya gane jami'an MP ne. A dai-dai kuma lokacin yake canja channel daga tv da nufin kallon labarai aka nuna jirgin sojoji ya samu haɗari da yamma a wani ƙauye, kuma jirgin na ɗauke da wasu masu laifi ne da aka kama kwanan nan a rikicin daya auku na yammacin ƙasar. Ai cikin tashin hankali Imran ya yanke kiran batare da cigaba da tambayar Bilal ba, dan kai tsaye ya samu amsar tambayarsa ne..... <<•>><<•>><<•>>            Duk da rufa-rufar da ake ta kama Zak-Shadow zuwa safiya dai zance ya gama fita cewar an kama shi ɗin. Abin mamaki kuma wata ɓoyayyar gidan jarida ta fara fidda bayanan kamashi a shafinta na X, tare da hoton lokacin da jami'an MP ke tare da shi, harda hoton dake da handcuffs a hannunsa. Kafin awa guda mutane miliyoyi sun zuba sharhi akan batun, manyan kafafen yaɗa labarai sun bazama binciken gaskiya.        A gidan soji kuwa wasu hankalinsu a tashe matuƙa. Wasu ko na dariyar ALLAH ya ƙara da farin ciki mara misali. Nan fa wasu sabbin zantuka ma suka fara fita iri-iri masu ban mamaki. Kafin ƙarfe biyun rana ƙasa gaba ɗaya ta gama ɗauka. Babu wani labari dake trending sai batun kama Lieutenant Colonel Haysam Abdul-rasheed Shehu. A ɓangaren al'ummar ƙasa da yawa basu yarda zarge-zargen da akema Zak-Shadow ɗin ba, sun fi gaskata al'amarin da batun siyasa ce kawai ko wani abu daban. Su ko maƙiya na hura hanci da hanƙoron bada tabbacin zai iya fiye da haka....       ★Ga su Mammah kuwa fassara halin da suke ciki ita da iyalanta ma ɓata lokaci ne. Dan tuni sun taru ƙwansu da kwarkwata a gidan sunata kuka. Sai dai Mammah baiwar ALLAH tana cikin nutsuwarta a zahiri, babu abinda take sai ambaton ALLAH.       Imran, mahaifinsa, Uncle Nasiru, Ja'afar, Ma'aruff tunda safe da zancen ya fito suka bazama inda akace an ajiye Zak-Shadow, amma anƙi basu damar ganinsa. Dan wani mugun tsaro aka bama wajen ma da duk mai hankali ya gani yasan lallai akwai magana, sannan al'amarin bamai sauƙi bane ba.       ALLAH sarki COAS da kansa ya gana da su yana mai kwantar musu da hankali akan suyi addu'a in sha ALLAHU babu abinda zai faru, gaskiya zata fito dan yanzu haka shima ya baza jami'ai ana kan binciken number motar da akace wanda sukaje ɗaukar Ojo sun tafi da ita. Sannan a yanzu haka ana kan bincike a ƙauyen da aka samu haɗarin wancan jirgin dan kai tsaye an samu tabbacin an harbo jirgin ne gangan ba haɗarin kai da kai ya samu ba.....             <<•>>      A can kuwa ƙungiyar duhu na cikin matsanancin farin ciki ne su da duk wasu munafukai dake ƙin Zak-Shadow. Dan kuwa babu wani kace nace aikinsu ya faɗa fiye da yanda suke so da fata batare da sun sami kowace irin tangarɗa ba. Sun sha bikin cin nasara a daren jiya, sun kumayi rabon dukiya ga duk wanda ya taimaka musu aikin ya tafi dai-dai. Ƙungiya kuma ta ɗauki sabbin members da za'a tada sabon jadawalin aiki da yafi na baya muni da zubar da jini. Dan sunyi alwashin duk wanda yace zai tare musu gaba kamar Zak-Shadow sai sun masa kisa irin na wulaƙanci. Shi kansa Zak-Shadow ɗin sunfi buƙatarsa a raye ne dan ya dinga kallon nasarrasu a gaɓar da bazai iya komai ba. Tunda yace shi mai kishin ƙasa ne da baƙin ciki zasu kashe shi. Dan sunyi alƙawarin dasa masa ciwon zuciya.      A yanzu haka Ojo na hannunsu, dan sune suka saka aka ɗakko musu shi. Haka ma su Dagger na hannunsu, sune suka saka aka harbo jirgin nan, saboda suna buƙatar su Dagger a tafiyarsu, babu wanda zai musu kamar yanda Dagger ke musu su sami natsuwa, dan sun gwada yaransa amma basu sami biyan buƙata ba. Shiyyasa suka sake sabon shirin dawo da shi ta hanyar jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya, kuma sun sami nasara, dan haka yanzu lokaci ne na sake SABON WASA........✍️      Alhamdullahi 🙏.   Tabbas yanzu shine lokacin sake SABON WASA kam masu karatu. Dan anan book 1 ɗinmu zai ƙare. Ku muje zuwa book 2 inda ainahin baje kolin cakwakiyar take. Idan nace daku cakwakiya kawai kaɗan ma kenan, dan book 2 ɗin nan ba'a magana. In sha ALLAHU zai zo muku da fiye da abinda kuke tunanin gani. Dan book 1 tamkar shinfiɗa muka baza, yanzu zamu tsunduma ainahin labarin KIƊA A RUWA MAI TADA HANKALIN DODO... ★Ya zata kasance da Zak-Shadow?. ★Abin zai tsaya kansa ko zai haɗa da Imran?. ★Zasu sake shi da wuri ko kuwa zasu turashi kurkuku?. ★Ina batun Nabeeha da ƴan uwansa da uwarta?. ★Mi uwarta ke shiryawa? ★Nimrah ƴar Amana, yaya girman wannan tsuntsuwa zai kasance a gidan su Zak-Shadow? Ina batun aurenta da Zakinmu? Wane wasa za'a buga ita da Nabeeha ne?. ★Ina mahaifin Nimrah ne? Ya rasu a cikin wanda suka rasu ko kuwa an ɗaukesu tare da su Dagger?. ★Ƴan uwanta da gaske duk sun rasu babu ko ɗaya daga dangin uwa dana uba?. Kai jama'a kada na cika ku da zance, Amma fa KIƊA A RUWAN kiɗa a ruwan ne fa, dan za'a buga wasa iya wasa, soyayya iya soyayya, cakwakiya iya cakwakiya. Rikita rikita iya rikita-rikita, gumurzu iya gumurzu. Dan ni kaina Bilynku na saka sulken yaƙi😎🏃🏼‍♀️.      Ku muje zuwa book 2 kawai mutanensa❤️❤️❤️💃🏼. Bilyn Abdull ce. ((C--2025)) _________________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JuUwr2QU7XMEYXZ7L7 Mmn surayya me kayan kamshi Ina amaran da uwayan gidan tou kumatso kusa Mmn surayya ta gwangwaje ku da kayan kamshi munada Turaran wuta na danal banat Kajiji Turaran kaya watau abbasiyya Kabbasa spray Humra Kwallacca Uwa uba Ina kuyarda yadda xaki hadasu Zaku iya samuna ta wannan number wayar kamar haka👇 08103143517 Ina katsina Ina aika kaya ko ina __________________ _Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._ *_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_* *_+227 98 94 12 81_* *_My NITA_* *_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_* _Shaidar biya👇_ *_Whatsapp number_* *_+227 98 94 12 81_* *_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_* *9032345899* *_Moniepoint MFB_* *_BILKISU MUSA IBRAHIM_* *_KATI MTN (1k)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya: 👇_* *_Telegram Number 09032345899_* *_AREWABOOKS (Vvip)_* *_Chapters & Audio_* @BilynAbdull *_WHATSAPP (500)_* *1487616276* *_Access Bank_* *_Bilkisa Ibrahim Musa_* *_Kati MTN:- (500)_* *_09032345899_* *_Shaidar biya:-_* *_Whatsapp Number +234 805 568 7449_* *_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_* *_WhatsApp Number 👇_* *+234 805 568 7449* *_Telegram Number👇_* *+234 903 234 5899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels